Author : zallah Category : African Stories & Novels
ya. sashi tantamar
anya kuWa Rukayya tana gidan‘.’
' Gabanshi ya yanke ya fadi,yaja daga
tsugun0n da yayi ya zauna yana kallon Kaka ya
ce
‘ "Harkun kwanta kenan?" Kaka ta ce, "To me
muke jira?" Ya danyi jim yana ta sakesake a
.zuciyarshi, so yake kawai Kaka ta tare shi da
maganar Rukayyar amma tai burus ta share shi,
abinda ya Kara sashi cikin rudani kenan, ya rinka
waige-waige cikin dakin, babu ta inda ya hangi
alamarta. '
Wata zufa ce ta soma keto mashi da yaga ya
share fiye da minti talatin a zaune, ita Kaka ma
tuni har ta soma barcinta. Ba yanda ya. iya
shima haka ya mike ya fice jikinsa a kasale bai
‘xo da Shirin kWana garin ba, amma kuma yanzu
baiga ta tafiya ba ina zai sa kanshi yanzu ’ idan
aka ce Rukayya ta Bace?
Sai da ya leka (toilet) yaga babu kowa a _ciki
sannan ya wuce‘ tsohon dakinsa ya budc ya
shigé ya kwanta akah katifarsa, babu alamar
barci a cikin idanuwansa haka yaita juyi shi kadai
a cikin daki daga qarshe kuma ya mike yaje‘ya
‘dauro alwala ya dawo dakinsa yaita . jero
nafilfili: yana addu'ar Allah Ya bayyana
mashi ruky
Bangaren Rukayya kuwa tunda ta jiyo muryar
Abubakar yana sallama ta wantsara ta. fada
bayan gado tai kwanciyarta, tana jinshi ya qaraci
zamansa har ya fice sannan ta mike ta haye kan
gadon tai kwanciyarta.
Washegari misalin qarfe. takwas Abubakar ya
gama shirin tafiya (office) ya shiga dakin 'Kaka
da niyyar yai ma Kaka sallama,‘ akai sa'a
Rukayya tana kewaye tana watsa ruwa, saboda
wankan safen da ya riga ya kama mata jiki, don
haka har ya gama yiwa ‘ ,Kaka sallama ya filo ya
hau motatsa ya tafi
bata sani ba. ~
A moto Abubakar ya rasa abinda ke
mashi dadi, ya shiga cikin matukar damuwa da
tashin hankali Tabbas ya sani Rukayya bata
gidan Kaka, to ina ta tafi? To kuma idan har bata
'zo gidan ba ya akai Kaka bata tambaye shi
.yaya Jika ba? Sannan bata tambaye shi yaushe
ya dawo daga tafiyar shekara daya da rabin daya
tafi ba, da kuma bata daure mashi ba ta ‘ :karbe
shifaran-faran anya kuwa babu wata
maqarqashiyar da Kaka ta :shirya masa‘? ldan
kuma akwai ta yaya zai iya ganewa tunda bata
bashi fuskar hakan ba? Da wannan tunae tunanen
har ya iso (office) dinsa zuciyarsa babu dadi duk
ya fita hayyacinsa. Shi ji ma yake tamkar bai da
lafiya, saboda da qyar yake iya jan qafafuwansa,
sai kace mai ciwon lakka kwatakwata bai da
kuzari a jikinsa.
Cikin kwana uku duk inda Abubakar yasan
Rukayya zata iya zuwa sai da yaje ya nemota,
amma bai sa meta ba gaba daya ya zabge ya fita
hayyacinsa, shi baima san zuciyarshi ta kamu da
son Rukayyar ba sai *yanzu data kufce mashi,
don haka washegardi safiyar.juma'a yana tashi.
daga (office). Karfe hudu ya nufo dandagoro
gidan Kaka, ya yanke :‘shawarar zai sanar da ita
kawai tunda barin kashi a ciki baya maganin
yunwa. . ‘ Da sallamarsa ya shiga cikin gidan
babu kowa a. tsakar gidan sai Lami mai aiki tana
“wanke a’laiyyahu a bakin famfo sai da ya gaisa
da ita sannan ya wuce dakin Kaka kai tsaye inda
yake jiyo sautin redio wanda ya karade gidan da
wakar mutanen Niger wadda aka sako a gidan
radio, Abubakar ya yaye Labule cike da mamakin
'yau. Kuma Kaka kida ake sha
‘ kenan, ita da take fada idan wani ya kunna'ta .
ce xa'a cika mata kunne.
Ya yaye labulen dskin tare ‘ da sallamarsa, sai
dai wa zai gani? Rukayya ce kwance akan gadon
da radio a kusa‘da ita daga' ita sai farin dogon
siket irin
'budadden nan, sai 'yar Bingilar bes dinta iya
cibiya mai siririn hannu, babu k0 kallabi akanta.
Ai Abubakar bai san lokacin da ya fado cikin
dakin ba yana kiran sunanta
"Rukayya, dama kina nan kika barni nai
.ta wahalar _ neman ki?"
RuKayya maganar tasa ta daki dodon kunnenta
tamkar saukar markade bata san lokacin‘ data
zabura ta mike ba ido waje
Abubakar ya bita da kallo tundaga sama har
qasa, kafin ya hadiye Wani abu mai kamar yawu
a abakinsa, ya langaBe kai cike da alamun
gajiya ya ce . "Kin tayar min da hankali Rukayya,
kin 'wahalardani, kin wahalar da zuciyata.
Haba Rukayya, me yasa kika biyewa Kaka ku ka
~ dauki alhakina?"
Rukayya ta cigaba da kallOnShi cike da mamakin
kalaman ,dake 'fitowa .daga bakinshi, shi kanshi
bai san lokacin da suke fitowa daga baccin nashi
ba, sai dai abinda ya sani kawai shi ne. gaskiyar
abinda ke zuciyarshi ne yake ‘ furtawa ganin tayi'
shiru tana kallonshi‘yasa " shi matsawa da niyyar
damqo hannunta. ' , Tai saurin ja da baya tare da
bata fuska, cikin sanyin murya Abubakar ya ce . ‘
"'Fushi kike. dani? Kiyi haquri, nasan nayi kuskure
kimin afuwa insha Allahu hakan ba zata sake
kasancewa b...". . Tsakin da Rukayyar taja ne ya
'katse shi daga cigabada zayyano jawabin naSa,
ya bita da‘kailo cike da mamaki. A dai ,dai nan
kuma
Kaka ta fado dakin riqe'da butar data fito daga
makewayi da ita sai faman haki take, ta dubi
Abubakar. ' "Kai malam, fice min daga daki kaji,
mutumin banza mutumin wofi". Abubakar ya juya
inda take yana fadar. . "Haba_ Kaka, yanzu‘
dama Rukayya tana gidan nan shi ne ku ka
Kyaleni cikin tashin . hankali tsawon sati guda?
Duk da dai ni din
mai laifi ne amma ai..Kaka ta katse shi, "Habu ba
surutu na
nema ba da kai, cewa nai ka fitar min daga
‘ daki kawai"
_ Abubakar ya langobe kai, "To naji zan fita
amma tare da matala".
’ Yana maganar ya nufi inda Rukayya take da
niyyar cafko hannunta, Kaka ta daga butan dake
hannunta ta maka mashi akai duk ruwan dake
ciki suka juye mashi a jiki, yai saurin rike butan
yana fadar '
"Allah Ya baki hakuri nasan nayi laifi koma dai
me: akai min ni dai hakuri ne nawa, kuma ‘
zan ta baki shi har sai ranar da kika huce kika _
bani matata".
Yana gama maganar ya juya jikinshi a sanyaye
ya bar dakin Kaka ta raka shi da harara har ya
fice sannan ta maida kallonta wurin Rukayya ta
ce
"Ke kuma sakaran banza kinyi tsaye sokoko yana
ta tsaraki da wannan dadin bakin . nashi da yake
ba wayau ya isheki ba. Yo in nice har ya isa ya
matso inda nake ma ban rotsa mashinkai ba inga
ta karyar rashin kunya". Rukayya dai bata 'tanka
ba sai dai ta koma da baya ta zauna akan. gadon
bata da ta cewa ita ganin abin ma take tamkar a
shirin film in banda abin Kaka k0 giyar wake
tasha ta yarda ‘ta Kara komaWa gidan Abubakar
mutumin da bai sonta, bai qaunarta, haka kawai
ya cigaba dabautar da ita a banza. _ .
_ Bangaren Abubakar kuwa‘ ganin Rukayya ya
rage mashi tashin hankali a cikin zuciya saboda a
yanzu yasan inda take yaqi guda ya rage mashi
wato yanda zai yi ya shawo kan Kaka ta? bashi
matarshi ya sani ba abu bane
mai sauqi ba yin hakan. to amma ya ya iya da
samarin kakarsa? Haka dai zai ta haquri harya
samu ya tadda nasara. Duk da baizo da shirin
kwana garin ba amma a yanzu dole ya tare don
baiga ta tafiya ba har sai ya Shawo kan Kaka. '
Sai dai duk yanda yai zaton' abun ya wuce nan,
don gaba daya Kaka ta ida birkice mashi. k0
kadan bata sauraren shi da ta gama ya samu
wuri ya tare a gidan saita tura Rukayyar ta
“tafi wurin .dangin mahaifinta wai ta gaishe su
tai masu kwana biyu.
Lokacin da Abubakar ya fahimci Rukayyar bata
gidan ba qaramin tashin hankali ya shiga ba, ya
tisa Kaka gaba yana fadar.
"Don girman Allah Kaka ina kika tura mani
mata‘?" _ ' ‘
Sai data harare 'shi kafin tace“habu tun wuri ka
fita idona in rufe na fada maka, na kuma
maimaita maka takardar sakin yarinyar nan nake
jira kaqiji to mu zuba‘ na rantse sai dai kaga
sammaci, don wallahi kotu zan maka ka". ' -.
Abubakar ya dafe kai yana maimaita.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Wai Kaka sai
yaushe zaki ji tausayina ne? Kullum ina qokarin
in ’kwatanta maki ba zan iya sakin yarinyar nan
ba, amma kinki ki yarda na fahimci’ so kawai kike
ki kasheni da raina? Yarinya da aurena akanta
amma ki daukéta ki kaita wani 'wurin da ban san
k0 ina bane don dai kawai kinga banda yanda
zanyi. ' ‘
’ Kaka ta ja filo ta haye saman gado tana fadar,
“In “ma da yanda zaka yi din ba sai kayi ba, aure
ne ance ba'a yi ka bawa yarinya takardar sakinta
tunda ba kai bane autan maza ba kaqiya. To ba
sai kai ta riKo ba duk ranar daka gaji‘ka'saki
amma Rukayya kam kai da gininta sai dai a gidan
wani. Tana can na kaita inda 'zata samu mijin da
ya fika tayi aurenta, kai kuma saki ne kai ta riqo.
Gaban Abubakar ya yi wata mummunar faduwa
da bai taBa yin irinta ba, tabbas yasan Kaka
‘tana da sanin addini dai dai gwargwado, , amma
hakan bai hana shi gasgata zata iya aurar da
Rukayya da aurensa ba saboda yasan shekaru
sun ja akwai rudu da rikicin tsufa a
a
tattare da ‘ ita. Wasu irin hawaye masu zafi suka
tarar masa a cikin idanuwa, yanzu ya zai yi?
Wannan wane inn bala'i neya tunkaro shi'! Lallai
yana cikin jarrabawar rayuwa.
Ya bude bakida niyyar ya cigaba da yiwa Kaka
magiya sai gani ya yi tana kwasar munshari, lallai
ashe ya dade cikin duniyar tunani bai sani ba.
_Jiki a sanyaye ya. mike yai gaba. Washegari
tunda sanYin safiya ya shirya ‘ ya koma Katsina
bayan ya ajiye mata kudi
masu yawan da zata yi amfani daSu. ' " Sai daya
kwashe tsawon sati biyu bai dawo garin ba har
saida ya turo mata su Oga Mahmud . tare da
matarsa Hajiya Maimuna' suma sukai nasu
lallashin da ban baki amma Kaka taKi sakkowa
daga dokin naqin da ta hau, kira kawai take idan
bai kawo' takardar sakin da tacc ba sai ta ishe
shi har gida da takardar tsammaci. Ba yan'da su
Hajiya Maimuna suka iya haka suka dawo bayan
sun juye mata sakon
tarkacen kayan abincin da Abubakar ya shake
masu but din mota, ya ce a kawo mata.
Duk rashin arzikin, da take mashi bai jin zai Iya
hana ta abu daya daga cikin abubuwan jin dadin
rayuwar da yake bata, duk da yana jin zafi da
kuma ciwon rashin tausayin da take nuna masa
qarara, bayan yanzu shi abin
shi yanzu shi abin a tausayawa ne mutumin da
yakr zaune da matarsa kamar Suhailat amma
yanzu ya zama gwauron qarfi da yaji, komai shi
yake yiwa kansa dai-dai da sharar falukansa da
gyaran daki daga girki kafin ya fita (office) sai ya
samu dan dama k0 da kunu ne k0 ruwan (tea) ya
ci da bircdi sannan ya tafl, haka idan ya
daw0_duk uwar gajiyar daya' kwaso sai ya age
ya dafa abinda zai ci sannan yai wanka ya
zauna, tunani ya aure shi babu inda yake jin
dadin zuwa shi yasa yake zamansa a gida daga
shi sai maigadi ,sai kuma yaronsa Laminu mai
kula da fulawoyi shi ne kuma ke mashi wanki da
sauran 'yan aikace aikacen da ba'a rasa ba. '
Hmmmmm su kaka manya gaskia na tausaya ma
habu
A,I,S
RIKON KAKA
CHAPTER 25
Abubakar ya zama bai da :abokin hirar da ~ya
wuce t.v sai' kuma tunanin RuKayya wanda yake
kwana dashi ya kuma tashi da shi wannan ita ce
rayuwar Abubakar a sabon gidansa. Satin
Abubaka biyu ya kasa daurewa ' ya nufo
Dandagoro bayan ya sha jinyahar ta tsawon
kwana uku’, shi kadai babu wanda ya sani, duk
'wanda ya. kalle shi a yanzu zai fahimci halin da
yake ciki saboda irin ramar da yayi ya zama
kuma wani (so silent) kamar ba
shi ba.
Lokacin da ya iso gidan Kaka bata nan 'sai dai
Lami_ wadda ke ta darzar ’wanki, Abubakar yaja
kujera 'yar tsugunne ya zauna a gajiye kamar
wanda yasha gasar tseren gudu ya gaji. Ya
gaishe da Lami cikin sakin fuska, La‘mi ta amsa
cike da, tausayin Abubakar din yanda yabi ya
zabge kamar bashi. ba, ita dai daukar alhakin
yaron ya isheta haka. Ta zauna akan kujerar da
take wankin akai tana kallon Abubakar dinda yake
tambayarta k0 Rukayyar
ta dawo?
Lami ta sassauta murya kamar mai tsoron wani
ya jiyota, tace. "bata dawo ba, sai dai k0 in fada
maka
inda take". Abubakar ji yayi tamkar ta tsunduma
Shi
cikin gidan aljannah, don tun kafin ta fada mashi
ya soma jero mata ruwan godiya. Ai tana fadi
mashi tana Bakori gidan qanin“ mahaifinta tsam
ya mike yai mata kyauta mai tsoka ya fice ya
fada motarshi, kai tsaye ya dau hanyar‘ Bakori,
bayan ‘ya tsaya gidan man Dandhgoro ya shake
tankin motarshi taf da mai
,,,,,,,,,,,, ,,,,,,,,,,,,,
Bakori gidan qanin mahaifin Rukayya ne marigayi,
uWarsu daya ubansu daya, yana zaune a
gidanSa_ shi da matansa guda ukuTasallah,
Lantana da kuma‘ amaryar su Larai. Yana da'
ya' ya a qalla sun kai ishirin da wani abu, wasu
sunyi aure wasu kuma basu yi ba, suna nan mata
da maza.
zuwan Rukayya garin ba qaramin mamaki ya
bawa Kowa ba, saboda tun Rukayya tana yarinya
suke son Kaka ta rinka: turota tana ganin 'yan
uwanta suna zumunci amma Kaka taqi, ita allan
kalafar bata yarda Jika tai nesa da ita ba, sai dai
ta dauketa suje su wuni tare su dawo. Wannan
ne: yasa ba wani zumunci mai qarfi ‘tsakanin
Rukayya da'yan uwanta.
Don haka yanzu da tayi aure tazo masu wannan
dogon zaman ba qaramin mamaki ya _ basu ba,
don haka sukai tunanin aurenta ne ya mutu.
Itama kuma ta tabatar musu da hakan.
‘ Kawu yaji haushi ba kadan ba, don ’ a ganinsa
irin hakan ceke sawa a guji auren zumunci don
gudun bata zumunci. ‘
Rukayya taji dadin zama a cikin kauyen
’saboda 'yan uwanta da kowa na son ace ' 'yar
gayun nan 'yar uwarshi ce hakan ne yasa har
rububinta ake a cikin yara da matasan gidan. ‘
“ Jamilu .yana daya daga‘cikin matasan " gidan‘
'yan gayu masu ji da karatun N.C.E,
wanda yana ganin Rukayya zuciyarshi ta ayyana
mashi ya samu matar aure irin wadda yake burin
aure, don haka ya yi kane-kane ya hana kowane
saurayi na gidan raBarta don gudun‘ kada ma
wani' yai masa shigar sauri..
Duk da bai furta son da baki ba amma aiyukanshi
sun nuna, don duk inda Ruqayya zata jeshi ne
mai kaita da sabon mashin dinshi Jincheng roba-
roba, a gidan har sun fara fahimtar inda ya dosa.
lnda ita kuma Rukayyar ‘ take daukar duk
zumunci ne kaWai;
A yanzu haka ta riga ta shirya komawa gida gobe
don haka yau shirye shiryen taflya _ kawai take,
tun safe suke yawo da Jamilu tana bankwana,
.zuwa yanzu haka gidan Mariya . zasu qanwar
.jamilu dake aurc cikin garin, amma basu samu
fita ba sai bayan sallar magariba. '
Tayi kyau sosoi cikin riga da siket na shadda
maroon colour, ta yane kanta da (milk) ’ din
mayafi mai Shara-Shara, sai dai yana da
dan girma ba Iaifi Ta Saka takalminta mai tsinin
dunduniya. ita kanta tasan tayi kyau balle Jamilu
da ya goyota saman mashin dinsa, sai yaba
kwalliyar yake tare da kwarzanta ta. ' ita k0 sai
dariya take mashi, don ta'san duk zolaya ce irin
tasa, don haka ta biye mashi suna ta kWasar
dariya. '
Suna qokarin hawa titi Abubakar na ‘ qokarin
shiga layin_ da suka baro, idanuwanshi sukai
tozali da su suna ta kwasar dariya, wani irin
gingimemen abu ya tokare mashi zuciya ~wanda
yasa saura kadan da motar ta kwace mashi. . " _
Ya taka wani mahaukacin birki wanda « yasa
qura ta tashiya juya kan motar yai a sukwane ya
rufa masu baya, ya bar jama'ar wurin na faman
atishawa tare da Allah Ya isa ga wanda bai ma
san sunayiba saboda an shiga haqKinsu kuma
hakan haramun né a Musulunci.
’Abubakar bai samu shan gaban su ba har sai da
suka sauka daga kan babban titi suka hau .
Karamin titi sannan ya samu nasarar shan
gabansu da mota, ya haske su da farin hasken
fililun motarsa
Jamilu ya ja birki a haukace, sannan ya soma
aunawa mai motar zagi. itama Rukayya ranta yai
masifar Baci, sai da Abubakar .ya gama qare
masu kallo suna ta kare-karen idanuwa tare da
zage-zage sannan ya bude motar ya fito.
' Tun kafin ya qaraso Jamilu da Rukayya suka
sakko daga kan mashin din suka kaucewa
. dogon hasken da_Abubakar ya haske su dashi.
Abubakar na qarasowa Jamilu ya cire hannu da
zummar ya mare shi, Abubakar‘ yai caraf da
hannun ya rike gam,’ muryarsa a sanyaye ya ce.
"Ina zakaje mani da mata?" Jamilu ya fincike
hannunshi cikin zafin zuciya yana fadar. ‘ ‘ "Uwar
wacc ce-matar taka?" .
‘ Abubakar ya nuna Ruqayya ' da danyatsanshi
manuni ba tare da yayi magana ba.
. Takaic'i , ’ya_ .kama Jamilu, ya haske. '
Abubakar da kallon banza kafin' ya ce.
"Lallai kai ka tabbata mahaukaci, qaramin ,dan
shaye-shaye. To k0 salansa kake sha qarewar
hayaqi ni na fika iskanci".
Abubakar ya ce, "Ai na lura tunda har ka
iya daukar matar aure" Haushin maganar
Abubakar ta kama
Jamilu har ya daga, murya yana nuna Abubakar
yana auna' mashi ashariya, abinda ma ya janyo
hankalin 'yan tsirarun mutane masu wucewa
kenan sukayo kansu tare da buqatar jin ba'asin
maganar Jamilu ne ke ta faman kora masu
jawabi '
cikin bacin _rai, sai da'aka gama sauraronsa
‘sannan aka ,bukaci jin ta bakin Abubakar wanda
ya harde hannuwa a 'Kirji yana kallon su' daya
bayan daya. Ya maida kallonsa akan '
Rukayya,yace ita ya kamata ku tambaya, gata
nan".
. Jamilu ya dubi Rukayya yana rawar haBa, ya
ce. ’ "Ai ni nasan wallahi bata sanshi ba, irin
yan iskan gari ne kawai, k0 kin sanshi Rukayya?"
Sai data tabe baki kafin ta ce
"Ni ban sanshi ba". Ai kuwa jama'a kamar jira
suke aka
hayayyakowa abubakar, don Jamilu qarfin hali ma
har kwalar rigar Abubakar yake ciyowa wai a
duke shi. Ai kafin ma ya cire hannun nashi daga
kan kwalar abubakar ya dunkule yatsun
”hannunshi ya kai mashi ‘wani dan marayan
naushi a mahagurba, yai wani irin ihu ya dafe
wurin da tuni ya baci da jini.
Abubakar ya qara mika hannu ya cakumo shi
yana Kokarin sake narka mashi wani naushin
jama'a suka tattare masu zakalkalewar ciki suka
dawo neman sasanci naya saki wuyan rigar
Jamilun, amma babu alamar zai saki din duk da
idanuwan Jamilu da suka
yo warwaje yana ta kakarin wahalar Majiya masu
qarfin ciki ne suka fara qokarin bambare hannun
Abubakar din, amma k0
gezau bai yi ba, don haka aka soma rokonsa da
ya sake shi din '
Bai saurare su ba ya maida kallonshi akan
Rukayya dake tSaye tana ta rawar haBa tare da
rarraba na mujiya, ya daka mata tsawa.
"Yanzu kin sanni k0 sai na kashe: shi
tukunna za ki sanni?" ‘ Rukayya jiki ya dauki ciri,
muryarta na rawa ta ce ‘
"Idan na sanka sai me? Ina ruwana da kai?
Mugu, azzalumi kawai, wallahi Allah sai
. Yai mana sakayya". Abubakar yayi wani
malalacin murmushi‘
sannan ya saki Jamilun .yana fadar.
’ "To kaji k0 ni wane ne a wurinta, mijinta
ne data gudo ta bari kuma kaine baka sanni ba
amma ni na sanka shi yasa ma tun farko ban yi
niyyar taBa lafiyar jikinka ba, kaine kaja da
taurin kai irin naka, amma kayi hakuri". Jamilu ya
rasa abinda zaice sai faman
mazUrai yake Abubakar ya ”tura ‘hannu cikin
aljihu ya damtso kudi mai yawa ya soke mashi
cikin aljihu yana fadar.
ga wannan‘ ka rage zafi".
Bai bari yace'wani abu ba ya damki hannun
Ruqayya tana turjewa tare da borin kwacewa
haka yaja ta da qarfi ya sakata a mota ya rufe ya
zagaya ya shiga mazaunin dirrba yaja suka tafi.
Kai tsaye gidan Kawu ya nufa ya kulle Rukayya a
motar shi kuma. ya nufi cikin gidan, saukinta ma
akwai AC a ciki daya kasheta.
da zafi
‘ A zaure ya samu kawu a kwance yana sauraren
rediyo, Abubakar ya durkusa a gabansa suka
gaisa. Bai gane Abubakar dinba sai da yai mashi
bayani sannan ya shaida shi. Nan fa Abubakar ya
sanar da shi duk