Chapter 22 Reading Jidda Sirri da zai iya rushe komai by Maman Maama READ HAUSA Novels

Jidda Sirri da zai iya rushe komai by Maman Maama

Author :  MAMAN MAAMA Category :  African Stories & Novels

Chapter   22 / 106

63K to 66K   out of 316K words

din 08067081020

Please banda kira, WhatsApp only

*Episode Sixteen : Ummi*

Kafin in bashi amsa ya bude kofa ya fita, na jima a zaune, na kasa ma yin addu'a dan lugude kawai kirjina yake yi, anya kuwa sauran amare haka suke jin tsoro irin wannan? Anya kuwa ni nawa tsoron bai yi yawa ba?

Amma kuma shima kansa Umar din is not helping matters at all, shine ma yake kara tsorata ni wallahi. Misali yanzu, menene na wani cewa in tashi mu tafi yanzu, making me think of what will happen in munje gidan.

Na tashi na nade sallayar sannan na fara kokarin gyara fuska ta. Aunty ta shigo "ashe tafiya zakuyi Jidda? Yanzu naji Umar ya aiko wai ki fito in kin kammala"

Na dauke kaina gefe na juya idona, wato yasan in ya aiko zasu matsamin in fita tunda yana jira na,amma in ba haka ba ai ya gaya min already kuma zai iya kirana a wata ya sake tuna min.

Na juyo ina kirkirar murmushi, "eh Aunty, tafiya zamu yi" sai ta jani muka zauna a bakin gadon ta sannan ta jawo drawer ta dauko wata leda ta miko min "kinga wannan sister ta ce ta kawo min, sai naga da amare yafi dacewa shine nace bara in baki" na karba jikina yana bani ko menene a ciki, nayi mata godiya.

Sai kuma ta sake karba ta bude tana yi min bayanin yadda ake using. "Kinga wannan ma ance kamar yanzu za'a sha, bara in hada miki ki shanye kafin ku tafi dan in nace in kunje ki sha ba lallai ne ki sha ba" ta fita sannan sai gata ta dawo da cup a hannun ta ta bani ta ce in shanye, ina cikin sha ya shigo dakin yana duba agogon hannun sa, Aunty tace "gata nan zuwa sarkin gaggawa, wannan kai da maye ne in ka kama mutum sai ka kai shi lahira zaka rabu dashi" sai yayi murmushi kawai bai ce komai ba ya fita.

Muka fito palo nayi wa Mama sallama, sai ta bani wata leda ita ma ta gaya min spices ne a ciki na girki, "in akwai wani abun da kuke bukata a gidan ki kira auntyn ku ki gaya mata, kar ki kira gida, shi kuma in kin gaya masa ba lallai ya san inda zai samo muku wani abun ba, a hankali kema zaki san inda zaki samu komai. Na bayar ma za'a yi muku garin kunu tunda yana so, za'a aiko muku da shi" na durkusa nayi mata godiya na kuma yi mata fatan Allah ya kiyaye hanya.

Afnan tazo ta zauna a kusa dani tana yi min rada "Aunty zan biki kinji?" Na shafa kanta nace "maza dauko kayanki mu tafi" sai ta mike da sauri tana murna "mommy ki hada min kayana aunty Jidda ta yarda zan bita" Affan ya mike "wallahi nima sai naje mommy" Aunty ta girgiza kai "kuna da school gobe, ku bari sai da weekend sai kuje kuyi musu two days" Mama tace "da weekend din ma suna da islamiyya, sai dai in anyi hutu" suka fara rikici, sai na rarrashe su da cewa ai an yi hutun sai suje suyi min two weeks.

Sai dana fadi haka sannan suka fara murna, a lokacin ne kuma naji ana maganar Ummi ita ma bata nan akayi bikin sai anyi hutu zamu hadu, ban gane wacce Ummi suke nufi ba kuma ban tambaya ba.

Umar ya sake lekowa. Ya tsaya kawai a bakin kofa ya saka hannu a aljihu yana kallon mu. Hajiya ta taba ni "tashi maza ku tafi yana jiran ki, kinsan unguwar ku da nisa" ina mikewa ta kwalla wa Mufida kira tace tazo ta karbi kayan hannuna sannan ta dauko mana abinci a kitchen mu tafi dashi tunda bamu yi dinner ba. Mufida ta fara buga kafa tana shagwaba, "Mama ita ta dauko mana da kanta" Aunty tayi dariya "yayarki ce dai yanzu ko kin ki ko kinso" ta juyo tana harara ta ni kuma na yi mata gwalo sannan na sake yiwa su Mama sallama na fita.

Yana cikin mota a zaune, sai na tsaya a jikin motar ban shiga ba, na sauke glass yana kallona amma bai yi magana ba, nace "Mufida nake jira, zata kawo min kaya inji Mama" sai ya dage glass din. Sai naji ni bana son wannan shirun nasa, fushi yake yi dani na sani. Na hadiye yawun tsoro.

Mufida ta fito tare da Muhsina, suka saka mana kayan a mota sannan mukayi sallama na bude gaba na shiga na rufe.

Bai ce min komai ba ya tayar da motar muka fita muka hau titi, na juya ina kallon sa ta hasken street light ina jujjuya hannuna nace "kayi hakuri" ya juyo yana kallo na "hakurin me fa?" Na mayar da kaina kasa, "naga kamar kayi fushi ne" yace "fushin me zanyi?" Nace "akan abinda nayi" yace "me kika yi" na ji kamar zanyi kuka "dana boye maka gaskiya" yace "gaskiyar me fa?" Na fara yarfa hannu na "aika san maganar da nake yi wallahi kawai so kake ka nuna baka sani ba"

Yace "so nake inji kin fadi laifin ki da bakin ki. Kin kuma amsa cewa kin yi laifi kin yarda kuma cewa baki kyauta min ba" nace "to ai na yarda ban kyauta din ba shi yasa na baka hakuri ai, kuma ina sake baka hakuri. Allah ya baka hakuri" yayi shiru yana kallon gabansa.

Na fara share hawaye na "sau nawa zan baka hakuri ne to wai ba zaka hakura ba?" Ya juyo yana kallona yana jin sautin kuka a muryata. Sai ya danyi murmushi yace "cry cry Baby. Zan hakura mana, amma ba yanzu ba. Ask me again tomorrow morning zaki ji nace miki na hakura"

Na gane abinda yake fada, sai kuma naji damuwar rashin yin hakurin sa ya tafi tsoro kuma ya dawo min. Na jawo kafafuwa na kan kujera na nannade su a cikin skirt dina na kwanta a jikin kofar mota na rufe ido na.

Ina jin motar ta tsaya, na bude ido na na gan mu a kofar wani guri da ban gane ba, sai kuma na lura kamar gurin sayar da gasassun kaji ne, ya bude ya fita bayan mintuna kadan ya dawo da leda ya saka a seat din baya. Kamshi ya cika motar gabakidaya amma ni sai naji kamar hawa min kai kamshin yake, sam banji ina son cin kazar ba, dan gabakidaya bani da appetite.

Ya tayar da motar muka dauki hanyar gida, yayi horn mai gadi ya bude muka shiga yayi packing ya kashe motar. Na dago kai ina kallon sa, ina jin alamar kamar zazzaɓi yana neman rufe ni nace "in na roke ka nace ka hakura da wannan abin zaka hakura?" Sai naga yayi dariya har yana dafe kansa, na bata rai ina jin haushin dariyar sa yace "my dear sweet Jidda. No. Ko kin bani hakuri ba zan hakura ba saboda babu laifin da kika yi min. Ni wannan abin da kike yi ma in baki sani ba shi yake kara min son abin"

Na harare shi ina magana kasa kasa "kayi dariyar ka ka gama, tunda bai kashe kowa ba nima ba zai kashe ni ba" ya juyo sosai sannan ya kama hannayena biyu ya damke a cikin nasa yace

"look at me Jidda. Trust me, ina neman alfarmar kamar yadda kika danka min zuciyarta ki daure ki danka min kijinki shima and I will not hurt either of them. I will not hurt you Jidda. I promise I will never hurt you"

Na lumshe idona na bude. Ya dawo da hannayenmu a tare zuwa fuskata yana goge dan guntun hawaye daya fito a kasan idona.

Ya na kallona cikin ido yace "I can't do it in ranki baya so, in hawaye yana fita daga idonki. Duk matsuwar da nayi da ke Jidda in baki ce kin amince ba ba zan miki komai ba. Zan cigaba da kallon ki ina lallabaki har sai kin ce min kin amince. That's how much I love you"

Na cire idona daga nasa na sauke su kasa, sannan a hankali naji tsoron dake raina ya ragu, gyada kai na "na amince"

Yayi alƙawarin cewa he will not hurt me, but he did, it hurts alot at first har sai da nayi tunanin ajali na ne yazo and then he took away the pain with the pleasures ta yadda har sai da nayi tunanin babu wani sauran pain a duniya. Nayi tunanin babu sauran komai a duniya sai abinda muke yi, na kuma yi tunanin babu sauran kowa a duniya sai shi.

A ranar ya mallaki jikina ya mayar da shi nasa, kamar yadda ya mallaki zuciyata ya mayar da ita tasa.

Wannan dare ne da bazan taba mantawa dashi ba a tsahon rayuwata.....

Ban san sanda muka yi bacci ba, amma nasan nayi dogon bacci dan ban farka ba sai da rana ta fito sosai. Shima kuma feeling din cewa rana ta fito ne da kuma feeling din ana kallona ne ya tashe ni.

Na bude idona a hankali, sannan na sauke su a cikin nasa. Yana kwance a kusa dani, kansa a kan pillow na, fuskarsa kusa da tawa, sannan idonsa akai na. Ina bude ido na yayi min murmushi. Zan iya rantsewa ban taba ganin murmushi akan fuskar sa mai kyawun da yakai na ranar ba.

Na jawo hannayena da sauri na rufe fuskata nima ina murmushi, sai ya rankafo yayi kissing goshina sannan ya saka hannu yana gyara min gashina daya baje akan pillow yace "tun dazu nake ta so in gyara gashin nan, hannuna har kaikayi yake yi amma bana son in tashe ki because you looked so beautiful when sleeping and I love you so much. Maybe a little bit too much. Ina so ki sani cewa daren jiya is the best night of my life so far, ban sani ba ko akwai wani daren da zanfi so fiye dashi nan gaba, in ma akwai inajin daren da zaki haifa min kyakykyawar baby irin ki ne" ya fada yana shafa karan hanci na sannan ya goga nasa akan nawa.

"Na gode Jidda. You gave my everything that I have ever dreamt of. Duk abinda nake so kuma nake da burin samu na samu anan wajen. Ina fatan Allah ya biya ki da aljanna ni kuma ya bani ikon faranta miki kamar yadda kika faranta min. Nagode"

Ya dauke hannayena dana rufe idona dasu sannan yayi kissing idanuwan da suke a rufe. Na bude su ina kallon sa, ina jin sonsa yana kokarin yiwa zuciyata yawa nace "godiyar me kake yi ne wai? Me na baka da zaka gode min? Dama ai naka ne. Abin ka ne da nake ajjiye maka kuma kazo ka karbi abinka. My heart and my body are yours, na Umar ne shi kadai"

Ya dora goshinsa akan nawa, hancinsa akan nawa ya rufe idonsa sannan a hankali shima yace "my heart and my body are yours. Na Jidda ne ita kadai"

And then he kissed me.

Hasken ranar daya matso kan fuskokin mu ne yasa na janye fuskata daga tasa tare da kare hasken da hannuna. "Rana ta fito ba muyi sallah ba" na fara kokarin mikewa sai dai wani suka da naji a kasana ce ta sakani komawa in kwanta tare da yin yar karamar kara. Sai yanzu na tuna da pain din da naji jiya, har yanzu yana nan sai ma tsami da gurin yayi yanzu. Ga karin cinyoyi na da suke ciwo kamar wadda nayi tsallen kwado, sannan ga cikina kamar anyi min yasa, bayan abinci ma kamar harda hanjina aka hada aka kwashe.

"Oops, sorry baby"

Sai kuma yayi dariya. Na juya na harare shi "dariya ma kake yi min ko?" Ya daina dariyar sannan yayi fuskar tausayi "sorry dear, ni ne ko? Ki bar ni da ni zan yi maganin ni. Bulala nawa kike so nayi wa ni?" Na fara matso hawaye duk da bana gaskiya bane ba. Ya mike "sorry sorry, don't start with the crying please. I am going to take care of you" ya sauka daga kan gadon, nayi sauri na rufe idona saboda lura da nayi ashe babu komai a jikinsa, amma na kasa cire image din daga raina.

Ya shiga toilet sai kuma ya fito "babu ruwan zafi a toilet din nan ashe. Bara in duba toilet dinki" na dan bude idona kadan sai kuma na sake mayarwa na rufe. "Please ka saka wani abun a jikin ka" ina jin shi yana dariya sannan ya fadi wani abu da banji sosai ba sannan naji ya bude kofa ya fita.

Na sauke ajjiyar zuciya na bude ido na ina kallon hotonsa da yake dakin, sanye da kayan su na doctors da stretescope a wuyan sa, fuskarsa dauke da murmushi. Nima nayi murmushin ina ji kamar babu wadda ta kaini dace da miji a duniya.

Ina jin motsin sa na mayar da idona na rufe, yace "can din ma babu, but na kunna yanzu. Bara in kunna anan ma. Let me get you something to eat kafin ruwan yayi" na dan bude ido naga ya saka jallabiya, sai ya kunna heater sannan ya sake fita. Few minutes ya dawo da tray a hannunsa ya ajiye sannan ya fara kokarin tashina zaune ni kuma nayi ta zuba masa shagwaba, sai da ya hada min pillows da kuma jikinsa na jingina sannan na tashi ya bani cup din tea daya hada min mai kauri na karba na shanye tas, ya daga hannu "to kin shanye tea din da me zaki ci bread din kuma?" Na langwabe "wani zaka hada min".

Ya dauki cup din "an gama ranki ya dade" sai ya koma ya hado wani ya dawo, sannan ya dauki bread ya shafa min butter na kuma cinye na sake shanye tea din. Ya dauke tray din ya fita dashi sai gashi da apple ya kawo min,shima nace ba zanci ba sai ya yayyanka min, ya koma ya dauko wuka da plate ya zauna yana yanka min ina ci har na cinye.

Sai da na gama sannan nace "banyi brush ba fa" yace "kar ki damu, nayi miki already"

Toilet ya koma ya hada min ruwa sannan ya dawo yana tattare hannun rigarsa da murmushi a fuskarsa. "Yauwa, lokacin yiwa baby wanka yayi" na bude ido "wa za'a yi wa wankan?" Ya kashe min ido, "wai da" kafin in sake magana ya yaye bargon, nayi kokarin tashi da sauri sai kuma nayi kara ina rike waist dina da naji shima ashe ciwon yake yi.

Dole na hakura ina ji ina gani ya dauke ni zuwa toilet, ya saka ni a cikin ruwan zafin da naji kamar ya zuba jajjagaggen attaruhu a ciki, na rike shi kam ina jin ruwan yana shiga kofar da da take a rufe sai jiya aka bude ta, jikina har karkarwa yake yi shi kuma yana ta jera min sannu, a hankali kuma sai na fara jin dadin ruwan sai na sake shi na koma na kwanta. Ina jinsa ya fita.

Ban jima sosai ba saboda sallah da nake ta tunanin banyi ba. Na tsarkake jiki na sannan nayi wanka na tsarki dana sabulu. Na dauko toothbrush dinsa, a raina ina tuna ranar da yace zamu yi sharing toothbrush da toilet, nayi murmushi sannan na saka paste nayi brush sannan na daura towel dinsa na dafa bango na fita.

Baya dakin amma naga alamar ya gyara bed din, duk da dai kana gani zaka fahimci cewa wanda yayi gyaran gadon bai iya ba, bani da kaya a dakinsa dan haka na tafi dakina na lallaba na saka riga da hijab nayi sallah ina jin guilty feeling a raina na rashin sallah da wuri.

Bayan na idar na tashi na shirya cikin riga da wando masu fadi wadanda basu takura jikina ba amma sunyi min kyau sosai kuma sun fitar da shape dina sosai. Na gyara gashina na daure shi a keyata sannan na gyara fuskata lighly. Na bude kofa na fita palo duk da cewa da kyar nake daga kafata amma tunani na Umar, ko ya ci abinci?

Ina shiga palon yana shigowa shima daga waje, da leda a hannunsa, yazo ya kamani "wa yace ki tashi ne wai. Ke fa patient dina ce yanzu" ya zaunar dani akan kujera sannan ya dauko robar ruwa ya bude min ya kuma dauko ledar daya shigo da ita ya ballo min magungunan da suke ciki. Ina gama sha ya kwantar dani akan kujera tare da saka min pillow, shi kuma ya zauna a gabana yana shafa fuskata.

"Don't worry, zaki yi bacci idan kika farka kuma zaki ji ciwon duk ya tafi. Kar ki manta, you have a doctor waiting on you dan haka baki da wani problem"

Na lumshe idona ina masa murmushi, realising cewa harda maganin bacci ya hada min ban sani ba. Ko minti daya banyi ba kuwa baccin ya dauke ni

Cikin baccin naji kamar muryar Farhan tana magana da Umar, na dan bude idona kadan sai na ganta a tsaye tare da Amira, nayi kokarin tashi amma kaina yayi min nauyi sai na mika mata hannu "Farhan" ta karaso inda nake ta rike hannuna

"Amarya. Kar dai baki da lafiya ne, mu da muka zo ziyara" bance komai ba Umar yace "eh bata jin dadi. But tasha magani kuma na bata maganin bacci dan ta huta sosai. Ku barta tayi baccin in ta tashi zata ji dadi sosai" daga nan na koma bacci na.

Sanda na kuma farkawa wajen karfe biyu, naga Amira tana zaune da remote a hannunta tana kallo, na dafe kaina tare da kokarin tashi zaune ina cije lebe da tunanin zanji ciwo a kasa na amma sai naji babu kamar yadda nayi tsammani, sai dan ciwon jiki kadan da kuma wani feeling na yaji yaji a kasan.

Amira ta gaishe ni tayi min sannu sannan naga Farhan ta fito daga kitchen, ita ma tayi min sannu sai na tashi na shiga toilet nayi alwala nazo nayi sallah ta. Ina idarwa Farhan ta zubo mana abinci muka hadu muka ci, tana ta yi min labarin gida da abubuwan da suke latest a

22 / 106