Author : zallah Category : African Stories & Novels
babu k0 kifi ballantana ’
suci arzilqin nama.
Ta juyeta a kula ta rufe k0 lemu bata hada ba sai
dai ta dauko na‘kwali ta hada da robar ruwa ta
jera akan tire ta dauka ta fito
Tana ajiyewa akan table tai gaba abinta ba tare
_da ta kalli inda suke ba, saboda hawayen dake
faman zubowa a cikin idanuwanta har a lokacin.
Tana shiga Bangarenta ta maida kofar ta ' .ruga
da gudu dakin baccinta ta fada akan gado ‘
‘tare da rushewa da wani sabon kukan mai ban
tausayi.
Tana cikin baqin ciki tare da Jin haushin kanta da
zuciyarta da har ta bari son Abubakar ya Shigeta,
sai yanzu ne ta soma takaicin yanda' ta biyewa
Aunty Maimuna akan wai dole Abubakar zai sota
alhalin tafi kowa sanin irin
tsanar da yai mata.
. Tabbas itama zata kwatanta mashi kadan daga
cikin irin kiyayyar. da yai mata, dole zata
fatattaki soyayyarsa koda da qarfin tsiya ne
daga. zuciyarta. Ta qara makalkale filo tare da
rushewa da wani irin kuka mai ban tausayi.
. Washegari tunda Rukayya ta kammala sallar
asuba bata sake komawa bacci ba, ta . shiga
tattaro komatsanta tana zubawa cikin Katuwar
jakar kayanta, sai data hada kan komi sannan ta
zube qatuwar jakar ta dauko atamfarta ta‘ jiya ta
saka, sannan ta saka hijabin _ sallarta, karfe
bakwai daidai ta dauko jakar ta tai hanyar barin
gidan.
. Tun kafin ta ida isa bakin get ta soma tunanin
irin qaryar da-zata shirgawa maigadi ta samu ta
bar gidan, sai dai cikin ikon Allah tana zuwa ta
samu qofar a bude da alama ya zagaya ne. Cikin
farin ciki Rukayya ta sa kafa ta bar ~gidan jikinta
na rawa, bakinta kuma na addu'ar Allah Yasa ta
samu ficewa daga layin -ba tare da wani ya
ganta ba, saboda unguwar tasu G,R,A CE ; k0 tsit
yake k0 da yaushe zaka samu babu kowa. Don
haka har ta samu ta iso bakin titi mutanen data
gani basu wuce uku ba, suma
amman babu wanda ta sani cikinsu. ta jima a
bakin titi kafin ta samu mai keke napep ya
dauketa daga nan zuwa Dandagoro naira dari
biyar. Rukayya bata samu nutsuwa ba sai da
taga sun fice daga‘unguwar gaba daya sannan ta
samu sukuni Karfe takwas saura mintina shidda
taiwa Rukayya a kofar gidan Kaka wanda rabonta
dashi tun randa Kaka ta kaita gidan abubakar, sai
yau data gudo da qafafuwanta
haka rayuwa take. Rukayya ta biya mai keke
napep sannan ,
ta dauki kayan nata duk da uban nauyi
ta nufi cikin gidan na Kaka.
tana Sallamar farko Kaka ta amsa tare da duban
qofa, sukai ido hudu da Rukayya. Kaka :ta dau
salati tana fardar
Rukayya yau a gidan nan ko ko dai gizo idona ke
mani?"
:Rukayya ta sauke jikarta a gaban Kaka taja
;kujera 'yar tsuguno tana
kokarin zama
agaban tabarmar da kaka ke zaune, 'Kaka ta
‘tsarrta da idanuwa tun kafin ta zauna ta soma
fadar.
"Ke 'yar nan ya naga idanunki luhuluhu kamar
wadda ta sha kuka? Wannan uwar jakar ma wai '
daga ina?“ Rukayya ta zauna tare da sa gefen
hijjabinta tana share kwallar dake qokarin
zubomata ' Kaka ta sake daukar salati saida
takai aya ta ajiye sannan daga karshe ta furta. ',
"Kada kice min yaji kika yo Kada " ki fada mani
wannan bakar kalmar" '
Rukayya ta tsaya da sharar kwallar tana
kallonta.
Haushi ya fara kama Kaka, tace.
' "Ke nak saurare Jika, me ya fito dake ciki
gidanki. Babu dai abinda kika nema kika rasa to
akan wacce hujjar? . A wane dalilin?" ‘ Rukayya
tacigaba da Sharar kwallarta, tabar ~. Kaka nata
sababinta har sai da Lami mai aikin kaka ta fito
daga cikin dan karamin dakinta
ta iso inda suke' tana fadar. .
"Haba Kaka. kin tasa ‘ya a gaba da sababi
akan'abinda baki sani ba, sai‘ kace baki swn
halin mazan nan na yanzu ba lalatattu, na kirkin
cikinsu ragaggu ne". '
”Kaka ta karkace kai tana fadar;
"Shi ne kuma za'a rinka lullubo zani a taho yaji?
Da kika ganni nan Lami shekarata arba'in da
mijina ban taBa zuwa gida --. kararsa ba balle in
rufa zani in tafi gida yaji ba kuma don baya saba
min ba".
' Lami ta ce, "To k0 dai mene ne yanzu ai .kin
tsaya kiji ta bakinta lukun sai ki yanke hukunci
Kaka tace, "ai gata nan sai .ta gaya miki, ina
saurare
Lami ta juya kan Rukayya ta dafa kafadarta tana
fadar.
‘ "Yi shiru mana haka nan Rukayy'a, kiyi
hakuri ki fadi abinda ke faruwa sai a san ts inda
za'a taro al'amarin Ai ke kinyi sa'a ma
abin'duk na‘ gida. ne ba zai yi wahalar gyaruwa
ba Sai 'da Lami ta bata lokaci wurin 'lallashin
Rukayya kafin ta bude baki ta ~ Zayyano duk
_'abinda ya faru tsakaninta da
Abubakar har izuwa yanda Tun kaifin ta kai aya
Kaka ta soma
‘sallallami tana rusawa Habu zagi, tana
mmmmm. "Yanzu in wanke' yar in bashi shi ne
zai
zuba mata ido yana kallo saboda rashin mutunci
da wulakanci? Ni habu zai nunawa iyakata?" . ' '
Rukayya na kaiwa qarshe Kaka ta rushe da kuka,
k0 kalonta Rukayya bata tsaya tayi ba ta mike tai
Cikin daki ta haye kan gadon Kaka taci gaba da
kukanta.
Tabbas abin ba qaramin bakin ciki yaiwa Kaka ba
don yau tai mashi zagin da bata taba kwatanta
yiwa wani irinshi ba don ma dai
lami na‘gefe tana tausarta da ban san irin abinda
za tai mashi ba
Duk yanda Kaka taso ta lallashi Rukayya taqi
saurarenta, ita ala dole fushi take da ita. ‘_ Kaka
kuwa duk tabi ta damu, har suka kwanta
~dadaddare. .
Kaka dai ta kasa daurewa don gaba daya baccin
ma ya gagari idanuwanta, ta tashi zaune tana
kiran Rukayya ya kai sau uku kafin ta amsa. '
Kaka ta ce "Tashi kiji abinda zan gaya miki".
‘ Rukayya ta ce, "Ni fa bacci nakc ji, ki fada
kawai ina jinki".
Kaka batai musu ba ta cigaba da fadar.
"In har'dai ba habu bane autan maza a duniya to
kin gama aurensa tunda har ya wulaqanta ki
haka, ki barni dashi. K0 gaisuwa ban yafe ba idan
ta hadaki da shi kinji abinda na fada' ‘ . miki".
Rukayya dai bata tanka ba, _amma a zuciyarta
gani take gaisuwar ma bazata qara hadasuba
Mutumin da ya wulakanta ta, ya nunawa duniya
’ita da dan uwansa namiji amfaninsu daya
wajensa, to gaisuwar mece ce zata hada su? Ai
ba ma zata yarda ya sake ganinta ba.
****** **********
. Bangaren Abubakar kuwa tunda gari ya waye
misalin qarfe bakwai ya gama shirinshi na tafia
(ofiice) a matsayin shi na' sabon ma'aikacin da
aka tura (curse) .su goma su uku ne kawai sukai
nasarar fitowa da (result) mai kyau, don haka aka
dauke su aiki, yau kuma ita . ce rana ta farko da
zai fara zuwa (offlce) din.
Suhailat na kwance akan katafaren gadonsu, tana
ta sharbar barci, har ya kammala shiryawarsa.
Bai yi tunanin tayar da ita ba saboda .bai ga
amfanin hakan ba tunda babu . wani abu da zatai
mashi yasa kai ya fice yana daura tsadadden
agogonsa a hannu.
Ya so ya biya ta sashin Rukayya yaga yata
kwana? Sai daisaurin da yake ba zai barshi ba
don haka inda so‘ samu ne ya dan karya 'da "
lafiyayyen girkin Rukayyar kafin ya tafi To hakan
ba zata samu ba, saboda qarfe bakwai dinma
harta dan gota
Hmmmmm kaka dai tace indai habu ba autan
maza bane a duniya ba to ba habu ba ruky
lol muje zuwa wai mahaukaci yahau kura admin
is back
RIKON KAKA
CHAPTER23
aka ce tai musu a can don haka bai tsaya Bata
lokaci ba ya dau motarsa a gaggauce ya tafi.
‘ Tunda suka isa wurin aiki shi da sabbin da aka
dauka irinShl basu samu sun shiga (office) ba sai
qarfe sha biyu tunda ya shiga (office) din nashi
sallar azahar da la'asar ce kadai ta fiddo dashi,
k0 abinci bai iya fitowa ya nema ba sai ruwan
(tea) kawai da yake ta faman kwarara ma cikinsa,
amma duk da haka har qarfeshidda bai samu ya
gama (clearing) din komi ba, a dole ya taho gida
saboda lokacin tashi ya riga yayi. '
‘ . Bai taho gidan ba sai da ya biya ta crepcy ya
kwaso tarkacen su (snacks) ice cream da lemuka
yayo leda biyu na Suhailal da kuma Rukayya
sannan ya nufo gida.
Tunda ya shigo falon bai nuti Bangaren kowacce
ba, kai taye wurin teburin cin abinci ya nufa
saboda wata irin yunwa da yake‘ji tana neman
kayar dashi.
Sai dai da mamakinsa ya iske tcburin wayam ji
yayi gabanshi yai wata irin faduwa wani irin
masifaffen Bacin rai ya shige shi, ya
'juya a zafafe ya nufi Bangaren RuKayya tamkar
ita kadai ce a matsayin matar shi a gidan. Ya
tura kyauren falon, kai‘ tsaye yasa kai a cikin
falon nata yana kwala mata kira.
Jin da_ yayi babu alamar za'a amsa, yasa shi ‘sa
kai cikin‘ dakin baccin 'ta sai dai mamakinsa, nan
ma wayam babu kowa a ciki. Ya maida kallonsa
akan qofar toilet din wadda ke a'bude.
Gaban Abubakar .yai wata mummunar bugawa,
ya juyo a firgice yayo waje. Dakin Suhailat ya
nufa, tana tsaye gaban (home theater recorder)
tana ta tikar rawa da wakar Adam Zango ta gayu
komai na mata ne.
Takaici ya kama Abubakar ganin bata ma san ya
shigo ba har sai da yaje ya kashe wakar sannan
ta waigo a tsorace sukai ido hudu dashi, ta
yamutSa fuska a gajiye tana fadar.
' "Am sorry, wallahi banji shigowar ka ba". . _ ._ .
Abubakar yaja tsaki kafin ya ce.
"Ai dama ba‘zaki ji shigowata ba tunda kin qure
volume kina ta tikar rawa sai kace
"yar nanaye. lna Rukayya ta tafi ne?" Suhailat ta
bata tuaka tana kallonshi kafin tace. , "Rukayya
kuma? Akan wanc dalilin zaka lambayeni inda
take? Ka bani ajiyarta ne?" Abubakar ya hade
girar samadata qasa kafin yace
‘ "Ban gane na baki ajiyar taba? Ya zan lafi in
barki da yariya a gida in dawo kuma in tarar bata
nan in maki magana kuma kice na baki ajiyarta?
Jinan Suhailat, ban son rainin wayo kinji?"
itama ranta ya soma Baci, a ganinta ma in ba ya
rainata ba ya za'ai yai mata wannan tambayar? ’
Ta dauke kai tana fadar, "To na koreta ‘daga
gidan tunda ba gidan ubanta bane, ko nima zaka’
koreni ' ' ne‘?" Ran Abubakar ya yi wani masifar
baci, wai har 'Suhailat tayi bakin da zata xagi
'yar uwarsa‘? Lallai shi ya bata fuska, don haka
cikin
matukar Bacin rai ya shiga fadar
"Kin koreta kin kyauta, amma kamar
yanda kika ce ba gidan ubanta vane to nima ai ba
gidan uban babe hakaxalika tunda har gori ya
fara shigowa ciki nima zan bar gidan
yau kamar yanda itama ta barshi. Nine ke aurenki
Suhailat bake ke aurena
ba, don haka na baki zaBi k0 ki koma sabon
gidan da na gida da kudina kiyi zaman aure, k0
kuma ki zauna anan, .zaBi ya rage naki".
Yana gama maganar ya fada dakin barcinsu.
Suhailat ta bishi da bala'i tana fadar.
"Yo aurenka din banza, Abubakar kai har kayi
kudin da zaka gina gidan da zaka sakani a Ciki‘.’
Ai dama tun kafin mu dawo qasar nan“ na gane
take-takenka, ka ajiye aikin kamfanin mahaifina
ne kanemi wani .aikin don kaji dadin'cin zarafina,
to baka isa ba, wallahi kayi tsururu. In banda ma
qaddara ai kasan nafi kariin ajin'. aurenka, ita
wadda kakewa rawar jikin dama can ita ce ajinka
ita ce dai dai kai ba __ ' ni ba"
wohoho mata kaiiii muje zuwa
Duk abin nan da take Abubakar na tsaye gaban
(wardrop) yana hada kayanshi a cikin akwati, bai
sake kallonta ba ballantana ya kulata. haka ya
hada duk ‘wani abu mai muhimmanci a cikin
akwatinshi ya gama zuge abarsa yaja hannun
akwatinsa ya fice daga gidan.
Har ya fice Suhailat ta raka shi da sababi, bai
sake kulata ba ya saka akwatinsa a bayan mota
ya fice ya zagaya gidan direba ya shiga yaiwa
motar; (key) yai gaba abinsa, ya barta nan. Da
Wauta kuma yana ficewa daga gidan sai. kuma ta
rushe da kuka cikin tashin hankali
' sai' kace ba ita bace yanzu ke zazzaga masifa
‘ba har baki ’na kumfa. . '
Kai tsaye Abubakar gidan Haj. Maimuna ya fara
tsayawa, yai sa'a kuwa ya samu, oga mahmud a
gida, don haka suka baje a falo inda Hajiya
Maimuna ta qawata masu tebur da kayan abinci
da soye-soye kala-kala.
' Abubakar ya ' kasa taBa komi saboda tsananin
damuwa da yake ciki Mahmud ya
tsura mashi idanuwa yana fadar.
"Lafiyar ka dai Abubakar naga kamar baka .da
lafiya?" Abubakar ya jingina da makarin kujerar da
yake zaune yana kallon Mahmud da jajayen
idanuwansa cikin matukar damuwa ya soma
fadar
' "Lafiya qalau Oga, damuwa ce kawai". ,Haj.
Maimuna dake tsiyaya masu lemu a glass cup ta
dago ta dan dube shi tana fadar
"Wallahi naga alama, don ni har na danji tsoro
don ban taBa ganika cikin irin wannan yanayin
ba" .
Abubakar ya shaki numfashi yana fadar.
"Ni ' kaina ina tausayin‘ _kaina Hajiya Maimuna
Suhailat ta. kOri yarinyar nan Rukayya -
ina' (office) ban san ina ta ina zan fara
'nemanta ba, na' tabbatar matukar taje wurin
kaka ka'shina ya bushe". ' . ’ .Haj. Maimuna
dake duke ta_ koma da baya ta zauna 'akan
kujera tana fadar. "ta kori Rukayya yaushe?"
"‘Dazu". Abuhakar ya bata amsa.
Haj Maimuna ta dafe kai cikin matuqar mamaki
tana fadar
“Ikon Allah, kuma har Rukayya ta baro gidan ba
tare data biyo tanan ba?"
Mahmud ya dubi Abubakar yana_ fadar.
"To kai tayaya ka sakarwa mace haka harta iya
korar wanda ka dauko ka kawo cikin gidanka
baka nan?" _ Kafin yai qokarin fadar wani abu
Haj. Maimuna ta karbe zancen da' '. "Ai
Honarable duk abinda yake faruwa a cikin gidansa
ba laifin kowa bane laifin sa ne da sakacinsa.
Dama k0 da Suhailat bata kori Rukayya ba itama
Rukayyar ta soma tunanin guduwa ta bar maka
gidanka. _ . , Abubakar ka ajiye mata biyu a cikin
gida amma ka tauye faya akan daya saboda wani
son zuciya can ~ naka. Shin ita Rukayyar ba
matarka' bace? Ko ita ba mace bacc? K0 kana
tunanin bata buqatarka? Amma ka' biyema “mace
ka tauye yarinya, ka mayar da ita 'yar aikin
gidanka ba' wai matarka ba, ku ka dinka '
wahalar da.ita'don kawai an aura maka ita ba
. , . don kana so ba. Shin kana ganin Ubangiji zai
barka ne k0 kana ganin kana da wani makari da
zaka iya kare kanka a wurin Ubangiji?
Dama ni jiranka nake kawai ka dawo in hadaka
da Honarable yai maka nasiha tunda kuma an
koreta ai shi kenan, dama abinda kake
so kenan tatafi ta baku wuri ta yunkura ta mike a
zafafe tai falonta zuciya ta kawo mata wuya
kamar zata fashe saboda bakin ciki, ita a ganinta
Abubakar ya cancanta a kirashi azzalumi mai
bautar dana qasa da shi.
oga Mahmud ya dubi Abubakar yana fadar. "To
kai ta yaya duk wadannan abubuwan ~suka faru
haka Kana aikin me?". ' ' ‘ Abubakar ya kasa
magana, ya rasa abinda ke mashi dadi daga
yanda yaga Hajiya Maimuna ta hau yasan zai
iske dubun haka a wurin Kaka. _ .
Oga Mahmud Yace"Kaifa nake saurare Abubakar
kayi shiru
Abubakar ya sauke numfashi kafin ya soma
magana.
"Wallahi Mahmud duk aikin zuciyane kasan
Rukayya ba sonta nake ba kakace tasa dole“: na
aureta, tasa dole na hada su da suhailat Gashi
gidan da nake zaune mahaifin Suhailat din ne ya
bamu aronshi kafin nayi nawa, gashi kuma ba son
Rukayyar nake ba, wannan ne ye ‘taimaka wurin
tauye mata haqqinta.
Amma da taflya tai tafiya ni da kaina
naji hakan bai kamata ba, hakan ne yasa na
harhada kudi masu yawan gaske nasai qaton fili
a Batagarawa low cost don a ganina idanna ce
zan bawa Rukayya matsayi na mata a ‘wurina a
cikin gidan uban Suhailat duk abinda akai mana
ni na ja.
‘ Ban fara ginin ba na samu tafiya qasar nan yin
wannan (course) din, na dauki Suhaila muka lafi
kudin alawus din da aka rinqa biyanmu daSu na
gina filina, daga can qasar na turo da zanen gida
da nake so muna dawowa
aikina na ajiye a ciki a kamfanin mahaifin
Suhailat tunda nayi nasara akan (course) din da
aka tura mu yai mana murna sosai
Tun kafinmu iso gidanmu na sanar da Suhailat a
gidana zamu_ sauka, amma ta qiya a dole muka
dawo gidan mahaifin nata.
Ni don da yanda naso in fara ajiyeta a gidan nawa
sannan in dawo in dauki Rukayya itama na kaita
gidan. Sashi uku ne iri daya nawa da na RuKayya
da kuma na Suhailat to sai ta Kiya a dole na
kyaleta, amma dai na sakawa raina zan dauki ita
Rukayyar da sunan na kaita' qauye sai in kaita
can gidan nawa indai data matsayinsu na matana
sannan da na dawo in sanar da Suhailat gidana
na kaita na bata irin matsayin da itama na bata
nasan Suhailat tana matuqar sona zata haqura
idan ma bata yarda ' ba to sai ayi duk yanda
za'ayi tunda ni dai nasan inda .na dosa sai gashi
ta koreta ban sa yanda zanyi ba nasan da wuya'
idan kaka zata saurareni ballantana har ta
fahimce ni". ‘
*Oga Mahmud yajinjina kai kafin yace.
"Ai duk da haka Abubakar kayi matuqar wauta,
amma ni a ganina shiryawa kawai zaka yi ka tafi
biko da sunan kai baka ma san yanda akai ta
taho ba, a can ne za'a fada maka kishiya . ce ta
korota, kaga daga nan sai kasan sauran "‘
bayanin da zaka yi ka samu a baka matarka ku
taho. '
Abubakar yayi murmushi cikin matukar jin dadi
yana fadar
”Aiko ka ba da shawara yanzun nan zan je don
banga abinda nake jira ba".
Oga Mahmud ya ce, 'Amma kafin ka tafi din ya
kamala ka fara biyawa ta gidansu Suhailat din ka
sanar da mahaifinta duk abinda ya faru
tsakaninka da Suhaila! din don kada ta rigaka
zuwataje tai maka 'yan qulle-qulle'. Abubakar ya
ce, 'Yanzu fa barima ka gani
Ya mike tare da miqawa Mahmud hannu suka
Kara yin musabiha sannan sukai sallama ya tafi
‘Abubakar ya isa gidan su Suhailat yai sa'a kuwa
mahaifinta yana nan' don ‘haka a
falonsa akai mashi masauki, sai dai Abubakar bai
san yanda ake kai qara ba tunda bai tababa gashi
yana matukar Jin nauyin sirikin nasa hakan ne
yasa sai da yai tA 'yan zagaye zagaye kafin ya
iya zayyanowa mahaifin Suhailat din abinda ke
faruwa tun daga aurensa da Rukayya har izuwa
yanzu.’
Alhaji ya jinjina kai yana fadar;
lkon Allah, yanzu wuyan .Suhailat har yayi
kwaridn da'zata dubi mijin aurenta tai .mashi
wannan rashin mutuncin? To ba‘komai, kada ka
damu, kayi haquri gida dai nawa ne don haka
tunda Allah Ya buda maka kayi naka to nima na
karbi nawa kuma bance ka dawo gidan nan
bikonta ba, yanda kace ta koma naku gidan tasa
Kafa ta shure to haka zata kwaso qafar dai nata
taje ta iske ka Ka'bani , dan lokacu
ln banda sukarcinta ai shi aure nufi ne na Allah,
idan Allah Ya nufi mutum da shi babu Wanda ya
isa ya hana Don haka Abubakar kaje ka maido da
matarka, kada ka bari mace tayi
rinjaye akanka“.
Hmmmm lol an kammala da iyayen suhailat
sauran mai ran qarfe hajia kaka koya zasu
kwasota da abubakar oho naku har kullum A,I,S
ke cewa mu tara donjin ci gaba da yaddah zataci
gaba da kasancewa
cont it
RIKON KAKA
CHAPTER 24
Abubakar ya amsa da, "Insha Allahu". Sannan
sukai sallama da Alhaji ya tafi abinsa cike da
qarrfin gwiwa ya dauki mota ya nufi Dandagoro
zuciyarsa cike da addu'a tare da fatan samun kan
Kaka ta bashi matarsa k0 ya samu natsuwar
zuciyarshi.
Karfe tara na dare ya iso qofar gidan Kaka, ya
faka motarshi ya’fito ya kukkulle' qofar motar,
sannan ya ‘nufi .cikin gidan ”zuciyarshi cike da
fargaba ya . soma jera sallama. Daga daki ya jiyo
muryar Kaka na
amsawa, don haka ya nufi dakin kai tsaye yana ta
faman addu‘a a zuciyarshi. Ya yaye labulen‘ dakin
ya shiga Kaka na daga kwance da hasken wutan
lantarki
Ya durqusa daga bakin qofa yana gaishe daKaka
cikin girmamawa-, tamkar babu abinda. ya faru,
ta amsa mashi cikin sakin fuska, abinda ya fara
bashi mamaki kenan wanda