Chapter 4 Reading GA IRINTA NAN!!! Fitinar Zuciya by Bintu Umar Abbale READ HAUSA Novels

GA IRINTA NAN!!! Fitinar Zuciya by Bintu Umar Abbale

Author :  Bintu Umar Abbale Category :  African Stories & Novels

Chapter   4 / 12

9K to 12K   out of 35.5K words

tsakar gida kisha iska sosai."

Girgixa kanta tayi tace."Khalid 'kyaleni anan yafi min kwanciyar hankali akan na fita Gwaggo ta fad'a min ba'kar magana."


Yace."Ummatu idan da sabo yaci ace ki saba da halin Gwaggo wata irin macace mai wani irin hali bayan haka kuma akwai rikicin tsufa a tare da ita." Girgiza kanta tayi tace."Khalid dama ai kai baka ganin laifin Gwaggo duk abinda tayi daidai ne a gurinka."


Girgiza kansa yayi yace."Ba haka bane wallahi Ummatu yanzu a matsayin na shekarun Gwaggo dole ayi mata uziri shiyasa kikaga duk abinda tayi nake biye mata saboda samun nutsuwarta ba wai bana san laifinta bane."


Tsaki taja tace."Duk da da akwai tsufa to da akwai iskanci wannan tsohuwar guda ce Khalid ni kad'ai nasan irin takaicin da take kuntuka min a gidan nan."


Yace."To kiyi hakuri dan Allah komai mai wuce wa ne gashi kema na siyo miki nama." Kar'ba tayi tana duba ledar tace."Sai da ka kai musu suka za'ba tukkuna ni aka kawo min saura ko."

Girgiza kansa yayi yace."Aa Ummatu duk d'aya ne wallahi dake da Gwaggon." Tace."Ai kamata yayi ka daina daidaita ni da ita tunda ni na haifeka idan kana neman albarka sai kayi min biyayya."

Yace."Ummatu dan Allah ki daina irin wannan maganar wallahi dake da Gwaggo duk daya kuke a gurina ke kika haifeni dole kina da martaba ta mussaman a gurina Gwaggo kuma itace ta raine ni har na girma Gwaggo bata san 'bacin raina komai ta samu nawa ne abinci wannan Gwaggo bata ci sai tare dani sai dana na tafi makaranta tukkuna muka raba kwano da ita Gwaggo takan iya hana cikinta abu ta ajiye min Ummatu kada ki manta Gwaggo itace tayi rabin dawainiyar Karatuna idan tayi sana'arta haka zata tattara kudin ta bani nayi hidimar makaranta dasu duk lokacin da nazo hutu sai ta bani kudi wata bukatar zata taso Gwaggo tayi Baba yayi a haka fa akayi ta tafiya har Allah ya kawo ni wannan lokacin da nake daf da kammala makaranta kinga kuwa dole na kyautata mata domin ta taka muhimiyyar rawa a rayuwata."


"Khalid wato ka sani a gaba kanayi min gori ko? to ko banyi maka hidima ba ai ba zaka iya biyana irin dawainiyar cikin ka da haihuwar ka ba, saboda haka kada ka sake sani a gabana kana kawo min wata banzar magana."

Shuru yayi yana jinta sai fad'a take masa yace."To Ummatu kiyi hakuri dan Allah insha Allahu ba zan kara ba." Shuru tayi masa ta mike ta nufi kicin plate ta dauko tazo ta zauna tana kokarin sa naman a ciki.....mikewa yayi ya fita daga gurin, nan ya samu Gwaggo a kashingid'e har taci ta gyatse tana gyangyad'i! zamansa a kusa da ita yasa da sauri ta tashi zaune tana fad."Khalid ka fito."
"Umm." kawai yace ya zauna ya dafe kansa, cikin kulawa tace."Menene yake damunka."? Shuru yayi yana girgiza kansa, 'kasa-'kasa tace."Kada ka damu da barazanar Sa'ida akan abinda kayi mata d'azu nan ta titsiye ni tanayi min jaraba wai sai ta kaimu kotu ni dakai."

Cike da mamaki! yace."Akan wane dalili zata kaimu kotu kuma me nayi mata da har take wannan furucin."? Da sauri tace."Yi magana a hankali Dan bana tsammanin tayi bacci."

Tsaki yaja 'kasa-'kasa yace."Me tazo tace anyi mata."? Gwaggo murya a 'kasa tace."Wai cewa tayi kana tare ta a soro kana lalubeta."

Yanda Gwaggo ta fadi maganar yasa dariya ta 'kwace masa yace."Ni sharri kawai tayi min abinda ma yau ban yini a gida ba." Gwaggo tace."To nima haka nagani ta shigo fuska a murtuke ta dinga jaraba dan har mahaifiyarka taso ta biye mata na shiga tsakaninsu, jin tana maganar kaimu gaban alkali yasa na bata hakuri nace zan ja maka kunne."

Yace."Gwaggo da kin sani ma baki wahalar da kanki gurin bata hakuri ba ni ba d'an iska bane da zatayi min irin wannan sharrin nima zan dauki mataki a kanta dan kafin ta kaini 'kara kotu ni zan kaita tunda tayi min sharri."! Sosai ya fitittuke yake kare kansa Al'amarin ya dinga bani mamaki! dan duk maganar da suke ina jinsu raina kuma ya 'baci sosai da naji Gwaggon na rarrashinsa har tana cewa ai dama tasan Sharrin nai masa ba zai aikata ba, naji tamkar na fita naci masa mutunci sai dai kawai na taushi zuciyata na hakura na kyaleshi ina tunanin irin matakin da zan dauka a duk ranar da ya sake kuskuran ta'ba jikina..



*Masoya a taimaka da sharing a gruops👏🏼*




*IDAN KINA BUKATAR KI BIYA KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE.....VIP #600 NORMAL#300 ACCOUNT.... 0542382124.....BINTA UMAR GTBANK....IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER.*
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 8:46 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*


*DUNIYAR HAUSA NOVEL*

_*Cannal ne na mussaman da zaku samu littafan hausa ko wane iri ne maza ku tafi YouTube kuyi sarcing d'in Cannal din zaku samu 'kyatattun littafai masu dadi! kada ku manta da sunan channal din *DUNIYAR HAUSA NOVELS*_


*5*
"Sa'ida tun kafin mu fito daga ofis nake miki wani irin kallo sai nake ganin kamar kina da damuwa a ganina bancanci ki 'boye min abinda ke damunki ba tunda nima duk wani abu da yake damuna bana 'boye miki."
Hauwwa ce kenan wannan maganar a lokacin da suke cikin motarta domin komawa gida.

Ajiyar zuciya na sauke nace."Wallahi Hauwwa ba 'karya kikayi ba ina damuwa na kuma rasa yanda zanyi na warware ta al'amarin dai sai godiyar Allah.

Murmushi tayi tace."Haba 'kawata abokin kuka shi ake fad'awa mutuwa ki fad'a min damuwarki ko akwai shawarar da zan iya baki."


Murmushi nayi nace"Dama ina tunanin fad'a miki kikayi magana Hauwwa kin san wannan yaron na gidanmu ko.''?

Tace."Khalid ko bashi kike nufi ba."? Nace."Shi nake nufi Hauwwa Khalid ya takura min a gida wallahi wai saboda tsabar rashin mutunci da raini kamar ni zai duba yace yana so."


Hauwwa dariya tasa tana kallona da mamaki a tare da ita, tace."So.''? Ta'be bakina nayi nace."Kwarai kuwa Hauwwa Khalid sona yake dan duk wasu alamu ya nuna harda fad'awa Gwaggo wai zai aure ni yaron da a gabana ya girma meye nasa ban sani ba amma da yake yanzu yaga ya fini tsayi da girman jiki shine yake furta min wannan kalma.''


Hauwwa draving take tana girgiza kanta tace."Sa'ida Khalid yayi tsaurin ido amma kuma idan an duba tarihi za'a ga baiyi tsaurin ido ba tunda hakan kamar sinna ce mai zai hana ki aureshi tunda hakan ba haram bane."


Wani irin kallo na watsa mata "Hauwwa wannan wace irin magana kikeyi me zan aura a tare da Khalid bana tsammanin zan iya auran 'karamin yaro a yanda nake a haka nafi bukatar cikakken namijin mai kima wanda yasan rayuwa amma auran yaro mai 'karanci shekeru akwai kalubale a ciki."

Murmushi tayi tace."Sa'ida wane 'kalubale kike hangowa a tattare da auran Khalid? Yaro kyakykyawa da siffar mazantaka Khalid bai da makusa matsalar kawai kice bashi da kudi sannan kuma bashi da aikinyi in banda haka menene abin'ki a tare dashi."?


Girgiza kaina nayi nace."Hauwwa Ra'ayi na ne kawai haka bana sha'awar auran k'ananun yara dan sai nake ganin kamar basu san meye aure ba wannan dalilin yasa gabadaya bana kulasu nafi tsayawa na saurari magidanta masu iyali da suka dad'e a cikin harkar."


Hauwwa ta'be bakinta tayi tace"Sa'ida mazan fa suna suka tara kamar yanda matan ma suka tara duk kallon kitse kike musu ni zan fad'a miki wannan kinga dai ni bazawara ce ko to wallahi ba zan auri namiji ba sai na tsaya na duba tukkuna saboda ni kad'ai nasan bala'in dana shiga a gidan aurena kafin na fito."


"Hauwwa kenan kin san kowa da tunaninsa amma gaskiya bana yi miki sha'awar auran 'karamin yaro domin kinfi 'karfinsu ki auri namiji daidai dake dan Allah kada kibi son zuciyarki daga baya kizo kina nadama."


"Sa'ida kin san Allah ko d'an 20years ne yazo da niyyar aurena na gamsu da shi sai na aureshi domin hakan ai ba haramun bane akan naje na auri babba nazo na sake shiga wata matsalar gwara na auri yaron na cigaba da rainonsa har yayi 'kwari."


Cikin wani irin yanayi na mamaki nake kallonta.....tasa dariya da fadin"Kina mamaki ne.''? Girgiza kaina nayi nace."Sosai kuwa idan kin auri dan 20years kin auri d'an cikin ki ko ba haka bane."

Still tana dai dariyar tace."Aa Sa'ida bana san sharri a ina na haifi dan shekara ashirin Walid yarona na farko duka shekaransa tara Safna kuma shekararta bakwai."

Nace"Kin gani ai tunda kika haifi dan shekara tara kin zama uwa me zai baki sha'awa a gurin auran karamin yaro dan shekara ashirin.


Hauwwa baki ta ta'be tace."Ke Sa'ida bari dai na fito miki a mutum! ni Hauwwa ina da tsananin bukata wannan dalilin ne ya janyo mutuwar aurena domin babansu Walid bashi da maida hankali a wannan gurin yafi mayar da hankalinsa gurin neman kudinsa nasha wahala a hannunsa Sa'ida ina fada miki Walid da Safna tsanani rabo ne yasa aka haife su saboda babansu sai ya shafe wata biyu ko uku bai had'a shimfida dani ba, kullum yana yawo a jirgi sai kace tsunsu shi dai ya samu kud'i ni kuma ya barni cikin wahala da bukata wannan dalilin yasa na yankewa kaina shawarar yanke zama dashi dan ba zan iya da halinsa ba."

Na jima ina mamakin maganarta kafin nace."To Hauwwa shi 'karamin yaron da kike 'kulafuci a kansa kina da tabbacin zaki samu abinda kike bukata mazan fa duk kusan haka suke tunda dai ba 'kwan'kwasawa zakiyi ki gane daidai dake ba ."


Murmushi tayi tace."Sa'ida ana ganewa wallahi shiyasa ai nace miki kafin nayi auran sai na tantance tukkuna kuma ina rokon Allah ya bani daidai dani."


Nace."Ta ina zaki gane jarumin namiji Hauwwa." murmushi tayi tace."Sa'ida kenan." draving d'inta ta cigaba dayi ta barni cikin tunani nima irinta ce mai yawan sha'awa da son soyayya shiyasa gabad'aya na shiga tunanin ta inda zan gane jarumin namijin da zai iya daukar lalurata......Alhaji Nura ne ya fad'o min a rai na dinga tunanin siffofinsa dogo ne mai ma daidaicin jiki kwayoyin idanunsa jajaye ba irin na Khalid ba da kullum suke da haske, nace"Hauwwa tunda kin'ki fad'a min ai na gane."

Tace."Yawwa ai dama so nake ki gane sai kiyi min bayani." Dariya nayi nace."Kamar dai Alhajina ina nufin Alhaji Nura ya cancanta da wannan sunan.

Shuru tayi tana nazari tace."Eh gaskiya kam kwayoyin idanunsa ma sheda ne ina miki sha'awar auransa gashi yana bala'in sonki to amma ai matarsa ce matsala Sa'ida a rayuwata bana san kishiya wallahi."


Ajiyar zuciya na sauke nace."Hauwwa ni wallahi kishiya bata firgita ni za'bin Allah kawai nake nema idan Allah ya kaddara Alhaji Nura ne mijina babu ruwana da matarsa tunda ba itake aurena."

"Hakane Sa'ida to ina rokon Ubangiji Allah ya za'ba mana abinda yafi alkairi." na amsa da ameeeen ya rabbi......Da wannan hirar ta sauke ni a bakin layin mu ta juya kan motar hannu na daga mata da fadin"Nagode 'Kawata sai gobe idan Allah ya kaimu." ta amsa da "Ameen Allah ya kaimu lafiya." sai da ta bar gurin sannan na nima na bar gurin........


Tunda na hangoshi a zaune a kofar gidan naji gabana ya fadi! hakika Khalid ya zame min 'karfen 'kafa, kici-kici nayi da fuskata, kafin na karasa naga ya mi'ke ya shiga gidan, ajiyar zuciya na sauke naji dad'in hakan saboda na tsani kallon da yake min......Ina shiga soran naji an fizgo hannuna kafin nayi aune naji ya ru'kun'kume ni ta baya! numfashinsa naji yana fita da sauri da sauri ya d'ora kansa a kafad'ata sosai ya ri'ke 'kuguna! gabana ya dinga fad'uwa! murya na rawa nace."Khalid wane irin iskanci ne wannan? zaka sake ni ko sai nai maka rashin mutumci d'an iskan yaro kaw......Kafin na 'karasa naji yayi cikin bayan k'yaure ('kofa) dani, a zabure! na juyo fuskokinmu suka had'u guri guda!

Hawaye ne naji suna kokarin kufce min wane irin fitinan nan yaro ne wannan? matseni yayi a kirjinsa yana kiran sunana cikin wani irin sauti "Aunty Sa'ida kina so na mutu ko? ki taimakawa rayuwata kada ta salwance." hawayen takaicin da nake kokarin dannewa sune suka kufce cikin rawar murya nace."Khalid sake ni."

"Um!um! Aunty naji dadin rungumeki ki bari na samu nutsuwa ina cikin tsananin damuwa."
Yafad'a yana goga gefan fuskarsa a tawa.

Shuru nai jikina gabad'aya ya mutu ko yaya nayi motsi da niyyar kwace jikina zai sake matseni sai wani irin nishi yake!


"Khalid ni kake wa wannan iskancin ko? ni kake matsewa a soro saboda baka da mutunci Khalid."! murya a sha'ke nake magana.


" Aunty Sa'ida har abada babu tozarci a tsakani na dake abinda kikayi min d'azu ya 'bata min rai ko abinci na kasa ci Aunty me yasa zaki za'bi wancan Alhajin ki barni me nai miki ko ni ba namiji bane."
Cikin sanyin murya yake maganar yana yawo da hannunsa a jikina.


"Khalid ka daina mafarkin abinda ba zai faru ba kasan Allah duk maitarka akaina sai ka hakura dan ni nafi karfin'ka kaje ka nemi daidai da kai."


Fuskata ya d'ago yana kallona, naga idonsa yayi jajawur a take tsigar jikina ta tashi! fuskata na fizge! da sauri na daga hannu da niyyar kwad'a masa mari! yayi saurin ri'kewa.

Girgixa kansa yake Cikin 'kunar zuciya yace."Ni nafi karfin ki mare ni auntyna! na amince ni maye! ne amma akanki aunty Sa'ida ba zan fita a rayuwarki ba sai na tabbatar da cewa kin zama mallakata mu zuba ni dake."!

Tsaki naja na tureshi da fadin"Shashasha mara hankali kawai." gabana ya tare cikin 'bacin ran da banta'ba ganinsa dashi ba yace."Kada ki 'kara kirana da shashasha zan baki mamaki."

"Me zakayi min."? nafada ina watsa masa harara......Murza yatsun hannunsa yayi yace." Sai ranar da kika 'kara kirana da kalmar sannan ne zakiga abinda zanyi."

"Mtwwws! tsaki naja na ra'ba ta gefansa na shiga gidan.....Ajiyar zuciya ya sauke bayan shigewarta gidan ya shiga shafa kirjinsa yana lumshe ido har yanzu yana jin tudun nonowanta a kirjinsa, cikin mutuwar jiki ya fita daga gidan.


" To shikkenan Uwale zan duba maganarki wallahi dama nima sai da nayi wannan tunanin ace yarinya kwata-kwata bata so ayi mata maganar aure bayan tana da mane ma dole ne a nemi taimako." Uwale na kokarin magana na shiga dakin, sai ta washe baki da fadin"Babban mace hakima kin dawo kenan sannu lallai kin dauko rana."

Sama-sama na gaisheta na cire hijab din jikina na fita daga dakin na tsani alaqar Gwaggo da Uwale ko kad'an......Bayan fitarta Uwale tace."To shikkenan Gwaggo sai kinzo ina sauraranki." Gwaggo mi'kewa tayi domin yi mata rakiya tana fad'in "Insha Allahu gobe zanzo sai muje Allah dai ya rufa asiri." kallo na bisu dashi ina tunanin inda zasuje....Gwaggo ta dawo gidan tana kallona a fakaice kafin ta shiga dakin, mikewa nai nabi bayanta domin na kafa mata hujjata akan irin iskancin da Khalid keyi min...


*Masoya a taimaka da sharing a gruops👏🏼🥰*



*IDAN KINA SO KI BIYA KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE.....VIP GRUOP...600 NORMAL 300 ACCONT...0542382124.....BINTA UMAR GTBAK IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER*
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 8:46 AM] 💜: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️*

*Pegen na yau naki ne*
_*Gwanata FATIMA SUNUSI RABI'U Matashiyar marubuciya mai fasaha da amfani da basirar ta a inda ta dace Ina kaunarki Takwara kamar yanda kike 'kaunata💗😊*_




*7*
Cikin nutsuwa na kalleta tana ta shiryawa nace."Wai Gwaggo ina zakije ne da sassafe haka."? Tana shafa mai a kafafunta tace."Wallahi ugunwa zamuje da Uwale amma ba zan dad'e ba zan dawo dan ina da aiki a gabana Salisu mai kanti yace nayi masa lagwani zai siya."

Nace."Gwaggo wannan wace irin unguwa ce da zakuje da safe karfe bakwai da rabi kifa duba lokaci ki gani ko karyawa bakiyi ba amma kina kokarin fita."

"Kinga Sa'ida kada ki takurawa rayuwata ina ruwanki da inda zani zaki dameni da surutai.'' Nace." Babu ruwana amma bari naje na fad'awa Baba Iro cewa Uwale zata jaki yawo."

Da sauri nayi yun'kurin fita ta ri'ke gefan rigata da fad'in "Dawo na fada miki inda zamuje." komawa nayi na zauna ina kallonta, tace."Jikar Uwale ce take aljanu shine zamuje mu kar'bo mata magani gurin wani malami."


Cike da mamaki nace."Gwaggo Uwale ta fara d'ora ki a turba mara kyau ko yanzu tsofai-tsofai daku ina ku ina zuwa gurin malami."


"Sa'ida kada ki fassara mu da wata manufa bakiji abinda na fad'a ba jikar Uwale Nafisa itace take aljanu shine zan rakata ta kar'bo mata magani."

Nace."Dole sai kin rakata ita bata san hanya ba."? A tausashe tace."Tasan hanya mana nima ai inso malam d'in ya taimaka min."


"Me yake damunki da zakije gurin malami ya taimaka miki ba zakiyi alwala ki roki Allah ba."

shuru tayi bata bani amsa ba, nace." Gwaggo ki kiyaye kada Uwale ta jaki gurin bokaye da girma da mutuncin ki me kike nema a duniya wanda ba zaki rok........."Sa'ida wai ni sa'arki ce ne da zaki zauna kina kokarin fad'a min maganar banza waye yace miki gorin bokaye zamuje."?

Ganin yanda ta fusata yasa na sassauta murya "Gwaggo kiyi hakuri idan kinji shaushin maganata halin Uwale na sani na rashin tsoron Allah da san duniya."


"To naji wuce kiyi tafiyarki nama fasa zuwa tunda zargin da kikeyi min kenan." Murmushi nayi na cigaba da shirye-shiryen tafiya makaranta.......Ummatu ce ta daga labulan dakin ta shigo da sallama a bakinta, dukkaninmu muka amsa mata ta ajiye jug din kunun dake hannunta tace."Gwaggo ina kwana."? Ciki ciki ta amsa tana dauke kanta

4 / 12