Author : NONE Category : African Stories & Novels
haquri.
sai kallon bakinta take tana salati.."la ha ila ha illahu, anya taawure kina da hanklin kuwa da kikaje majiya kika aikata musu irin wann tijara da dumbin asara? toh da yanzu sun kamaki sun suka kashe ki fa ma ubam waye zakiwa asara inba yarki ba.
kusan a zuciye cikin fushi taawure tace "hajiya koda naje majiya a shirye nake, akasheni mana,dama..meye zan samu na farinciki a duniyan nan bayan juma yay wa ƴata sharrin zina ya tozartata snnn ya walaknta gawarta, yanzu inba don ahannun jikanki ayanaah ta fado inace da har na mutu bazan san inda yata take ba? hajiya, gaskya bazan iya yafe masa ba, inda ace ma nabiye wa zafin zuciyata da har lahira saina kaishi wallah, yayi kadan ya kasa..amma kinga ai bankasheshi ba, dukiyarsa da lafyarsa na rabashi dashi kuma banajin dandanasani yin haka, dan ko yanzu akace na sake masa haka wallah wallah zan iya sakewa, kaf majiya ba'a isa a walakanta ni snn a walankanta rayuwar yayana ba. ..
tana maganan ne tana kuka sosai rungume da ayaanah
ganin irin birkicewa da fushi da taawure tay yasa hajy mairo kasa cewa komi kawai ta karkada kai tana hawayen itama can dai tafara bata hakuri tana lallashinta kana ganin taawuew kasan ba acikin hayyacinta take ba dan sosai mutuwar inayah ya ruguza mata duk wani kofar tunani ya kuma saka mata baqin ciki me tsanani.
tun hajya na lallashinta har ta hakura ta kyalesu da ayaanahn dan suyi jimamin rasa inaya da sukayi atare..
jikinta a sanyaye ta basu waje tana rufe musu kofa ahnkli ta tsaya agefe tanamai share hawayenta, can kafin tafito har waje ta isa gaban motar taje ta samu ibaad ya jingine kansa da stiring motarsa idanunsa a lumshe yay shiru kamar wanda yay nitso acikin tunani
kwankwasa mai kofar motar tay ya daga kai suna hade ido ya bude motar ya sauko kasa, wani iri hajy tay da fuska kmar wacce zata masa kuka, tuni ya bi ya hade ransa, tun kafin ta fara kukan cikin katseta yakawo mata offer cewa kafin ya amince yawuce mata da ayanah can gida sai inhar zata amince tazubar da makaman neman gaskiyarta ta tattara inata inata tabar garin tudu, if not shi bazai kai ayanah ko ina ba, snn zaije kano yagaya ma su bappa zaidu da uncle moh cewa tazonan ta sato yar mutane tariketa bada cikakken izinin iyayen yarinya ba. sabuwar musu suka dingayi, kusan ince ma wayo ya mata sosai, ya nuna mata kawai bata da mafita, ai tunda aurensun ma is invalid uban kowa ma yasan labarin shi baidamu ba, inkuwa har bata amince zata bar tudu ta koma kano ba saidai abari har juman yazo tudu ya dauki yarsa kawai inyaso yaje can ya kasheta.
still suna cikin wnn musun sai ga nan taawure ta fito da sauri saurinta tana share hawayenta da suka ki tsayawa, anan ta samesu agaban motar ibaad, tana isowa ibaad ya rusuna har can kasa cikin nuna tausayi da ladabi ya gaisheta, ya mata proper gaisuwa, snn yamata ta'aziyar mutuwar yarta inayah yadan babbata hakuri shima haka tadinga bashi hakuri akan abunda ya faru dashi akan taimakon ayaanah dayi..
cikin kwantar mai da hankali tace masa babu komi itama tafahimce shi, tasan kuma gidan su babban gidane, bazata so wani abu na rashin mutunci yazo ya faru tsakaninsu da juma ba, inde bazai wuce birni da ayanan ba babu damuwa zata san yadda zatayi a rike mata ita har sai ta dawo.
hajy mairo da ba akasa da ita ba, nan ta tuma ta cafe zancen tace sam sam bata aminta da wann hukucin ba, inde har zata kwashe inata inata tabar tudu r yadda yakeso, saidan inshi ibaad din zai amince ya zama guardian in ayanaah, snn ya wuce da ita cikin kano ayau ta zauna agaban fatima kafin itama tagama parking din tadawo ta samesu acan.
ibaad yay shiru yaki cewa komi ba, duk rakin da hajy mairo tayi, taawure tace musu ita zata wuce wani kauye acan jigawa dan batason matasan garin majiya susan me tay bare azo a dauketa anan tudu aje kasheta a majiya. dan haka zataje can yankin jigawan dama tana da yan uwan mahaifyarta awajen, su irin fulanin tashin nn ne suna yawan zuwa kiwo zata nemesu tazauna awajensu kafin komi ya lafa...
haka sukasha kukan rabuwarsu agabansa da hajya mairo har gwanin ban tausayi...duk kudin ajiya dana jinya dake wajenta hajy mairo tace mata ta rikesu kawai halak malak taje tanemi tsira.
jikin taawure amatukar raunane ta juya, da shirin komawa cikin asibitin dan tay sallama da aayanah, ibaad yana gama shanye hawayensa daya kusa zubo masa ya bi bayanta anatse ya tsareta, saida suka koma can gefe inda babu idon mutane akansu ya tabbata she feel safe with him, snn ya mata bayanin duka duka manufarsa akan hajiya da kuma ayaanah, sosai ya zage ya nuna mata cewa ya fahinceta ya gane halin datake ciki kuma karta damu, yay mata alkwari zai tsaya mata akan yarta har tasamu tay karatun, he will be her quide, snn ya ciro wallet dinsa duk ya rasa inda zaisamu paper, sai ya rubuta mata number wayarsa kawai ajikin sabon dubu daya, snn ya kara fitowa da sabbi sabbin 1k notes din masu yawa baima kirgasu ba ya damka mata su duka ahannunta batare da ya sake hannuntan ba yace mata "Dan Allah kartace masa a'a, tay amfani da kudin duka tay kudin mota dashi, taje duk inda zataje tanemi tsira daga juma snn duk abunda takeso kawai ta kirasa he promised her dat yarta will be in safe hands with him in sha Allahu..
yana maganan nan kawai kuka taawure take masa kamar zata cire ranta, dan bata taɓa samun wani wanda ya iya karantar duka turirin damuwa da baqin cikin dake yawo aranta ba kamar shi..yaro ne, amma gashinan da hankali da tausayi da halin manya atattare dashi.
cikin nuna mata tausayi da girmamawa ya tausasata da kalamai masu sanyi ya kuma lallabeta har saida ta amshi
kudin, fadin irin albarka da godiyan data masa ranar bazai kiyascu ba, ganin lokaci na tafiya yasa tay marmaza ta karasa ciki dan tay sallama da ayaanah
babu wani bata lokaci
tadagota suka rungume juna ta masa nasiha masu ratsa jiki tare da jadadda mata cewa mutuwar inayah ba shine karshen rayuwarsu ba, su hada hannu sucika manyan burikan su, tay mata hakan, dan tasan inayah zatafi jindadi in rayuwarsu tay kyau ba muni ba,
..,snn umarni tabata akan da tay ma ibaad biyayya, ta kallesa a a matsayin dan uwanta kuma yayanta karta saɓa masa..tare damata alkwarin wata rana inkomai ya lafa zatazo har kanon ta nemesu...
gabaki daya ayaanah ta raunana sai tanajii kamr magangnun sun mata tsauri da mugun nauyi dan bama ganewa take ba dan bakaramin kukan rabuwa da mamantan taci ba, haka kuwa tana kallo taawure tabar asibitin taje waje tasamu ko magana ibaad basuyi da hajy mairo ba.
sai fushi take dashi wai yaki karban ayaanah, taawuren tana zuwa ibaad ya mata sallama sukayi bankwana sai yawuce ciki yabarta da hajiya.
anan ne ta sanar da hajiya duk yadda sukayi dashi tabi ta nuna mata kudin daya bata, duk mamaki saiya rufe hjya, suna hawaye ta rakota har waje ta tsare mata abun hawa har saida taga tay nisa snn ta dawo.
dawowarta kenan tazo ta samu har ibaad ya gama biyan kudin jinya da duk wani abu da ake binsu ita sai tawuce ta dauko ayanahn suka fito, tun da suka kama hanya, basuyi wani magana ba har saida suka isa gidanta nan ma sharesu yayi ya hada ruwan zafi a heater yayi wanka yazo ya samu hajya ta sa anhado masa break fast mai nauyi yazauna yana ci itakuma ayaana aka kaita wajen wanka
hawaye duk yaki tsayawa a idonta dan duk inda ta zaga a gidan saitaga kamar zataga addanta da mamanta, she was seriously ill, nd grieving. gabaki daya memories dinsu yanata dawowa mata kai...
dakyar ta shirya adayan dakin hajy mairo ta sakata dan dole taci abinci snn aka kawo mata riga da zani brown colour na coté d' ivoiré kayan yama mata oversized ma amma haka ta saka tana gama cin abincin bacci me nauyi ya dauketa awajen..
tsakanin ibaad da hajiya mairo dakyar suka sauko sukafara magana musmmn data fara tsokanoshi da batun alherin da yay ma taawure, ya hade ransa tamau, yace mata aidqma can ta daukesa mugu ne shiyasa bata yadda dashi ba, dan haka karta damesa kawai tunda zai wuce kano da yarinya ta gaya masa exct ranar da zata gama tattarawa ta dawo gida itama.
badon son ranta ba hakanan suka warware maganan, aka sa ranar, 14days lissafin ranar da zata gama parking da kudin sallamar wasu wokers intan, da wanda zata basu incharge dan su cigaba da mata sana'ar abincin anan tudu dan akwai katon gidan almajirai datake ciyar dasu atunaninta inhar tabar tudu gabaki daya wazaina ciyar da yaran nan. duk suka gama lisasafi, taso ya bata tsawon wata guda amma ibaad yace sam sati biyun kawai ya isheta tunda tana case da yan ta'adda. shi zai gaya ma bappa zaidu da uncle moh ranar tahowarta inyaso za'a kawo mota kawai azo a dauketa da tarkacenta gabaki daya.
ganin babu yadda ta iya dashi yasata kyaleshi, ibaad ne kawai yake iya mata haka tayi shiru saboda sosai take kaunar sa aranta duk dama koyaushe acikin fada zaka same su, jim kadan bayan sun yi hirar karatun sa yace mata shi zaiwuce kano yanxu sabida zai kai ayanahn asibiti adubata acan
wajajen karfe 10:30am saura nasafiya aayanah ta farka duk baccin bai wani isheta ba, haka haj. mairo ta sakata agaba tay mata nasiha mai shiga jiki, duk kusan irin abunda taawure ta gaya mata ne dazu akan tay ma ibaad din biyayya sann ta sani cewa mutuwar inaya ba shine karshen rayuwarta ba, nn ta hadata da ibaad din ta musu atare akan suy hakuri su zauna lafiya tunda qaddara ne ya hadasu. shide baice komiba harta gama surutun ta within few minutes ya fita yabarsu, yagoge motarsa tsaf, yana shigowa yadau jakarsa yace mata kawai su tashi shizai tafi yana da practicals karfe 2 na rana..
daga ayanahn har hjy mairo kuka sukeyi rungume da juna tazo tasakata a mota harda sakamata seatbelt yana sallamar kakansa ko kallo daya bai kara ma ayanah yasa kai ya kunna motar suka kama hanyar kano.
tafiyar kurame sukayi banda kukan da ayanah takeyi babu abunda kakeji, baison yace mata tay mai shiru ba dan yariga yasan abunda takeji is alot to carry, ga zafin mutuwa gana abunda yake faruwa da su, iyaka da abun ya ishehi ya kunna karatun qur'ani ya dan kure musu volume tun tana cigaba da kukan har zuciyanta yay sanyi tafarabin sautin karatun da zuciyarta tana tuna addanta inayah, her fav thing in this world was qur'an ..sai kuka mai zafi take tana tuna irin murnan da sukayi ranar da inayahn tay sauka har bacci me nauyi ya kara daukarta.
ABUNDA KE ƁOYE
SURAYYAHMS
08060712446
idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
[07/11, 20:04] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: ⏯️1️⃣7️⃣Abunda ke ɓoye
bayan tafiyarsu hjy mairo na shiga gidanta ko aje mayafinta batay ba matasan majiya suka diro kofar gidantan yuuuu wai sunzo neman taawure haka hajiya mairo tabirkice da ihu tahau sauke musu bambalastar ruwan bala'i ta tara musu taron jama'a tabi tajuya maganan kaf akansu tace sune suka sace mata yar rikonta taawure dan haka kawai ace musu su fito mata da yarta ko kuma hukuma ne zata rabasu, haka akayi ta hatsaniya tsakanin matasan majiya da hajiya mairo, can dai da sukaga ta fisu bori tanace musu akan su susuka sace taawure tabita laka musu harda sharrin da ko shaidan bai isa ta ciresu aciki ba ahaka ahaka abanza aka bar maganan suka koma garin majiya batare da sun cimma komi ba, ga dumbin zargin su na tunanin taawuren tazo nan duk ya gushe, basusan kuma ina zataje bayan nan din ba, yau dayakamata ace ranar farinciki da samun daukaka ne awajen juma sai ya zamo masa tamkar wata baqar rana dan bakaramin muguwar asarar dukiya taawure ta masa ba,
shikansa dakyar ya tsira da ransa, sanadiyar wasu fatake masu fitowar jeji da sassafe da sukaga wuta na tashi a rumbun abincinsa suka kawomai dauki yau kaf garin majiya sai da aka tashi da labarin abunda ya faru da juma masu tausayinsa suna yi mahassadansa masu masa dariya suna kai, yau tsabar baqin cikin ganin konewar dukiyarsan kurmus koda aka kwanceshi ya fito sarari suma kawai ya dingayi ana yayyafa masa ruwa...
yarasa meke masa dadi, gashi yafi kowa sanin cewa da akwai kakkarfan aikin tsarin jiki na usalin fulanin daji ajikin taawure da yayanta, yasan koda zai dau fansa ta hanyar musu sihiri ko sammon da zaisaka rayuwarsu ya lalace bazai iya ba saidaima abun yadawo kansa..
iya ka dabbobinsa ne kawai tabar masa su araye ahakanma waidan bataso ne tay ma abu me rai azaba da wuta yasa bata konasu da ransu ba.
ranar gabaki daya duniyar juya masa ta dingayi yanata suma ana dagashi yana komawa musmn ma da aka dawo gida akacemai ba aga inda taawuren ta nufa ba duk anje har tudu suma can tudun nemanta akeyi har ansaka hukuma ajeji suna nemanta. yau ya kasance ma juma ranar tsananon bakin ciki da jimami wanda bazai taɓa iya mancewa arayuwarsa ba.
bayan komi ya lafa wajajen karfe daya da rabi saura ibaad ya shigo garin kano kai tsaye baije gidansu ba yawuce Al-eeman private hospital inda babban kawar mamansa take aiki a matsayin babban nurse snn ya damka mata ayanahn a hannu shikuma ya wuce private club dinsu domin halartar practical da sukeyi agefe nasu na yayan masu shi, few minute drive just few minutes away from his main school of medicine na buk, ya gaji sosai ga uban stress din hanya a jikinsa amma baidamu ba hakanan ya shiga aji ya fada aiki. yau ana kkrin koya musu sabuwar darasi ne game da introductory practical anatomy amma gabaki daya sqi yanaji kamar yarasa nitsuwrsa dan harga Allah baisan ma tayadda zaiyi ya cika dumbin alkwarun daya dauka ma tawure nacewa zai kula mata da rayuwar yarta ba...aiki sukayi sosai don komi practical ake nuna musu, har zuwa 3:30pm snn yaje yay sallahn asr aka koma lab still saiga wani visiting doctor yazo musu daga kasar india shima, shi yafara fayyace musu basics introdction naduka duka courses din da zasuyi a main cadre nasu da medicine gabaki daya, kai daga ganin yadda yake koya musun ma zaka san babu me iya karawa dasu a ajinsu yanzu, bcos they are far far advance, sun kamo hanyar wuce mates dinsu na aji sosai, kusan dukkan wasu abubuwan da ba a musu tukuna a ainin lectures dinsu ba shi ake ta kkrin koya musu anan just like private lesson. can da magrib aka sakesu sukabar wajen kusan kowa yagama gajiya. hanklinsa dam kwance dake yariga yagaya ma amminsa dasu bappa zaidu awaya cewa ya dawo kanon already amma bazai wuce gida ynxu ba.
yana shiga motarsa asibitin inda yabar ayanahn ya wuce ya samu waje ya zauna yay shoru yanamai cigaba da zaman jiran jin me likitocin zasuce, anan yay sallan isha, ya fita yaje yaci abinci, kawar maman nasa har ta gama duty ta wuce gida, bashi da samun kan doc ba sai wajajen goma na dare, mace ce, nd she is a well know cardio doctor ana ce mata Haj sakeena shehu dakyar ake samun hanklinta sabida yawa da mutane suke mata. at arnd that time of 10pm na dare tay ushering ibaad cikin office inta ,yana zama suka gaisa a natse snn tafara mai cikakken bayani akan ciwon ayaanah
tacemai bincikensu ya nuna cewa yarinyar originally was born with a strange congenital heart weakness wanda baya nunawa kwata kwata sai inta shiga mummunan hali na tsorata, bacin rai me tsanani ,kakkarfan rauni, jimami me yawa, ko wani nau ikan intense fear ko emotional overwhemlness. daga zarar hakan ya sameta zuciyarta zai fara kokari wajen ganin yay coping da pain in amma akokarin hakanne yake kawo mata symptoms kala kala na raunin zuciya, kmr zafi da ciwon kirji,wahalar fitar numfashi da su panic attacks da zufa me dan banzan yawa har izuwa loss of counsiounes. hoto nan scan da suka dauka ta nunna masa snm takara da cewa Abu mafi muhimmanci ynxu shine a tabbatar mata da samun natsuwa. Kada a tada mata hankalinta. Kada a matsa mata tayi magana ko tana tuna wasu abubuwan da suka wuce mata abaya. snn Idan ta fara jinsu ko suka dawo mata kawai a zauna kusa da ita cikin shiru da bata kulawa cikin tausayawa,yarinyar yar karamace, so zata fi bukatar kulawa da kwantar da hankali fiye da duk wani maganin da zaa bayat yanxu..."jin yau shiru yasa ta kara kallomsa ahnkli tace 'are u her elder brother?babu yabo babu fallasa ya gyada kai, Dr tace okay, toh ga wannan. wano paper ta miƙamai ya karba tace" zaku iya komawa gida, there are the list of her drugs, snn zakuje nan pharmacynmu ku saya alluran sedatives amata su ynxu. idan jikinta bai sarara ba after 3 days adawo mana da ita. gyada kansa still yay cikin nitsuwa yace mata ya gode snn ya rike takardan ya fita dashi a hannu..
baije ya duba ayaanahn ba kai tsaye yajeshi pharmacy ya basu papern snn biya kudi akazo har dakin da ayaanah take kwance aka mata allurai har guda biyu...
hawaye ta dingayi sabida ta tsani allura har cikin kokon zuciyarta, but the more tana kallon fuskar ibaad a bakin kofa sai tanaji kamar ma tafi jin tsoronsa fiye da komi ynxu. jiri me dan banzan yawa takeji amma yadda ta tsaya kyam cikin shanye zafin alluran kamr wata soja yasaka nurse din data mata allurar tace masa
"yallabai zaku iya tafiya..
ibaad ya gyara zaman jakar laptop dinsa kallo daya yay ma aayanahn tay maza ta gyara zaman zaninta da dan kwalinta cikin saibin jiki ta saka takalmi, har saida yawuce gaba snn tafara takawa ahnkli tana bin bayansa yanayin fuskarsa da