* MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSO* ~~~~~~~ *'Kir'kirarren labari ne kuma ba'ayi dan aci zarafin wani ko wata ba. Wanda yaga yayi dai-dai da yanayi na labarinsa to a rashin sani ne* ~~~~~~ *NASIHA* ```A wasu lokotan sauyi na rayuwa yakan zowa mutum. misali da farko kana cikin 'kunci sai Allah ya "saukar maka da farin ciki wanda zai sa ka manta ba'kin cikin ka na baya. Idan kaga haka ya kasance da kai/ki to tabbas ka/ki ji'banta dukkanin al'amuranka ga Allah. Na biyu kuma kana cikin farin ciki katsaham! Ubangiji sai ya saukar maka da ibtila'i na rayuwa gabad'aya al'amuran ka su dagule! To idan irin haka ta kasance da kai sai ka nutsu kayi tunanin shin wane laifi kayi wanda Allah ya saukar maka da ibtila'in rayuwa, kada ka/ki ce bari kaje gurin malaman duba su duba maka ko wani ne yayi maka asiri daga ka/kin aikata hakan shikkenan ta'bewa da lalacewa ta tattara a kanka ko a kanki, idan ka/ki fad'a ko wane irin bala'i na duniya Ubangiji kad'ai zaka/zaki fuskanta da matsalarka lokaci guda zai magance maka/miki, Allah ba'a had'ashi da abokin tarayya! Idan ka kuskura ka had'a Ubangiji da wani to zaka/zaki" dawwama cikin 'kunci da lalacewa har 'karshen rayuwar ka/ki.``` *SADAUKARWA GARE KU* 'Yan Uwa Rabin Jiki *SADDIQA UMAR ABBALE* *HALIMATU UMAR ABBALE* *NAJA'ATU UMAR ABBALE* ~~~~~~~~~~~~~ *1 """Innalillahi wa'ina ilaihi rajiun.""! Abinda Baba Talatu tafad'a kenan ta kalli Saddiqa dake gefe a tsaye tana" "hawaye tace"" Yi sauri ki d'ebo ruwa suma tayi."" Saddiqa ta futa daga d'akin da sauri, karo suka ci da Baba Malam da Babban d'ansa Alhaji Magaji."" Baba Malam yace."" wato dai har yanzu Kuka kuke yi ko da alama dai kuna so ku hana Halima ta kwanta lafiya a kabarin ta."" Tana girgiza kai had'e da 'kokarin mayar da hawayen idonta tace""Baba Malam mun daina kuka Yaya Naja'atu ce tafad'i ta suma shine Baba Talatu tace na d'ebo ruwa."" Da sauri Baba Malam da Alhaji Magaji suka shiga d'akin. ita kuma ta" "futa da saurin gaske, ruwa ta d'ebo cikin kofi ta shigo d'akin dashi." Baba Malam dake tsugune kusa da Naja'atu yana mata addua ya kar'bi ruwa ya shiga yayyafa mata a "fuska, Baba Talatu hawaye kawai take sharewa tana girgixa kanta." Baba malam sai da ya yayyafa mata ruwan sau uku sannan ta saki wata ajiyar zuciya mai kar'fi! idanunta "ta shiga kiftawa, sai ta mi'ke zaune da sauri ta shiga rarraba idanunta a kansu." "Baba Talatu ta ri'ke hannunta tana fad'in ""Naja'atu kiyi hakuri kada ki jazawa kanki lalura."" Ihu! ta" "zumduma! tasa hannu ta toshe kunnuwanta jikinta na wata iriyar kyarma! tace""Baba Talatu kunnuwa ba zasu iya d'aukar wannanmaganar taki ba! a ina aka ta'ba haka *Uba ya Auri 'Yarsa* ashe dama dake da Baba malam dashi kansa Abban nawa dukkanin ku maguzawa ne ku baku san addin Kafin ta" "'karasa Alhaji Magaji ya kwad'a mata mari! yace.""Ke ki nutsu ki shiga hankalin ki bama son shirme da" "shashanci ki saurara ayi miki bayanin yanda al'amura suke.""" "A zabure! ta mi'ke tsaye! kamar wacce zata tada iska tace""Baba Magaji ni bazan fuskanci komai ba ba" "kuma zan nutsu ba, saboda ni ba kafura bace wallahi sai na kashe kaina idan kuka d'aura min aure d Ubana, wai baku ji sunansa bane Abban Naja'atu fa sunansa amma shine zaku daura mun aure dashi! to" dukkaninku sai na kaiku *Hizbah!.* Ta'karashe maganar tana wani irin kuka mai cin rai. "Baba Malam ya goge guntin hawayen idonsa ya ri'ke hannunta da fad'in ""Auta zauna ni da kaina zan" "warware miki abunda baki sani ba."" Fuzge hannunta tayi tana 'kokarin tsallakeshi ta wuce! Alhaji Magaji yayi sauri tare mata hanya Yace.""Naja bakya jin magana ko? To shikkenan idan baki kaimu *Hizbah*" "bakya 'kaunar Allah."" Yafad'a babu wasa a tare dashi." "Hannunsa ta ri'ke jikinta sai mazari yake tace""Abba Magaji ka duba maganar nan da kyau fa! Kayi duba" "na tsanaki! ya za'ayi dan kawai Mamanmu ta mutu sai suce zasu d'aura min aure da Ubana wace irin rayuwa ce wannan.""!!! Tafada cikin wani irin sauti!! Shima a fusace! Yace.""Wai ke waye ya fad'a miki Alhaji Abbas Ubanki ne.""!? Shuru tayi tana binsa da wani irin kallo! bakinta sai rawa yake yi. da kyar ta iya bud'e bakinta tayi magana. ""Baba Magaji bangane maganar ka ba.""! murya na rawa tayi maganar," "Baba Malam ya zaunar da ita kusa dashi hannunsa cikin nata ya rike sosai yana kallonta, tausayi take bashi sosai, tabbas yasan dole ne ta shiga rud'ani da tashin hankali sakamakon bayyanuwar abinda yake" rufe tsayin shekaru goma sha shida! da suka wuce. Wanda ta d'auka a matsayin mahaifinta dashi ake "maganar d'aurin aure a tsakaninsu, babu shakka duk wanda ko yaji wannan lamarin dole ya shiga halin" d'imuwa da tashin hankali 'Dakin ne yayi shuru na tsayin mintina uku kowa jikinsa yayi sanyi mussaman Naja'atu wacce take jin "wata irin fargaba da fad'uwar gaba, tunda Abba Magaji yayi furucin cewar ba Abba Abbas ne mahaifinta ba take wata zabura tana rarraba idonta a kansu bakinta motsi kawai yake tana so tayi magana amma ta rasa me za tace! fashewa tayi da wani kukan tana kallon Baba Malam da kansa yake sunkuye sai zufa yake gogewa, tace""Baba malam kuna so nima na mutu ko? kuna so kamar yanda kuka rasa mamana nima ku rasa ni ko ? zuciyata daf take data daina aiki sakamakon bala'in da kuka jefata a ciki! Baba Magaji yace wai Abbana bashi ne Ubana to shikkenan sai ku fad'a min wanene ya haifeni.""? Murya na" rawa ta 'karasa maganar. "Baba Malam ya d'ago kansa a nutse yace.""Naja'atu Nine Ubanki ni na haife ki Alhaji Abbas Uban ri'kon ki" "ne kuma miji ga 'yar uwarki Halimatu."" wani irin kallo ta shiga yi masa tana girgixa kanta sai hawaye ya wanke mata fuska! murya a sanyaye tace""Baba malam ya akayi haka? ya kuka yi mun wasa da hankalina? ni ban yarda kaine mahaifina ba, Abba Abbas shine Ubana shi na sani tunda na taso shine yaci dani yasha dani ya tufartar dani ya tsaya a kaina nayi karatu kuma shi nake so ya aurar dani ga mijin dana za'bawa" "kaina.""! Ta'karasa maganar cikin yarda da abinda take fad'a." "Abba Magaji ya fusata! sosai ya bud'e baki zaiyi magana Baba malam ya d'aga masa hannu yace.""Kada" "kayi mata tsawa ko ka hantare ta, dole ne dama haka ta kasance da ita damu bakid'aya, ha'kika mutuwa itace ta janyo mana wannan tashin hankalin dan da Halimatu na raye to babu shakka Naja'atu zata cigaba da zama a matsayin 'yar data haifa alhalin kuma 'kanwa take a gareta, Yanzu zamu bari ta nutsu tukkuna zuwa dare sai mu sake wani zaman domin mu sanar da ita abinda ya faru a baya wanda bata sani ba."" Abba Magaji ya sauke ajiyar zuciya a nutse yace.""Shikeenan Allah ya za'ba abinda yafi alkairi.""" Baba Malam ya amsa da amin kana ya mi'ke suka futa a tare. "Suna futa, Naja'atu ta kalli Baba Talatu tace""Baba dan Allah dan annabi kada ki bari al'amarin nan ya" "tabbata, ke macace ce mai hankali da sanin ya kamata kuma kina zuwa isilamiyya kin san dai haramun ne Uba ya auri 'yar sa ko.""? A zauce! take maganar." "Baba Talatu tace""Naja'atu Alhaji Abbas ba Ubanki bane an fad'a miki Mijin Yayar ki ne Halimatu Allah ya" "ji'kanta, Alhaji Abbas kinga wacce ya haifa nan ita da 'yan uwanta su Mussadiq.'' Ta nuna mata Saddiqa dake zaune a kusa da ita." "Wani irin kallo ta shiga binsu dashi tana girgiza kanta, ta rasa a'ina zata ajiye wannan babban al'amari a" "cikin zuciyarta, *Abbah Abbas* ba shine ya haife ta ba *Baba malam* ya haife ta? anya kuwa da gaske suke wannan maganar ko dai kawai suna so bukatarsu ta biya ne gurin ganin sun d'aura mata aure da" *Ubanta* tabbas dole ne ta nemawa kanta mafita dan ita kam bata yarda da wannan maganar da suke ba. "Tana kallon Baba Talatu da Saddiqa suka suka futa daga d'akin, ta shiga girgiza kanta tana masifar" "mamakin a'lamarin, kwanciya tayi kan tabarmar dake shimfid'e a dakin ta shiga tunano rayuwar ta ta baya tare da mutanan data dauka a matsayin iyayenta." * MADADI!!! * _(Ba Haram Bane!!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi._ ~~~~~~~~ ~~~~~~~~ *SADAUKARWA GA DUK WANI A HALINA DAKE CIKIN WANNAN UNGUWA * *2* "*'Kofar Na'isa* Unguwa ce mai cike da d'umbun tarihi, duk wanda ya kwana ya tashi a cikin birnin kano" "ya san da zaman unguwar. 'kofar na isa unguwa ce ta malamai masana addini da kuma 'yan boko masu aiki da iliminsu, duk wanda yake mu'amula da d'an cikin unguwar zai gane cewar suna da wani irin quality wanda Allah yayi musu, saboda sun iya mu'amula da mutane sosai! akwai masu kudi a unguwar akwai marasa karfi a ciki, dai-dai gwargwado masu rufin asirin dake cikin unguwar suna taimakawa marasa shi mussaman da azimi suna hidima sosai da sosai da wuya kaji ance maka ga wata hatsaniya ta tashi a unguwar irin ta *Daba!* ko kuma *Sace-sace* dai-dai gwargwado suna bawa yaransu tarbiya" had'e da ilimin addini dana boko! Alhaji Sama'ila mai kwano wani attajirin mai kudi ne a cikin unguwar wanda yayi suna sosai dan idan "kana neman gidansa daga bakin titi ka ambaci sunansa za'a nuna maka Alhaji Sama'ila mai kwano mutum ne mara ganin 'kyashi mai kaunar dan uwansa da ma'kotansa, Yana da 'yaya Uku kacal wanda" "matarsa Hajiya Abu ta haifa masa su, Biyu maza mace d'aya, amaryarsa mai suna Hajia Rabi bata ta'ba" haihuwa ba tsayin shekarun da sukayi a tare! Yana zaune da ita haka dan shi mutum ne mai mi'ka al'amuransa ga Allah yasan tabbas Allah ne ke bada haihuwa kuma shine yake hanawa. "*Ramlatu* itace babba a cikin 'yayansa sai wanda yake bin ta, Abbas sai Alhasan shine na karshe! tunda" "su Abbas suka taso a cikin unguwar nan suka ga yanda mahaifinsu ke mu'amula arziki da makotansa sai suma suka fara kwantantawa, hakan yayi wa mahaifin nasu dadi sosai ya kuma 'kara nuna musu cewar hakan da sukeyi shine dai-dai dan cikin jinsin mutunan da Allah ya hallita a duniya babu wanda yafi wani a gurinsa sai wanda yafi bauta masa, kada su nuna sunfi karfin yin mu'amula da wanda suka fi rufin asiri, to babu shakka watarana Allah zai iya 'kwace damar dake hannunsu ya mi'kawa wanda suke ganin bai isa ba. Wannan dalilin ya sanya suka saki jikinsu da kowa suke mu'amula a cikin unguwar tamkar" sauran mutane. "'Karamin gida ne madaidaici mai kofa gami da dakalin siminti a kofar gidan, gidan na kallon gate din" "gidan Alhaji Sama'ila hanya ce kawai ta raba tsakaninsu! Malam Baba shine mai wannan gidan, kamilin mutum nitsatstse mai kamala da dattako, malam baba mutum ne shi mai yawan ibadah da karatun al'kur'ani kusan duk azimin yana zaman tafsiri a kofar gidansa, inda Alhaji Sama'ila ke sawa ana fito da sadaka daga gidansa, akwai jituwa mai kyau a tsakaninsu dan sai nace halinsu ne yazo daya na gudun duniya shiyasa suke zaune lafiya da kowa, Alhaji Sama'ila ya dauki ragamar gidan Malam Baba a hannunsa ba wai dan shi malam din ya gaza ba Malam na futa sana'arsa kuma sa'i da lokaci al'amajiransa na kawo masa abun arziki gidansa babu yunwa ko kad'an! malam nada 'Yaya Uku wanda suka haifa tare da matarsa Baba Talatu Babban cikinsu shine Adamu wanda yaci sunan mahaifinsa sai suke kiransa da Magaji, Halimatu itace ta biyu sai kuma Naja'atu da tazo a karshe! Lokacin da suka haifeta har sun cire tsammani da sake haihuwa sai kuma Allah ya kawo cikinta, lokacin Halimatu na daf" da kammala secondary skuul lokacin tana da shekara goma sha shida a duniya. Tsakanin Abbas da Magaji akwai jituwa sosai suna abota mai kyau da tsabta komai nasu tare sukeyi "karatu tare su d'inka kaya iri daya hula iri d'aya takalmi iri daya kai hatta da agogo iri daya suke daurawa! Sai kuma Allah yasa shekarunsu suka zo daya da juna yanzu haka suna matakin shekaru talatin da d'aya koda biyu Lokacin ne kuma iyayensu suka fara yi musu maganar aure dan sun riga sun mallaki hankalin kansu! kuma suna zuwa kasuwa suna harkokinsu, Alhaji Sama'ila yanzu ba ya fita kasuwa sosai su ya d'ora kan harkokinsa na yau da gobe! Alhaji Sama'ila nada shaguna sama da talatin a cikin kasuwar sabon gari kuma dukkanin rumfunan sa harkar siye da siyarwa akeyi a ciki, suna harkar kayan rufin gida da kofofi da ta gogi sannan kuma yana da gidajen bulo suna buga bulo da harhad'a intar lock da ties, mutane da yawa naci da sha a karkashin wannan bawan Allahn, to ganin 'Yayansa sun kai munzali ne yasa ya d'ora su kan harkokinsa na kasuwa kwata-kwata baya nuna bambanci tsakanin Abbas da Magaji Abinda zaiyi wa d'ansa Abbas shi yake wa Magaji, har jama'ar unguwa na surutu kan cewar ba haka kawai Baba Malam ya barshi ba wasu suna gani kamar yayi masa asiri ne domin ya mallake shi shida dukiyarsa, wannan cece kucen da mutane keyi bai dameshi ba, dan saboda yasan Malam baba ba zai" ta'ba cutar dashi da zuriarsa ba. Mama Ramlatu babbar Yaya gasu Abbas tayi aure a cikin unguwar dan gaba dasu kadan cikin unguwar "Tudun wuzurci! wanda ta aura yana da rufin asiri dai-dai gwargwado amma tana da kishiya, Ramlatu wata irin mata ce mai izzah da ta'kama! bata da hali mai kyau! Tayi ta wulakanta kishiyarta kasancewar ta yar talaka gorin yau daban na gobe daban! a duk sanda Alhaji Sama'ila zaiyi mata aiken kud'i ko kuma tufafi sai ya had'a da kishiyarta kafin ta bawa kishiyarta sai ta gama yi mata gori sannan! Ita kuwa da yake mai hakuri ce sai dai kawai ta girgiza kai ta kyaleta, gabadaya Ramlatu bata dauko halin mahaifinta" da 'yan uwanta ba. "Lokacin data haifi 'Danta na fari! sosai Mahaifinta ya gatantata daki guda aka cika mata da kayan barka," "shi kuwa maigidan mota guda ta kayan abinci ya sauke masa, aikuwa Ramtalu ta samu abunda take so shiga take tana fita tana sakin habaici da gori! Cewar da abincin ubanta mutum ke rayuwa sannan kuma da tufafin ubanta mutum ke tun'kaho! Allah Sarki Sakina kishiyarta tasan da ita take, sai ta shiga daki taci kunanta ta koshi kuma ta dauki aniya kan cewar idan mijin nasu ya dawo zata fada masa abinda ke faruwa a gidan dan gaskiya ita ta gaji da wulakancin da matarsa keyi mata, gabadaya ta lura Ramlatu bata san mutunci ba ba kuma tasan mai kyautata mata ba, tunda ta haihu take hidima da ita ta kasa zama ta hutu kullum a tsaye take amma babu sannu bare nagode kullum cikin fada mata bakar magana" take to gaskiya ta gaji hakurinta yazo karshe kudi ai ba hauka bane. Maigidansu na dawowa bayan yaci a binci ya huta sai ta shiga fada masa abubuwan da suke ta faruwa a "gidan wanda shi bai san dasu ba, tabbas ransa ya 'baci sosai kuma ya sheda halin matarsa Sakina tana da hakuri sosai da kawaici ba zata takali Ramla da rigima ba duk da cewar itace Uwargida amma ta hakura da komai burinta ta kawo zaman lafiya da daidaito a gidin! Yace.""Kiyi hakuri insha Allahu zan sameta nayi mata fad'a amma kada irin haka ta sake faruwa kiyi shuru da bakin ki duk abinda ke faruwa tsakanin" "ki Ramla ki sameni ki fada mun zanyiwa tufkar hanci."" Tace.""To insha Allah.""" Lokacin da ya shiga dakin Ramlatu tana zaune gefan gado taci uwar kwaliya da less an turo dauri gaban goshi kana kallonta zaka fahimci 'Yar Alaji ce hannunta da kunnata gami da wuyanta duk Gold ne sai walwali take...Zama yayi kusa da ita ya mika hannu ya kar'bi yaron dake hannunta da ta gama bashi nono ya tofa masa addua kana ya kwantar dashi ya fuskanceta. Babu cikakkiyar walwala a tare dashi "yace.""Yanzu Ramlatu abinda kikewa Sakina a gidan nan ya dace.""!? Wani irin shan kunu tayi ta kumbura fuska tace""Me nayi mata ashe! zaunar da kai tayi tana fad'a maka karya da gaskiya ko.""? Yace.""Abinda Sakina za tayi nasa ni haka kuma abinda Ramla za tayi nasa ni dukkanin ku nasan halin ko wacce ba wai ina so nace Sakina tafi ki a gurina ba A'a dik matsayin ku d'aya a zuciyata, amma ki sani abinda kikewa abokiyar zamanki bai dace ba! wace iri ce ke mai manta alkairi? menene Sakina ba tayi miki ba, ina cewa gabadaya sai da kika daina girki sai dai ta dafa ta kawo miki har d'aki kuma hakan bai hanaki kwana da miji ba! idan muguwa ce ai zata hanaki ki kwana dani ba tunda itace take girki amma ta dafa ta baki kici kina kwance kuma ki rasa sakayya da zaki mata sai irin wannan.""!! Fashewa tayi da kuka tace""Shikkenan to ai ba sai ka futo fili ka nuna kafi kaunarta a kaina ba, amma meye haka daga zuwa babu tambayar ba'asi sai ka kama wasu maganganu ai bani ce nace tayi min girki ba ita taga zata iya ta dauka tayi ni ba burgeni tayi ba, kuma koda ba tayi min girki ba zansa a turo mai aiki daga gidanmu tazo ta kula dani har" "na haihu.""" "Yace.""Ni dai na fad'a miki wallahi duk sanda kika 'kara ci mata fuska ko kikayi mata gori kan wani abu da" "aka kawo shi gidan nan sai ranki ya 'baci!! Cikin 'bacin rai tace""To ai shikkenan tunda uwata ce ita sai na kwanta ta takani saboda tana da daurin gindi a gurinka, akan me? kai da ita kuna cin arzikina amma kuma kuce sai nayi muku biyayya wallahi ba zai yuwu ba.""""! Takarasa maganar tana buga cinya.""! Cikin fusata yace.""Zanyi maganin ki ai shashasha mara tunani meye abinci da kike gori a kansa, meye kuma tufafi wanda zasu lalace su barki da mutum! to zanje na samu Alajin da kaina zan fad'a masa bana bukatar k'wayar abincinsa a gidana ko ya aiko dashi na dawo sai an mayar."" A fusace ya mike ya futa daga dakin Shuru tayi tana tunani addua take kada Allah yasa yaje gurin mahaifinta da wannan" maganar tabbas tasan idan yaji matsalar daga gurinta ne to babu shakka ranta sai ya 'baci. Aikuwa misalin karfe biyar da rabi na yamma ta fito daga wanka kenan wani yaro ya shigo gidan yana "fadin ""Wai Ramlatu tazo soro mahaifinta ne yazo." "Gabanta ya fadi da sauri tasa kayanta ta futa da tabarma a hannunta, tana zuwa soron sai taga Sakina a" "durkushe suna gaisawa da Alhajin, shuru tayi tana jinsa yana bata hakuri dangane da abubuwan da suke faruwa, koda ta gaishe shi 'kin amsawa yayi ya rufe ta da fad'a sosai yace kuma ta bawa abokiyar zamanta hakuri! tana kuka ta shiga bawa Sakina hakuri! Tace "" Babu komai ta mike ta shiga gidan, Alhaji ya kalleta da fad'in ""Wallahi Sakina duk sanda mijinki ya sake kai 'karar ki gurina to babu ni babu ke! dama ashe mugun hali ne dake ko? to na kara jin na kawo muku wani abu gidan nan kiyiwa wani gori ranar sai na 'bata miki rai! Hakuri take bashi tana share hawaye, ransa ya a 'bace! ya futa daga soron ya barta a tsaye hannunta ri'ke da tabarma.......To tun daga ranar Sakina ta samu lafiya a gidan Yanzu Ramlatu ta daina yi mata gori da kallon banza amma dai duk da haka idan 'yan wulakancin na kusa tana" ta'bawa sai dai kawai ta kau da kanta domin dai a zauna lafiya. **** "Irin kulawar da Abbas keyi kan Halimatu ya sanya iyayensu suka ga kamar sonta yake yi, shi kuma ba" "haka bane a zuciyarsa kawai yana tausaya mata ne a matsayinta na mace kuma mai nakasa, Halima bata da lafiyar k'afa sosai kafarta ta dama ta samu tawaya tun tana yarinya anyi magani na hausa dana Asibiti tafiyarta bata dai-dai ta ba, sai kawai suka hakura suka bar mata hallitarta da alama haka Ubangiji ya hallice ta, kafarta ta dama itace take da nakasa ta inda in tana tafiya take jefata, Amma a fuska Halima bata da muni kyakkyawa ce sosai mai madaidaicin tsayi! komai nata cikin nutsuwa take gudanar" dashi. "Magaji ya fitar da matar aure A lokacin da iyayensu suka bukata, shi kuma Abbas din har yanzu ya rasa" "wacce zai tsayar a matsayin uwar 'yayansa! Mutum ne mai ruwan idon tsiya ko wace mace ba tayi masa ba! Da kyar da ya tsayar da Halisa a matsayin matar da zai aura gidansu na bayan layi! kuma Halisa kawar Halima ce tare ma suke tafiya makaranta, Allah sarki Halima tunda Taji labarin Abbas zai auri kawarta sai ta rasa nutsuwa komai nata ya tsaya cak! bata san tana sonsa ba sai da taji zaiyi aure!" damuwa ta shiga sosai ta rage walwala har sai da iyayenta suka gane! Da yake Baba Talatu macece mai saurin fahimtar abu nan da nan ta fahimci abinda ke damun 'yar tata! "Ta sameta tayi mata fada da nasiha sosai tace""Kada ta janyowa kanta lalura mutum baya ta'ba auran mijin da bana sa ba, dan haka ta cigaba da addua Allah itama ya za'ba mata miji nagari."" Duk da wannan" "nasihar da mahaifiyar ta tayi ma bai sanya ta daina damuwa ba, ita gani take waye zai aureta tana da" nakasa (gurguwa) tana ganin watakila ma haka zata 'kare rayuwarta ba tayi aure ba. Ita kuwa Halisa tunda ta fahimci Halima na shiga damuwa a duk sanda taje mata da maganar Abbas sai "ta dauki d'amarar muzguna mata kullum kan hanyarsu ta zuwa isilamiyya sai tayi mata zancensa da irin soyayyar da sukeyi, Halima tayi shuru bata tanka mata, ita kuwa Halisa tai tayi mata dariya. Akwai" "lokacin da Abbas yaje zance gurin Halisa ta tsare shi wai dole sai ya fad'a mata tsakaninsa da Halimatu! mamaki sosai ya kamashi Yace.""Halimatu kanwata ce amma babu wata soyayya a tsakanina da ita."" Halisa tace""To idan kai baka sonta ita tana sonka dan ba kaga halin damuwar da ta shiga ba lokacin da ta samu labarin abinda yake tsakanina da kai, dan haka gaskiya gwara kayi wa tufkar hanci tun kafin tafiyar" "tayi nisa duk da take kawata bana tunanin zan iya zaman kishi da ita.""" "Mamaki ya rufe shi da yake mutum ne mai tsare gida sai yace.""Okey yanzu kina so ki nuna min ga yanda" "zanyi kenan? Idan na fahimce ki kina so kice ke ba zaki zauna da Halimatu ba a matsayin kishiya ko me.""? Da sauri tace""Kwarai kuwa ai naga kusancin dake tsakanin gidanku da gidansu ne ina tunanin idan iyayenta suka fahimci halin da take ciki a kanka zasu ce ka aure ni kuma bana so gaskiya shiyasa nake so tun kafin tafiya tayi nisa kayi wa tufkar hanci."" Ya girgiza kansa yana kallonta yace.""Bari kiji Halisa ni ba irin mazan da mata zasu zauna suna tsarawa magana bane! abinda nasa kaina shi nake yi ke baki isa kice ga yanda zanyi ba, bani da ra'ayin zama da mace d'aya ki rubuta wannan ki ajiye bayan na aureki zan sake auran uku mutukar Allah ya bani iko saboda haka sai ki daura d'amarar zama da kishiya Halimatu kuma da kike magana na jawa kunne a kan tana sona to kin sanya ma naji sha'awar auranta zan aureku rana d'aya tunda dama 'kawayen juna ne."" Da jin abinda ya fada sai ta mike a fusace! tace""Wallahi sai dai ka za'ba ko ni ko ita dan na rantse da girman Allah ba zanyi kishi da gurguwa ba.""!!! Ya bude bakinsa yana kallonta cikin tsananin mamaki! lallai Halisa muguwar jahila ce yanxu me bambamcin muskini da mai lafiya? saboda jahilci da hauka kishi ma sai ta za'bi da wanda za tayi! Ya mike tsaye fuskarsa a murtuke yace."" Tunda kin rantse ba zakiyi kishi da Halimatu ba to nima kuma ba zan janye 'kudirin dana dauka a kan auranta ba, saboda haka sai kije ki r'ike duk wani abu da nasa aka kawo miki da niyyar auranki na bar miki, ki samu wani mijin ki aura ni kuma zanje na auri muskiniya sai naga abinda zai cinye ni."" Yana 'kare maganarsa ya futa daga soron gidan nasu. durkushewa tayi kasan soron ta fashe da kuka tana data sanin abinda ta aikata, tun farko ta lura Abbas din ba irin lusaran mazan da mace ke tursasawa bane yana da wani irin baud'addan hali tabbas kamar yanda ya fad'a din babu me sashi yayi abinda baiyi" niyya ba mutukar ba iyayansa ba. Tofa al'amarin yayi tsanani dan Abbas yaja tunga ya tsaya kan maganarsa kan cewar ya janye maganar "auransa da Halisa saboda wasu dalilai saboda haka Halimatu itace matar da ya za'ba a matsayin uwar 'yayansa, Baba malam da Alhajinsa suka dinga bashi hakuri suna rarrashinsa, kan yayi hakuri ya auresu gabadaya, nan ya futo ya fada musu abunda ke faruwa! Yace.""Halisa tayi mummunan furuci ga Halima kuma tayi izgili ga hallitar da Ubangiji yayi mata, dan haka to shi ba zai auri macan da zata dinga kokarin nuna masa yanda zaiyi ba, saboda haka shi ya janye maganar auranta Halimatu yake so. Baba Malam da Alhaji Sama'ila ba suji dadin faruwar al'amarin ba kasancewar mahaifin Halisa din mutumin kirki ne duk tare suke zama bakin titi ranar juma'a da yamma, dan haka sai suka yanke shawarar fada masa halin da ake ciki, suna kuma fatan Allah yasa hakan shi yafi alkairi. Koda mahaifin Halisa yaji yanda al'amarun" suka kasance sai hankalinsa ya tashi sosai! babu shakka yarinyarsa tayi wa kanta wauta ba kad'an ba ta "cutar da kanta kuma shi sam baiga laifin Abbas ba, da irin hukuncin da ya yanke yana bala'in son yaga" jajurtaccen namiji mai tsayuwa kan magana daya. Halisa tasha fada sosai gurin mahaifinta "yace.""Tunda ba zata auri mai mata ba to taje ta nemo wanda bashi da mata wanda kuma yayi mata alkawarin da ita kadai zai zauna, mutukar ta kawo masa komai illarsa da rashin nagartarsa to shi kuma zai daura mata aure dashi tunda itace taji ta gani." "Hankalinta a tashe ta nufi gidan Ramlatu, tana kuka ta zayyane mata abinda ke faruwa, a ganinta tinda" Itace take gaba da Abbas din zata fada masa yaji tace dan Allah ta bashi hakuri yanzu ta yarda zata zauna da Halimatun a matsayin kishiyarta. Ramlatu ta fusata ta dinga surutai tana aibata Halimatu da "iyayenta a cewarta sam Abbas bai dace da auran muskiniya ba, saurayi dashi mai kyau da kudi da Ilimi yama za'ayi ya auri nakashshiya wacce take ci take sha a 'karkashin alfarmarsa dan haka sai ta shiga bawa Halisa hakuri tace ta kwantar da hankalinta za taje ta same shi, insha Allahu zai aure ta. Da" "safe da wurwuri ta sauka a gidan kowa yayi mamakin zuwanta, ko gaisawa ba suyi da mutanan gidan ba ta nufi dakinsa, lokacin yana kokarin fitowa da shirin fita kasuwa! Yace.""A'a barka da safiya kece a gidan."" Tace.""Eh gurinka nazo."" Cike da mamaki yace.""Gurina.""? Tace""Eh yace.""To Kinga ni yanzu sauri nake zan fita ki bari na dawo ko kuma ki koma gida da yamma idan na dawo zan shigo gidan naki sai naji" abinda yake faruwa. "Cikin d'aga murya kamar wata uwarsa tace""Yanzu kai Abbas ka rasa wacce zaka aura sai Halima" muskiniya nakashshiya ashe dama anan ruwan idonka zai 'kare gaskiya ka bani mamaki wallahi! Ga Yarinya mai hankali da nutsuwa 'yar gidan mutunci mai kaunarka amma kace ka fasa auranta ka koma gurin wata banza wacce take ci da sha a 'karkashin mahaifin 'Daga mata hannunsa yayi fuskarsa a "murtuke yace.""Wallahi ban san sanda zakiyi hankali ba! kullum kina girma kina cin 'kasa! Yanzu ke ko kunya baki ji ba ki shigo har dakina kina daka min tsawa da nuna min yanda zanyi, haifata kikayi da zaki dinga yi min haka? ina ruwanki da aurena da Halimatu idan ba zaki saka albarka ba to kiyi shuru da bakin ki dan ni wallahi duk abin nan da kuke yi 'kara mun 'karfin gwiwa kukeyi babu gudu babu ja da baya sai na auri Halimatu in yaso ku kasheta saboda 'kiyayyya."" Fashewa tayi da kuka tana nuna shi da hannu tace""Ni kake zagi ko Abbas dama ai baka da mutunci baka dauke ni a bakin komai ba kuma kai dama ba'a fada maka magana kaji."" Yace.""Da kinzo min da lisilama zan fahimce ki amma kinzo kina yi mun hayagaga! a kunne ai kin san halina ni ba'a haka dani."" ratse ta yayi ya futa dada dakin, kallo ta bishi dashi tana jijjiga kanta, dama tun yana yaro bata iya lankwasa shi gwara Alhasan shi tana fada masa" magana yaji amma banda Abbas futo na futo yake da ita girgiza kanta tayi ta futa daga dakin. To haka al'amura sukayi ta kasancewa kowa na fadar albarkacin bakinsa kan wannan auran yayin da Abbas ya shafawa idonsa toka ya tsaya kai da fata sai da yaga auransa da Halimatu ya tabbata sannan hankalinsa ya kwanta. Gida gudu biyu iri d'aya Alhaji Sama'ila ya mallakawa Abbas da Magaji Gidajen nasu na cikin unguwar *Gwangwazo* wajejen gidan Sarki. "kowanne ya tare da matarsa a ciki, Maryam matar Magaji 'yar cikin gari ce dai-dai gwargwado tana da" "hankali da nutsuwa shiyasa tasu tazo d'aya da Halimatu suke zamansu lafiya, kamar yanda mazajensu ke zaune da juna lafiya suma haka suke mutunta junanmu." *3* Halisa hankalinta yayi masifar tashi ganin irin uban gidan da'a kai Halimatu ga uban lefen da Abbas yayi "mata atampopi da lesuka masu tsada kuka ta yini tana yi ta rasa nutsuwarta, mahaifiyar ma ba'kin ciki ne fal a cikinta zuciyarta tana aikace-aikacen ta na yau da kullum ta nayi wa 'yar tata fad'an wautar da tayi, in banda rashin tunani da kuma jahilci ina kai ina kushe hallitar Allah alhalin kaima baka wuce Allah ya mayar da kai wata hallitar ba, gashinan lokaci guda Allah ya juya al'amarinsa, tayi kuka tayi nadama gami" da dana sani wanda hausawa suke kira da 'keya ce. Zama mai tsafta ne yake wanzuwa a tsakanin Abbas da Halimatu! tawayarta bata hanata sauke "hak'kokin mijinta dake kanta ba, Tana kula dashi sosai dan wani sa'in idan yaga tana hidima dashi har tausayi take bashi dalili yanayin tafiyarta da rashin kuzarinta ma abin tausayi ne, amma abin na bashi mamaki sosai! kafin ya dawo daga kasuwa ta gama komai na gida tayi masa kwalliya mai burgewa. duk sanda ya shigo gidan yayi tozali da ita wani farin ciki ne yake rufeshi, wai shin meye aibunta ne?" Halimatu bata da wani abu ko nakasu a gurinsa tinda duk wasu hakkokinsa tana saukewa kwata-kwata "nakasarta bata dameshi ba zahirinta yake so ba wani abu na jikinta ba, zaman lafiyar da suke da juna ya sanya yake ji a cikin ransa zai iya zama da ita har'karshen rayuwarsa." ***** "Wata goma cif da auransu Maryam matar Yayanta magaji ta haifi d'a namiji, murna da farin ciki a gurinta" "tamkar ita ta haihu kullum tana gidan tare da mai jego tayi ta hidima da ita da jinjirin 'Yan uwan Maryam suyi ta tausaya mata idan sunga ta wani abun na wahala sai suce ta zauna, murmushi kawai take musu ta rabu dasu idan kuma sun matsa mata takan ce dasu itafa babu abunda ba zata iya ba saboda haka su daina yi mata kallon mara lafiya da rashin kuzari! To suma ganin ranta ya 'baci yasa suka daina cewa da ita komai! kafin ma suzo ta shiga gidan ta gyara tsaf ta gyara yaron sannan ta had'awa maijego abun kari, sannan ta dawo gidanta tayi wanka ta shirya ta sake komawa, haka ta dinga zurga zurga har sai da akayi suna inda yaron yaci sunan Maigidanta Abbas sai take kiransa da Amir. KullumAmir a" "hannunta yake wuni sai dare take mayar dashi ko kuma idan ya bukaci nono sannan, gabadaya dai ita" "Maryam haihuwar yaron tayi amma raino yana gurin Halimatu, idan ta dauki yaron tun safe to sai dare ita dashi." Abbas bashi da matsala ta 'bangaran wannan dan shima mutum ne mai son yara duk sanda ya dawo ya tarar da ita tana fama da takwaransa yakan ji dadi yayi ta addua Allah suma ya basu nasu mai albarka. "Shakaru uku da auransu Halima bata ta'ba 'batan wata ba, gashi har anyiwa Amiri 'kanwa Ilham, Abbas" "tun yana daurewa dai har ya kasa hakuri yace ta shirya suje asibiti a dubasu, koda sukaje likita ya dubaso gabadayansu babu abunda ke damunsu kawai dai lokacin haihuwarsu ne baiyi ba, likita ya rubutu musu magani mai kyau yace suje suyi amfani dashi insha Allahu za'a dace. Dukkaninsu a sanyaye suka koma" "gida, kuma ba suyi 'kasa a gwiwa ba suna amfani da maganin kuma suna sake kula da kansu." "Ramlatu kuwa a duk sanda suka had'u da Halimatu a taro sai ta zage ta tayi mata gorin rashin haihuwa," "duk taro na family dinsu sai ta tara mata mutane tayi ta nuna ta tana fad'in mugwayen kalamai a kanta, wata irin tsana Ramlatu keyi wa Halima ko ta mece oho! dan akwai ranar da tazo har gida taci mata zarafi da fad'in sun gaji da jiran gawon shanu dan su duk irinsu babu mara haihuwa saboda haka sun gaji" da daci da ita idan ba zata haihu ba to zasu kawo wacce zata cika musu gida da 'ya'ya.' Wannan cin zarafin ya 'bata marai rai sosai ta yini tana kuka dan ki girki ba tayi ba ballanta tayi wanka ta "shirya kamar yanda ta saba, koda maigidan ya dawo rasa gane kanta yayi, tambayar duniya tayi masa shuru sai kuka take yi, tsayin shekaru uku da auransu bai ta'ba fuskantar irin wannan matsalar daga gurinta ba, da kyar ya samu yayi wanka ya futo palon tana dai zaune a inda take tana kukan da take, zama yayi kusa da ita yana sake rarrashinta kan ta fada masa abinda ke faruwa, da kyar tayi masa magana tana hawaye gwanin tausayi tace ita taga ji tunda bata haihuwa ya 'kara aure ko kuma ya" saketa dan cin zarafin da Yayarsa take mata ya isheta. Ransa idan yayi dubu ya 'baci! shin wai me yake damun Ramlatu ne? ina ruwanta da matarsa ina kuma "ruwanta da rashin haihuwarsa, idan zai mutu bai haihu ba bai dameta ba shine yaga zai iya zama da" "matarsa a haka, shi kam ya rasa wace irin 'kiyayya Ramla keyi wa Halimatu, hakuri ya bata sosai yace zai same ta yaja mata kunne kan kada ta sake zuwar masa gida." Jin abinda ya fad'a yasa hankalinta ya tashi sai ta dinga bashi hakuri tana nuna masa illar abinda zai "aikata, mutukar ya tunkari Ramlatu da wannan maganar to babu shakka ya sake rura wutar gaba mai zafi a tsakaninsu, kuma ita ba zata so su samu matsala da 'yar uwarsa ba, Nuna mata yayi ya hakura ba zaije gidan Ramlatun ba. Washe garin ranar kafin ya tafi kasuwa sai da ya tsaya gidan Ramlatun sukayi ta" "babu kyau babu dad'i a tsakaninsu, dan ya nuna mata mahimanci da matsayin Halima a gurinsa kuma ya nuna mata cewar itama ta tsaya a matsayinta na 'yar uwarsa mutukar tasan wata fitina ce zata kaita gidansa to kada ta sake zuwar masa gida, dan tuntuni shi ya riga yasan Allah ne ke bada haihuwa ba wani mahaluki ba! Ramlatu kuka taci ta 'koshi 'dan uwanta da take alfahari dashi shine yazo ya ci kata mutumci a gaban kishiryata lallai babu shakka dole sai ta tashi tsaye kan Halima dan da alama Iyayenta" suna tsaye a kanta gurin ganin ta mallake mata d'an uwa. "*Kaji rigima ta Ramlatu ke ba uwar Abbas ba komai ba amma kina kishi da matarsa, Uwar miji aka sani" da kishi da matar d'anta Uwar mijin ma irin wacce bata san abinda take ba.* Abbas zuciyarsa wasai yaje kasuwa yayi harkokinsa. koda suka tashi daga kasuwar kai tsaya 'Kofar Na'isa suka nufa dan ji yake idan bai fad'awa mahaifiyarsu abunda Ramla ke masa ba za'a iya samun matsala nan gana gwara ya fada mata ta kira ta ta ja mata kunne. "Hajiya Abu ranta ya 'baci sosai tace""Ni dik abinda ke faruwa a tsakaninsu ban sani ba wallahi amma" Wannan yarinya anyi babbar kwabo wallahi dan taga matar taka mai saukin hali ce shiyasa take mata cin kashi a ko'ina amma kayi hakuri ka kuma bawa Halimatun hakuri insha Allah zan aika yara har gidanta su kira min ita zan mata tsakani da matarka duk sanda ta sake zuwa gidanka domin ta kuntatawa matarka to babu shakka na samu labari da Alhaji maihifinku zan had'ata.... To tun daga wannan rana Halimatu ta samu lafiya Ramlatu ta saurara mata da gorin haihuwa ammafa sa'i da lokaci suka had'u a wata sabgar sai ta yar mata da habaici al'amarin Ramlatu sai addua. ***** "Halisa ce ta shiga kara kaina a gidan, mussaman ranaku guda biyu Juma'a da Lahadi ranakun da ta" "tabbatar da cewar maigidan nan bai futa sai taci uwar kwalliya ta sanyo turare mai 'kamshi tazo ta yini a gidan! idan sun had'u dashi tana nuna masa kamar babu wani abu a ranta, ta hakura dashi kawai ta zuwa ziyara ne gurin 'kawarta! Sai dai ya girgixa kansa kawai ya shareta dan shi ba yaro bane ballanta ta raina masa hankali Ita kuwa Halima zuciyarta ce ta shiga sa'ka mata wani abu! tana ganin tunda dai" har yanzu Halisan bata da tsayayye mai zai hana ya aureta ya had'asu tunda ta lura da Halinsa tayi hankali kuma duk wasu alamu da take nunawa a kan mijin nata ta gane sabida shi take zuwa gidan Koda ta sameshi da maganar cewa yayi zaiyi shawara zai fada mata kome ya yanke! "Kwana biyu ta sake tuntu'barsa da maganar ya dinga kallonta yana mamakinta yace.""Ke kina ganin idan" "na auri Halisa na had'aku babu matsala kuma zaki iya zama da ita.""?" "Cikin farin ciki tace""Zan zauna da ita tsakani da Allah nasan ko ta nufe ni da sharri zai koma kanta tunda" "ban cuce ta ba, sannan kuma ina so ka aureta kaga tanan za'a tabbatar da rashin haihuwar mu shin waye yake da matsala tsakanina da kai.""! Wannan magana da tayi sai ta sake sa masa 'kwarin gwiwa shima yana so ya tantance waye mara lafiya a cikinsu, kai tsaye ya tunkari Halisa sa maganar, ranar kamar ta zuba ruwa a 'kasa tasha dan farin ciki! ta dinga murna da godewa Allah! Yace.""Ina so ki zauna lafiya da Halimatu dan da yawun bakinta nazo nan neman auraki kada ki shiga gidana ki tayar mana da" "hankali mun gina rayuwarmu cikin mai kyau da inganci"" Halisa taji wani irin d'aci a ma'kogwaronta!" wato ma ba'a karan kansa yazo neman auranta ba sai da izinin matarsa! 'kwafa tayi a cikin ranta! a zahiri "kuwa cewa tayi"" Haba Alhajina kada ka damu zan zauna lafiya da ita ai ko lokacin baya ma kuruciya ce ta janyo nayi wannan furucin amma ka daina kokwanto da shakku a kaina.""" Yaji farin ciki ya kamashi dama can yana son Halisa halinta ne baya si to tunda dai yanzu tayi hankali zai aureta su zauna tare cikin inuwa daya. "Ba'a wani ja dogon lokaci ba aka d'aura aure Halisa ta tare a dakinta, da yake gidane mai dauke da" "bangare uku sai kowa ya dauki d'aya, kasancewar babu yara a gidan yasa maigidan ke bin 'Dakunan matayen nasa bai tare a nasa part ba din sai ranar da ya tara iyali tukkuna." * MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~ *Wallahu galibun Ala amrihi * *4* "Sati biyu da shigowar Halisa gidan al'amura suka sauya, Halimatu ta kasa gane kan mijin nata gabad'aya" "Halisa ta ri'ke masa wuya ko yana kasuwa bashi da nutsuwar kirki mutukar bai dawo gida yayi tozali da ita ba, ranar girkin Halimatu sam bai da wani kuzari da walwala yakan dad'e ma a waje bai shigo ba, idan ma ya shigo d'in babu wani abun arziki da yake tsinana mata ba kwanciyarsa yake yi yai bacci! Halima ta shiga damuwa matsananciya ta rasa wanda zata samu ta fad'awa damuwarta gabakidaya Abbas ya sanja mata baya kula da ita sannan ba ya zama yaci abincinta kamar da idan tayi masa magana sai yace.""A" "koshe yake shine dalili, Ita kuwa Halisa data fahimci rashin jituwa a tsakaninsu sai ta sake zage damtse" "gurin ganin ta sake mallakarsa, kissar yau daban ta gobe daban, duk abincin da zata bashi sai ta bad'e shi" "da magani abun mamaki kuma Yayarsa Ramlatu itace ke kawo mata maganin mata dana mallakar zuciyarsa, ita dai burinta Halimatu ta wulakanta a gidan." "Ranar Asabar har ya futa kasuwa da jaraba ta ciwo shi ya dawo gida, a maimakon ya nufi 'bangaran" "Halimatu tunda Girkinta ne sai kawai ya nufi bangaran Halisa, domin a yanda yake jin kansa yana ganin kamar Halimatu ba zata iya dashi ba, sai yanzu ya gane cewar Halisa ce dai-dai dashi dan tana iyawa da fitinarsa ita kuwa Halimatu rashin kuzarinta a ko'ina ma gwadawa take, ada hakan bai dame shi ba sai da ya auri Halisa ya gane cewar itace zata iya dashi, dan jaraba irin tashi baya tsayawa kan hallitar da Allah yayi masa duk karfi da kuzarinsa sai ya had'a da maganin 'karfin maza, kullum akwai wanda yake kawo" musu magani kasuwa suyi ta siya suzo suna gallabar matansu da daddare. Halisa duk da tasan ba girkinta bane bai hanata nuna masa kulawa ba kar'barsa tayi hannu biyu suka shiga d'aki suka shafe awa kusan hud'u suna abu daya Halimatu ce ta shiga sashin tana sallama a palon taji shuru idanunta ne ya sauka kan hular maigidan da key dinsa na mota da kuma rigarsa kan kujera. Tabbas kayan daya sa ya futa dashi ne a dakinta ya shirya kuma asali ma itace ta dauko masa kayan dole "kuma tayi mamaki! kafin ta dawo daga tunaninta suka fito daga dakin a tare dashi da halisan daga shi sai gajeran wando, ji tayi yana fad'in ""Zo ki bani abinci naci a gurguje na koma kasuwa na bar mutane na jirana."" Had'a ido sukayi ita dashi! sai ya wani dake! kamar ba mara gaskiya ba, ya bude baki zaiyi" magana kawai sai ta juya ta fita daga palon. "Jikinsa ne yayi sanyi ya zauna kan kujera yana kokarin mayar da kayansa, tabbas yasan wani abun da" yake a gidan baya kyautawa sam be san meya sa ba yanzu kwata kwata baya damun cikakken "satisfaction da Halimatu! bata da ni'ima kuma bata gamsar dashi kamar yanda Halisa ke gamsar dashi, gashi Halisa ta iya salo-salo shi kuma haki'kanin gaskiya yana so a dinga kula dashi kan shimfida." "Halisa ta fito daga kicin da abinci a hannunta, mikewa yayi da fad'in"" Bana jin zan tsaya cin abincin nan" zan koma kasuwa yanzu.'' """Haba dai don Allah ka zauna kaci gashi da zafinsa dama ban jima da gamawa ba."" Girgiza kansa yayi ya" "nufi hanyar fita yana kallon agogon hannunsa da fad'in ""Biyu da rabi yanzu na fada miki akwai mutanan dake jirana.""" "Sakin bakinta tayi ta bishi da kallo tana girgiza kai, da sauri kuma ta ajiye plate din abincin taje bakin" "window ta d'aga labule tana le'kensa, gani tayi ya nufi gurin Halimatu, shi da yace sauri yake yi to mai kuma ya kai shi gurin ta. Takaici kamar ya kasheta ta zauna kan kujera tana cizar yatsa." Koda ya shiga palon samunta yayi zaune a kan kujera ta tsirawa guri guda ido tana kuka! yaji wani irin "tausayinta ya kama shi, yana sonta baya son ganinta cikin damuwa shiyasa yaji wani irin rashin kuzari a jikinsa." Kafin ya karasa inda take sai da ya tanadi kalaman da zai wanke kansa a gurinta. "Cikin wata mayaudariyar murya ya kira sunanta had'e da kamo hannunta, shuru tayi bata amsa ba," "yace.""Ki gafarce ni hakika nasan ni mai laifi ne a gurinki, kin san dan adam ajizi ne, ina tausaya miki ne shiyasa bana so na dinga d'ora miki lalurata.""" "Hannunta ta cire a cikin nasa tace""Wallahi ban ta'ba tsammanin haka daga gurinka ba, ashe dama duk" "wani abu da kake fad'a a baki ne? Halisa ko wata uku cikakku ba tayi ba ka sauya gabadaya ka daina kula dani baka sauke hakkina dake kanka, yausha rabon daka hada shimfida dani? ina tunanin tunda Halisa ta shigo gidan nan tsayin wata uku sai biyu ka kwanta dani shima sai dana nema sannan kuma abun har ya kai ka dinga satar kwanana kana kai mata, ina hankali da tunaninka suka tafi? idan ni bana ganinku ai Allah yana kallonku kuma kasan sai ya saka mun."" Jiki na kyarma yace""Na sani wallahi kiyi hakuri ki dauki hakan a matsayin tsautsayi! na fada miki ajizanci ne irin na d'an adam amma ba zan sake ba kuma" "inaso kice kin yafe mun.""" "Tace"" Sai ka fad'a mun sau nawa kana satar kwanana kana kai mata."" Da sauri yace.""Yau ne kawai shima" "kuma akashi aka samu."" Ta goge hawayenta a hankali tace""Na yafe maka amma dan Allah ka dinga kiyayewa kana kokarin sauke hakkina dake kanka." "Yace.""Insha Allah ki tayani addua nima cikin 'yan kwanakin nan wani iri nake jina."" Tace.""Insha Allah zan" "cigaba dayi maka addua harkarshen numfashina."" Mikewa yayi yana fadin."" Muje ki rakani ko."" Ta mike tana mirmushi tamkar baiyi mata laifi ba suka jera tare suka futa har inda motarsa take." Halisa har yanzu na tsaye bakin window tana kallonsu suka futo suka tsaya a bakin mota suna magana! "gani tayi Halimatun na dariya tana kallonsa shi kuma ya kamo fuskarta ya sumbuta, ya shiga mota hade da daga mata hannu Zaman da'baro tayi kan kujera tana hargitsa gashin kanta, kai jama'a!! wai shin" "Halimatu wace irin macace ne? wacce bata da zuciya bata kishin kanta! ai idan itace mijinta ya saci kwananta ya kaiwa kishiyarta ranar sai ta kusa kashe shi da tashin hankali, amma ita duba dariya ma" take harda rakoshi bakin mota. "Wayarta ta dauka ta kira Yaya Ramlatu! ta daga wayar suka gaisa, Murya na rawa tace""Yaya al'amura fa" "sun dagule wallahi! ban san wane irin so Abbas kewa Halimatu ba! daga aiki ya fara sai kuma ya karye! gashi itama kamar mayya duk abinda za'ayi mata bata fushi, 'karewa ma kwananta ya kawo min a maimakon taji haushi sai ma take dariya harda rakoshi bakin mota."" Yaya Ramlatu ta shiga girgiza kanta tace"" Nasha fad'a miki Uwarta da Ubanta ba'a zaune suke ba dan ita bata da kuzari da 'kafar yawon gidajen malamai Ubanta 'kasurgumin dan tsubbu ne duk wasu asararai yana dasu, ina kyautata zaton" "yayi aiki mai zafi akan Abbas din, amma duk yanda zanyi sai nayi na wargatsa shirinsu."" Halisa tace""Ni" "wallahi yanzu babban burina ta fita ta bar min gidana sannan naga na samu ciki na haihu."" Ramlatu tace''" "Kada ki damu zaki haihu ita kuma zata fita ta bar miki gidanki zaki zauna tare da 'yayanki insha Allah zanyi miki kokari akan wannan lamarin."" Tace""Nagode Yaya Ramlatu! Sallama sukayi Ramlatu tace""Yauwa dama inaso kiyi dubara a gurin mijin naki ki samu 'yan kudi masu kauri sai ki kawo min dasu" "nake so naje a taimaka miki."" Tace""Insha Allah zanyi kokari kamar nawa ."" Tace""Dubu hamsin ma ta isa.""" "Ajiyar zuciya ta sauke tace"" Zan duba inda yake ajiyar kudinsa idan ya bar key din a jiki zan dauko zan" "kawo miki anjima dan nafi so ayi komai da zafi-zafi.""" "Ramlatu tace""A'a kada ki daukar masa kudi ya gane fa."" Tace""Ai suna da yawa ba zai gane ba tunda" "kusan kullum sai ya shigo dasu kafin ya kai banki."" Tace""To shikkenan ina sauraranki idan kin kawo min ni kuma nayi miki al'kawari komai yamma zan tafi gidan *Yar Sa'adu.""*" Halimatu kuwa zuciyarta fes ta futo daga bangaranta ta nufi na Halisa domin yi mata sallama tana so "taje su gaisa da iyayenta sannan kuma ta shiga gidan Dan uwanta su gaisa da matarsa Maryam, abinda yasa Maryam ta rage shigowa gidan saboda zuwan Halisa dan bata so wata hatsaniya ta tashi a tsakaninsu sunanta ya fito, dama kuma ta lura da irin wulakantaccen kallon da Halisa ke mata, shiyasa" "gabadaya ta dauke kafarta daga gidan, sai dai sa'i da lokaci ita Halimatun ta shiga su gaisa." "Halisa na kokarin zaro kudi cikin drowar taji sallamar Halimatu a palonta, da sauri ta zabura ta futo palon" "tana kallonta, Halimatu ta fahimci rashin gaskiya a tare da ita, girgiza kanta tayi tace""Halisa zan je gida mu gaisa dasu Baba Malam sai nadawo."" Cikin ya'ke tace""To sai kin dawo dan Allah ki mi'ka min" "gaisuwata gurinsu.""" "Tace""Zasuji insha Allah."" Juyawa tayi ta fita, Halisan ta rakata da wulakantaccan kallo tana cin laya a" kanta. Tsaki taja ta koma dakin ta cigaba da ciku-cikun dauko kudin daga drowar da take a kulle dan ba taga key din ba amma dan jaraba sai da tasan yanda tayi ta zura hannunta ta zaro kudin duk sun ya "mutse, da kyar ta samu ta ciro dubu talatin da biyar ta hakura haka, kaya ta sanja ta zuba kudin a jaka tasa kai ta fita daga gidan ba tare da maigidan ya sani ba." Baba Malam da Baba Talatu sunji dadin zuwan 'yar tasu duk sanda ta kai musu ziyara sukan yi murna da farin ciki ganinta cikin nutsuwa da wadata! Bayan taci abinci sai suka shiga hira da mahaifiyarta Na'ajatu ce ta shigo gidan hannunta rike da buhun "kayan wasanta duk tayi bud'u-bud'u da jikinta, Baba Talatu ta harareta da fadin"" Kin gama yawon wasan naki yunwar cikin ki ta koro ki ko.""'? Zum'bura bakinta tayi tana kokarin yin kuka. Baba Talatu tace""Ai sai ki nemi me baki abinci dan banyi dake ba dama na fada miki tunda baki zuwa makaranta to zakiyi ta zama da yunwa."" Kuka ta fashe dashi ta jefar fa buhun kayan wasan nata tana kallon Yayar tata. Halima ta riko hannunta tana rarrashinta, kwanciya tayi a jikinta tana kuka cikin rashin iya magana sosai tace""Ni ba zani makaranta malam ya dakeni ba kuma sai an bani abincina."" Halimatu ta dinga dariya tana kallonsu suna drama Baba Talatu tace""To sai naga wanda zai baki abinci a gidan nan."" Kuka take sosai" "tana fad'in ""Ni sai an bani abinci yunwa nake ji.""" "Halimatu tace""Yi shuru autar Baba Ni da kaina zan baki abinci ki fad'a min ma me kike so na siya miki kici" "ki kyalewa Baba abincinta.""" "Hawaye tagoge tana kallonta tace""Zan biki gidanki ki dinga bani shayi da bredi ita Baba Talatu kullum" "koko da kosai take bani, sannan bata bani na siyo alawa da biscuit. "" Baba Talatu ta ri'ke ha'ba! tana fad'in ""Ikon Allah! Wato Naja'atu abinda zakiyi mana kenan! kullum fa sai na dafa miki shayi malam ya siyi miki bredi da madara ga kwai amma kice koko da kosai nake baki."" ? Halimatu tace""Gaskiya Baba bakya ji da wannan autar taki! dubeta dan Allah yanda kika barta tayi daud'a dubi kitson kanta duk ya tsufa, gashi bakya bata ta siyi sweet da biscuit saboda haka ni zan tafi da ita gidana, zaki bini ko Auta.""!? tafada tana kallonta, Da sauri ta daga kanta tana dariya. Baba Talatu ta gyara zamanta tana ta'be baki" "tace""Ai sai kuje dama nima na gaji da bari bari yarinya kullum nakan layi tana yawo ta'ki zama a" "makaranta malam na kaita kafin ya dawo gida ta rigashi, ki tafi da ita ku sata a makaranta tayi karatu watakila idan taga babu idanmu zata zauna a makarantar." "Halima tace""Aikuwa dai bari Baba Malam ya shigo na fada masa. To koda Baba malam yaji kudirin" "Halima na tafiya da Naja'atu gidanta, be'ki ba yace dai idan taga da akwai matsala to ta dawo da ita."" Baba Talatu ta hada mata kayanta tsaf suka tafi." "*Wannan shine mafarin dawowar Naja'atu hannun 'Yar uwarta, a lokacin tana da shekaru hud'u a duniya" dalili kenan da yasa ta girma da tunanin cewar Abba Abbas da Halimatu sune suka haifeta.* Ita kuwa Halisa koda ta fita kai tsaye tudun wuzurci ta nufa gidan Yaya Ramlatu! basu ja dogon lokaci ba "suka dauki hanyar gidan *'Yar Sa'adu* abin mamaki mata ne dan'kam! a gidan! d'aki guda idan waccan ta shiga ta fito sai waccan ma ta shiga ta fito har akazo kansu! koda suka shiga dakin *'Yar Sa'adu* na zaune kan wata kujera katuwar macace mai ki'ba taci uwar kwalliya ga hancinta da wani abu mai kyalli a jiki, hannu da wuyanta duk gold ne! taci ubab bleecig kana ganinta kaga 'yar duniya, suka gaisa da juna, Halisa sai kallon dakin takeyi ganin ko ina manne da hotonan mace da namiji tsirara! sannan ga wasu manya manyan drowars ko wanne kayan mata ne a cike a gurin kala-kala! Yaya Ramlatu ta ciro kudin jakarta dubu talatin da biyar ta zube gaban *'Yar sa'adu* tace"" Uwar dakina wannan itace matar 'kanina da nake baki labari gata nan na kawo miki ita don Allah ki san maganin da zaki bata wanda zai sanya ta" "mallaki mijinta ita kad'ai.""" "*'Yar Sa'adu* tasa dariya ta bata hannu suka tafa tace""Lallai 'kawata kina ji da matar 'kanin nan naki!" "Allah yasa idan ta samu duniya ta tuna dake, akwai wata mallaka da zan bata! Amma gaskiya tana da tsada kuma naga kudin da kuka ajiye bashi da yawa! Wannan mallakar tana da sirri dan da yawa mutane sunyi amfani da ita sun tabbatar da gaskiyar maganata, ina zaune ake zuwa anayi min tukwuci da kujerar makka had'e da gida da filaye, dan haka idan kuna da bukatar na baku ita to gaskiya zaku ajiye min dubu" "dari biyu.""" "Halisa tayi saurin kallonta tana marairaice fuska tace""Dan Allah ki bani wallahi nayi miki al'kawarin idan" "bukata tabiya zanzo na kawo miki kudinki har inda kike."" Ramlatu tace""Eh kwarai kuwa ni zan zama" sheda a tsakaninku tunda dai kin tabbatar da ingantuwar maganinki to ki amince ki bamu insha Allah "cikin sati guda za'a kawo miki sauran kudinki.""" "*'Yar Sa'adu* tayi shuru tana tunani! Wani littafi ta dauko ta mikawa Halisa da biro tace""To na amince" "zan baki amma kisa hannu! sannan ki rubuta abinda kika bani da farko.""" Halisa ta kar'ba da sauri tasa hannu! sannan ta rubuta kudin data bayar dubu talatin da biyar! *'Yar "Sa'adu* ta kar'ba ta ajiye, sannan ta mike taje ta dauko mata wata 'yar mitsitsiyar kwalbar fiya-fiya! wani abu mai mai'ko da yau'ki! ne a ciki tace""Gashinan duk sanda zakuyi auratayya da mijinki to sai ki lakata kad'an a d'an yatsan ki! sai ki tofa maliki yaumin dini 'kafa takwas a jiki sai ki lakata maganin a gabanki, kafin kwana biyu zaki bani labari."" Halisa ta dinga washe bakinta tana godiya, *'Yar Sa'adu* tace''Mijin ki zai zame miki kaska sannan ba'kin ciki zai kashe kishiyarki wannan shine la'kanin maganin."" Wani sanyi ya sauka a zuciyoyinsu jin abinda 'Yar Sa'adu ta fada, godiya sukayi mata sosai tare da al'kawarin insha" Allahu cikin satin nan zasu kawo mata kud'inta........ "*Ayar Allah da ita ake wasa, wai kuma mutum yace yana so yaga dai-dai a rayuwarsa, Ubangiji Allah ka" karemu daga fad'awa halaka. * MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~ *5* "Kamar dai yanda 'Yar Sa'adu tafad'a musu hakane ya kasance, kwana biyu zamantakewar gidan ta samu" "tangard'a! Abbas hankalinsa ya dauke gabad'aya baya ganin kowa a gabansa sai Halisa! Komai ta tambayeshi baya yi mata musu da gardama, kuma koda ya duba gurin da yake ajiyar kudinsa yaga ba yanda yake ba, da yayi mata magana kai tsaye tace""Ita ta dauka tayi ba'ki ta sallamesu! shuru yayi mata baice komai ba, tana ganin ya shiga toilet ta bude drowr ta dauki dauri d'aya ta mayar ta rufe! Sai da ya fita sannan ta lissafa kudin dubu dari ne, kai tsaye ta yafa mayafinta ta nufi gidan Yaya Ramlatu da kudin," "Gidan 'Yar Sa'adu suka nufa, nan Halisa ta zauna tayi ta basu labarin yanda al'amura suka kasance ta" dinga basu labarin irin abun da Abbas din yake mata idan suna kwance da daddare! 'Yar Sa'adu da "Ramlatu suka dinga dariya suna tafawa! ita kuwa Halisa tace""Ai gaskiya maganin nan karshene kuma yaci kudinsa, dan a tsakanin kwanaki bakwai d'in nan sai da na samu kudi a gurin sa sama da dubu dari! kullum in zai futa sai na tambayeshi kudi kuma sai ya bani! baya tambaya me zanyi na lura yana tsoron kada dare yayi yazo da wata magana nace masa wani abu daban."" 'Yar Sa'adu ta gyara zamanta kan kujera tana dariya had'e da 'kas-'kas! da cingum din bakinta, tace""Ke waye ya fad'a miki dama mata na zama yanzu! ai yanzu dama na hannuki kiyi kiyi ki samu abunda kika samu kuma ba zama zakiyi ba idan" "maganin ya kare ki sake zuwa ki siyi wani.""" "Halisa tace""Insha Allahu ai na gane hanya kuma."" Cike da farin ciki sukayi sallama da 'yar Sa'adu suka" nufo gida. **** "Bayan wata uku kullum jiya iya yau a gidan, Halisa ta k'wace miji gabadaya Halimatu ita dashi sai ido da" "gaisuwa, Kullum kafin ya futa zai shigo su gaisawa ya zauna suyi ta wasa da Naja'atu! yana kaunar yarinyar sosai kasancewar sa mutum mai son 'yaya gashi har yanzu Allah bai bashi ba! Itama Naja'atu d'an zamanta a gidan ta saba dashi sosai idan ya shigo zuwa take ta zauna a cinyarsa tayi tai masa labarin makaranta da kawayenta shi kuma ya dinga biye mata, dan wataran gurin tsayawa sauraran shirmenta har makara yake a kasuwa, Idan kuwa zai futa sai ya tambaye ta me take so ya siyo mata, sautu iri-iri take masa na kayan wasa dasu biscuit da chocolate, aikuwa duk abinda tace ya siyo mata baya mancewa sai ya tsaya a danja ya siya mata ya shiga ya kai mata, wannan abinda yake yana masifar 'batawa Halisa rai! ta tsani taga yana nuna kulawarsa kan yarinyar ko kadan tana so kamar yanda ya banzatar da Halimatun to ya kasance itama yarinyar itama ya daina kulawa da ita, Idan tana fushi kan" "abinda yake wa Naja'atun har mamaki take bashi, rabuwa yake da ita idan tayi ta gaji sai ta hakura." "Ita kuwa Halimatu ganin yanda yake kula da kanwarta yasa ta rage jin zafinsa a zuciyarta, addua takeyi" "kullum Allah ya karkato da hankalinsa kanta tabbas tasan abinda yake yi ba a hayyacinsa yake ba, tunda tasan irin kauna da son da yake mata, babu shakka Halisa ba'a haka ta barshi ba." "To Haka dai Halimatu ta cigaba da zaman hakuri a gidan, tana ji tana gani mijinta yafi karfinta dan sai" yayi wata biyu uku bai kwanta da ita gabadaya an cire masa sha'awarta a cikin zuciyarsa. *IDAN RABO YA RANTSE* Ranar Juma'a bayan an sauko daga massalaci ya dawo gida a gajiya ga kuma sha'awar dake damunsa "tun daran jiya dan kwana sukayi rigima da Halisa ta yanko masa uban kudi wai sai ya bata sannan zata amince ya biya bukatarsa, shi kuma yace ba zai bayar ba sai ta fada masa abinda za tayi dasu, nan ta shiga inda-inda! ya fahimci bata da hujja sai yace ba zai bayar ba, shine tayi fushi tace itama ba zata bashi kanta ba, da yake mutum ne mai zuciya kawai sai ya kyaleta ammafa daurewa kawai yake dan baida hakuri ta wannan 'bangaran Washe garin ranar Halisa naganin ya futa itama ta shirya ta futa" itama ta nufi gidan Yaya Ramla domin tafada mata abinda yake faruwa. koda ya shigo gidan kai tsaye gurin Halisa ya nufa gabadaya idonsa a rufe yake bukatarsa kawai yake so ta biya yanzu ya amince zai bata kudin mutukar dai zata biya masa bukata. "Ya dubata ciki da waje bata gurin, rai a 'bace ya nufi gurin Halimatu, suna Tare! Da Naja'atu a palo tana" koya mata karatu ya shigo bakinsa dauke da sallama! "Naja'atu ta mike a guje taje ta d'ane jikinsa tana fad'in ""Oyoyo Abbana.""! Dariya yasa ya mi'ka mata" "kumatunsa kamar yanda suka saba! aikuwa ta manna masa kiss a gurin! shima yayi mata sannan ya sauketa kasa, yana d'an ya mutsa fuska ya kalli Halimatu dake ta faman yi musu dariya! hannunsa ya mi'ka mata da fad'in "" Ranki ya dad'e zo muje daki ina da magana."" Halimatu ta tsira masa ido tana" kallonsa da mamaki a tare da ita! "Gira ya daga mata yana yi mata wani irin kallo. Girgiza kanta tayi ta sunkuyar da kanta 'kasa, lallai wato" sai yau take da amfani a gurinsa kenan! duk sanda yake cikin halin sha'awa tana ganewa. "Ji tayi ya kamo hannunta ya mikar da ita tsaye, gudun kada yayi abun kunya a gaban Yarinya yasa tayi" "saurin cire hannunta tace""Kaje ganin nan zan shigo."" Babu kunya ya nufi bedroom dinta yana wata irin tafiya." Zama tayi kan kujera tana kallon Naja'atu na rubutunta sai da ta tabbatar abinda take ya dauke mata hankali sannan ta mike a nutse ta bishi dakin. Wannan had'uwar tasu ta firgita Halimatu gabad'aya mijin nata ya sanja mata hallitarsa ma kamar ta "sauya, ya zage karfi a kanta yana bugunta babu tausayi da jin 'kai irin wanda yake mata, sosai yake sarrafata salo-salo duk ya fice daga hayyacinsa itama sai wuya yake bata, kukan wahala take masa tana bashi hakuri ya saurara mata haka, sam ba haka ya saba yin mu'amula da ita ba, da kyar ya saurara mata ya kwanta gefanta yana maida numfashi To tun daga wannan had'uwar Ubangiji ya zartar da ikonsa" "ciki ya shiga ya zauna daram a mahaifar Halimatu, cikin kuma da bai bayyana kansa ba sai da yayi wata hudu tukkuna sannan Allah ya bayyana shi, saboda ita kanta Halimatu bata san da ciki a jikinta ba kasancewar ba ko wane wata take al'ada ba shiyasa duk ta rikirkice, ta dinga kokwanto a kan ciki Kai" "tsaye asibiti ya dauketa sukaje, likita ta dubata sosai dan har scanning akayi mata ciki wata hudu kuma yana cikin koshin lafiya. Abbas ya rasa inda zai saka kansa saboda farin ciki, tun a mota ya kira wayar mahaifiyarsa ya sheda mata abinda ke faruwa, Hajiya Abu tayi murna da farin ciki sosai ta kuma yi addua kan Allah ya sauke ta lafiya. Halisa kwanan kuka tayi da taji labari wai Halimatu nada ciki, ya akayi" "haka ta faru? wai dama mijin nata ashe yana lallabawa gurin Haliman yana biya bukatarsa bata sani ba," lallai zai shigo ya sameta. Shi kuwa da farin ciki a tare dashi yake sake jaddada mata k'aruwar da ya "samu! ta hasala! sosai ta dinga zazzaga masa rashin kunya kamar zata zage shi! aikuwa ta fuskanci 'bacin rai! dan lafiyayyun marika tasha wanda hakan bai ta'ba faruwa ba tsayin shekarun auransu, Yayi mata gargadi sosai kan tsaurin idon da take masa kana kuma ya dauke mata wuta gabadaya ya daina kulata," ya tare sashen Halimatu!! Halisa ta zama tamkar mahaukaciya gashi *'Yar Sa'adu* bata gari ta tafi Nijar dama 'Yar can ce kullum "ita kenan a tafe gurin zuwa gidan Yaya Ramlatu, suna tattauna yanda zasu 'bulluwa al'amarin, Ramlatu tsoron zuwa gidan takeyi saboda tasan halin 'Kanin nata zai iya kunyatata shiyasa ta zauna a gida, Halisan na zuwa inda take Sau uku yana dawowa gida ya tarar bata nan a'lamarin da ya fusata" "shi sosai, ya tsaya harabar gidan nashi yana kai kawo kana ganinsa kasan ransa a 'bace yake, Tana shigowa ya buga mata tsawa da fad'in ""Ta koma inda ta fito! gabanta ne ya fad'i baki na rawa tace''Wallahi naj. Hannu ya daga mata yace."" Bana bukatar naji komai daga bakinki sau uku ina" dawowa gida bakya nan ina kike zuwa ba tare da na sani ba? saboda haka ki fuce min daga gida sai nazo "gidanku inaso kafin nazo ki fada musu inda kike zuwa.""" "Halisa ganin yayi fushin mai tsanani yasa ta juya jiki a sanyaye ta futa daga gidan, kai tsaye gidansu ta" nufa tana kuka. A takaice dai sai da Halisa tayi sati biyu a gidansu sannan Yaje yayi bikon ta iyayenta ran su ya 'baci sosai "jin irin abinda take aikatawa na fita yawo ba tare da izinin mijinta ba mahaifinta yace da Abbas duk sanda ta sake futa bata fada masa ba to ya sanar masa sai ranta ya 'baci sosai! Halisa ta tsorata sosai d'a zaman da tayi a gidansu har jikinta ya soma sanyi tsayin sati biyu da tayi a gidan nasu ji take tamkar shekara biyu tayi, ganin ya shere ta da ita al'amarinta yasa jikinta yayi sanyi tana addua kada Allah yasa yace zai saketa. To tunda ta samu yanzu ya mayar da ita sai ta dauki aniyar gyara kuskuranta a gurinsa" amma dai duk da haka ba zata fasa yiwa Halima zagon 'kasa ba. "Koda ta dawo gidan d kafin ya sakar mata fuska sai da ta dade tukkuna sannan ya warware gabadaya," tun daga sannan ta kiyaye abinda zai dugunzuma masa zuciya wanda zai haifar da sa'bani tsakaninsu har ta kaishi ga korata gidansu. *** "Cikin Halimatu nada wata bakwai Allah ya bawa Halisa nata, Halisa aka dinga murna da zumudi ana iyayi!" "shi kuwa maigidan ya dinga biye mata da duk abinda take so burinsa kawai yaga matayen nasa sun haihu lafiya shima ya shiga sahun mutanan da ake kira da Abbah, duk da sunan da Naja'atu ke kiransa dashi kenan Abbana, ko Abban Naja, a duk lokacin da zata kirashi da sunan yakan ji wani iri dan saboda" yasan ba shine ya haifeta shi dai yafi bukatar 'yayansa na cikinsa su kirashi da wannan suna. ***** Lafiya lau Halimatu ta haihu inda ta haifi 'yar ta mace ta d'an d'ebo kammanin mahaifinta gurin hasken "fata gami da siririn hanci, Abbas mai kyau ne sosai irin namijin da mata keso yana da haske da cikin zati dogo ne amma ba sosai ba, yana da manya ido da dogon hanci wanda ya kyata masa fuskarsa, amma kuma bashi da fara'a da saurin sabo! Mutum daya ya amince dashi cikin abokansa shine Magaji Yayan matarsa kenan Abba magaji yasan sirrinsa kamar yanda shima yasan nasa. Halisa ganin Halima ta" "haifi mace sai ta dinga addua Allah yasa ita ta haifi namiji dan tasan farin cikin da mijin nasu zaiyi sai yafi wanda yake yi a yanzu, hankalinta na masifar tashi a dik sanda taga ya shiga gurin Haliman ya jima bai fito takan shiga tashin hankali da damuwa saboda tasan yana can yana shiriritar da ya saba da shegiyar yarinyar nan Naja'atu da Babynsa wacce ya sanyawa suna Fatima amma sai suke kiranta da *Saddiqa*" dalili kenan da ya sanya take Allah Allah itama ta haihu itama taga yana nuna kulawarsa a kan d'anta. "Haihuwar *Saddiqa* ta janyo masa bud'i da alkairai da yawa, harkokin kasuwancinsa suka bude sosai" yake harkar gwangila na gina gidaje da ma'aikatu da sauransu........Wani 'katon gida yake ginawa a cikin "unguwar *Danbare* sabuwar unguwa ce da masu kudi suka siyeta suke ta gasar gidana gida a gurin, gaskiya gidan da yake idan aka gama aikinsa babu shakka zai zama abun kallo a gurin jama'a." "Halisa ta haihu lafiya lau ta haifi namiji kamar yanda Scanning ya nuna mata, sai dai kuma cikin ikon" Allah kwanan yaron d'aya a duniya ya koma. Ihu! ta dinga zabgawa tana kuka dan rashin tawakkali cewa take wallahi Halima ce tayi mata asiri d'anta ya mutu saboda tana bakin cikin ita bata haifi d'a namiji ba. "Abba Abbas tun yana rarrashinta har ta si'ke shi haushinta ya rufeshi, ya shiga nuna mata illar abinda" "takeyi, Allah ne ya bata kuma ya kar'bi abinsa dan me zata d'orawa wani! sai da yayi mata kaca-kaca! sannan ta daina ikirarin cewar Halima ce tayi mata asiri." *** Bayan shekaru uku Halimatu ta sake haihuwa inda ta haifi 'Da namiji! Wanda wannan haihuwar ta janyo tashin hankali sosai a gidan dan iskokai Halisa ta dinga tayarwa na 'karya dana gaskiya tana yun'kurin kashe maijego da jaririnta......Babu arziki ya tarkata ta ya kaita gidansu dan al'amarin yafi karfinsa haka kawai yana ji yana gani ta illata masa d'ansa. "Ashe iskanci ne Halisa na ganinta a gidansu, sai ta dawo hayyacinta mussaman da mahaifinta ya samo" "malamai, masu ru'kiya suka dinga jibgarta, babu arziki ta dai-dai ta nutsuwarta ta dinga kiransa a waya yazo ya dauketa taji sauki!" "Shi kuwa dama tuntuni ya yanke shawara kan cewar zai raba musu gurin zama, dan gudun aikata" mummanan aiki idan baya nan shima ya fahimci duk wani abu da Halinsan keyi sharri ne da ba'kin kishi da ganin kyashi! Gidansa dake *'Dan bare* suka tare shida Halimatu da 'yayansa kana yasa aka gyarawa Halisan wanda suka bari ta zauna a ciki yana ganin hakan shine yafi alkairi a tare dasu baki daya... "Wannan al'amari ya sanya zuciyar Halisa kusan bugawa, gidan da take kulafucin zama a cikinsa shine zai" "ce ba zai je da itaba, kuka taci ta koshi tana tunanin mafita babu shakka ta ko'ina Halima tayi mata zarra! ta haihu har sau biyu kuma ta tare a sabon gida. tabbas dole ne ta nemawa kanta mafita yanzu ne ta sake gazgata maganar Yaya Ramlatu inda take cewa mugun sihiri iyayen Halimatu sukayi akan Mijin nata," itama idan hakane to tabbas zama bai kama ta ba. "To da yake yanzu bata da matsalar kudi yasa ta d'auki d'amarar shiga malamai domin bukatarta ta biya," duk ranar da ya kasance ba a gidanta yake ba to idan ta fita tun safe sai yamma zata dawo gida tare suke yawace yawacen malamansu da Yayar mijin nata. Yaya Ramlatu bata da matsala saboda mijinta "matafiyi ne shiyasa takeyin abinda take so a gidan, haka zata fuce ta watsar da 'yayanta a tsakar gida, kishiyarta Sakina mutuniyar kirki ita ke mata dawainiya da 'yayanta tayi da nata, tabbas albasa ba tayi" "halin ruwa ba, dan da Ramlatu ta gado halin iyayen nata to ba zata aikata abinda take ba." * MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~ *PEGEN YAU NAKU NE* *My Son Najib Sa'id* *Abue Sale alqurami* *Bashir Saleh* *Umar Abbas Yusif* *Muhammad Karim* Ina mutukar godiya da kulawarku a kaina da 'kokarin yi min sharing ina rokon Allah ya sadaku da alkairin duniya dana lahira Allah ya za'ba muku abinda yafi alkairi a rayuwarku ~~~~~~~~~~~~~~~ *6* "A takaice dai duk wannan fad'in tashin dasu Halisa sukeyi a kan Halimatu ba suyi tasiri a kanta ba," "saboda halimatu ta kasance mace mai ibada kuma dukkaninsu bata nufe su da sharri ba shiyasa kullum Ubangiji ke kara kareta daga sharrin su da makircin su, duk wani asiri da sukeyi baya tasiri idan ma yayi baya dadewa yake karyewa, ta inda Halisa take samun galaba akan Abbas din shine ta gurin shaye- shayen magungunan mata to tana d'an janye hankalinsa watarana dan gaskiya irin magungunan da Halisa take sha suna da tsada har dana turawa sha take ita dai burinta ta janye hankalin Abbas din ya wulakanta matarsa uwar 'yayansa, abinda Halisa bata sani ba kuwa shine irinsu Abbas asiri baya saurin kama su idan ma ya kama su to baya wani tasiri a jikinsu zai karye! saboda Abbas mutum ne me yawan azkar da karatun al'akurani mai girma gashi sallahr asubah bata wuce shi, shiyasa duk wani asirin da" suke masa baya zama a jikinsa. "Halisa tun haihuwarta ta farko take samun matsala daga zarar ta samu ciki baya yin kwari zai zube, ta" "shiga tsananin damuwa da tashin hankali! ganin 'Ya'yan Halimatu sunyi wayo har sun soma zuwa makaranta gashi mahaifinsu naji dasu yana yi musu hidima kamar hauka, ai babu shiri ta bazama yawon gidajen masu magani har gurin 'Yan bori zuwa take su bata magani tazo ta jika tasha, ta yini tana amai, da murkukusu, amma taki ta gane hanya madaidaiciya ta fawwalawa Allah domin shine mai bayarwa da hanawa, Kullum kokarinta ya za'ayi ta haihu ko ta halin 'kaka. Abbas ganin ta tashi hankalinta dan har ramewa tayi sai yayi musu viza domin zuwa 'kasa mai tsarki su roki ubangiji hakan be mata dadi ba taso ita ya kaita kasar waje likitoci su dubata idan ma dashe za'ayi mata zata amince ita gani take idan sukaje saudian ba zata sanja zani ba! Gabadayan su dashi da iyalinsa suka nufi kasa mai tsarki, Halisa ta dinga" wani iyayi tana shige masa gani takeyi ai saboda ita aka zo kasar! Halima dai sai dai tayi mata dariya "kawai dan ita wataran idan Halisa na wani abu har dariya take bata, tana kallonsu zasu shirya su fita ita" "da Abbas wai zasuje asibiti sai dai tayi musu fatan dawowa lafiya, ta lura shima mijin nasu na biyewa Halisan ne dan kawai a zauna lafiya." "Ita kuwa Naja'atu mugun haushin Halisan take ji dan ta soma hankali a lokacin, idan taga tanayi wa" "mamanta wani abu ranta 'baci yake sai tayi yun'kurin magana sai Halimatun ta hanata, sai dai tayi 'kwafa kawai! ita hakurin mamanta ta har mamaki yake bata, kuma a duk sanda za taga Abban nasu yana magana da Halisa sai taji haushinsa, tashi ma take ta bar gurin, wani lokacin kuma idan taga sun shiga daki da Halisan sun dade kuka take zuwa taci ta koshi! ta fito tana kumbura fuska, Halimatu ta gane yarinyar na kishinta shiyasa takejin ciwon abinda ake mata, ta kuma fahimci yarinyar za tayi kishi sosai dalilin da ya sanya take yi mata 'yar nasiha a fakaice! Naja'atu kam jinta kawai take yi tana ganin kamar wani abun ma itace take bada goyon bayan Halisan nayi mata, 'kiri-kiri sai suna zaune a guri daya Halisa zata tsiri wasu abubuwa wanda suke sawa ta janye hankalin Abban nasu! duk sanda haka ta faru taga ya tashi yabi bayan halinsa ji take kamar zuciyarta zata babbake! ko ya fito bata kulashi idan yazo yana musu magana banza take dashi sai dai yai ta tambayar Halimatu ko wani abun ne yake damunta Halimatu tasan abinda take fad'a masa maganar ta wuce! Naja'atu gabadaya daina walwala tayi ta daina sakin fuskarta, rashin kunya takeyi wa Halisa a duk sanda tasa mata baki a cikin maganarta dan Halisa akwai katsalandan daga zarar tazo taga suna hira da wasa da 'yan uwanta su Saddiqa da Mussadiq sai tazo ta dinga buga musu tsawa tana hantararsu, aikuwa dama a ciki take da ita, tace watarana suna wasa tazo tana yi musu tsawa! Tace""Mu dan Allah ki daina zuwa kina takura mana muna maganarmu ke waye ya takura miki eye? ina cewa abinda kike so shi kikeyi saboda haka ki daina zuwa kina mana tsawa" "mtwsss!."" Takarasa maganar tana jan tsaki." Halisa ta fusata sosai hannu ta fitar ta tsinka mata mari tana d'ura mata ashar! sai ambato sunanan "Baba malam take tana zagi! Naja'atu ta dinga kuka tana fad'in ""Allah ya isa ba kakana kike zagi ba naki kike zagi!" "Halimatu tazo tana doke bakinta cikin 'bacin rai tace"" Ashe baki da kunya Naja'atu."" Tana kuka" "tace""Mamma kina ji fa tana zagin Baba Malam me yayi mata? wallahi sai na fad'awa Abbanmu."" Kai tsaye ta nufi dakin da yake kwance yana bacci! Halisa da Halimat suka bita da kallo cike da mamaki! Halisa mamakin yarinyar take na mayar da uban wasu nata komai akayi sai tace Abbanta ko a gidan" ubanwa ya zama Ubanta oho. "Yana tsaka da bacci yaji kukanta a kansa, ya bude idonsa da sauri! yana kallonta a tsaye a kansa tana" "goge fuska hawaye wani na sake zubowa, mikewa yayi zaune ya kamo hannunta ya zaunar kusa dashi." "Cikin tausasawa yace.""Waye ya saki kuka."" ? Cikin shashsheka tace""Gata can Anti Halisa muna wasa da" "dariyarmu tazo tana hantarar mu wai sai mun tashi mu bata guri zatayi kallo, shine dan nayi magana ta mareni har da zagin Baba Malam.""" "Ransa ya 'baci! Yace."" Kan wane dalili zata tashe ku a guri kuna wasa? saboda za tayi kallo sai ta" hantareku! hannunta ya ri'ke suka mike a tare suka fita palon "Halisa da Halima na tsaye sai musayar yawu suke Halisa na fad'in ""Wannan iskancin da 'kanwar taki take" "yayi yawa haka kawai saboda samun guri ta mayar da uban wasu nata to tun wuri ki fada mata ba ubanta bane kada ma ta dauka tanada gadonsa.""" "Halimatu ta bude baki kenan za tayi magana ta hango fitowarsu yana rike da hannunta, Halisa ta kallesu" "ranta idan yayi dubu ya 'baci! Hura hanci ta shigayi tace""Au! zuwa tayi ta taso ka daga baccin.""?" "Ya 'bata fuska sosai yace.""Koda bata tasheni ba dama dai-dai wannan lokacin nayi niyyar tashi, shin me" "yaran nan suke miki kullum kike matsa musu bakya barin su su huta.""!" "Halisa ta rik'e bakinta cikin mamaki take dubansa! Yace.""Magana nake miki."" Ganin yanda yasha kunu ne" "yasa ta sassauta murya saboda tasan halinsa sai tace""Kawai dan nace su tashi su bani guri zanyi kallo shine fa yarinyar nan ta hau yi min rashin kunya harda zagina.""" "Da sauri tace""Ni wallahi sharri tayi min ban zageta ba."" Halisa tace""To nayi miki karya ko."" Zumbura" "mata baki tayi ta murguda mata shi! Halisa ta shiga jijjiga kanta tana mamakin saken da yarinyar ta samu a gurin maigidan, kauna da son da yakewa yarinyar ta lura ko 'yayansa bayayi wa.""" "Yace.""Kawai saboda zaki zauna kiyi kallo sai ki tashesu mai suka tsare miki! bana so ki sake hantarar min" "'yaya duk wani abu da nake nema a duniya saboda su nake nemansa, kafin Allah ya bani sai da na cire" "tsammani dan haka dole ne na kyautata musu dan bana son abinda zai 'bata musu rai! duk abinda suke su zasuyi cikin nutsuwa da kwanciyar hankali kamar yanda kema kikeyin abinda kike so.""" "Halisa takaici kamar ya kasheta, har ta bud'e bakinta zata ce ""Ai ita wannan d'in da kake magana a kanta" "ba 'yar ka bace. Sai kuma ta sanja shawara, tace"" Shikkenan me 'yaya nima Allah ya bani."" Tana 'kare" "maganarta sai ta fashe da kuka ta nufi daki Jikinsa ne yayi sanyi kuma, Halimatu ta kalleshi murya na" "rawa tace""Haba Abban Naja'atu ba haka ya kamata ka yanke hukunci ba! kasan kowaye akayi wa haka" "dole yaji rashin dadi, yarinyar nan Naja'atu itace tayi mata rashin kunya kamata yayi ka fara hukuntata" "tukkuna.""" "'Dan ya mutsa fuskarsa yayi kamar zaiyi magana kuma sai ya fasa, hannun Naja'atu dake cikin nasa ya" saki ya juya ya nufi dakin da Halisan ta nufa Ita kuwa Naja'atu bata so hakan da yayi ba taso ya kyaleta taje tayi kuka taji ciwon a ranta kamar yanda take yini tana 'kuntatawa mamanta rai to itama yau ta d'and'ana taji. "Halima ta rufeta da fad'a kan abinda tayi tace""Wallahi duk sanda na sake ganin Kinyi mata tsaki sai ranki" "ya 'baci ko an fada miki sa'arki ce."" ? Kuka tasa ta nemi guri ta zauna tana fad'in ""Mama kina ji fa tana zagin mahaifinki Baba malam Kinyi shuru dan nayi magana sai kice nayi laifi .""" "Jikinta a sanyaye tace""Dan ta zage shi sai me? ni nasan ba Ubana ta zaga ba nata take zagi saboda haka" "na fada miki babu ruwanki da ita har mu bar 'kasar nan."" Shiru tayi kawai ba tace komai dan gaskiya ita ba zata dauki cin kashi da wulakancin da Halisan keyi mata ba" haka suka cigaba da zaman doya da manja tsakanin Halisa da Naja'atu babu sassauci kowa najin haushin "dan uwansa, Naja'atu taci alwashi kan cewar duk sanda Halisa ta sake kuntatawa mamanta rai to itama sai ta 'kir'kiri abinda zai janyo musu fad'a a tsakaninta da Abbansu, Halisa tunda taga take-taken Naja'atu da irin iskancin da take mata sai ta shiga taitayinta ta rage yiwa Halima wasu abubuwan na rashin arziki badan komai ba sai dan sanin matsayin Naja'atu da tayi a zuciyar maigidan nasu, tasan idan ta tsananta" ranta ne kawai zai 'baci a banza. "Sati biyu sukayi a kasa mai tsarki suka dawo gida, Likita ya d'orasu Akan magani, kan cewar in dai Allah" ya nufa da akwai sauran rabo a junansu to zasu haihu Wata uku da dawowarsu Halisa ta samu "ciki murna ta dinga yi tana adduar Allah ya zaunar mata dashi, to shima maigidan yayi farin cikin ganin cikin yayi wata hudu bai samu matsala ba, sai ya umarce data zauna ta daina aikace aikacen gida, mai aiki yace zai dauko mata, tace ya bari zata dauko 'yar yarta sai ta dinga taimaka mata, aikuwa hakane ya" kasance Unguwar Aisami ya kaita da kansa taje ta dauko Shamsiyya 'Yar yarta budurwa ce 'yar kimanin shakara goma sha hida ta "girmi Naja'atu da shekaru biyu, Shamsiyya irin masu shegen iyayi ne gata mummuna amma saboda tsabar shafa mai tayi fari da haske! murna sosai Shamsiyya tayi da zuwanta gidan Halisan tasan kafin ta" dawo gidansu sai ta sauya tayi ki'ba dan gaskiya ko zuwa gidan sukayi da ziyara basa dawowa ranar da sukaje sai sun kwana dan har daukar kawayenta takeyi ta kaisu gidan tana musu iyayi kanwar mamanta na auran *Alhaji Abbas Dan kwagila*. To cikin ikon Allah Halisa ta haihu kalau ta samu 'ya mace sai "dai ba haka taso ba taso ta haifi d'a namiji dan gaskiya Mussadiq ya tsone mata ido. Ita kuwa Yaya Ramlatu har akayi suna cikin yada habaici take mussaman idan taga Halimatu tazo gidan sai ta tsiri shige da fice tana sakin maganar da duk tazo bakinta. ""Duk cikin da ya haifi mace watarana shi zai haifi" "namiji Halisa ki kwantar da hankali gabadaya dangi munfi bukatar mu samu zuria dake dan haka tunda kin fara dasa 'kwan ki a gidan Abbas to kiyi abinda kike so babu me ce miki don me.!! Ire-iren maganganun da Yaya Ramlatu keyi kenan Shamsiyya na taya ta, Halima bata ta'ba tanka musu ba abinda" ya kawota takeyi ta tafi. "Ranar suna da kyar Abbah Abbas ya lalla'ba Naja'atu ta shirya ya kaisu, dan cewa tayi ita ba zataje ba" bata da lafiya wanda shi da Halima duk sun san 'karya take yi kawai rashin jituwar dake tsakinta da Halisan yasa tace ba zataje ba. kwalliya sukayi sosai gabadayan su harshi angon 'karni suna sanye cikin dakakkiyar shaddar galila mai kalar sararin samaniya(sky blue) sun yi iri daya da juna Halima da Naja'atu da Saddiqa! dinki iri daya ne a jikinsu doguwar riga ce wacce tasha uban stone work da aka kashe kudi gurin yin sa Abbah Abbas shida Mussadiq sunyi iri daya cikin babbar riga da 'yar ciki hularsu iri daya hakanan "takalman su iri daya, agogo iri d'aya, sunyi kyau sosai dan kafin su fita sai da sukayi hotona sannan ya kira Salim dan Yayarsa Ramlatu a waya ce yazo ya daukesu. Salim dan kimanin shekaru ashirin da" "biyar a duniya matashin saurayi mai jini a jiki d'an kwalisa ne sosai kuma yana kan lokacinsa dan babu abinda Abbah Abbas baya yi masa na rayuwa ya dauki yaron tamkar d'an cikinsa, shine ya tsaya masa kan karatunsa har yayi degree kuma ya d'ora shi kan harkokin kasuwancinsa Salim yasan wasu daga cikin sirrinkan Abbah Abbas amma kuma bai san wasu ba, Salim tun kafin Naja'atu ta kai girman haka yake sonta yana so su kammala secondary tukkuna ya tunkari Kawunsa da maganar tabbas yasan shi zai shige masa gaba gurin ganin ya mallaketa, amma dai duk da hakan yana ta kokarin kafa gwamnatinsa a" "gurin Naja'atun, itace take nuna masa bata gane me yake nufi ba." Koda Salim yayi tozali da Naja'atu kasa nutsuwa yayi ya dinga kallonta yana sosa kansa ga wani shegan "mirmushi a fuskarsa, Naja'atu ta 'bata ranta tana kallon Abban nasu dake gyara babbar rigarsa domin shiga mota, murya na rawa tace""Abbah kace ya daina kallona."" Abba Abbas na gyara zamansa a motar ya kalli Salim yana d'an 'bata fuska yace.""Kai bana son shashanci ka shigo mota mutafi na lura da kai tun d'azu ka damu yarinyar nan da kallo sai wani sosa kai kakeyi na fad'a maka ba zan baka itaba sai da amincewarta."" Salim yasa dariya yana kallonsa Yace.""Haba Kawu dube ni fa kaga ni da kyau! ni ba irin mazan da mata zasu ce basa so bane, ni nasan nan gaba kadan Ita dakanta zata furta maka ni take so."" Abbah Abbas na murmushi yace.""Ni dai na fada maka malam ka nemi yardar ta dan cikin 'yayana babu wacce zanyiwa auran dole."" Salim yace.""Insha Allahu Naja'atu tawa ce."" Mussadiq ya rike hannunsa da" "fadin""Nima ina so ka auri Yayarmu."" Rank'washin sa Naja tayi ya shiga motar yana kuka, Halima ta" "d'auka Abban nasu zaiyi mata fada mai yasa ta dakeshi sai taji yana cewa""Kai Mussadiq bana son rashin" "kunya ka tsokane ta ta hukuntaka kuma sai ka kama kuka."" Mamaki sosai ya rufe Halima! Girgiza kanta kawai tayi dan bata da bakin magana tana iya yiwa Naja'atu fad'a yace dan me shiyasa tayi shuru da bakinta, hakika kulawar da yake nunawa a kan 'kanwartata tana burgeta haka nan suma su Baba malam suna jin dadi yanda Abbas din ya r'ike musu 'yarsu tamkar shi ya haifeta, duk abinda zaiyi wa 'yayansa shi" yake mata wani sa'in ma har yana bambamta ta dasu gurin wani abun. Gabad'aya Naja'atu kasa sakewa tayi a gidan sunan ganin yanda jama'a ke musu wani irin kallo wasu ma "sai nuna su sukeyi, dalilin da yasa kenan ta zauna guri guda tana kalle kalle. Halima kam kasa zama" "tayi ta mike ta shiga cikin mutane ana hidima da ita duk da irin kallon banzan da suke mata hakan bai sa ta koma ta zauna ba, ta kau da kai tana ta shiga jama'a cikin fara'a ana gaisawa da ita." Tana zaune a palo wasu 'yan uwan Halisa suka shigo suna she'ka dariya d'aya daga cikinsu tana fad'in """Ku tsaya kuga yanda kishiyar Anti Halisa take tafiya."" duk sai su katsaya suna kallonta, sai ta shiga cangala 'kafarta d'aya tana cillata kamar yanda Halima keyi idan tana tafiya! Dariya suka kwashe da ita suna tafawa! Shamsiyya tace""Kuma wai a haka a nakashe take matar so a gurin miji."" Duk sai suka ri'ke bakinsu suna kallonta 'karin bayani suke jira tayi musu! Shamsiyya ta bud'e bakinta za tayi magana taji" saukar mari a fuskarta! Naja'atu ce tsaye a tsakiyarsu tana zubar da hawaye itace kuma ta mari fuskar Shamsiyya! Wacce take "gwada tafiyar Halimatu ta nuna murya na rawa tace.""Yanzu hallitar Allah kike gwadawa? Ke baki ji kunyar abinda kika yi ba Allah yayi hallitarsa yanda yake so kina gwada kuna dariya kema fa baki wuce Allah ya mayar dake haka ba.""!! Afusace Shamsiyya tace""Dan kutumar Ubanki ta gwada d'in! shegiya yar karoro! har ni zaki tsinkawa mari! lallai zan nuna miki nafi ki zafin kai!! kafin Naja ta ankara ta rufeta da duka! Sai sauran ma suka shiga taya ta suka rufar wa Naja'atu da duka har sai da ta durkushe a gurin!!" Ihu! takeyi tana kokarin kwatar kanta.... Halisa ta fito daga daki a guje! jama'ar dake waje suka shigo palon suna tambayar abinda ke faruwa. Shamsiyya tana hura huci! ta shiga fada musu karya da gaskiya. Yaya Ramlatu tazo ta tsaya a kan "Naja'atu tana zaginta ta uwa ta uba! Naja'atu kasa motsi tayi dan ta daku sosai! Halima ce tazo ta kama hannunta ta mikar da ita, tana kuka itama tana kuka su Saddiqa da Mussadiq na kuka! abin gwanin ban tausayi! Ita kuwa Yaya Ramlatu kamar kara zugata akeyi ta tara mutane sosai sai aibata Halima da Naja'atu take da iyayensu kowa na tofin ala tsine a kansu! Halisa ganin abin ya kwa'be! yasa tazo tana bawa Ramlatu hakuri saboda tasan idan maigidan ya samu labarin abinda ya faru to babu shakka al'amura zasu 'baci! dan rayukan kowa sai ya 'baci! da kyar ta rarrashin Yaya Ramlatu tayi shuru taja tawagarta suka fita harabar gidan domin cigaba da rabon abinci Halisa ta dinga yiwa su Shamsiya" "fada kan abinda suke kokarin janyo mata, dukan Naja'atu da sukayi yana nufin abubuwa da yawa a" "gareta hakan na iya barazana ga auranta, shiyasa bayan ta shiga dakin tasa Mussadiq ya kira mata" Naja'atun! K'in zuwa tayi sai da Halima ta rarrasheta sannan ta shiga dakin. "Halisa ta kwantar da kanta tana fadin ""Naja'atu kiyi hakuri kinji ko abinda su Shamsiyya sukayi miki kinga" "dai a gabanki na hukunta su kuma nayi musu fada dan Allah kada ki fadawa Abbanku."" Zum'bura bakinta tayi tace""To me yasa baki rama mun dukan da sukayi min ba! Ni wallahi bazan yarda ba sai na fada masa sun zageshi sun zagi Baba malam sun dake ni kuma sun kushe hallitar Allah.""" "tana k'are maganar ta ta fita daga dakin, Halisa rakata tayi da kallo baki a sake." "Tana fita daga dakin ta dauki wayar Mamanta wani guri ta 'buya ta kira numbarsa, ganin numbar" "Halimatu yasa ya dauka da sauri yace""Ranki ya dade yaya ina fatan komai lafiya.""? ai kawai sai yaji fashewar kukan Naja'atu a kunnansa! Ya mike tsaye da sauri! Yace''Naja'atu lafiya kike kuka yi shuru ki fada mun abinda akayi miki?"" cikin sar'kewa tana jawo numfashi irin na sharri ta shiga wassafa masa abinda ke faruwa a gidan sunan."" Ranshi idan yayi dubu ya 'baci! Yace.""Daina kuka kinji ko? zan dauki mataki wato Halisa ta tara mutane ne dan ta tozarta ni! babu laifi ki bawa maman taki wayar zamuyi magana."" Tana shashsheka da goge fuska tace""To."" Zuwa tayi ta kaiwa Halima wayar da fadin ""Gashi Abbanmu zaiyi magana dake."" Halima ta fita daga cikin mutane ta samu guri tana amsa wayar, Jinsa a fusace! yasa ta sassauta mirya tana so ta fahimtar dashi yaki sauraranta yace.""Zai turo Salim yanzu yazo ya daukesu ya mayar dasu gida ita kuma Halisa zata gamu dashi."" Kafin ma tace wani abu ya kashe wayarsa. Kasa'ke tayi da waya a hannunta tana mamakin wannan al'amari! gabadaya idan Naja'atu" "zata fada masa magana baya tsayawa yayi nazari zai hau kai ya zauna, tabbas ba sune suke da laifi kan faruwar hatsaniyar ba, to amma yana da kyau yabi komai a sannu tasan halinsa da mugun zafin zuciya" zai iya aikata abinda ba shikkenan ba. Aikuwa dai bayan watsewar taron suna da ya shigo gidan Halisa sai da ta fuskanci 'bacin rai sosai dan "cewa yayi ta ajiye masa 'yarsa ta fice masa a gida tunda dama abinda ta shirya yi kenan shiyasa ta damu sai tayi taron suna dan haka ta ajiye masa 'yarsa ta bar masa gida, kuka wurjan-wurjan ta dinga yi tana bashi hakuri tana kuma gaya masa yanda al'amarin ya kasance cewar ita sanda abun ya faru ma tana" daki bata da laifi. Jin tana ambatar sunan Shamsiyya a maganar yasa ya 'kwala mata kira tana zaune a palo tayi tsuru "tsoronta Allah tsoronta annabi kada yace ta bar masa gida, Da sauri ta shiga dakin, yace""Kece mai gwada yanda matata Halima take tafiya ko.""? Girgiza kanta ta shiga yi tana rantse-rantse! Yace.""Duk abinda kukayi wa Ubangiji ku dashi ne dan haka bana bukatar ganin ki a gida nan ki dauki kayanki ki tafi."" ai ta haihu babu wani sauran aiki yanzu."" Hannu ya zira cikin aljihu ya dauko dubu daya ya mika mata da fadin""Ki shiga mota."" Kar'ba tayi jiki a sanyaye ta fita daga dakin, zuwa tayi ta shiga hada kayanta tana" kukan takaici taso ta zauna a gidan har sai ranar da Antin nata tayi ar'bain sai ta tafi amma mutsiyaciyar Yarinyar nan Naja'atu tasa an koreta. Abba Abbas bai bar gidan ba sai da ya tabbatar da cewar Shamsiyya ta bar gidan sannan hankalinsa ya kwanta ko sallama baiyi da Halisan ba yayi tafiyarsa. "Gidan Yaya Ramlatu ya nufa koda taga yanayin da yazo mata dashi sai tasha jin jikinta, ta shiga yi masa" "rawar jiki, ya dinga kallonta takaici kamar ya kashe shi, Ramlatu ta girma amma bata san ta girma kullum abubuwa take irin na marasa tunani, ganin yanda take rawar jiki a kansa ne yasa ya sassaura zuciyarsa ya shiga nuna mata illahr abinda takeyi take kuma tara mutane na wulakanta masa matarsa hakuri ta bashi kamar gaske tace insha Allahu ta daina. Yaji dadi sosai hakan yasa ya zauna sukayi hira irin ta 'yan" uwantaka. Fushi sosai ya shiga yi da Halisa duk domin ya nuna mata kuskuranta a ganinsa idan da bata bada goyan "baya ba to babu wanda ya isa yaci zarafin matarsa da iyayanta, Halima ba tayi musu laifin komai ba amma sun dauki karan tsana da tsangwama sun dora mata." *BAYAN SHEKARU UKU* Lokacin Naja'atu nada shekara goma sha shida a duniya komai nata ya fito a zahiri macace doguwa mai "fadin 'kugu da cikar kirji bata da haske sosai amma ba za'a sata a layin bakake ba fatar ta mai kyau ce mai kuma wahalar samu, tana da kyau a fuska da jikinta wannan dalilin yasa bata fiye yin kwalliyar fuska ba, kuma bata sanya mayafi sosai tafi amfani fa hijabai saboda ta tsani kallon da maza ke mata a duk sanda zata fita babu hijab a jikinta takan fuskanci 'bacin rai sosai! maza sun dinga kallonta kenan har da masu tsayr da ita, shima Abban nasu ya fahimci yarinyar nada wani irin jiki mai daukar hankali duk wani lafiyayyan namiji, wannan dalilin yasa kullum idan yana gida zasuje wani gurin idonsa a kai! idan sun saka hijabin da be rufe musu jiki sosai ba sai yace suje su sanja wani, sosai yake kula dasu da takatsantsan a kansu. mussaman ita Naja'atun da ya lura tana kan lokacin balagar ta. to a dai dai" lokacin ne kuma suka gama secondary ita da Ilham 'Yar gidan Baba Magaji ita kuma Saddiqa na aji ss1 aji hudu kenan....... Lokacin kuma Halimatu nada tsohon ciki haihuwa ko ya yau ko gobe. a wannan "lokacin ne kuma sha'kuwa gami da soyayya mai kar'fin gaske ta shiga tsakanin Salim da Naja'atu, hatta da manya sun san da maganar! mahaifiyar Salim wato Yaya Ramlatu kwata kwata bata kaunar al'amarin ta zuba musu ido ne kawai tana kallonsu! Ita kuwa Naja'atu soyayyar da takewa Salim din tasa ta manta wacece mahaifiyarsa tana gani ita in dai Salim din zai aureta babu ruwanta da masifar Mahafiyarsa, Abbah Abbas kuwa ganin yanda suke kaunar junansu sai al'amarin yayi masa dadi sosai yana fatan Allah" "ya tabbatar da alkairi a tsakaninsu, kenan shi ya kasance waliyyin mutum biyu Salim din da ita Naja'atun." "A dai-dai lokacin da suke kokarin tafiya babbar makaranta, Allah ya saukar da ikonsa kan Halimatu gurin" "haihuwar cikin dake jikinta Ubangiji ya dauki ranta! bata tare data haife abinda ke cikin nata ba, mutuwar data girgixa zukatan al'umma da dama! mussaman Yaya Ramlatu da Halisa kwana sukayi suna sambatu da zabure zabure! Halima ta mutu da kalmar shahada a bakinta kuma ta mutu sanadiyar haihuwa babu shakka abun alfaharin ko wane musulmi kenan, duk wani mai kaunar Halimatu zai taya ta farin cikin samun rahamar Allah da tayi dalili kenan da ya sanya mijinta da iyayenta ke jin sassauci a cikin zuciyoyinsu idan suka tuna da cewar fa Halima tuntuni ta manta da rayuwar duniya domin ta riga ta gama dacewa, duk wanda zai budi baki alharin ta zai fad'a! Tabbas Annabi yayi gaskiya da yake cewa mutuwar mumini itace ke sawa mutane su girgiza kuma duk wanda ya mutu jama'a na fadar alherinsa" babu shakka Allah yaso shi da rahamarsa. *Ubangiji Allah kasa muyi kyakkyawan karshe ameen* To Bayan kwana bakwai ne da rasuwar Halimatu al'amarin ya kasance....... Inda su Baba Malam Alhaji Samaila Abba Magaji dashi kansa Uban gayyar suka zauna suka tattauna maganar yin *MADADI* da Naja'atu wato Naja'atu ta maye gurbin 'Yar uwarta Halimatu data dauka a matsayin mahaifiyarta. *A Pege na gaba zamu dawo ainihin labarin da muka fara da farko* *NAGODE 'KWARAI DA ADDUARKU A GARE NI NAGODE * * MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~ "_*Na gaishe daku 'Yan 'Kungiyata ta Manazarta Writers Association, Hakika ina jin dad'i had'in kanku," kuma ina alfahari daku mutu'ka! gabad'ayan ku ina rokon Allah ya d'aukaka min ku d'aukaka mai amfani Ubangiji Allah ya baku ikon rubuta abinda al'umma zasu amfana dashi*_ *PEGEN YAU NAKI NE* *UMMU HANIFA* Marubuciyar littafin *ANYA MUTUM CE? * "Ina mutukar alfahari dake 'Yar d'akina Allah ya 'kara miki basira da haza'ka, ki cigaba da rubuta littafai" masu dadi da ma'ana *7* Kanta a tsakanin cinyoyinta ta d'ora duka hannuwanta saman kanta ta takure kanta guri guda sai kuka "take tana girgiza kanta, Baba Talatu ta dafa bayanta a sanyaye tace""Naja'atu yanzu kinji komai daga bakin malam ko? Alhaji Abbas bashi ne ya haife ki ba kamar yanda kike tunani, A'a ba haka bane shi d'in ya kasance miji ga 'yar uwarki Halimatu Allah ya ji'kanta da rahama, wannan dalilin ne yasa su malam suka yanke wannan hukuncin a kanki babu laifi dan kin auri mijin 'yar uwarki kuma dukkanin mu bamu aikata haramci ba kamar yanda kike tunani da farko, idan kin auri Alhaji Abbas hankalin mu zai kwanta saboda mun san zai ri'ke mana ke da kyau da amana kuma su Saddiqa da d'an uwanta Mussadiq zasuji dad'in kasancewar ki a matsayin matar babansu zasu dinga kallonki tamkar mahaifiyar" "su."" ............Fuskarta jage-jage da hawaye ta d'ago kanta tana kallon mahaifiyar tata, girgiza kanta ta" "shiga yi kana tace""Ni wallahi bazan iya zaman aure dashi ba, a Uba fa na daukeshi kuma ya za'ayi kuce" "zaku daura min aure dashi, bayan dukkanin ku kusan da maganar Salim wannan ai abun kunya ne a gurunsa ace ya aure ni bayan shine ya raine ni ya rike ni a matsayin 'yarsa, kawai kuma saboda mutuwa" "ta ratsa tsakaninsa da matarsa sai kuce zakuyi masa *MADADI* dani ni wallahi bana sonsa.""" Ta'karashe maganar cikin gursheken kuka mai karfi. "Baba Malam yace.""Ai dama ba cewa muka yi dole sai kin so shi ba, cancanta muka duba shiyasa muka" "yanke wannan hukuncin saboda haka ina so ki cire maganar ko wane namiji a cikin ranki domun kuwa mutukar ni ne na haifeki to baki da miji sama da Mijin 'yar uwarki wato Alhaji Abbas, zaki aure shi ko" "bakya sonsa nan gaba idan kinyi hankali zaki gane abinda muke nufi dayin hakan.""" "Da rarrafe ta isa inda yake ta ri'ke hannunsa jikinta sai kyarma yake tace""Wallahi Baba malam zaku jefa" "rayuwa ta cikin garari saboda na fada muku iya gaskiya shine ni ba zan iya zaman aure dashi ba, na farko yayi min tsufa kuma abun kunya ne ace ya aure ni alhalin Ni 'yarsa ce bayan haka kuma yasan shine waliyi na gurin daurin aurena da Sali Abba Magaji ya fusata! ya kai mata mari da bayan hannu! jikinsa" "na tsuma! yace.""Dan ubanki har wata cancanta kike nema? dame kika fi Alhaji Abbas din ? da har kike kiransa tsoho! ana nuna miki abinda ya dace dake kina maganar abin kunya, kina nufin dukkaninmu bamu san abinda ya dace ba kenan? to wallahi tallahi na 'kara ji kin bud'e baki kinyi wata magana anan" "gurin sai na futar miki da jini shashashar banza da wofi.""" Shuru tayi jikinta sai rawa yake hawaye kuwa kamar an bude famfo! sai famar girgiza kanta take tana toshe bakinta tamkar wata zautacciya. "Tausayi ta bawa Baba malam ya kalli Alhaji Magajin a nutse yace.""Yarinyar nan taurin kaine da ita ina" "ganin zamu sake zama mu tattuna kan maganar, bana so ayi abu daga baya kuma azo ana dana sani." "Alhaji Magaji yace.""Malam babu wani zama da za'a sakeyi idan wata magana ta fito daga 'bangaran mu" "ba zasuji dadi ba, tunda kaga sune suka zo mana da maganar yana da kyau mu basu goyon baya kan abinda suka zo mana dashi duk mutumin da ya nuna yana kaunar had'a zuria da kai to ka tabbata ba 'karamin so yake maka, hakika nasan abokina Abbas yaji dadin zama da Halimatu shiyasa ya bukaci a bashi Naja'atu ta zame masa *MADADIN TA* dan haka tunda mun riga mun gama magana babu dadi" "kuma aje ace musu wani abu daban.""" "Baba Malam yace.""Yarinyar ce take bani tausayi bana son wannan kukan da take yi yana d'aga mun" hankali amma tunda kace haka shikkenan Allah ya sanya alkairi cikin al'amarin ya kauda kowace irin fitina da zata biyo baya. "Baba Talatu dashi Magajin suka amsa da ""ameen"" Mikewa yayi yai musu sallama da niyar tafiya gida dan" lokacin goma na dare ma ta wuce! Fatan sauka lafiya sukayi masa ya dauki hularsa da key dinsa ya fita daga gidan. "Cikin tausawa ya kalleta da fad'in""Ki tashi kije ki kwanta komai yayi tsanani maganinsa Allah kuma ina so" "ki zauna kiyi tunani kan wannan hukuncin da muka yanke a kanki, mune muka haife ki ba zamu cutar dake ba, da mutumin nan da ba nagartacce bane to da baza mu amince da bukatarsa ba to mun tabbatar da cewar idan muka dauke ki muka bashi muna da tabbacin zai kula dake kamar yanda ya kula dake a lokacin da baki san kanki ba.""" "Mikewa yayi ya shiga da'ki bayan ya gama maganarsa, Baba Talatu ta jima tana rarrashinta kafin ta mike" itama tabi bayan Malam din suka barta ita kadai a tsakar gidan tana kukan zucci. Mamaki take sosai! wai ashe dama Abban Abbas din ne ya bukaci auranta ita duk a tunaninta su Baba "malam ne, girgiza kanta kurrum take tana mamakinsa, to ta aureshi tayi yaya dashi? ta yaya za ta iya rayuwar aure dashi? lallai ma! ita abun ma mamaki yake bata ko kunya bai ji ba yace zai aureta bayan yana amsa sunan Uba a gurinta, gashi kuma yasan da maganar Salim hummm! aikam ba zata yarda ba duk yanda za tayi sai ta rushe wannan auran, sam ba zata auri tsoho dan shekara hamsin ba haka kawai sun gina soyayyarsu da masoyinta yazo yayi musu kutse a rayuwarsu ko kunya baya ji zai zo da wannan" maganar! 'Kwafa tayi ta mike ta shiga d'aki! Tana shiga dakin taji shashshekar kukan Saddiqa suna kwance ita da Mussadiq a katifa ta rungume shi sai kuka take! "A gigice ta kunna haske wayarta, tana haske su! Saddiqa ta rufe idonta tana sake takure jikinta guri" "guda. ""Ke Saddiqa menene? dama ba kiyi bacci ba.""? Saddiqa ta mike zaune tana goge fuskarta," "'Karasawa tayi ta zauna gefan katifar tana kallonta, a sanyaye tace""Meye kika kuka? nafada miki ki dainawa Mamma kuka idan kina so ta dinga samun rahamar ubangiji.""" "Saddiqa ta goge fuskarta tana kallonta tace""Ni ba Mamma nakewa kuka ba, nasan abinda nake yi a halin" "yanzu Mamma babu abinda take da bukata a gurinmu sai addua ba kuka ba.""" "A d'an sanyaye tace""To me kikewa kuka.""? Saddiqa ta kalleta wasu hawayen na sake zubo mata" "tace""Yaya Naja'atu me yasa kike nuna 'kiyayyar ki 'karara a kan Abbanmu.""!? Gabanta ne ya fad'i! sai tasha kunu! tace""Wace irin magana ce wannan Saddiqa? kada kice min kema kina goyon bayan na" "aureshi.""" "Saddiqa taja majina tana goge hancinta tace""To menene aibu a ciki? dan kin auri Abbanmu ai ba wani" "abun bane kuma ba ke kad'ai ce kika ta'ba auran *MADADI* ba Yaya Naja'atu idan kika maye gurbin mahaifiyarmu zamu ji dad'i sosai dan Allah kiyi mana wannan alfarmar ki daina nuna 'kiyayyar ki a fili.""" Shuru tayi tana nazarin maganar yarinyar! Wai shin da suke ta wannan maganar ta yaya zata fara ne? "wane matsayi zata ajiye shi miji ko mahaifi? bafa zai yiwu ba.! Ta kalli Saddiqan data kura mata ido tana jiran amsarta tace""Saddiqa nayi wa Abbanku 'kan'kanta kuma shima yayi mun girma bayan nan kuma ni matsayin mahaifi yake a gurina bazan iya rayuwar aure dashi ba, kuma ki daina tunanin ina 'kinsa wallahi bana 'kinsa saboda Abba Abbas yayi min abinda ba zan ta'ba mancewa dashi ba, kawai dai bana" "tunanin zan iya rayuwar aure dashi.""" "Saddiqa tace""To idan baki aureshi ba kin san dole yayi aure kuma gabadayan mu bamu san matar da zai" "aura ba, kinga zamu shiga halin 'kaka na kayi tunda dai kin san ba 'kaunar mu Anti Halisa take ba, kinga rayuwarmu na cikin 'kalubale nida Mussadiq.""" """Eh gaskiya ne duk maganar da kika fad'a to ai ba dole sai kun zauna tare da matansa ba, sai ku dawo" gidan Alhaji da zama ko kuma ku dawo gidanan nan nasan Baba Talatu zata ri'ke ku to meye abun tashin hankali. "Saddiqa ta shiga girgiza kanta zuciyarta na wani irin d'aci! tace"" Yaya Naja'atu kin manta maganar" "Abbanmu kenan kin san fa yasha fad'a cewar mutuwa ce kawai zata rabashi da 'yayansa bana tunanin zai amince ya kawo mu nan mu zauna ke ko gidan Alhajin da kike magana ba zai barmu muje ba duk da cewa gidansu ne.""" Naja'atu shuru tayi tana tunanin al'amarin Babu shakka zaman Saddiqa da Mussadiq hannun Halisa "gagarimun had'ari ne zata iya cutar dasu ta ko wace siga! Itace zata rike su tamkar uwarsu, to ita kuwa" "ko a mafarki bata tunanin zata koma gidansu a matsayin matar mahaifinsu, insha Allahu ta bar gidan har" abada. "Ganin Saddiqan ta tsura mata ido yasa tace""To ki kwanta kiyi bacci zanyi tunani kan maganar ki.""" "Saddiqa taji farin ciki ya rufe ta tace""To shikkenan Yaya Naja'atu nagode Yaushe zaki gama tunanin.""? Kallonta tayi na minti biyu tace""Ke dai tunda nace zanyi to zanyi duk hukuncin dana yanke zan fada miki.""" "Saddiqa tace""To Ubangiji Allah yasa naji alkairi."" Amin tace a takaice, Saddiqa ta juya ta kwanta tana" adduar Allah yasa ta amince da maganar ta......... Tsuru tayi ta tsirawa guri guda ido tana tunanin yanda za tayi ta rusa wannan gagarimin al'amarin daya "tunkaro ta, kira ne ya shigo Wayarta dake gefanta, ta dauka hannu na rawa, a kunne tasa wayar, ta fashe da kuka 'kasa-'kasa tace""My prince kaji abunda Abbah Abbas ya 'bullo dashi ko.''" "Salim dake kwance kan katifar sa yace."" Menene ya faru ni banji komai ba."" Juyawa tayi tana kallon" "bayanta, dan bata so tayi wata magana ya kasance Saddiqa taji, sai da ta tabbatar da bacci takeyi sannan ta sake sassauta murya ta shiga fada masa abinda ke faruwa. Mi'kewa zaune yayi da sauri! lokaci" "guda gumi ya tsatstsafo masa, yace.""Da gaske kike wannan maganar ko kuma dai tsokanata kikeyi.""?" """Humm! wane irin tsokana wallahi tallahi da gaske nake wai Abba Abbas shine ya bude bakinsa yake" fadawa su Baba malam yana so ayi masa *MADADI* dani!!! "Katifar da yake kai ya doka! da hannunsa da 'karfi! Yace."" Kai kaji wata tatsuniya! shi yanzu dan girman" "Allah baiji kunyar fad'ar wannan maganar ba!!? To shin wai ko ya manta abinda yake tsakanina dake ne da har zai bijiro da wannan tatsuniyar.""" "Tace""Oho! ni gani nake kawai san zuciya ne yama za'ayi yace haka bayan shi da bakinsa ne yace.""Mu" "daidaita kanmu zai daura mana aure kuma saboda mutuwa ta ratsa tsakaninsa da matarsa sai yace a mayar masa dani a *MADADINTA.""*" "Salim yayi wani murmushi na takaici yace.""Ke nifa na daina mamaki! wallahi zai aikata dama yanda yake" "wani kula dake da wani takatsantsan a kanki akwai alamun tambaya dama so yake matarsa ta mutu ya aure ki! saboda haka ni kuma wallahi bazan bar masa ba, to in banda ma rigima ina ke ina shi! shekara hamsin har yake tunanin auran yarinya 'yar 'karama kamar ki 16years fa to idan ya aure ki yayi yaya dake?" "mtwwss.""!!" """Humm! ni wallahi Salim mamaki ma ya hana ni nace komai ba kaga yanda su Baba malam suke murna" "ba, wannan ai tauyewa mutum hakki ne. Ni duk na rasa ma yanda zanyi.""" "Yace.""Kece kuwa kike da yanda za kayi, tun kafin yafiya tayi nisa ki kokarin ganin kin rusa maganar ni" "kuma gobe idan Allah ya kaimu idan naje daukarshi domin zuwa kasuwa zanyi masa magana akan inaso yazo gurin Baba malam kan maganar auramu sai naji me zaice.""" "Tace""To yauwa kayi masa hakan nasan dole kunya tasa ya kasa magana ni wallahi duk mutuncin sa ma" ya zube a idona mtssssw!!! Takarashe maganar tana jan tsaki! "Yace.""Baby ki daina wani damuwa ki kwanta kiyi bacci bazan bari wannan al'amari ya tabbata ba, duk" yanda zanyi to zanyi na rusa al'amarin. "A sanyaye tace""Tom shikkenan my Prince kayi bacci mai dad'i kaji ko."" Yace.""Ke ina wani maganar bacci" "mai dadi a gurina Wannan dattijon na nema yasa zuciyata ta buga.""!!" """Hummm! kawai tace dan ta rasa ma abin cewa, kashe wayar tayi ta zurfafa cikin tunani da nazari!" gabad'aya bata so tayi masa rashin kunya saboda shi mutum ne mai muhimanci a gurinta to amma tunda ya 'bullo da wannan maganar kashi hamsin na 'kima da mutuncinsa suka zube a gurinta. "Numbarsa ta laluba ta dinga kallon numbar kamar shi take kallo, shawara take da zuciyarta shin ta tura" "masa text ko kuwa, wata zuciyar tace"" Idan kika tsaya lako-lako kan wannan al'amarin to za kiyi kuka da idonki Da sauri ta shiga rubuta masa text kamar haka." _Assalamu alaikum Abba nmu barka da dare ina tafan kana nan lafiya? Abbah wata magana naji daga bakinsu Baba malam kuma sun ce kaine kazo musu da maganar shine nake so naji daga bakin ka._ Tana tura masa text din ta kashe wayar! kwanciya tayi tana takure jikinta hawaye ne ke kokarin 'kwace mata tana kokarin hana shi fita. "Sai bayan da ya dawo daga sallahr asubahi ne ya kunna wayar tasa, aikuwa text din ne ya shigo yayi" saurin bud'ewa yana dubawa. Ya karanta ya kai sau biyar ya girgiza kanshi! lallai To bata yarda ba "kenan tana so taji daga bakinsa, shi kam bai san abinda zaice mata ba, kawai sai ya share bai mayar mata da amsa ba, ya cire jallabiyar jikinsa, ya kwanta rigingine kan bed din yana tunanin rayuwa, Halisa ce ta shigo dakin jikinta sanye da hijab kamar wata mutuniyar arziki, tun bayan mutuwar Halimatu wata" shiriya tazo mata takeyi komai cikin rashin kuzari. * MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~ *PEGEN YAU NAKI NE* *UMMU HANIFA* Marubuciyar littafin *ANYA MUTUM CE? * "Ina mutukar alfahari dake 'Yar d'akina Allah ya 'kara miki basira da haza'ka, ki cigaba da rubuta littafai" masu dadi da ma'ana *7* Kanta a tsakanin cinyoyinta ta d'ora duka hannuwanta saman kanta ta takure kanta guri guda sai kuka "take tana girgiza kanta, Baba Talatu ta dafa bayanta a sanyaye tace""Naja'atu yanzu kinji komai daga bakin malam ko? Alhaji Abbas bashi ne ya haife ki ba kamar yanda kike tunani, A'a ba haka bane shi d'in ya kasance miji ga 'yar uwarki Halimatu Allah ya ji'kanta da rahama, wannan dalilin ne yasa su malam suka yanke wannan hukuncin a kanki babu laifi dan kin auri mijin 'yar uwarki kuma dukkanin mu bamu aikata haramci ba kamar yanda kike tunani da farko, idan kin auri Alhaji Abbas hankalin mu zai kwanta saboda mun san zai ri'ke mana ke da kyau da amana kuma su Saddiqa da d'an uwanta Mussadiq zasuji dad'in kasancewar ki a matsayin matar babansu zasu dinga kallonki tamkar mahaifiyar" "su."" ............Fuskarta jage-jage da hawaye ta d'ago kanta tana kallon mahaifiyar tata, girgiza kanta ta shiga yi kana tace""Ni wallahi bazan iya zaman aure dashi ba, a Uba fa na daukeshi kuma ya za'ayi kuce zaku daura min aure dashi, bayan dukkanin ku kusan da maganar Salim wannan ai abun kunya ne a gurunsa ace ya aure ni bayan shine ya raine ni ya rike ni a matsayin 'yarsa, kawai kuma saboda mutuwa" "ta ratsa tsakaninsa da matarsa sai kuce zakuyi masa *MADADI* dani ni wallahi bana sonsa.""" Ta'karashe maganar cikin gursheken kuka mai karfi. "Baba Malam yace.""Ai dama ba cewa muka yi dole sai kin so shi ba, cancanta muka duba shiyasa muka" yanke wannan hukuncin saboda haka ina so ki cire maganar ko wane namiji a cikin ranki domun kuwa "mutukar ni ne na haifeki to baki da miji sama da Mijin 'yar uwarki wato Alhaji Abbas, zaki aure shi ko bakya sonsa nan gaba idan kinyi hankali zaki gane abinda muke nufi dayin hakan.""" "Da rarrafe ta isa inda yake ta ri'ke hannunsa jikinta sai kyarma yake tace""Wallahi Baba malam zaku jefa" "rayuwa ta cikin garari saboda na fada muku iya gaskiya shine ni ba zan iya zaman aure dashi ba, na farko yayi min tsufa kuma abun kunya ne ace ya aure ni alhalin Ni 'yarsa ce bayan haka kuma yasan shine waliyi na gurin daurin aurena da Sali Abba Magaji ya fusata! ya kai mata mari da bayan hannu! jikinsa" "na tsuma! yace.""Dan ubanki har wata cancanta kike nema? dame kika fi Alhaji Abbas din ? da har kike kiransa tsoho! ana nuna miki abinda ya dace dake kina maganar abin kunya, kina nufin dukkaninmu bamu san abinda ya dace ba kenan? to wallahi tallahi na 'kara ji kin bud'e baki kinyi wata magana anan" "gurin sai na futar miki da jini shashashar banza da wofi.""" Shuru tayi jikinta sai rawa yake hawaye kuwa kamar an bude famfo! sai famar girgiza kanta take tana toshe bakinta tamkar wata zautacciya. "Tausayi ta bawa Baba malam ya kalli Alhaji Magajin a nutse yace.""Yarinyar nan taurin kaine da ita ina" "ganin zamu sake zama mu tattuna kan maganar, bana so ayi abu daga baya kuma azo ana dana sani." "Alhaji Magaji yace.""Malam babu wani zama da za'a sakeyi idan wata magana ta fito daga 'bangaran mu" "ba zasuji dadi ba, tunda kaga sune suka zo mana da maganar yana da kyau mu basu goyon baya kan abinda suka zo mana dashi duk mutumin da ya nuna yana kaunar had'a zuria da kai to ka tabbata ba 'karamin so yake maka, hakika nasan abokina Abbas yaji dadin zama da Halimatu shiyasa ya bukaci a bashi Naja'atu ta zame masa *MADADIN TA* dan haka tunda mun riga mun gama magana babu dadi" "kuma aje ace musu wani abu daban.""" "Baba Malam yace.""Yarinyar ce take bani tausayi bana son wannan kukan da take yi yana d'aga mun" hankali amma tunda kace haka shikkenan Allah ya sanya alkairi cikin al'amarin ya kauda kowace irin fitina da zata biyo baya. "Baba Talatu dashi Magajin suka amsa da ""ameen"" Mikewa yayi yai musu sallama da niyar tafiya gida dan" lokacin goma na dare ma ta wuce! Fatan sauka lafiya sukayi masa ya dauki hularsa da key dinsa ya fita daga gidan. "Cikin tausawa ya kalleta da fad'in""Ki tashi kije ki kwanta komai yayi tsanani maganinsa Allah kuma ina so" "ki zauna kiyi tunani kan wannan hukuncin da muka yanke a kanki, mune muka haife ki ba zamu cutar dake ba, da mutumin nan da ba nagartacce bane to da baza mu amince da bukatarsa ba to mun tabbatar da cewar idan muka dauke ki muka bashi muna da tabbacin zai kula dake kamar yanda ya kula dake a" "lokacin da baki san kanki ba.""" "Mikewa yayi ya shiga da'ki bayan ya gama maganarsa, Baba Talatu ta jima tana rarrashinta kafin ta mike" itama tabi bayan Malam din suka barta ita kadai a tsakar gidan tana kukan zucci. Mamaki take sosai! wai ashe dama Abban Abbas din ne ya bukaci auranta ita duk a tunaninta su Baba "malam ne, girgiza kanta kurrum take tana mamakinsa, to ta aureshi tayi yaya dashi? ta yaya za ta iya rayuwar aure dashi? lallai ma! ita abun ma mamaki yake bata ko kunya bai ji ba yace zai aureta bayan" "yana amsa sunan Uba a gurinta, gashi kuma yasan da maganar Salim hummm! aikam ba zata yarda ba" "duk yanda za tayi sai ta rushe wannan auran, sam ba zata auri tsoho dan shekara hamsin ba haka kawai" sun gina soyayyarsu da masoyinta yazo yayi musu kutse a rayuwarsu ko kunya baya ji zai zo da wannan maganar! 'Kwafa tayi ta mike ta shiga d'aki! Tana shiga dakin taji shashshekar kukan Saddiqa suna kwance ita da Mussadiq a katifa ta rungume shi sai kuka take! "A gigice ta kunna haske wayarta, tana haske su! Saddiqa ta rufe idonta tana sake takure jikinta guri" "guda. ""Ke Saddiqa menene? dama ba kiyi bacci ba.""? Saddiqa ta mike zaune tana goge fuskarta," "'Karasawa tayi ta zauna gefan katifar tana kallonta, a sanyaye tace""Meye kika kuka? nafada miki ki dainawa Mamma kuka idan kina so ta dinga samun rahamar ubangiji.""" "Saddiqa ta goge fuskarta tana kallonta tace""Ni ba Mamma nakewa kuka ba, nasan abinda nake yi a halin" "yanzu Mamma babu abinda take da bukata a gurinmu sai addua ba kuka ba.""" "A d'an sanyaye tace""To me kikewa kuka.""? Saddiqa ta kalleta wasu hawayen na sake zubo mata" "tace""Yaya Naja'atu me yasa kike nuna 'kiyayyar ki 'karara a kan Abbanmu.""!? Gabanta ne ya fad'i! sai tasha kunu! tace""Wace irin magana ce wannan Saddiqa? kada kice min kema kina goyon bayan na" "aureshi.""" "Saddiqa taja majina tana goge hancinta tace""To menene aibu a ciki? dan kin auri Abbanmu ai ba wani" "abun bane kuma ba ke kad'ai ce kika ta'ba auran *MADADI* ba Yaya Naja'atu idan kika maye gurbin mahaifiyarmu zamu ji dad'i sosai dan Allah kiyi mana wannan alfarmar ki daina nuna 'kiyayyar ki a fili.""" Shuru tayi tana nazarin maganar yarinyar! Wai shin da suke ta wannan maganar ta yaya zata fara ne? "wane matsayi zata ajiye shi miji ko mahaifi? bafa zai yiwu ba.! Ta kalli Saddiqan data kura mata ido tana jiran amsarta tace""Saddiqa nayi wa Abbanku 'kan'kanta kuma shima yayi mun girma bayan nan kuma ni matsayin mahaifi yake a gurina bazan iya rayuwar aure dashi ba, kuma ki daina tunanin ina 'kinsa wallahi bana 'kinsa saboda Abba Abbas yayi min abinda ba zan ta'ba mancewa dashi ba, kawai dai bana" "tunanin zan iya rayuwar aure dashi.""" "Saddiqa tace""To idan baki aureshi ba kin san dole yayi aure kuma gabadayan mu bamu san matar da zai" "aura ba, kinga zamu shiga halin 'kaka na kayi tunda dai kin san ba 'kaunar mu Anti Halisa take ba, kinga rayuwarmu na cikin 'kalubale nida Mussadiq.""" """Eh gaskiya ne duk maganar da kika fad'a to ai ba dole sai kun zauna tare da matansa ba, sai ku dawo" gidan Alhaji da zama ko kuma ku dawo gidanan nan nasan Baba Talatu zata ri'ke ku to meye abun tashin hankali. "Saddiqa ta shiga girgiza kanta zuciyarta na wani irin d'aci! tace"" Yaya Naja'atu kin manta maganar" Abbanmu kenan kin san fa yasha fad'a cewar mutuwa ce kawai zata rabashi da 'yayansa bana tunanin zai "amince ya kawo mu nan mu zauna ke ko gidan Alhajin da kike magana ba zai barmu muje ba duk da cewa gidansu ne.""" Naja'atu shuru tayi tana tunanin al'amarin Babu shakka zaman Saddiqa da Mussadiq hannun Halisa "gagarimun had'ari ne zata iya cutar dasu ta ko wace siga! Itace zata rike su tamkar uwarsu, to ita kuwa ko a mafarki bata tunanin zata koma gidansu a matsayin matar mahaifinsu, insha Allahu ta bar gidan har abada." "Ganin Saddiqan ta tsura mata ido yasa tace""To ki kwanta kiyi bacci zanyi tunani kan maganar ki.""" "Saddiqa taji farin ciki ya rufe ta tace""To shikkenan Yaya Naja'atu nagode Yaushe zaki gama tunanin.""?" "Kallonta tayi na minti biyu tace""Ke dai tunda nace zanyi to zanyi duk hukuncin dana yanke zan fada miki.""" "Saddiqa tace""To Ubangiji Allah yasa naji alkairi."" Amin tace a takaice, Saddiqa ta juya ta kwanta tana" adduar Allah yasa ta amince da maganar ta......... Tsuru tayi ta tsirawa guri guda ido tana tunanin yanda za tayi ta rusa wannan gagarimin al'amarin daya "tunkaro ta, kira ne ya shigo Wayarta dake gefanta, ta dauka hannu na rawa, a kunne tasa wayar, ta fashe da kuka 'kasa-'kasa tace""My prince kaji abunda Abbah Abbas ya 'bullo dashi ko.''" "Salim dake kwance kan katifar sa yace."" Menene ya faru ni banji komai ba."" Juyawa tayi tana kallon" "bayanta, dan bata so tayi wata magana ya kasance Saddiqa taji, sai da ta tabbatar da bacci takeyi sannan ta sake sassauta murya ta shiga fada masa abinda ke faruwa. Mi'kewa zaune yayi da sauri! lokaci" "guda gumi ya tsatstsafo masa, yace.""Da gaske kike wannan maganar ko kuma dai tsokanata kikeyi.""?" """Humm! wane irin tsokana wallahi tallahi da gaske nake wai Abba Abbas shine ya bude bakinsa yake" fadawa su Baba malam yana so ayi masa *MADADI* dani!!! "Katifar da yake kai ya doka! da hannunsa da 'karfi! Yace."" Kai kaji wata tatsuniya! shi yanzu dan girman" "Allah baiji kunyar fad'ar wannan maganar ba!!? To shin wai ko ya manta abinda yake tsakanina dake ne da har zai bijiro da wannan tatsuniyar.""" "Tace""Oho! ni gani nake kawai san zuciya ne yama za'ayi yace haka bayan shi da bakinsa ne yace.""Mu" "daidaita kanmu zai daura mana aure kuma saboda mutuwa ta ratsa tsakaninsa da matarsa sai yace a mayar masa dani a *MADADINTA.""*" "Salim yayi wani murmushi na takaici yace.""Ke nifa na daina mamaki! wallahi zai aikata dama yanda yake" "wani kula dake da wani takatsantsan a kanki akwai alamun tambaya dama so yake matarsa ta mutu ya aure ki! saboda haka ni kuma wallahi bazan bar masa ba, to in banda ma rigima ina ke ina shi! shekara hamsin har yake tunanin auran yarinya 'yar 'karama kamar ki 16years fa to idan ya aure ki yayi yaya dake?" "mtwwss.""!!" """Humm! ni wallahi Salim mamaki ma ya hana ni nace komai ba kaga yanda su Baba malam suke murna" "ba, wannan ai tauyewa mutum hakki ne. Ni duk na rasa ma yanda zanyi.""" "Yace.""Kece kuwa kike da yanda za kayi, tun kafin yafiya tayi nisa ki kokarin ganin kin rusa maganar ni" "kuma gobe idan Allah ya kaimu idan naje daukarshi domin zuwa kasuwa zanyi masa magana akan inaso yazo gurin Baba malam kan maganar auramu sai naji me zaice.""" "Tace""To yauwa kayi masa hakan nasan dole kunya tasa ya kasa magana ni wallahi duk mutuncin sa ma" ya zube a idona mtssssw!!! Takarashe maganar tana jan tsaki! "Yace.""Baby ki daina wani damuwa ki kwanta kiyi bacci bazan bari wannan al'amari ya tabbata ba, duk" yanda zanyi to zanyi na rusa al'amarin. "A sanyaye tace""Tom shikkenan my Prince kayi bacci mai dad'i kaji ko."" Yace.""Ke ina wani maganar bacci" "mai dadi a gurina Wannan dattijon na nema yasa zuciyata ta buga.""!!" """Hummm! kawai tace dan ta rasa ma abin cewa, kashe wayar tayi ta zurfafa cikin tunani da nazari!" gabad'aya bata so tayi masa rashin kunya saboda shi mutum ne mai muhimanci a gurinta to amma tunda ya 'bullo da wannan maganar kashi hamsin na 'kima da mutuncinsa suka zube a gurinta. "Numbarsa ta laluba ta dinga kallon numbar kamar shi take kallo, shawara take da zuciyarta shin ta tura" "masa text ko kuwa, wata zuciyar tace"" Idan kika tsaya lako-lako kan wannan al'amarin to za kiyi kuka da idonki Da sauri ta shiga rubuta masa text kamar haka." _Assalamu alaikum Abba nmu barka da dare ina tafan kana nan lafiya? Abbah wata magana naji daga bakinsu Baba malam kuma sun ce kaine kazo musu da maganar shine nake so naji daga bakin ka._ Tana tura masa text din ta kashe wayar! kwanciya tayi tana takure jikinta hawaye ne ke kokarin 'kwace mata tana kokarin hana shi fita. "Sai bayan da ya dawo daga sallahr asubahi ne ya kunna wayar tasa, aikuwa text din ne ya shigo yayi" saurin bud'ewa yana dubawa. Ya karanta ya kai sau biyar ya girgiza kanshi! lallai To bata yarda ba "kenan tana so taji daga bakinsa, shi kam bai san abinda zaice mata ba, kawai sai ya share bai mayar mata da amsa ba, ya cire jallabiyar jikinsa, ya kwanta rigingine kan bed din yana tunanin rayuwa, Halisa ce ta shigo dakin jikinta sanye da hijab kamar wata mutuniyar arziki, tun bayan mutuwar Halimatu wata" shiriya tazo mata takeyi komai cikin rashin kuzari. * MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~ *8* Tana tashi da asubah ko sallah ba tayi ba ta dauki wayarta ta kunna ta shiga dubawa wai ko ya turo mata "da amsa, wayar ta kai minti goma a hannunta tana jiran shigowar replay dinshi bai shigo ba, a sanyaye ta mike ta fita domun daura alwala, tana shigowa dakin ta sake daukar wayar tana dubawa, ganin alamun shigowar sa'ko yasa hannu na rawa ta bud'e! tsaki! mai 'karfi taja ganin messege din daga *Mtn* ne, jefar da wayar tayi kan katifa, idanunta na kokarin kawo ruwa ta shiga tayar dasu Saddiqa daga baccin da suke. Suna bude ido tace""Ku tashi kuyi alwala kuyi sallah."" Saddiqa ta sauko da sauri ta bude" akwatin kayansu makilin da brush ta dauka ta fita domin daura alwala. Cikin tsawa ta kalli Mussadiq "kamar shi yayi mata laifin tace""Kai ba zaka tashi ba sai na gaggaura maka mari ko.""! Yaron ya tashi a" "furgice yana kallonta! da hannu ta nuna masa 'kofar fita tace""Kaje kayi alwala gari ya waye."" sakkowa yayi daga katifar shima ya dauki abun wanke baki ya fita." "Hijab ta zura ta gyara dadduma ta tayar da sallah, Tana idarwa ba tayi wata adduar kirki ba ta sake" "daukar wayar tana dubawa, har yanzu dai babu amsa! Tsaki ta dinga ja zuciyarta na wani irin tafarfasa!" babu shakka Abbah Abbas da gaske yake! tasan yaga text d'inta kunya ta hana shi bata amsa shiyasa ya shareta. Numbar Salim ta laluba ta shiga kira. sai dai wayar a kashe take dan bai tashi ba ballanta ya kunna "wayar. Mi'kewa tayi ta koma bakin katifar ta zauna had'e da cire hijab din jikinta, Numbar Abbah" Abbas din ta sake nema ta 'kara tura masa wani text in kamar haka. _Abba ina jiran amsa nasan dai kaga text d'ina dan Allah ka bani amsa shin kaine ka nemi aure na? ko "kuma su Baba malam ne suka baka ni.""?_" Tura masa tayi ta tsirawa wayar ido tana adduar Allah yasa yayi mata magana. Shi kuwa Abbah Abbas yana kwance Halisa na matsa masa a jikinsa yana lumshe ido baccin da ya tara kwana da kwanaki "ne yake damunsa, tinda Halimatu ta rasu bacci da nutsuwa suka 'kaurace masa, mutuwar Halimatu" "babban gi'bi tayiwa rayuwarsa, gani yake ma ba zai ta'ba samun mace tagari kamar ta ba, Yayi yun'kurin auran Naja'atu ne ba dan komai ba sai dan yasan ita d'in tarbiyyar Halimatu ce yana kwadayin ta zama matarsa domin hausawa suna cewa gida bai 'koshi ba to ba za'a bawa dawa ba, bayan haka kuma yana tausayawa 'yan 'ya'yansa sosai saboda yanxu suna bukatar mai kula dasu sun saba da mamansu sosai dole idan suka dawo gidan suka ga babu ita su shiga damuwa, amma duk rintsi idan suna kallon Naja'atu" a gidan kuma a matsayin matarsa to zasu samu sassauci a tare dasu. Babban abinda yake d'aga masa hankali acikin al'amarin shine! yanda zai tunkare su da maganar! Salim "da Naja'atu gabadayan su bai san abinda zai ce musu ba, Salim bashi da Uban da yafi shi, hakan nan itama Naja'atu bata da uban da yafi shi, tabbas da zai iya hakura da ya hakura ya kyalesu sunyi auransu, amma ba yajin zai iya janye kudirinsa ba dan komai ba sai dan samun walwala da farin cikin 'yayansa guda biyu, saboda ya riga ya sani cewar babu wata mace da zai aura ta ri'ke masa su tsakani da Allah!" shiyasa yake ganin auran Naja'atun shine yafi alkairi a garesu baki daya. 'Dan juyawa yayi ya d'auki wayarsa ya bud'e text din ya sake bud'awa domin ya sake karanta sai yaga "wani ya sake shigowa, Ya bude idonsa sosai yana karantawa! Murmushi yayi wanda yasa Halisa kallonsa da sauri tace""Allah yasa alkairi ne naga kana murmushi."" Kallonta yayi yana kokarin rufe wayar dan ganin tana le'ko da kanta tana so ta ga abinda yakewa murmushin, a hankali yace.""Alkairi ne insha Allahu."" Tace""To Allah ya tabbatar mana dashi, mikewa tayi ta fita daga dakin tana fad'in ""Bari na shiga kicin na shirya abin karin kummalo."" Ya bita da kallo Ba tare da yace mata komai ba, ajiyar zuciya ya sauke bayan fitar ta daga d'akin, tabbas idan Halisa taji wannan babban al'amarin akwai tashin hankali! ya riga yasan halinta da mugun kishin tsiya! uwa uba kuma tsakaninta da Yarinyar basa jituwa ko kadan yanzu yanda zai tunkareta da maganar yake tunani Kira ya shigo wayar dake hannunsa, koda ya duba numbar" Naja'atun ce yayi serving da My doghtar! kamar kada ya daga sai kawai yayi 'kundumbala ya d'aga wayar "yana d'an gyaran murya, kafin ma yace wani abu yaji shashshekar kunanta a kunnasa." "Jikinsa ne yayi sanyi ya sassauta murya irin yanda yake mata idan tana irin wannan kukan yace.""Dota ya" "akayi kuka da sassafe kiyi shuru muyi magana ko.""!! hanci ta sha'ka! zuciyarta sai tafarfasa take tace""Abba tun jiya na turo maka da text baka bani amsa ba kuma nasan ka gani dan girman Allah ka bani amsar abinda na tambayeka ko na samu zuciyata tayi sanyi."""""""" Jim yayi kafin yace.""Kinga ni ban ga text" "d'inki ba ballanta na baki amsa amma kome kika rubuta min a text din ina sauraranki yanzu ki fad'a min.""" "Cikin rawar baki tace""Jiya bayan kasa Salim ya kawo mu gidan Baba Malam shine naji suna wata magana" "wacce tasa raina ya kusa futa daga jikina, ashe wai kai ba kaine ka haifeni ba , sannan babban abinda ya furgita ni yasa na shiga cikin halin damuwa da tashin hankali wai kaine da bakin ka kace musu su baka ni na zama *MADADIN* matarka da ta rasu, shine nake ganin kamar sune suke so suyi wannan had'in da bai dace ba! ai abun kunya ne ace wanda nake amfani da sunansa ako ina a matsayin mahaifina aji shine" "kuma zai aureni ina zan saka raina idan hakan ya tabbata.""!! Cikin sar'kewar murya ta 'karasa" maganar. Shuru yayi kawai yana jin saukar numfashinta a kunnansa bakinsa yayi masa nauyi gabad'aya ma ya rasa me zai ce mata. "Murya na rawa tace""Abbah wannan shurun da kayi yana nuna min cewar da gaske ne maganar daga" "bakin ka ta fito!!! Innalilihi wa'ina ilahi raji'un! kaico da wannan furucin naka! Abbah! dan girman Allah ka janye wannan maganar da kayi, na rantse da Allah ba zan iya zaman aure da kai ba ni a matsayin Uba na dauke ka.""" "Tana wani irin kuka take masa maganar, Yaji jikinsa duk ya mutu! Gumi ne ma yake tsatstsafo masa" "kamar ba safiya ba, da kyar ya iya cewa"" To naji maganar ki zanyi shawara a kai idan da akwai yuwuwar na hakura dake zan samu su malam d'in na fad'a musu duk shawarar dana yake, ki daina kuka haka kada ki janyowa kanki wani ciwon na daban."" Tace""To Abbah ni da daina kuka ai sai naji maganar wannan auran ta rushe sannan zan daina kuka.""!! Mamaki ya kama shi, da jin maganarta sai ma ta bashi dariya yayi kad'an kafin yace.""Naja'atu me yasa bakya son na zama abokin rayuwarki.""? Taji wani irin fad'uwar gaba jin abinda yace. Tace.""Abbah Please ba girman ka bane dan Allah kada ka 'kara yi min wannan maganar kai ubana ne *Salim* kuma shine abokin rayuwata."" Kishi ne ya kama shi jin abinda tace kawai" sai ya kashe wayar ba tare da ya sake cewa komai ba. "Ajiyar zuciya ta sauke bayan kashe wayar tasa, ta juya tana kallon Bayanta, Saddiqa da Mussadiq sun" "futa daga dakin tun d'azu! taji dad'in hakan, sai ta mike itama tabi bayansu dakin Baba Talatu." "Suna zaune a kusa da Baba Malam suna karyawa da kunu da kosai ta shiga da sallama a bakinta, a" "hankali ta tsuguna kusa da Baba Malam tana gaishe shi ya amsa cike da kulawa yana d'an nazarinta ganin idanunta sunyi jawur! yasa yace.""Ya kwanan kuka.""?" "'Kasa tayi da kanta! Baba Talatu tace""Kina so ki janyowa kanki damuwa da ciwo da kinyi halin Halimatu" "da ba kiyi mana gardama ba, Halimatu komai muka umarceta dashi tana mana biyayya dai-dai gwargwado amma ke tun jiya ake magana daya dake, idan kika bujirewa umarninmu baki kyauta mana ba kuma baki kyautawa 'Yar uwarki ba, a yanzu babu abinda za kayi kisa ta farin ciki illah ki zama" "*MADADIN TA* Ki tallafi abinda ta bari gasu nan suna kallonki."" Ta nuna su Saddiqa dake zaune." Shuru tayi ta kasa magana ba wai dan bata da abin cewa ba kawai dai bata son suyi ta sa'insa da iyayenta. Baba Malam dai shuru yayi ya dauki kofin kununsa yana sha yana had'awa da kosan sa dake cikin wata silba dake gabansa. Saddiqa ce ta zuba mata kunun ta ajiye mata a gabanta sannan ta mi'ka mata abun da 'kosan ke ciki "tace""Yaya Naja'atu gashi nan ki karya kema."" Kallonta tayi sai taji zuciyarta ta tsinke! sosai yaran suke bata tausayi Saddiqa ta damu da ita sosai koda can bata son taga 'bacin ranta, tabbas a wannan lokacin" ne ya kamata tayi mata sakayyar abun alherin data dad'e ta nayi mata. Domin Saddiqar taji dadi yasa ta dauki kofin kunun tana kur'ba a hankali tana had'awa da kosan dake "gabanta, Baba malam na gama karyawa sai ya dauki redion sa ya mike yana kallonta yace.""Idan kun gama kun kintsa ku shiga gidan Alhaji dake dasu Saddiqa ku gaishe dasu."" A sanyaye tace""Inasha Allah.""" takalmansa dake bakin kofa yasa ya fita daga gidan hannunsa ri'ke da redionsa. Suna gama karyawa sai sukayi wanka suka shirya tsaf! Naja'atu da Saddiqa suka shirya cikin kaya iri daya "hatta da d'inkin jikin atamfar iri daya ne komai iri daya Abbah Abbas ke musu baya bambamta su sai da gurin d'inki na Naja'atu yana d'ara na Saddiqa da wani abun, milk din hijabi toyobo ne a jikinsu ya sauka har 'kasa! Suna kokarin fita daga gidan da nufin shiga gidan Alhaji Sama'ila, Shi da Salim suna kokarin" shigowa cikin gidan. 'Kamshin turaransa ne ya tabbatar mata da cewar shine Kafin ma tayi wani yunkuri sun shigo Shine a "gaba Salim na take masa baya, Yana sanye da farar shadda kar 'Dinkin tazarce har kasa, da adon surfani a wuyan rigar da hannunta kansa sanye da farar hula mai ratsin 'baki! a zahiri idan ka kalleshi ba zaka ce ya kai shekarun da yake dasu ba, za'afi tunanin shekarunsa ba sufi 43 zuwa 45 ba, Abbah Abbas mutum ne dan gayu mai yawan ado da kwalliya, kuma ma'abocin kamshi shiyasa kullum baka ganin tsufasa, dan idan yace ya kai matakin shekara 50 a duniya da yawa wasu ba zasu yarda ba, sai dai kuma masu nazari da tunani idan sukayi masa kallon tsanaki a zasu fahimci cewar ya kai shekarun da ya fad'a d'in Da gudu Mussadiq yaje ya rungumeshi yana fad'in ''Oyoyo Abba."" Yana d'an murmushi ya bashi" "hannunsa tare da fadin""Barka da Asuba magajin Abbah."" Mussadiq na dariya ya rike hannun mahaifin nasa suka gaisa sosai Saddiqa na murmushi tace""Abba ina kwana ka tashi lafiya.""? A nutse ya d'aga" "kansa yana kallonsu ita da Naja'atun Yace.""Lafiya lau na tashi Ina zakuje da sassafe haka.""? Yana kallon" "Naja'atu yayi maganar.""!" "A kanta a kasa ta gaishe kafin tace""Zamu shiga gidan Alhaji ne mu gaisa."" Yace.""To babu damuwa nima" "yanzu zan shigo gidan.'' Kokarin ratse ta yake ya shiga cikin gidan, tayi saurin bashi hanya, tana sunkuyar" "da kanta, gani tayi yau fuskar sa babu walwalar da ya saba yi mata koda yake ai dole dama ya kasa sakin jiki da ita saboda yasan abinda yayi." "Ta kalli Saddiqa tace""Kuje gani nan zan biyo bayanku."" Saddiqa ta kalleta tana kallon Salim da yayi wani" kici-kici da fuska yana kallonta ya wani zuba hannuwansa a cikin aljihun jins din dake jikinsa. Saddiqa jikinta sanyi yayi ganin yanda Naja'atun ta wani d'aure mata fuska! sai taja hannun Mussadiq suka fita daga gidan "Salim ya tsira mata ido bayan fitar su Saddiqa yace.""Me kike fahimta ne daga gurin wannan Dattijon.""?" "Cikin sanyin jiki da sarewa da al'amarin tace""Ni wallahi har yanxu na kasa gane inda ya dosa, dazu dai munyi waya dashi na ro'ke shi akan ya janye kudirinsa yace.""zai yi shawara idan ya yanke magana zai fad'awa Baba malam abinda ake ciki.""" "Cikin 'kunar zuciya Salim yace.""Jikina baya bani cewar Mutumin nan zai hakura dake My Princess shin" "idan ya kasance shine ya samu damar mallakar ki ya zanyi da raina watakila ma ina jin shikkenan 'karshen rayuwata ne yazo."" Cikin wata iriyar siga yayi maganar yana matsawa kusa da ita." "Hawaye ne suka 'kwace mata tace""My Prince ka daina wannan maganar dan Allah insha Allah Allah ba" "zai bashi nasara ba, Ni bani da wani miji sai k Maganar ce ta ma'kale a bakinta sakamakon zuwansa" "gurin! Ya kallesu sunyi wani daf da junansu kamar zasu rungume junansu, kana kuma kallon yanayin su zaka fahimci suna cikin mayen son junansu a lokacin kome zasu iya aikatawa! Tsawa ya buga musu yana" "kallon Salim din Yace. ""Kai meye haka ka tsaya daf da ita rungumeta zakayi ko me.""?" "Salim yayi gaggawar barin kusa da ita yana sosa kansa irin na kunya yace.""Kawu kasan sau tari nakan" "shiga wani yanayi idan yarinyar nan na kusa dani, dan Allah Kawu kayi wani abu akan al'amarin aurena da ita.""" Kallon shashasha yake masa kafin yayi 'kwafa ya kalleta tana ra'be a jikin bango tana goge fuska! Kamar "zai ce wani abu sai kuma ya fasa, ya kalli Salim din rai a 'bace! yace""Shige muje."" Salim ya shiga sosa kansa yana d'an kallonta ta 'kasan ido ya fita daga gidan, shima ba tare da ya sake kallon inda take ba ya fita ranshi a 'bace! wani irin kishi ne yake damunsa a zuciyarsa ganin abinda ya wanzu tsakaninta da" Salim.. * MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!))_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _Kungiyar Masu Nazari Da aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~~~~~~~ *9* "Cikin sanyi jiki da mutuwar jiki ta fita daga gidan, koda ta fita kai tsaye gidan Alhajin ta nufa tana tafiya" "kanta a kasa ga wani irin fad'uwa da gabanta yake, tana tunanin idan ta shiga gidan da wane irin ido zata kalli mahaifiyar Abbannasu matar data dauka a matsayin kakarta suke wasan jika da kaka da ita, yau an wayi gari wai itace take nema ta zama surukarta akwai kauna da fahimta a tsakaninta da Hajiyar tana ganin idan Abba Abbas din bai janye 'kudirin sa ba zata nemi taimakon matar tunda mahaifiyarsa ce" watakila idan tayi masa magana ya janye. "Tana shiga gate din gidan, ta hangi Abba Abbas din da Abba Alhassan 'kaninsa da kuma Salim d'in a tsaye" "a jikin wata mota suna magana, Tun daga nesa take kallonsu Abba Abbas din! Tsaki! taja a zuciyarta ta kalli Salim dake kusa dashi, humm yaushe ma za'a had'a! Salim saurayi mai tashe mai jini a jika gashi dan gayu dan kwalisa, babu abinda yake burgeta a dashi sai 'kayatacciyar fuskarsa mai dauke da siririn saje wanda yayi masa kyau sosai tana bala'in son Salim saboda kyawunsa kuma ya iya kwalliya mai burgewa, shi kuwa Abba Abbas ya wani bar gashin fuska (gemu ) ya cika masa fuska duk da cewa a gyare yake hakan bai burgeta ba, babban abinda yake 'kara sawa ta sake jin tsanar auransa, shine tsali- tsalin furfurar data fara fito masa a gashin fuskarsa(gemu) Ai abin dariya ne ma ta nunawa kawayenta shine mijinta, gaskiya ita kam ba zata iya auransa ba, a tsarinta tafi son ta auri Saurayi wanda zasu mori" 'kuruciyarsu amma auran Abbah Abbas babban nak'asu ne a tattare da ita "*(Humm! Waye ya fad'a miki haka Naja'atu."")*" A nutse ta iske inda suke tsaye kamar munafuka ta dinga 'boye fuskarta tana gaishe da Abbah Alhassan ya amsa fuska a sake yana d'an kallonta a fakaice hakika yarinyar na burgeshi mutuka tana da hankali da nutsuwa kuma babu shakka idan d'an uwansa ya aureta yayi dace da samun mace tagari. Abbah Abbas kuwa kokarin shiga mota yake yi bai ko kalleta ba dan har yanzu haushinsu yake ji ita da "Salim d'in Simi-simi ta wuce cikin gidan, Abbah Alhassan ya shiga motar ya zauna kusa da d'an" "uwansa, Salim yaja motar suka nufi kasuwa." Hajiya Abu na zaune a 'kasan kafet Saddiqa da Mussadiq na gefanta suna mata wasa kamar yanda suka saba idan sunxo gidan ita kuma sai biye musu takeyi ta ri'ke hannun Mussadiq tamau! wai sai ya bata kud'in shara na shekara biyu! Yaron sai dariya yake mata yana cewa ta sake shi zai tambayi Abbansu ko nawa take so za'a bata. Ita kuwa tayi kici-kici da fuska kamar gaske tace ita sai ya bata zata cika masa hannu idan kuma bai bata ba sai ta cire masa kayan jikinsa a bakacin kudinta. Saddiqa sai dariya take "musu, Mussadiq na ganin Naja'atu ta shigo yace.""Yawwa Yaya Naja'atu kizo ki cece ni a gurin tsohuwar" "nan tana so ta karya min hannu."" Hjy Abu tace'' Kina zuwa nan sai na murd'e miki hannunki dan dukkanin ku zan iya daku.""" "Naja'atu tasa dariya tana k'arasawa gurin tace""Lallai Hajiya 'karfi ne dake haka duba kin murd'ewa yaro" "hannu ki fad'i nawa ne kudin sai a biya ki."" Tace.""Ai ba zaku iya biya na ba."" Tace""To dan Allah sakar masa hannu ya tuba."" Tana dariya ta sake shi tace""Ja'iri ashe ba wani karfi ne dashi ba."" Yace.""Hajiya aike tsohon 'kashi ne dake ni kuwa sabo ne shiyasa da kika ri'ke ni na kasa kwacewa."" Gabadayan su suka sa dariya har da ita." "Naja'atu ta zauna a nutse tana gaisheta! Ta amsa cikin kulawa tana kallonta tace""Dama kuwa ina neman" "ki amma ki fara zuwa ku gaisa da Alhaji yana sama sai kizo mu tattuna magana kinji 'kawata."" Naja'atu ji tayi gabanta ya fad'i !!! to wace magana zasu tattauna da hajiyan? tabbas ta tsuniyar gizo bata wuce ta 'koki! sai" Tayi kokarin kauda damuwar fuskarta tana kokarin mikewa tace to shikkenan bari naje mu gaisa da "Alhjin.""" "Sama ta hau inda dakin Alhaji Sama'ila yake, nan ta tarar da Hajiya Rabi a dakin tana gyare-gyare suka" gaisa cikin mutunci kafin ta shiga dakin da yake ciki Tayi kusan minti goma a ciki kafin ta sauko "'kasa suna zaune a inda suke suna hira koda ganin zuwanta gurin sai sukayi shuru Saddiqa ta dinga bin fuskarta da kallo ganin kamar ta sauko da damuwa a tare da ita............zama tayi kusa da Hajiyan cikin tunanin mafita tace""Hajiya gani to na dawo."" Hajiya Abu ta gyara zamanta sosai ta bude bakinta kenan za tayi magana, Yaya Ramlatu ta shigo bakinta dauke da sallama. Amsawa sukayi gabadayan su, Ramlatu na ganin Naja'atu kusa da Hajiya sai ta 'bata rai! tayi kici-kici da fuska dan koda Naja'atun ma ta gaisheta bata amsa ba sai gaisuwar su Mussadiq ta amsa! Naja'atu jikinta yayi sanyi ta sunkuyar da kanta kasa" tana jinta tana tambayar su Saddiqa ina Abbansu suka ce ya tafi kasuwa! "Yaya Ramlatu ta kalli Mahaifiyar ta tace""Hajiya wata magana naji daga bakin Salim dazu da safe yake" "fada min shine nace to bari nazo naji shin da gaske ne abinda ya fad'a wai Abbas zai auri waccan yarinyar ta zaune."" Tana nuna Naja'atu da hannu tayi maganar." "Hajiya Abu a nutse tace""Eh kwarai kuwa hakane Salim bai miki karya ba! Abbas zai auri Naja'atu insha" "Allah sai ta zama *Madadin* 'Yar uwarta ko babu komai wad'annan yaran zasu samu walwala da farin ciki.""tafada tana nuna su Saddiqa." "Yaya Ramlatu ta zabga salati tana tafa hannu tace""Haba Hajiya da hankalinku da komai zaku bari" wannan al'amarin ya faru? Yanzu shi Abbas din ko kunya baiji ba zai auri yarinyar da ya ri'ke ta a "matsayin 'yar sa, yarinyar da kuma ya san Salim ne ke neman auranta shine kuma zai had'a takara dashi! a gaskiya wannan abu bai tsarantu ba! gwara tun wuri yayi wa kansa fad'a dan wallahi idan ya sake ya auri wannan yarinyar to duniya sai ta zage shi saboda ya aikata abun kunya, kuma baiyi wa Salim adalci" "ba.""" "Hajiya Abu tace""Kece kike ganin kamar hakan bai dace ba amma *MADADI BA HARAM BANE* Dan ya ta" "mutu a mayar da kanwa d'akinta ba laifi bane! Kuma naji kina cewa duniya zata zagi Abbas a kan me? duniya zata zageshi? naga ke da kanki kika nuna bakye so 'Danki ya auri yarinyar to me yasa kuma yanzu zaki zo da wata magana, idan Salim mai hankali da tunani ne ya dace yayi wa Kawunsa adalci ya hakura" "da yarinyar ya bar masa kodan marayun 'yayan dake gabansa.""" "Yaya Ramlatu tace""A'ah!! ni ban hana Salim auran yarinyar nan ba wallahi a duk lokacin da zamuyi" "maganar auransa yakan ce dani Abbas din ne yake cewa ya dakata tukkuna zaiyi magana da iyayenta, sai kuma yanzu kawai daga ya rasa matarsa ya 'kwace masa budurwa ai hakan sam bai dace ba.""" "Hajiya Abu tace""To ai sai kiyi tayi dan tuntuni an riga an gama magana insha Allahu kafin nan kafin sati" "uku za'a daura auran Abbas da Naja'atu insha Allah.""" Wani irin kuka ne ya kufcewa Naja'atu! da sauri duk suka juya suna kallonta! had'a kanta tayi da gwiwa "tana kuka sosai da sosai! Yaya Ramlatu tace""To hajiya gashi nan dai kin gani zahiri yarinyar nan bata son wannan al'amari dan dai ba zata iya fitowa ta fada muku bane! a wannan zamanin ba'a yiwa yaran yanzu auran dole kada ku tauyewa yara hakkinsu, ni a ganina Abbas ya hakura kawai ya barwa Salim shine" "maslaha.""" Hajiya jikinta ne yayi sanyi ganin irin gursheken kukan da Naja'atu keyi tana kokarin tayi magana Alhaji Sama'ila ya sauko daga sama! "Ganin Naja'atu na kuka sai hankalinsa ya tashi ya zauna kan kujera yana tambayar abinda ke faruwa," Yaya Ramlatu ta shiga warware masa duk abinda yake tsakin Salim da Naja'atun da irin soyayyar da suke. "Alhaji Sama'ila yayi shuru yana nazarin maganar, shi duk abinda akeyi bai san da maganar Salim a ciki ba," "to gaskiya idan hakane shi Abbas din shine ya dace ya hakura da yarinyar duba da cewar maganar Salim din ta dad'e kuma shi ya san da ita bai fad'a ba saboda biyan bukatarsa, wannan ba adalci bane, a matsayin sa na wanda suka dauka a matsayin uba a garesu to bai dace yayi musu haka ba, dole ya janye" maganar auran yarinyar ya kyale yara suyi auransu. "Ya kalli Naja'atu a nutse yace.""Daina kuka Naja'atu ki kwantar da hankalin ki insha Allah ba zaki auri" "Abbas ba tunda bakya sonsa zamu baki wanda kike so insha Allahu.""" Jin abinda Alhajin yace yasa Saddiqa ta fashe da kuka!! ta had'a kanta da gwiwa tana shashsheka! tofa "gida ya zama na makoki mutuwa ta dawo sabuwa dan Saddiqa rungume Mussadiq tayi tana fad'in ""Mussadiq mutuwa tayi mana tonan silili kowa sai gudun mu yake ana neman kai damu! meye laifin Ubanmu da ba'a sonsa! Ubangiji Allah ya zama gatanmu."" Hajiya Abu ta rikice da kuka ta kama yaran ta rungume a jikinta tana fad'in ""Babu wanda ya isa yayi neman kai daku! Kuma insha Allahu Naja'atu zata" "tare a gidan ubanku.""" Yaya Ramlatu jikinta ne yayi sanyi ganin mahaifiyar tata na kuka. Bayan alhajin ya fita Hajiya Abu ta "goge fuskarta tana kallon Ramlatu tace""Kin kyauta kan abinda kikeyi kullum burin ki ki tayar min da hankali bakya kaunar na zauna lafiya yanzu meye amfanin wannan abun da kika zo kikayi ashe kinfi kaunar d'anki a kan d'an uwanki? meye Abbas beyiwa d'anki ba amma da abunda zaki saka masa kenan! kinzo kin saka marayu kuka da damuwa suna cikin damuwa a maimakon ki taya su alhini sai kizo ki sake" "saka musu wata damuwar to sun gode da abunda kikai musu.""" "Yaya Ramlatu ta share guntin hawayen fuskarta a sanyaye tace""Hajiya ban san al'amarin zaiyi miki zafi" "haka ba dan Allah kiyi hakuri idan ranki ya 'baci kuma insha Allahu zan umarci Salim ya janye maganar auransa da yarinyar Allah yasa haka shi yafi alkairi.""" Jin abinda tace ne yasa Naja saurin kallonta hawaye na tsere a fuskarta shikkenan magana ta 'kare! jiki a sanyaye ta mike ta fita daga palon. "Salim na driving maganar dake damusa nata cin zuciyarsa, ya dan kalli Kawun nasa dake bayan mota shi" "da 'Kaninsa suna magana, Yace.""Kawu ina da magana da kai.""! Babu walwala a tare dashi yace.""Ina sauraranka."" Da kyar iya cewa ""Dama kan maganarmu ta kwanaki ce."" Kamar be san komai ba yace.""Wace irin magana kenan.""? Salim cikin dakewar zuciya yace.""Maganar Naja'atu mana a cikin 'yan kwanakin nan gabadaya zuciyata ta kasa daurewa sai nake ganin kamar akwai wani abu da zai faru dan" "Allah ina so kaje ka nema min auranta kamar yanda kayi min al'kawari a kwanakin baya.""" "Shiru motar tayi babu wanda yayi magana, Abbah Alhassan mamakin maganar da Salim din yayi yake" ashe dama soyayya ce a tsakanin Salim da Yarinyar? to me yasa dan uwan nasa yasan da soyayyar dake tsakaninsu ya bijiro da bukatarsa. "Shuru Abba Abbas yayi ba wai dan bashi da abin cewa ba, sai dan ganin cewar shi a gurinsa a bin kunya" "ne ace yana maganar aurensa da Salim d'in, yafi so yaron yaji maganar a bakin wani idan yaso ya gane ruwa ba'a sa'an kwando bane...." "Shurun da yayi tasa jikin Salim yin sanyi, tabbas yanzu ya gazgata maganar Naja'atu cewa Abba Abbas" din da gaske yake ba gudu babu ja da baya. Yaji wani irin d'aci! a ma'kogwaronsa! dishi-dishi! yake gani a idonsa tsabar bakin ciki da 'bacin rai! Ga wani masifar kishin Kawun nasa dake sasakar zuciyarsa! Wai yau an wayi gari wanda yake tunanin shi zaiyi masa wakilcin aure shine yake kassaya dashi Shi kuwa Abbah Alhassan ganin 'Dan uwan nasa bai ce komai ba yasa yaja bakinsa yayi shuru haka suka isa kasuwar kowa na sa'ke-sa'ke a zuciyarsa mussaman Salim da yake jin shigar zazzafan zazzabi a jikinsa. Yaya Ramlatu na fita daga gidan Alhaji Kai tsaye unguwar gwangwazo ta nufa gidan d'an uwan nata........Halisa na zaune a palo tana kallo Yaya Ramlatu ta shiga da sallama a bakinta. Halisa ta mike tana mata barka da zuwa taje ta kawo mata abinci da ruwa da lemo kana ta zauna suna gaisawa. "Yaya Ramlatu sai da ta cika cikinta ta 'koshi tukkuna, ta kalli Halisan tace""Kin san gagarimar maganar da" "nake tafe da ita kuwa.""" "Halisa taji gabanta ya fadi! a sanyaye tace""Ban sani ba Yaya sai kin fad'a.""" "Murmushin takaici Yaya Ramlatu tayi kafin tace""Kina zaune da baki a bud'e har kin samu damar zama" "kiyi kallo ana can ana shirya miki kasassa'ba.""!! Halisa miyau ya dauke daga bakinta tace""Yaya Ramlatu dan Allah fad'a min abinda ke faruwa.""" "Ajiyar zuciya ta sauke kafin tace""Mijinki Abbas nacan yana neman auran budurwa 'yar cikinsa, auran" "cuta da ha'inci Auran da duniya za tayi turr! dashi.""!" "Halisa ta zabura! ta dafe kirjinta gabanta na wani irin buguwa tace""Aure kika ce Yaya Ramlatu.""""?" "Tace""Kwarai kuwa."" Tafada tana tabbatar mata da gaskiyar magana" "Wani irin gumi ne ya shiga tsiyaya daga jikin Halisa! ""Aure!aure! kalmar ma ba babu dadin ji a kunnanta," "wato duk ladabi da biyayyar da take masa da nuna masa kulawar da Halimatu take masa bai sa yaji sha'awar aure ya fita daga ransa ba? ashe duk abinda takeyi masa na kulawa a banza take mutuwar Halima ko sati biyu ba'ayi ba amma har ya fara kokarin aure, shin wai dame ta gaza ne a gurinsa. wasu" "hawayen takaici da bakin ciki ne suka shiga sauka a kumatunta. Yaya Ramlatu tace."" Ai ba kiyi kuka ba" "ma tukkuna sai kinji yarinyar da zai aure.""! Bakinta na rawa tace.""Wacece.""? Kai tsaye Yaya Ramlatu tace""Naja'atu ce.'' Sai tayi kasa'ke tana kallonta tunani takeyi wacece ma Naja'atu! dan a lokacin gabadaya kwakwalwarta ce ta toshe ta mance a inda tasan mai irin sunan.""" "Yaya Ramlatu tace''Kina mamaki! ko da jin wacce mijinki zai aura bari na 'kara tabbatar miki da maganar," "Abbas zai auri Naja'atu kanwar matarsa Halimatu yarinyar da ya ri'keta tun tana 'karama yayi mata komai tamkar 'yar cikinsa! shine yanzu zai maye gurbin 'yar uwarta da ita."" Halisa ta dinga jin hajijiya tana daga xaune! rintse idonta tayi tana tunano siffofin Naja'atu a idonta!!! a gigice ta bude idonta ta zabura ta mike tsaye tare da cewar ""Wallahi ba zaiyi wuba !! ba zan yarda da wannan cin amanar ba! Ni Abbas zaiyi wa haka? me nayi masa a duniya zai had'ani kishi da yarinya 'karama 'yar cikina! kutumar uban nan kayyasa!! sai ta zube kasan kafet ta fashe da wani mahaucin kuka tare d'ora dukkanin" hannuwata a kanta. * MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~ *10* "Wani irin kuka Halisa takeyi tamkar wacce aka aiko mata da mutuwar iyayenta, ta d'ago kanta tana" "kallon Yaya Ramlatun fuskarta gaje-gaja da hawaye tace""Yaya Ramlatu ina zan saka kaina da wannan abun kunyar! shin wai me yake damun d'an uwanki ne? Ya rasa wacce zai aura sai 'yar cikinsa yarinyar da ya ri'ke tamkar shi ya haifeta amma saboda tsabar abun kunya yace zai aureta tsofai-tsofai dashi zai auri 'yar 'karamar yarinya babu shakka wannan karon komai zai faru tsakanina dashi sai dai ya faru dan na rantse da Allah ba zan bari ya tozartani ya had'ani kishi da matsiyaciyar yarinyar nan da na riga nasan" "matsayinta a zuciyarsa ba.""" "Ya Ramlatu ta sauke ajiyar zuciya tana fad'in ""Ai shiyasa nima dana ji labarin hankalina ya tashi sosai!" Kishi da irin jinin Malam Baba ai bala'i ne wane irin daurin gindi ne Halimatu bata samu ba a gurin Abbas "din, ai wallahi kece abar tausayi mutukar kika bari ya auri yarinyar nan to ki rubuta ki ajiye auran ki ya 'kare tsakaninki da mijinki.""" Yaya Ramlatu ta 'kare maganarta cikin karfafa maganar ta gami da 'kokarin 'kara ingiza zuciyarta. "Goge fuskarta tayi tace""Yaya Ramlatu ai na fad'a miki wallahi tallahi sai dai ya za'ba ko ni ko yarinyar nan" "dan ni ba zanyi kishi da Yayarta ba itama nazo nayi da ita ba, wannan karon duk abinda yake ji dashi dai- dai nake dashi zai dawo gidan ya same ni.''" "Yaya Ramlatu ta dauki lemo ta kur'ba tace""To ai dik da haka ba zama za kiyi ba dole ki d'an nemi taimako" "dan baki san irin shirin da iyayen yarinyar suke a kan al'amarin ba, dan wannan tsinannan Malam Baba mugun mutumi ne babu irin surkullan da bayayi."" Halisa tace""Yaya Ramlatu ni yanzu gabadaya ma banda kuzarin zuwa gurin wani malami da sunan taimako nifa gabad'aya auran Abbas ya fice min daga rai ya dawo ya sake ni."" Ta'karasa maganar cikin rawar murya. Yaya Ramlatu tace""A'a ba za'ayi hakaba ke yanzu idan kika kashe auranki saboda wannan yarinyar ai kin cutar da kanki! kada kice ya sake ki kawai idan ya dawo ki daga masa hankali ke macece kin san hanyoyin da zaka hanashi nutsuwa da kwanciyar hankali gefe guda kuma zamu sa malamai su taimaka miki insha Allah sai zuciyarsa ta karye yaji sha'awar" "auran ya fita daga ransa da kansa zaice ya fasa.""" "Halisa tayi shuru tana tunani! Yaya Ramlatu tace""Dole ki futo da kudi aje a taimaka miki ni gaskiya bazan" "so ki bar dakin ki ba, ki zauna kici ubansu daga shi har yarinyar idan Allah ma ya kaddara sai ta shigo gidan sharri kad'ai ya isheta." "Halisa taja ajiyar zuciya tare dayin 'kwafa, tace""Maganar ki haka take Yaya Ramlatu bari na kawo miki" "dan abinda ke hannuna dan Allah kiyi min kokari akan al'amarin."" Yaya Ramlatu tace""Kada ki damu zan shiga na fita insha Allahu maganar auran zata rushe ke idan ma Allah ya kaddara auran to wallahi ba zamu k'yalesu suji dad'in rayuwa ba."" Halisa ta gyada kanta tana dan jin sassauci acikin zuciyarta, bedroom dinta ta nufa, minti biyar ta fito hannunta rike da kudi 'yan dubu dubu. Ta mikawa Yaya Ramalatun da fadin ""Dubu ashirin ne zuwa gobe sai ki aiko a kar'bi dubu talatin din zanyi duk yanda" "zanyi na dauki key din gurin da yake ajiyar kudi na dauka.""" "Yaya Ramlatu ta mike tana gyara yafan mayafinta tace""Nima daga nan zan wuce gidan *'Yar shagamu*" "(wata hatsabibiyar 'kawar Ramlatun ce)Ta cigaba da cewa. ""akwai wani malami da mukayi hirarsa" "kwanaki da ita tace ya iya aiki idan dare baiyi ba zamuje idan kuma dare yayi to da sassafe zamu buga sammako dan kada muje mu tarar da mutane."" Halisa taji wani sanyi a ranta tace""Yaya Ramlatu nagode kawarai da kaunar da kike nuna min hakika ina alfahari dake a cikin 'yan uwan Abbas kina nuna min" "kaunar da mahaifiyarku ma bata nuna min.""" "Yaya Ramlatu ta dafa kafadarta tace""Kada ki damu cikin ko wane irin hali ina tare dake, maganar" "Hajiyarmu kuwa dama can tafi kaunar Halima a kanki saboda gidan Malam Baba sun riga sun gama dasu daga ita har Alhajin, dan baki ga yanda suke murna da wannan al'amarin ba, Hajiya har da kuka tana 'kokarin yi min baki akan nace auran Abbas da yarinyar bai dace ba, shine fa take kuka har dayi min gorin" "abinda Abbas din keyi wa Salim.""" "Halisa ta shiga girgiza kanta, cikin 'kunar zuciya tace""Ai ba sai kin fad'a mun ba dama tuntuni na san" "Hajiyarku bata sona ko lokacin Halimatu tafi nuna kulawarta a kanta, to kinga kuwa dole taso wannan al'amarin ni na rasa me nayi mata ta tsaneni.""" "Yaya Ramlatu tace""Wallahi duk sharrin daga gidan Malam Baba yake gabadaya fa sun gama da zuciyoyin" "jama'ar gidanmu nice kadai na gagaresu."" Halisa na jin d'aci a ma'kogwaronta tace""Insha Allahu sai mun karya alkadarinsu.""" To sallama sukayi da juna inda Yaya Ramlatu take sake tabbatar mata da cewar yanzu idan ta fita gidan *'Yar Shagamu* zata nufa domin su tattauna yanda al'amarin tafiya gidan malam zai kasance. "Koda Naja'atu ta koma gidan Malam kai tsaye dakinsu ta shige taje ta kwanta kan katifa, ta dinga kuka" tana birgima kan katifar! sai sambatun surutai take da kiran sunan Halimatu wai ta mutu ta bar baya da 'kura mutuwarta tana nema ta zame mata barazana ga rayuwarta. Sautin kukan tane ya cikawa "Baba Talatu kunne da sauri ta fito daga kicin ta nufi dakin, nan ta tarar da ita sai burgima take kan katifa tana dukan kanta da kanta kamar wata mahaukaciya sai surutai takeyi da fad'in in dai aka daura mata aure da wani ba Salim ba to sai ta kashe kanta ta kashe wanda aka aura mata. Baba Talatu ta shiga" dakin hankalinta a tashe ta birkitota wani wawan mari ta kifa mata a fuskarta tana wani irin huci!! Rintse idonta tayi ta mike zaune hannunta kan kuncinta idanunta a rufe amma hawaye ne kawai yake zurara. "Murya na rawa Baba Talatu tace""Naja'atu idan baki kashe kanki kin kashe Alhaji Abbas ba bakya kaunar" "Allah! Wai shin ke d'in wace irin yarinya ce butulu mai manta alkairi! yanzu da abinda zaki sakawa da wannan bawan Allahn kenan? wannan wace irin 'kiyayyace kike nuna masa 'karara? meye bai miki ba? ki sani idan da mutuwa bata ratsa tsakaninsa da matarsa ba ke baki isa ya kalleki ba ballanta yace zai aure ki dan saboda baki dace daki auri nagartaccen namiji kamar wannan ba! meye laifinsa? meye kuma illarsa!? Muna tsaka da alhani gami da rad'ad'in mutuwar 'yar mu mai biyayya kina nema ki d'ora mana ciwo! ashe bamu isa dake ba? ashe kuma Halima bata cancanci sakayya al'kairi a gurinki ba? Idan kin auri mijin Halimatu babu wanda zai kai ki Jin dad'i itama kuma zata samu farin ciki alkairin da kikayi mata kin auri mijinta bayan babu ranta kin tallafi 'yayanta! to wallahi duk sanda na kara jin kinyi wani mummunan furuci kan wannan bawan Allahn sai ranki ya 'baci! sai na fad'awa Magaji duk abinda kike yi tunda ni da malam kin raina mu bakya ganin mutuncin mu.""!! Baba Talatu ta kare maganarta cikin tsantsar 'bacin rai" gami da jin takaicin abinda 'yar tata takeyi. Baba Talatu fita tayi daga dakin ranta a 'bace! hakika yarinyar bata ta'ba 'bata mata rai ba irin yau! ita "rasa gane meye abin gudu a game da wannan auran da suke kokarin had'awa, a iya tunaninta da tsinkayen ta tana ganin kamar gata sukayi wa yarinyar har indai sun had'ata aure da mijin 'yar uwartata dan hausawa na cewa Naji dad'i shine gari ba nasa baba. Baba Talatu na fita daga d'akin ta zame a" "hankali ta kwanta kasan ledar dakin tana takure jikinta ta cigaba da kukan rashin mafita, a lokacin ji take yi dama Allah zai dauki ranta ta huta daganin wannan masifar. Koda Saddiqa da Mussadiq suka" "shiga dakin suka sameta a kwance tana kuka! Mussadiq ne kawai ya tsaya a kanta yana mata magana ita kuwa Saddiqa saboda tasan ko kukan me takeyi yasa ta juya ta fita daga d'akinta ranta a 'bace! hakika tana jin ba'kin ciki da takaicin irin 'kiyayyar da take nunawa mahaifinta, shiyasa itama ta soma jin" haushinta akan irin abinda takeyi kan al'amarin. Mussadiq ya 'karaci maganarsa ko kallonsa ba tayi ba haka ya fita daga dakin jikinsa duk a sanyaye! haka suke shiga damuwa koda can idan sun ganta tana kuka ko rashin lafiya daga su har mamansu da Abbansu duk su damu duk da bashi da wayo sosai shima ya fahimci cewar Antin tasu bata 'kaunar zaman aure da babansu. Zama yayi kusa da Saddiqa tana gyarawa Baba Talatu wake suna hira jefi- "jefi ya kalli Baba talatu da fad'in ""Baba me akayiwa Yaya Naja'atu take kuka.""? Baba Talatu tace."" Kyaleta Mussadiq ka fita daga sabgarta kaji ko."" Mussadiq yayi shuru jikinsa duk yayi sanyi To Har aka idar" da sallahar azuhur Naja'atu na kwance a daki tana juye-juye zazza'bi me zafi ne ya rufe ta wanda ya hanata mikewa taje tayi alwala tai sallah. "Saddiqa ta shiga dakin domin yin sallah ta kalleta itama ta kalleta babu wanda yace komai a tsakaninsu," "Saddiqa ta gyara dadduma ta tayar da sallaharta, koda ta idar mikewa tayi ta fita daga dakin ba tare da" "tace komai ba, to sai hakan da tayi ya bata mamaki sosai! kuma ya nuna mata cewar yarinyar fushi take" "da ita, jikinta ne yayi sanyi sosai ta rinste idonta murya na rawa tace""Ba laifi na bane laifin zuciyata ne Saddiqa bana 'kin mahaifinku sai dan zuciyata ta riga ta gama makancewa da kaunar Salim, a dai-dai lokacin da muke sanya rai da bukatarmu zata biya a dai-dai lokacin kuma za'a kawo mana cikas a rayuwarmu ha'kika rayuwarmu nida Salim na cikin kalubale mai girma mutukar akace baza'a daura mana" "aure da juna ba.""" "Muryar Mussadiq taji a kanta, tayi saurin bude idonta tana kallonsa. Mussadiq duk yaji abinda take" "fad'a ya fahimci wata maganar wata maganar bai fahimce ta ba, Yace.""Yaya Naja'atu ki tashi kiyi sallah kici abinci mu tuntuni munyi sallah munci abincinmu." "Hannunsa ta ri'ke ya zauna kusa da ita murya na rawa tace""Mussadiq bani da lafiya zuciyata na daf da" "tarwatsewa.""!! Da sauri yaron ya d'ora hannunsa saman goshinta yana fad'in ""Yaya Naja'atu kanki ne yake ciwo ? sannu bari na kira Abbanmu a waya ya kawo miki magani."" Girgiza kanta tayi tana kokarin mikewa zaune tace""Mussadiq wannan ciwon nawa Abbanmu shine ya haddasa mun shi dan Allah kace dashi yayi hakuri ya k'yaleni."" Mussadiq ya dinga kallonta cikin mamaki yace.""Yaya Naja'atu Abbanmu ba zai cutar dake ba kiyi hakuri ki aureshi ki zauna dashi.""! Taji wasu hawaye na kokarin kufce mata, wai kowa sai yace tayi hakuri ta zauna dashi to wai ta yaya zata iya zama dashi alhalin bata sonsa kuma a matsayin Uba take kallonsa, abunfa da wahala wai (gurguwa da auran nesa) mikewa tsaye tayi a hankali" "ta fita daga dakin, Shi kuma Mussadiq din ya dauki wayarta ya nemi numbar Abban nasu ya shiga kira." "Koda yaga Numbar Naja'atu na kiransa bai 'ki dauka ba, sai dai babu walwala a tare dashi yayi sallama!" "sai kawai yaji muryar Mussadiq yana fad'in ""Abbanmu nine Mussadiq na kira ka da wayar Yaya Naja'atu."" Murmushi yayi yana jin wani farin ciki yace.""Na gane ka Magajin Abbah Ina fatan lafiya ina Naja'atun take.""? Mussadiq yace.""Yanzu taje yin sallah bama ta da lafiya sai kuka takeyi tana cewa wai dan Allah ka 'kyaleta.""!! Shuru yayi yana nazarin maganar yaron daga bisani yace.""To shikkenan kace mata na kyaleta tunda bata son Allura ba zan kawo likita yayi mata ba."" Mussadiq yace.""Ba wannan ba Abba naji tana cewa kada ka aure ta ita tafi so ta auri ancle Salim Abbanmu tunda bata so ta zauna tare da kai ka kyaleta ta auri wanda take so.""!! Abbah Abbas ya jima yana mamakin maganar yaron, kuma yana mamakin abinda yarinyar take yi na rashin kyautawa! wato yaran take zaunawa dasu tana nuna musu a zahiri bata kaunar Ubansu har tana bawa 'Dansa sa'ko ya bashi! ranshi ya 'baci sosai da sosai! sai kawai yayi 'kokarin bagarar da maganar ta hanyar fad'in ""Ina Saddiqa take kace mata nace ku shirya gobe zan aiko Salim ya dauke ku xaku koma makaranta ranar Monday."" Yace.""Tom zan fad'a mata Abbah."" Yace."" Yawwa ka gaishe min da Baba Talatu da kyau."" Yace."" Za taji Abbah."" Kashe wayar yayi ya shiga nazarin irin iskanci da wulakancin da yarinyar ke masa, zai iya hakura da duk irin cin fuskar da za tayi masa amma kuma ba zai lamunci ta dinga cin fuskar 'yayansa ba, hakan da take yi zai sanya ransu ya 'baci! su shiga" halin damuwa da maraicin mahaifiyarsu. To da wannan 'bacin ran ya shiga gidansa. In da yaje ya tarar da tashin hankalin Halisa dan ko zama "bata bari yayi ba tabi shi d'aki! ta shiga zazzaga masa rashin kunya gami da farfad'a masa duk maganar da tazo bakinta kana kuma tace"" Sai dai ya za'ba ita ko Naja'atu dan wallahi ba za tayi kishi da Ya tayi da" kanwa ba. Babu Abinda yace mata ya shiga bandaki domin yin wanka zuciyarsa tamkar zata tsaga kirjinsa ta fito dan tsananin 'bacin rai!!!! Koda ya fito samunta yayi a kwance 'kasan ties tana kuka had'e da wata iriyar fuffuka tana burgima 'kasan ties kamar mai iskokai! Ya shirya tsaf ya tsallaketa ya fita ya barta a dak'in! Bin hanyar da yabi tayi da kallo hawaye na sharara ta mi'ke zaune tana cizon tsaya wato Abbas ko gani yayi zata mutu ba zai tanka mata ba kenan ballanta ya fada mata magana mai dad'i! aikuwa a zuciye ta "mi'ke tsaye! tana rangaji! da had'a hanya, ta nufi kicin d'inta." Yana zaune gurin cin abinci yaga fitowarta kallo ya bita dashi yana jan tsaki a fili ya shiga bude kwanonin abincin da ta jera kamar gaske! wayam! babu komai a ciki amma saboda tsabar iskanci da iya shega na Halisa ta shirya tevur kamar ta shirya lafiyayyan abinci Takaici ne ya kamashi ya tsirawa hanyar data "bi ido, kawai sai ya hangota ta fito daga kicin d'in hannunta ri'ke da shar'be'biyar wu'ka sabuwa dal da alama daga cikin kwalinta ta cire, kai tsaye ta durfafo inda yake jikinta na tsuma da rangaji! take fad'in ""Wallahi yau koni ko kai a gidan nan Abbas na gaji da wannan abun da kake min ni ka sake ni ma na huta da ganin wannan takaicin auran wannan yarinyar da zakayi masifa ne a gare ni da kai baka sani ba sai sanda nayi maka illah a rayuwarka sannan zaga gazgata maganata."" Mufida ta shigo palon tana" "sanye da uniform na makaranta ta hango abinda ke faruwa, a guje ta jefar da jakarta tayi kan mahaifiyar tata dake dumfarar mahaifinta da dalleliyar wu'ka! tana nema ta caka masa! "" Cikin karaji!! tace"" Mommy meye haka? me za kiyi? Wayyo Abbanmu ka gudu.""!! Tafad'a tare da zuwa ta rungumeshi tana jansa wai ya gudu. Shi kuwa yana tsaye turmin danya bai razana ba, wato wai-wai d'in da yake ji a gari a na cewar mata na kashe mazajen su idan za'ai musu kishiya abun yazo kansa, jira kawai yake ta 'karaso da wukar yaci ubanta! Halisa ido a rufe ta 'karasa inda suke Mufida na kuka tana jansa da fadin ""Abbah mu gudu kada ta caka maka wu'ka Abba me kayi mata n. Gani tayi ya kama duka hannuwan" "Mahaifiyar tata ya murd'e da iyakacin karfinsa Wu'kar ta su'buce ta fad'i 'kasan gurin! Ya kai mata wani lafiyayyan mari! da bayan hannunsa, wani 'karamin jini ne ya fito daga hancinta, kafin ma ta dawo hayyacinta ya sake kifa mata wani a d'aya gefan, sai kawai yaga ta yanke jiki ta fad'i ta shiga turje turje tana taune harshenta. Aljanunta ne suke ka da ita a gurin ta dinga turje-turje tana taune harshenta" "farar kumfa nata fitowa daga bakinta, Halisa na 'karyar aljanu ashe dama tana dasu da gaske! sosai take burgima a gurin tana ta wasu gwalantu wanda ba wanda yake ganewa a cikinsu, Mufida ta nufe ta tana" "kuka zata ta'ba ta, ya hanata Yace."" Je ki cire uniform din'ki idan ta gaji da iskancin da take zata tashi.""" "Tsakanin Uwa da D'a sai Allah tace""Abbah duba fa kaga abinda take wannan abun ba 'karya bane dan" "Allah kayi wani abu kai.""" Tsayawa yayi tsai yana nazarin Halisan da abinda takeyi Eh kwarai kuwa wannan abun da take yasha "bambam dana ko yaushe dan haka sai ya umarci Mufidan ta kawo masa ruwa a kofi, da sauri ta taje ta" "dauko masa, ya kar'ba ya shiga tofa ayatul'kursiyu da fala'ki da nasi 'kafa bakwai bakwai kana ya iske" "inda take, ruwan tofin ya guntsa a bakinsa ya shiga fesa mata a jiki, sai da yayi haka sai uku tukkuna sannan ta daina burgimar da take yi ta daina gwalantun surutan da take yi jikinta ya shika sosai tayi" "lakaf gumi duk ya jika mata jiki, Mufida na kuka taje ta rungumeta tana kiran sunanta................" * MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~ *12* Cikin wani mawuyacin hali Halisa ta tashi duk jikinta yayi mata mugun tsami! ga wani irin ciwo da "kanta ke mata, da kayar ta rarrafa ta shiga dakinta ta zauna bakin gado tana ri'ke kanta, a maimakon tayi addua kawai sai ta fashe da kuka tana fad'in mugwayen kalmomi a kan mijin nata saboda kawai yace zai yi mata kishiya shine take addua Allah yasa ya samu karayar ariki komai nasa ya lalace! Allah yasa ya taulace ya zama wanda bashi da cin yau bare na gobe insha Allahu kuma Naja'atu sai ta zame masa masifa a rayuwarsa, tana kuka take wannan surutan tamkar wata mahaukaciya, Cikin wannan yanayi suka shigo gidan shi da yaran gabad'aya dan dubara yayi wa Baba malam yace zai tafi dasu Mussadiq saboda zasu koma makaranta, baba malam baiji dadin haka ba dashi da Abba Magaji sun fahimci cewar abinda Naja'atu tayi musu ne yasa yaji sha'awar dauke yaransa. Kai tsaye Dakinsa ya nufa yana so ya" samu nutsuwa sosai kafin ya tunkari Halisan dan ya fahimci dole sai ya karyar da kansa mussaman yanzu da ya dauko nauyi 'yayansa ya d'ora mata. Mufida da Saddiqa Mussadiq suka nufi bedroom din "Halisan nan suka tarar da ita ba yanda take sai sambatun surutai take da alama dai har yanzu mutanan nata basu gusa daga jikinta ba, Mufida taje ta zauna kusa da ita tare da dafata tana kiran sunanta. Saddiqa da Mussadiq a bakin kofa suka tsaya saboda dama can sun san halin masifar" "Halisan ba kaunarsu take ba sai taga Abbansu take yi musu magana da wasa da dariya, shiyasa suka kasa 'karasawa, Halisa ta juyo tana kallon 'Yarta Mufida ganin su Saddiqa a tsaye a bakin kofa yasa ta mike tsaye a furgice tace""Ku dan Ubanku waye ya kawo ki gidana maza ku fuce mun daga d'aki shegu tsinannu 'yayan asara.""! Saddiqa da Mussadiq suka zabura! a tsorace suka fita daga d'akin sukaje suka nemi kujerar palo suka zauna jikinsu sai rawa yake dama can Saddiqa da Mussadiq suna masifar tsoron" "Halisa Naja'atu ce take musu maganinta. Mufida na goge hawaye tace.""Mommy ya kike zaginsu su" "Yaya Saddiqa ne fa 'yan uwana."" Wani irin bahagon mari ta kifawa yarinyar tana huci! tace""Zanci" "Kutumar ubanki wallahi shegiya munafuka ni zaki fad'awa su d'in 'Yan uwanki ne? Wallahi duk ranar da kika 'kara kiransu da sunan 'yan uwanki sai naci ubanki."" Mufida tana kuka tace""To mommy me yasa kika tsanesu bayan mamansu ta mutu dan Allah ki daina yi musu abinda kike musu babu kyau.""! A fusace! ta sake gaura mata wani mari tana wata irin fuffuka tace""Tashi dan babanki mara mutunci ki bar min dakina ko kuma yanzu na sumar dake."" A gigice! yarinyar ta mike hannunta dafe da kuncinta ta fita daga dakin tana kuka, wanda yayi dai-dai da fitowarsa daga daki yana sanye da jallabiya ruwan toka, Ganinsu Saddiqa sunyi muzu-muzu a zaune yasa jikinsa yayi sanyi ya kalli Mufida dake dafe da kunci tana kuka, yace.""Menene? Cikin rawar murya tace""Mommy ce ta mare ni tace na fito mata daga d'aki. Ba tare da yace.""Komai ba ya kama hanyar dakin Halisan, Har yanzu tana zaune gefan gado ta had'a tagumi babu maganar sallah a tare da ita, cikin nutsuwa ya shiga dakin bakinsa dauke da sallama, Kallonsa ma ba tayi ba ballanta ta amsa masa sallamarsa, gefanta ya zauna yana kokarin ri'ke hannunta ta fizge a fusace! ta mike tsaye tana nunashi da hannu tace""Kaga dan girman Allah ka fita ka bani guri naji da abinda ke damuna baka da abinda zaka ce dani."" Yaji zafin maganarta amma sai ya danne ya mike ya iske inda take, Rungumeta yayi a jikinsa yayi amfani da wata murya wacce ya tanade ta dan rarrashinta, yace.""Haba Halisa wai duk me yayi zafi ne kike nema ki zautar da kanki akan abinda bai kai ya kawo ba! Menene abin damuwa dan nace zan auri Yarinyar nan Naja'atu? idan kin kwantar da hankalinki kin ri'ke girmanki sai kinfi daraja da kima da martaba a idona! Shin wai baki ga yanda Halimatu ta sadaukar da rayuwata a kaina ba, bana shakka ko tantama Halimatu yanzu tana gidan aljanna saboda ta rabu dani da iyayenta lafiya, kuma ta mutu hanyar haihuwa, har na gama rayuwata ta duniya bazan ta'ba mantawa da Halimatu ba, a kwanakin baya kin soma kwaiwayon hali da d'abi'unta amma tashi guda zaki watsar da abin da kika fara na alkairi, wallahi auran Naja'atu da zanyi ba zai sanya ni na daina kaunarki ba, kin san dai kece macen dana fara furtawa kalmar so, ko Halimatu ma kece kika jawo na aureta, to itama Naja'atun ina so ki sani bani ne nace inaso ta zama *Madadin 'Yar uwarta ba* Iyayenta ne suka nemi haka dan ko yanzu sai da na fada musu cewar maganar auran su barta suka nuna sai anyi So inaso ki kwantar da hankali ki samu nutsuwa ki kula dani da yarana gasu nan na kawo miki su ni kuma insha Allahu zan baki mamaki zan nuna miki ni d'an halak ne auran Naja'atu ba zai sa na juya miki baya ba."" Shuru tayi jikinta duk yayi sanyi da kalamansa tace""Nifa ban hanaka aure ba wallahi ko budurwar zaka aura to kaje ka aura amma banda yarinyar nan bana kaunarta saboda bata ganin girmana."" Yace.""Na fad'a miki fa cewa kece uwargidana duk ragamar mu tana hannuki har ita Naja""atun idan tazo a 'karkashin ki take sai abinda kika tsara a gidan shi za'ayi."" Jin wannan maganar tasa yasa ta sauke ajiyar zuciya tace""Nifa wallahi nasan dadin baki ne kake mun yarinyar nan na zuwa zaka manta dani, dan haka gwara tun kafin tazo na san inda dare yayi min dan bana tunanin zan zauna da ita a karkashin inuwa guda."" Yace.""In banda abinki ba gidanku daya ba to me zai dame ki da ita ko wacce na gidanta idan wannan da kike ciki bai miki ba sai na sauya miki wani."" Tsaki taja tace."" bazan yarda ba wallahi sai dai ka had'amu gida daya dan bazan amince a cutar dani ba."" Yace.""To shikkenan duk abinda kike so shi za'ayi, Zan sa a gyara miki side d'inki dake gidana na *'Danbare* ina fata hakan yayi miki."" shuru tayi tana zum'bura baki, Ya saketa yaja hannunta suka zauna a nutse yace.""Ki fad'a mun duk abinda kike so na siya miki na fad'ar kishiya komai tsadarsa zan siya miki."" Tace""Sai nayi shawara tukkuna."" Dariya ta bashi amma beyi ba yace.""To shikkenan inaso na baki kudi kije ki had'o mata lefe kuma kema ki had'a naki hakan yayi miki."" Dadi ne ya rufe ta tace""To Hakan yayi amma inaso ka sanja min mota."" Yace.""An gama" ranki ya d'ade! amma dan Allah daga yau sai yau kada ki sake aikata abinda kika aikata a d'azu! rashin hankali ne kawai kije ki dauko wu'ka kina so ki kashe ni! kina tare da shed'an a lokacin idan da tsautsayi "sai ki aikata aikin dana sani ki 'kare rayuwarki cikin uku'ba kuma ki mayar min da yara marayu."" Hanci ta sha'ka! cikin takaici tace""Haba ai wallahi idan ma nayi maka rauni ban huce bacin raina ba, kana kallonta ina magana ka tsalleke ni ka tafi ai dole zuciya ta ta tunzurani a kanka."" Yace.""Tom yanzu dai duk magana ta wuce Gobe insha Allahu bayan sakkowar sallahr juma'a za'a daura auran amma ina tunanin ba zata tare ba sai nan da sati biyu."" Halisa gabanta ya fad'i tace""Da wuri za'a daura auran ashe.""?" "Yace.""Baba Malam ne ya yanke hukuncin haka."" Cikin tsabar bakin ciki da takaici tace""Aikin banza aikin hofi 'kwad'ayayyen tsoho mai son abin duniya ai dama dole ya gaggauta yin abun kodan bukatarsa ta biya."" 'Bata rai yayi yace.""To yanzu zamu 'bata dake kuma bana son wannan d'abi'ar taki ta zage-zage da rashin ganin girman manya."" Cikin fusata! ta mike ta nufi toilet tana surutai da 'kananun maganganu, kallo ya bita dashi, Al'amarin Halisa dai sai gyaran Allah, yaji dadi sosai da ya shawo kanta cikin ruwan sanyi *(Tabbas haka maza ya kamata su dinga rarrashin matansu idan zasu 'kara aure, sau tari wasu mazan sune suke ingiza zuciyoyin matansu ga aikata abinda ba shikkenan ba, idan ya kasance zaka 'kara aure to yana da kyau ka dinga nuna kulawarka a kan matarka ta gida, kuma banda kiran wayar amarya a cikin gidan dan hakan ma na iya janyo muku samun sa'bani a tsakaninku*) Mikewa yayi ya fita daga dakin yana dan jin sassauci a cikin zuciyarsa tunda ya gama da matsalar Halisa yana ganin duk abinda zai" biyo baya mai sauki ne. "Yana fitowa palon ya gansu a zaune duk sunyi tsuru-tsuru Mussadiq ma gyangyadi yake, Ya kalli Saddiqa" "data had'a tagumi hannu bibbiyu har yanzu zuciyarta na jin ciwon abinda Naja'atu tayi musu a d'azu duk da take yarinya wacce bata gama mallakar hankalin kanta ba ta gane ba 'karamar 'kiyayya Naja'atu keyi wa Abbansu ba, sai ta dinga tunanin to wai meye aibunsa da har zata dinga 'kinsa da kuma zaginsa, sam bata ta'ba tsammanin haka daga gareta ba. a nutse yace.""Saddiqa kuje ku kwanta kinji ko," "dukkaninku ku daina damuwa ku saki jikinku a gidan nan gidanku insha Allah ba zaku samu wata matsala ba."" Saddiqa murya na rawa tace""To Abbah."" Ya sunkuya yana d'an tashin Mussidiq ya tashi yana mutsika ido, ganin Abbansa yasa ya bude idonsa sosai, Abba Abbas d'in ya rike hannunsa ya mike tsaye.........Shi da kansa ya rakasu d'akin dama gado uku ne mai dauke da madaidaiciyar katifa da pillo da bargo, Mufida ta gyara nata ta kwanta, Abbah Abbas da kansa ya shimfidawa Saddiqa da Mussadiq sabon bedshirt ya gyara musu sosai sannan suka kwanta, Ya tsaya kansu yayi musu addua sosai kana ya fita daga dakin tare da kulle musu kofa. To bayan barin Abbah Abbas daga gurin Malam Baba" "shima Abbah Magaji sallama yayi masa kancewar kafin ya shiga gidansa zai tsaya ya siyi dik abinda za'a bukata gurin daurin auran, Malam yaji dadin hakan yace.""Dashi kafin ya tafi ya shiga gidan Alhaji domin ya sheda masa abinda ke faruwa, koda Alhaji yaji bayanin da Abbah Magaji yayi masa sai ranshi ya 'baci! ya za'ayi sun riga sun gama magana da Abbah Abbas din kan cewar ya janye maganar auran yarinyar kuma dan yaga baya gurin zai sauya magana, yaji haushin hakan ya dauki laifi kacokan ya d'orashi kan Abbah Abbas d'in, Dan 'kin tsayawa ma yayi ya saurari bayanin da Abbah Magaji ke masa, ya sauko daga samansa, kai tsaye futa yayi daga gidan, Abbah Magaji na binsa a baya. Malam Baba yayi mamakin" fusatar Alhajin kasancewar yasan shi d'in mutum ne mai saurin fahintar abu da kuma sau'ka'kawa cikin ko wane al'amari Da 'kyar Baba Malam da Abbah Magaji suka fahimtar dashi ya gane cewar ba laifin "Abbas din bane sune suka tursashi Alhaji Sama'ila yayi shuru yana ta nazarin al'amarin, daga bisani" "kuma addua yayi da fatan alkairi tabbas tunda Allah yayi haka to babu alkairi a cikin auran Naja'atu da Salim d'in,. Shine ya sake 'karfafawa Abbah Magaji, cewar yayi 'kokarin tana dar duk abinda ake" bukata a gurin daurin aure tabbas babu makawa gobe auran Naja'atu da Abbas sai ya d'auru Sai "misalin goma da rabi sukayi sallama da juna kowanne ya shiga gidansa cikin fatan alkairi ga junansu.........Baba Malam kafin ya kwanta sai da ya sanar da Baba Talatu abinda ake ciki na irin hukuncin da suka yanke cewar Za'a daura aure gobe dan jan lokacin bashi da amfani, Baba Talatu taji dad'in hakan sosai kuma tayi fatan alkairi dangane da al'amarin Naja'atu dake takure kan shimfidarta" "a lokan rumfar luf!! tayi kamar mai bacci tana sauraran maganganunsu, sai da taga sun shiga daki, da niyar kwanciya sannan ta mike a hankali ta dauki wayarta dake kusa da ita ta mike ta fita daga" "dakin Daya dakin ta nufa tana shararar da hawaye, xaman 'yan bori tayi tana toshe bakinta domin" "kada sautin kukan da take ya fita suji, wayar ta kunna hannunta na kyarma ta shiga laluben numbar Abbah Abbas d'in, tana jin idan bata zageshi ba zuciyarta na iya bugawa. Yana zaune a palo shi kadai" "da Loptop a gabansa yana duba sa'konnin abokan kasuwancinsa na 'kasashen waje, Kiran wayar ta ya shigo wayarsa dan duban wayar yake hankalinsa na kan typing din da yake cikin loptol din, koda yaga numbar Naja'atun baiyi gaggawar dauka ba, ya janye idonsa ya cigaba da abinda yake Naja'atu! ta dingi kiran wayar tamkar zata kashe masa dodon kunne dole ba yanda ya iya ya daga wayar tare da gyaran" murya babu wasa a cikin muryarsa yayi sallama.... 'Dif! tayi gabanta na wata irin fad'uwa! sakamakon jin sautin muryarsa mai cike da kwarjini da rashin wasa yasa ta mance abinda yasa ta kiransa a wayar sai mazari jikinta yake tana sha'kar hanci had'e da sauke ajiyar zuciya irin na wanda yaci kuka ya 'koshi 'Dan gyaran murya yayi a karo na biyu "yace.""Dota ya akayi ne dare yayi baki bacci ba."". Murya na rawa tace""Me yasa ka san ni 'yar kace kake" "shirin aurena.""? Shuru yayi yana nazarin maganarta, Yace.""Eh abinda yasa nake kiran ki da Wannan suna (Dota) saboda nasan a matsayin shekaruna da Allah ya bani haihuwa da wuri dana haife ki kamar ki ko wacce ta fiki so ina ganin babu laifi dan na kira ki da wannan suna.""!A hasale! tace."" To tunda dai da bakin ka ka fad'a cewa a matsayin shekarunka da Allah ya baka haihuwa zaka iya haifeta ko wacce ta fini me zai sanya ka zubar da k'ima da mutunka a gurina ni da ka 'rike kamar 'yar cikin ka, ka sani ba da badan mutuwa ta ratsa tsakanin ka da matarka ba da kowa yana maka kallon matsayin uba a gare ni."" Murmushi yayi wanda har sai da taji sautinsa a kunanta Yace.""Nifa ban haife ki ba ki daina kirana Ubanki yanzu sunan da yafi kamata ki kirani dashi shine Mijin ki dan gobe idan Allah ya kaimu iwar haka kin zama matata""! Taji tamkar ta d'ura masa ashar! sai dai ta daure taja wani matsiyacin tsaki! mai 'karfi! da fad'in ""Amma dai anji kunya wallahi.""!! Kit! ta kashe wayar tana wani irin huci!!! Abbah Abbas ya dinga bin wayar da kallon mamaki! Yau shi yarinyar nan take jawa tsaki har tana kokarin zaginsa, Kasa hakura yayi ya sake kiran wayar! A fusace! ta d'aga ta bud'e baki za tayi magana, ya buga mata wata masifaffiyar tsawa! da fad'in "" Dan Ubanki ni kike zagi ashe baki da mutunci dama.""!? Jikinta ya shiga karkarwa domin tsawar da ya buga mata bata ta'ba saninsa da ita ba, kashe wayar tayi gabad'aya ta kwanta tare da takure jikinta tana kuka mai tsuma zuciya, ta kirasa a waya domin ta farfad'a masa magana mai zafi 'karshe shi ya fad'a mata maganar data ya mutsa mata tunani har da zagin Ubanta. Abbah Abbas ya" ajiye wayarsa a fusace! ya rufe loptop din ya mike ya nufi bedroom d'in Halisa. *Sorry kuyi hakuri waya ta ta d'an samu matsala wallahi zaku ga yanayin typing din ba irin yanda na sababa. Ina ro'kon Ubangiji Allah ya kawo mana zaman lafiya a wannan 'kasa tamu ta Najeria Ubangiji Allah ka bamu nutsuwa da daidaito a tsakaninmu amin MY FANS KADA MU MANTA DA SALATIN ANNABI A WANNAN RANA MAI ALBARKA SANNAN KUMA MU DAURE MU KARANTA ABINDA YA SAWWA'KA DAGA CIKIN SURATUL KHAFI.* * MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~ *13* Ranshi a 'bace! ya aje loptop din kan wani tevur ya nufi toilet alwala ya daura ya fito ya hau kan "dadduma ya tayar da sallahr nafila, raka biyu yayi ya daga hannunsa sama yana rokan Allah ya za'ba masa abinda yafi alkairi a rayuwarsa, kwata-kwata ji yayi auran yarinyar ya fice masa daga rai! a sabili da irin iskancin da wulakancin da take masa da shida 'ya'yansa bai ta'ba tsammin faruwar hakan daga gurinta ba yana ganin barin auranta kamar shi yafi alkairi don baya so da girmansa da komai yarinya k'arama tazo tana fada masa maganar da duk ta gadama, mikewa yayi daga kan dadduma yaje ya" "kwanta kusa da Halisa, ya d'an janyo ta jikinsa," Bude idonta tayi ta wani fizge jikinta tana jan tsaki! Al'amarin sai ya bashi mamaki! ganin cewar d'azu "suka gama magana da ita kan cewar komai ya wuce amma saboda ya ra'bi jikinta tana fizgewa, bai yi zuciya ba ya sake kai hannu zai janyota ta mike zaune tana 'bata fuska tace""Nifa ba zan sake amincewa da bukatarka ba sai na yankewa kaina hukunci tukkuna dan gaskiya ni maganganunka na dazu basu shige" "ni ba.""" "Ya mike zaune yana kallonta cikin d'umbin mamaki! yace."" Wane irin hukunci zaki yankewa kanki bayan" "wanda muka yanke d'azu na dauka yanzu dani dake mun zama d'aya, ashe duk maganar da mukayi dake dazu ta banza ce."" Tace.""Kawai ka rabu dani na cigaba da tunanin mafita ni ba zan sake amincewa bukatarka ba kaje idan an daura auranka da 'karamar yarinya sai ka sauke bukatarka a kanta."" Cikin tsabar takaici yace.""Halisa ban ta'ba ganin mara hankalin mace irin ki ba wallahi kin girma amma har" "yanzu kin 'ki hankali 'Yar cikin ki Mufida ta fiki nutsuwa.""" "Tace.""Duk dai abinda za kace a kaina kace ba zan amince da kai ba wallahi sai yarinyar nan ta shigo" "gidanka naga irin zaman da zakayi da ita.""" "Murmushi takaici yayi cikin sigar 'kuntatawa yace.""Zanyi zama da ita irin na ma'aurata kuma ba zaki" "hana ni na ji dad'ina da ita ba."" A fusace! taja tsaki! da fad'in ""Kana tare da kunya kuwa duk ranar da 'yayanka su kaga ka kwana a d'akin wacce suka d'auka a matsayin yaya a gurinsu, sai ka tanadi abinda" "zaka fada musu.""" Girgiza kansa kawai yayi ya dauki rigarsa yasa a jikinsa ya sauka daga bed din hanyar fita ya nufa jiri naso "ya kayar dashi, gabad'aya ji yayi duniyar tayi masa zafi ko ina babu sassauci tabbas sai yanzu ne zai fara kukan rashin matarsa da yayi, a da baiyi kukan rashin Halimatu ba sai yanzu da Halisa da Naja'atu suke" gwara kansa a bango.... 'Bangaran Naja'atu kuwa yanda taga rana haka taga dare daga zarar ta tuna da cewar gobe za'a daura "mata aure da Abba Abbas din sai gabanta ya fad'i ta hau takure jikinta, ta jima tana sa'kawa da kwancewa da tunanin mafita a gareta, tana so gari ya waye ta kira Salim a waya ta sheda masa hukuncin data yanke. Aikuwa tana idar da Sallahr asubahi ta shiga kiran wayar Salim din inda akaci sa'a yau ya" "tashi da wuri, ya dauki wayar cikin mayaudariyar miryarsa yace..""My Princess kin tashi lafiya.""? Murya a 'kasa tace""Lafiya kalau my prince."" Ya wani narke murya irin yanda yake mata yana kashe mata jiki yace.""My Prince jiya kwana nayi da tunanin ki da begen ki har mafarki nayi dake muna kwance a gado" "d'aya kina bani kulawa.""" "Ta rintse idonta hawaye na zuba tace.""My Prince Abba Abbas naso ya yanke mana jin dad'inmu bana" "tunanin zan iya mallakawa wani da namiji kaina sai kai! bana sha'awar kowa sai kai soyayyar ka kawai nake muradi! amma ina tunanin mafarkina dakai ba zai tabbata dan ganin yanda magauta suke 'kokarin kassara mana rayuwarmu."" Mikewa zaune yayi yace.""My princess ki fad'a mun yanzu a wace matsaya" aka tsaya dangane da maganar auranki da Abbah Abbas din. "Tace.""Komai yazo karshe My Prince jiya da daddare Baba Malam naji yana fad'awa Baba Talatu cewa" "gobe bayan sallahr juma'a za'a daura aurena dashi, wannan dalilin yasa na yanke hukuncin guduwa daga garin gabadaya su neme ni su rasa.""" "Salim ya shiga goge gumi ma'kogwaronsa ya bushe sosai, yace.""Innalilihi wa'ina ilahi raji'un! abinda ya" "iya fad'a kenan, murya na rawa yace.""My bani da kuzarin yin magana yanzu saboda na shiga rud'u da tashin hankali jin wannan maganar taki, zan kira ki anjima kafin nan nayi nazari kan hukuncin da kika" "yanke.""" Kashe wayar yayi ya zauna yana tunani.......Ashe dai dattijon nan da gaske yake sai ya dasa masa 'kunci "da ba'kin ciki! to kuwa in dai ya kasance cewar ya samu nasara a kansa gurin auran Naja'atu to shi kuma zaiyi amfani da damar sa, a gurin ita Naja'atu duk wani abunda yake bukata a gurin yarinyar ba zai same shi ba sai ta zame masa mafisa wanda da kansa zai gaji ya saketa, koda ya saketa shi ba auranta zaiyi ba" yana so ya kawai ya dasa masa 'kunci da 'bacin rai kamar yanda ya dasa masa a zuciyarsa. "Mikewa yayi ya shiga cikin gidan...Yaya Ramlatu na kicin tana kokarin kunna wuta, taga shigewar d'an" "nata, sai da ta kunna wutar ta d'ora ruwan kunu kan murhun, sannan ta bi bayansa, koda ta shiga dakin gani tayi ya takure kansa hade da dafe kansa, Kafin ma tayi magana taga yana hawaye." "Tace.""Salim lafiya me yake faruwa.""? Cikin tsabar bakin ciki yace.""Yaya 'Dan uwanki bashi da kirki ya" "kasance mutum mai son kansa, ya cuce ni ya cutar da rayuwata kuma ya yaudare ni da yasa na amince" "masa na daukeshi a matsayin uba ya ha'ince ni, yarinyar dana 'kwallafa raina a kanta yau xa'a daura masa aure da ita, ba zan ta'ba mantawa da wannan mutumin ba.""" "Yaya Ramlatu ta dinga mamakin maganar tace.""Kai waye ya fad'a maka yau za'a daura auransa da" "Naja'atu da har kake wannan maganar. A fusace! yace.""Ita yarinyar ce ta fad'a min yanzu ta kirani a" "waya tana kuka tare da sheda min hukuncin data yanke kancewar zata gudu daga garin gabadaya.""" "Shuru Yaya Ramlatu tayi takaici da bakin ciki kamar ya kasheta, lallai Abbas bai da alkawari kamar dai" "yanda Salim din ya fada hakane Abbas yafi son kansa akan kowa bai duba soyayyar dake tsakanin Salim d'in da Naja'atun ba sai da ya shiga ya fita ya raba tsakaninsu. Tace.""To shikkenan sai ka hakura ka" "fawwala wa Allah tunda Allah yasa ya samu nasara a kanka, maganar Naja'atu zata gudu ta bar gari bata" "taso ba dan idan hakan ya kasance to kowa zai d'ora zarginsa a kanka, dan haka kace mata baka amince ba, dan bana son abinda zai janyo min 'bacin ran iyayena.""" "Yace.""Idan ya kasance Naja'atu ta tare gidan Kawu Abbas wallahi tallahi nayi al'kawari sai na 'kunsa masa" "ba'kin ciki da takaici kamar yanda ya 'kunsa min, tunda dai Naja'atu ni take so ai magana ta 'kare zuciyarta tana hannuna shi kuma yana tare da gangar jikinta.""" "Yaya Ramlatu tace""Duk wani iya shege da rashin arziki da zaka yi masa ban hanaka ba, kaje kayi domin" "shima yaji idan da dad'i abinda yayi maka d'aurin aure suje suyi babu inda zanje."" Yace.""To dama me zaki je kiyi a gidan gabad'aya ma da Alhajin da ita Hajiyan basa kaunarki da suna kaunar ki ba zasu bari haka ya faru ba, sunfi kaunar Kawu Abbas d'in saboda yana da kud'i."" Yaya Ramlatu ta dinga girgiza kanta" takaicin da ba'kin ciki dik ya cika mata zuciya. "Da asubah da kafin ya tafi massalaci sai da ya shiga ya tashi yaransa domin suyi sallah, koda ya fito daga" dakin nasu bai ko kalli dakin Halisa ba dan har yanzu haushinta yake ji yana ganin duk wani kokari da ya kamata yayi a kanta yayi zai dauke mata wuta gabad'aya dan ba zai cigaba da rarrashinta taba tana masa iskancin da taga dama. Bayan ya dawo daga massalaci ya koma dakin nasu nan ya tarar dasu sunyi sallah suna zaune Saddiqa da "Mufida suna magana, dukkaninsu suka shiga gaishe shi ya dinga amsawa cikin nutsuwa da kulawa, ya kalli Saddiqa a nutse yace."" Saddiqa ki shiga kicin ki dafa muku tea da abinda kike ganin zaki iya.""" "Tace.""To Abbah."" Mikewa tayi tana kokarin cire hijab d'inta shi kuma ya fita daga d'akin, Kai tsaye d'akin" Halisa ya nufa domin ya dauki loptop dinsa. "Tana kwance kan bed din ta tsirawa rufin dakin ido, da alama ma ba tayi sallah ba, Ko kallon inda take" "baiyi ba ya dauki loptop dinshi ya kama hanya ya fita daga dakin, Halisa tabi bayansa da kallon ba'kin ciki tamkar ya tarwatsa mata zuciyarta. Saddiqa na tsaka da aiki a kicin taji an buga mata uwar tsawa!" """Ke dan Ubanki waye ya baki dama ki shigo min kicin.""!? Jiki na rawa tace."" Abbah ne yace na dafa mana tea da indomee."" Da hannu ta nuna mata 'kofar fita da fad'in ""Fice ki bar min kicin 'yar iska munafuka masu gadon mugun abu."" Saddiqa hawaye ne suka tawo mata, tayi saurin mayar dasu tana kokarin fita daga kicin din Halisa ta kai mata ran'kwashi a kanta tana zaginta. Da sauri ta 'karasa ficewa daga kicin din hawayen da take ta kokarin mayarwa suka zubo Ganin yarinyar ta fito a firgice yasa ya kalleta yana" "tambayar ta menene.""? Tana share hawaye tace""Babu komai."" Tsawa yayi mata da fad'in ""Ba zaki fad'a min menene ba.""? Tace."" Anti ce tace na fice mata daga kicin."" Yace.""Zoki zauna anan."" Kusa dashi ya nuna mata, taje ta zauna tana goge fuska, cikin tausasawa yace.""Kiyi hakuri ki daina kuka kinji ko."" 'Daga kanta tayi tana goge hawaye, laptop din dake cinyarsa ya ajiye kan kujera ya mike ya nufi kicin din, Halisa na tsaye tana feraye doya ya shiga ya sameta. Babu walwala a tare dashi yace.""Me yasa kika hana" "Saddiqa ta had'a musu abun kari.""?" "Juyowa tayi dan ba tasan ya shigo kicin din ba, ganin fuskarsa a murtuke yasa itama ta murtuke tata" "fuskar tace""Ai sai ka tsaya ka gani idan nayi ban basu ba sai ka bata umarnin tayi musu meye wani zaka ce ta shigo min kicin.""!! Girgiza kansa yayi bai ce mata komai ba ya juya ya fita daga kicin d'in, sam bai dauka Halisa za tayi abinci ta bawa yaran ba dan ganin irin rigamar da sukayi ita dashi jiya shiyasa ya umarci Saddiqan ta shiga kicin domin ta samar musu da abinda zasu ci Suna zaune shida yaran Yaya" "Ramlatu tayi sallama ta shigo, turus tayi ganinsa zaune a palon, shima cike da mamaki yake binta da" "kallo, har ta'karaso ta zauna kan kujerar dake fuskantarsa, Yaran ne suka shiga gaisheta ta dinga amsawa tana washe bakinta." "Cikin nutsuwa ya gaisheta ta amsa tana ta dariya kamar wacce ta shigo gidan da abin arziki, Tace.""'Dazu" "Salim yake sheda min cewar anjima wai za'a daura auranka da Naja'atu hakane ko."" ? Yace.""Eh insha Allah bayan an sakko daga sallahr za'a daura anan massalacin jikin gidan Alhaji.""" "Tace.""Allah ya sanya alkairi yasa haka shi yafi alkairi, amma banji dadi ba da baka fad'a min ko a waya ba" "sannan daga can gidan Alhajin ma babu wanda aka turo domin ya fad'a mun sam ba'a daukeni a bakin komai ba, ace maganar daurin auren ma sai a bakin Yarinyar mukaji dan da asussuba ta kira Salim tana kuka tana fad'a masa cewar za'a daura auran kuma idan an d'aura to zata gudu ta bar gari a neme ta a rasa, wannan maganar ta tayar min da hankali sosai saboda nasan yarinyar nan ta gudu to da kai da Salim zaku shiga cikin masifa, dalilin da yasa na umarci Salim din maza ya kira ta a waya sheda mata cewar bai amince da 'kudirin data dauka ba, Kuma nace ya fad'a mata cewar shi tuni ya cire ta a zuciyarsa, dan haka ta daina tunanin guduwa a kansa ta zauna a gidan mijinta tayi zaman aure mai" "tsafta.""" "Abbah Abbas ya sauke ajiyar zuciya yana kallon Yaya Ramlatun yace.""Dukkanin abinda ki kaga yana" "faruwa to dama can haka Allah ya 'kaddara zai faru, ko a mafarki ban ta'ba tsammanin wai zan auri" "yarinyar nan ba, sai dai kuma babu yanda Allah baya tsara al'amarinsa, mutuwar Halimatu ta janyo min" "sha'awar auran yarinyar domin ina ganin yarinyar tarbiyar tace kuma zata zame min *MADADIN TA* ta gurin kyawawan halaye da sauransu, sai dai kuma ashe ba haka al'amarin yake ba , Allah shine ya hallici Halimatu ya kuma Hallice Naja'atu a bigire d'aya, sai kuma ya bambamta musu halaye, Halin Halimatu daban Halin Naja'at daban, A jiya mun zauna da Alhaji mun tattauna magana kan cewa na janye bukatata tasan auran yarinyar, zan kuma shige gaba gurin ganin Salim ya mallaketa, a lokacin da naje wa da Baba Malam da maganar shi kuma ya nuna bai amince ba, yace yarinyarsa bata da miji sai ni saboda ni yayi ra'ayin bawa auran 'yarsa, dik yanda naso na fahimtar dashi ya kasa fahimta, haka nayi musu" sallama na dawo gida ina fatan Allah yasa hakan shine alkairi a gare mu baki d'aya. * MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~ *14* "Yaya Ramlatu zagin Baba malam kawai take a cikin zuciyarta amma a Zahiri dariyar ya'ke tayi tace""To ai" "shikkenan ni a gurina da kai da Salim din duk d'aya ne, kuma na zaunar dashi nace masa ya cire yarinyar daga cikin ransa gabadaya domin kai ba tsaransa bane ballanta ya had'a neman aure da kai."""" Abba Abbas yayi murmushi yace.""Kwana biyu ma bana ganinshi a kasuwa ko kiransa nayi a waya baya d'auka nasan duk akan hakane."" Tace.""Ai yanzu komai ya wuce na nuna masa dama can kai kafi cancanta daka auri yarinyar."" Murmushi yayi yana girgiza kansa, gaskiya bai tsammaci zai zauna da Yaya Ramlatu haka" suyi magana ta fahimta ba yaji dadi sosai da sosai data fahimce shi. "Yaya Ramlatu a gidan ta karya kummalo suka shiga daki ita da Halisa, suna 'kulle-'kullensu, Halisa ta fad'a" mata duk yanda sukayi da mijin nata da maganar zai bata kudi ta had'o lefe kuma zai sanja mata mota bayan haka kuma yace ta fadi duk abinda take so zai bata kudi ta siya. Jin haka yasa Yaya Ramlatu "tace""Kinga aikin malam ya fara yi ko ai dama na fad'a miki sai Abbas ya dawo tafin hannunki sai yazo" "yana miki rawar jiki, dan haka ki daina d'aga hankalin ki kan auransa da yarinyar nan nasan idan muka ri'ke Malam mai al'mutsutsai! a hannunmu to bukatar mu zata biya dama kuma babban burin ki shine ki mallaki Abbas a hannu ina ganin nan da 'kan'kanin lokaci zaki mallake shi da duk wani abu nashi tunda har ya bud'e bakinsa yace miki dashi da duk wani wanda yake 'kar'karshinsa a 'kasan ki suke to kinga kuwa ai sai ki godewa Allah ki sake tanadar kudi masu kauri domin tukwici ga malam bisa ga aikin alherin da yayi miki."" Halisa tace.""Nifa Yaya Ramlatu sai nake gani kamar dan zai yi aura ne yasa yake kwantar da kansa ba wai asiri ne yayi tasiri a kansa ba, ki duba fa ki gani tsayin shekaru nawa muka dauka muna" "yawan bin malam tun Halimatu na raye asiri baya tasiri a jikinsa, sai yanzu.""" "Yaya Ramlatu ta 'bara rai tace""Kada ki sake wannan maganar, wato duk kokarin da nake miki bakya gani" "sai kin 'karya ta ni! kin 'karya ta aikin malam to babu ruwana wallahi idan kika lalata a aikinki, kada ki sake cewa na taimaka miki, inaso ki sani ko wane malami da irin kalar aikinsa, wani da ruhainai yake aiki wani kuwa da turawan aljanu yake aiki wani kuwa da ba'ka'ken aljanu yake aikinsa, to shi mai al'mutsutsai da ba'kaken aljanu yake aikinsa, idan kin san ba'kar wuyar da muka sha nida 'Yar shagamu kafin mu je zauren malam d'in sai kin tausaya mana, amma kin samu aiki yayi shine kike 'karyata wa to" "wallahi babu ruwana.""" "Halisa ganin ran Yaya Ramlatu ya 'baci sai ta shiga bata hakuri tace""Ba wai ina karyatawa bane nasan" "kina kokarina akaina kiyi hakuri dan Allah."" Yaya Ramlatu tace""Koda can ma ba wai asirin ne baya tasiri a jikinsa ba yana tasiri sai dai yana saurin karyewa ne saboda yawan addua da zama da alwala dashi mijin naki yake, amma nasan wannan aikin da akayi masa zai dade kafin ya bar jikinsa.""" "Halisa ta sauke ajiyar zuciya da fad'in ""To shikkenan insha Allahu zanyi kokarin ganin na kauda duk wani" "abu dake raina dangane da auran, ammafa nace ban yarda ya raba mana gida ba dan ina ganin kamar za'a cutar dani, sannan kuma wa 'yan nan 'ya'yan nasa daya kawo min sam bana son ganinsu wallahi.""" "Yaya Ramlatu tace""Eh kina da gaskiya gwara ya had'aku a gida d'aya duk da nasan ba wani d'okin auran" "yarinyar yake ba amma hausawa nace wa amarya ko mahaukaciya ce dole ayi d'okinta, dan haka tana tarewa ya kwashe yara ya kai mata dama ai saboda ta zama *Madadin* Uwarsu ya aureta.""" "Halisa tace""Yace idan an d'aura auran sai bayan sati biyu zata tare."" Yaya Ramlatu tayi shuru tana" "nazarin maganar tace""To shikkenan sai ki hakura ki ri'kesu kafin lokacin amma ban amince ki zalince su ba tunda basu ne sukayi miki laifi ba."" Cike da mamaki Halisa ke kallon Yaya Ramlatun wato idan ta fahimta tana so ta nuna mata cewar ita tana 'kaunar 'ya'yan d'an uwanta, Halimatu da Naja'atu ne bata kauna! To idan hakane kuwa 'kiyayyar da take musu ba takai har zuciyarta ba tunda ba zata bari a zalinci" jininsu ba. To Duk abinda Allah ya tsara ya hukunta sai ya kasance dama haka al'amarin yake mutum baya ta'ba "tsarawa kansa rayuwa sai irin wacce Allah ya tsara masa, Abba Abbas da Naja'atu ko a mafarki basu ta'ba tsammanin zasu zauna a inuwar ma'aurata ba, sai gashi Ubangiji ya zartar da ikonsa a kansu, Sai gashi a yau jama'a masu yawa suka sheda daurin auransu, kowa sai fatan alkairi yake gami da fatan zaman lafiya, Alhaji Sama'ila da Baba Malam da Abba Magaji bakin su ya'ki rufuwa sai gaisawa suke da jama'a Abba Magaji na raba goro da alawa fuskarsa tamkar gonar audiga. Shi kuwa ango fuskarsa kadaran" kadahan yana ta mi'kawa abokanshi hannu suna gaisawa suna taya shi murna da fatan alkairi yana amsawa fuska d'auke da murmushi. "Cikin gida kuwa, Naja'atu kasa gane kanta akayi ta rufe d'aki! da sakata, sai kuka take tana kiran" "mutuwa tazo ta dauketa, Baba Talatu da 'yan uwanta da suka cika gidan hankalinsu ya tashi suka dinga buga 'kofa suna kiran sunanta, tana jinsu tayi shuru sai ihu! take tana birgima 'kasan d'akin." "Baba Talatu ta fashe da kuka tana fad'in ""Wannan yarinya tana so ta jawo min abin kunya a idon jama'a" innalilihi wa'ina ilahi raji'un! Daki ta shiga ta zauna gefan gado tana share hawaye babu shakka Naja'atu ta fita zakka a cikin 'yayanta. Abba Magaji ne ya shigo gidan ya gansu tsaye a kofar d'akin! Gashi sai "gunjin kukan Naja'atun yake ji daga cikin d'akin, Ya karasa gurin da sauri yana tambayar ba'asi Baba" "Larai wacce ta kasance Yaya ga Baba Talatu itace tayi masa bayani duk abinda ke faruwa, Ya shiga bubbuga kofar yana kiran sunanta, tana jinsa taki kulashi." "Cikin rarrashi yace."" Naja'atu bude kofa kinji ko duk kinsa hankalinmu ya tashi yi hakuri ki bude kofar" "zanyi magana dake Cikin dashashshiyar murya tace""Sai dai ku dau'ko gawa ta amma wallahi bazan" "bud'e 'kofar nan ba.""" Abba Magaji ya kalli kofar 'kofa ce irin tada mai k'wari tabbas jijjige ta aikine babba amma yana ganin "hakan shine mafita, yana kokarin fita Baba malam na kokarin shigowa ganinsa a fujajan! yasa ya tsaya tambayarsa, Baba malam ransa ya 'baci sosai babu shakka Naja'atu ta shirya tsaf! domin ta tozarta shi a cikin unguwa, nan ya umarci Abbah magajin ya samo matasa majiya karfi suzo su jijjige 'kofar. Gidan" "ya shiga ya tarar da jama'a sai surutai suke kowa na fad'in albarkacin bakinsa, har da masu cewa dama a warware auran tunda yarinyar bata so Baba malam ya tsaya a bakin tagar dakin ya daga labule yana" "le'kanta da kiran sunanta, duk da tasan shine bai sa ta amsa masa ba, juya baya tayi ta cigaba da kukanta. Abba Abbas na tare da Dan uwanshi a bakin gate din gidan alhaji suna magana, kawai" yaga abokin nashi tare da zaratan maza majiya 'karfi harda Salim a ciki zasu shiga gidan Malam Ya bisu da kallo cikin mamaki! Jikinsa ya bashi da akwai abinda ke faruwa. Sai da suka fara sassa'ke 'kasan 'kofar da (diga) sannan suka sanya mata karfi! aikuwa a take suka cire ta. Mi'kewa tayi tsaye! "cikin firgici! tana rarraba idonta a kansu, ganin sun shigo dakin har Baba Malam d'in yasa ta takure jikinta a bango tana rawar jiki, Abba Magaji ya nufe ta a zafafe! da alama jibgarta zaiyi Baba Malam ya hanashi," "a fusace ya bar dakin, su kuwa jama'a 'yan zuwa taya murna sai fad'ar albarkacin bakinsu suke a" "kanta. Baba Malam yace.""Magana dai duk ta 'kare kowa yaje ya cigaba da sabgarsa aure tunda an" daura babu zancan a warware shi. "Dakin ne yayi shuru na tsayin minti biyar kafin yayi gyaran murya a nutse ya kira sunanta.""Naja'atu.''" "Shuru tayi tana sauke ajiyar zuciya, ya kalleta cikin yanayi na damuwa yace.""Kina so jama'a su zage ni a unguwa ko? ashe a matsayina na mahaifinki ban isa na nemi alfarma a gurin ki kiyi min ba! kin shirya tozartani a cikin unguwar ko, ba'a ta'ba samun labarin yarinyar data fujirewa umarnin iyayenta a cikin unguwar nan ba sai ke! wato tun munayin abun nan a cikin gida sai ki janyo hankalin jama'ar dake waje sun gane cewa tilas mukayi miki ki auri mijin 'yar uwarki, Kina ji da kunnan ki irin surutan da jama'a keyi a kanki, kina so duniya ta zage tayi tur! dake kan 'kin bin iyaye meye aibun Alhaji Abbas da kike masa wannan 'kiyayya! idan da al'kawari da amana Abbas bai cancanci haka daga gare ki ba, to saboda haka ni wannan itace magana ta ta karshe a tsakanina dake, an daura auraki da Alhaji Abbas to kada naji kada na gani, mutukar kin daukeni a matsayin uba to ina so ki zauna da wannan bawan Allah zama na amana kamar yanda 'yar uwarki ta zauna dashi, idan aka kai ki dakin mijinki aka samu matsala ta 'bangaranki to babu shakka zan yafe wa duniya ke babu ni babu ke har abada.""!! Kallonsa kawai take tana shararar da hawaye bakinta sai rawa yake tana so tayi magana amma ta rasa ma ta ina zata fara. Baba malam ya" mike ya fita daga dakin ya barta cikin zullumi da tararrabi gami da neman mafita. "Salim kuwa suna fita kai tsaye inda su Abba Abbas suke ya nufa, Yana so ya fara dasa masa 'bacin rai a" zuciyarsa. Ba tare da wani damuwa ba ya shiga sheda masa abinda Naja'atun tayi ta kulle kofa tana "cewa sai ta kashe kanta tunda ba'a aura mata wanda take so ba, dalilin da yasa kenan suka shiga gidan suka 'balle 'kofar har da cewa data ganshi zuwa tayi zata rungumeshi Yayanta Magaji ne ya hanata, Salim ya wani 'kasan'kantar da kansa yace.""Wallahi ni Kawu tuntuni na hakura da yarinyar nan tunda naji maganar auranka da ita naji ta fita daga raina saboda nasan kai ba mutumin da zan had'a takara dashi bane, to amma kullum sai ta dame ni da kiran waya babu dare babu rana, ko dazu sai da ta kira ni da safe tace zata gudu daga gari nine na hanata nace idan kaunar da take min gaskiya ce to ta nuna ta a kanka, dan na nuna mata a yanzu dai kai ka fiye min ita sau dubu, tunda ta zama mallakina ka nake" "daukarta a matsayin antina.""" Wannan al'amarin yayi masifar d'aga masa hankali mussaman idan ya tuno da maganar runguma sai yaji "wani sabon 'bacin rai na taso masa bai ta'ba d'auka 'kiyayyar da yarinyar nan ke masa ta kai haka ba, wato da tuni ta gudu da badan Salim din ya hanata ba, babu shakka dole ya tsaurara matakan tsaro a kanta." Baba Malam kam yana fita ya samu Abbah Abbas din da maganar lallai yau da daddare yake so Naja'atu ta tare a dakinta tunda an daura aure to maganar aja wani lokaci bai taso ba. Abba Abbas din ya "nuna masa cewar ba wai ya'ki maganarsa bane yana so yayi d'an gyare-gyare a gidan, shiyasa yace sai nan da sati biyu. Baba malam fafur ya'ki yarda da maganarsa Yace bai amince da wani gyara ba za'a kai" Naja'atu ta zauna a d'akin 'Yar uwarta a yanda yake. Abbah Abbas baya son yayi ta jayyaya dashi sai kawai ya amince da hakan. "Sai da yayi sallahr isha'i a 'Kofar na'isan sannan ya nufi gidan nashi, Halisa ana zaune a palo anci kwalliya" "cikin wani uban less tayi ado da gold hannu da wuya da kunne, tayi kyau dai-dai gwargwado, suna zaune ita da yaran suna kallo amma kallo daya za kayi wa su Saddiqa ka gane a tsorace sukayi ko motsin kirki sun kasa yi, shigowar Abban nasu yasa suka sauke ajiyar zuciya suna masa sannu da zuwa. Ya amsa" musu yana kokarin shiga dakinsa. "Halisa ta mi'ke tabi bayansa, yana tsaye yana kokarin cire babbar rigar shaddar dake jikinsa, Halisa aka" "'karasa kusa dashi kamar ba ita ba ta taimaka masa ya cire rigar ta ninke rigar ta ajiye gefan gado aka wani kalleshi ana fari da ido cikin kissa tace""Ango kasha 'kamshi.""! Dariya ta bashi amma beyi ba yace.""Nayi miki kama da ango a haka.""? Murmushi tayi tana ta'be bakinta tace""Sosai kuwa gakanan sai 'kyallin goshi kake."" Yasa dariya yana kallonta yace.""Ba haka ango yake ba ango zaki sameshi cikin walwala da farin ciki komai nasa sabo amma ni duba ban ma sa sababbin kaya ba fa, kuma yaushe zanyi" "'kyallin goshi bayan har yanzu na kasa samun kwanciyar hankali dake.""" "Wani fari tayi da ido tace""Zaka samu kwanciyar hankali dani idan baka tauye min hakkina ba ni kuma zan" "baka kulawa wacce tafi ta da."" Yace.""To naji maganarki kuma ina rokan Allah ya bani ikon kwakwanta adalci a tsakaninku, nima inaso ki dauke kanki kan dukkanin abinda zai faru a nan gaba inaso ki ri'ke yarinyar nan bisa gaskiya da amana, kece babba dan haka ki ri'ke girmanki ni kuma zan baki mamaki sosai ba zan ta'ba juya miki baya."" jin furucinsa yasa taji wani farin ciki ya cika mata zuciya, Toilet ta shiga ta hada masa ruwa yaje ya wanka ya fito ya shirya cikin sabuwar jallabiya milk sannan suka fito tare, Halisa sai wani ririta shi take, ta hada masa abinci da yaji magani ya zauna yaci da bisimillah a bakinsa. Sai bayan da ya kammala cin abincin ne ya sheda mata cewar Naja'atu zata tare a dakinta yau" "dan abinda mahaifinta yace kenan Cikin 'kokarin danne bala'in kishin da ya taso mata tace""To yau kana" "nufin acan zaka kwana kenan.""? Kai tsaye yace mata ""Eh."" sunkuyar da kanta tayi ba'kin ciki kamar ya kasheta, Yace.""Idan kina ganin kema zaki zauna a haka ba tare da anyi miki gyara ba gobe kina iya komawa."" Tace""A'a ni bana gaggawa na fiso ka sanja min kujeru da labulaye da kayan gado duk wani abu" "da babu a can inaso ka samin kafin na tare.""" "Yace.""Kada ki damu insha Allah cikin satin da zamu shiga za'a kammala komai.""" "To sai kusan goma da rabi ya bar gidan, Halisa ji take kamar ta dawo dashi amma ba yanda ta iya dole ta" hakura ta kyaleshi ya tafi ta nufi dakinta cikin takaici da damuwa. Naja'atu taci kukanta ta 'koshi bayan 'Yan kaita sun watse! tsoro ne ya cika mata zuciya gidan ya dinga yi "mata gizo gani take kamar zata ga Yayarta, motsin kirki ta kasa yi sai makyarkyata take ita kadai a takure a d'aki! kamar mujiya duk ta tsargi kanta. Mi'kewa tayi cikin tsoro taje ta murzawa 'kofar d'akin key ta" "barshi a jiki dan bata so ma idan ya shigo gidan ya shigo inda take, takurewa tayi kan bed tana kuka" "had'e da kiran sunan Allah, 'Yar uwarta kawai take tunawa tana zabura!" "Abbah Abbas ya shigo gidan cikin motarsa, gurin parking ya nufa, yayi parking din motar yana fitowa" "maigadi ya 'karaso ya mika masa hannu suka gaisa, maigadin yace.""Alhaji Ashe ka daura aure to ubangiji Allah ya sanya alkairi ita kuma Hajiya Allah ya jikanta da rahama. Abba Abbas ya amsa cikin kulawa kana yayi masa sallama ya nufi cikin gidan Ko'ina shuru sai hasken tarwai a palon, kujera ya samu ya" zaune yayi shuru yana jin wani irin yanayi a jikinsa! Gidan da yayi rayuwa da Halimatu yau shi zaiyi rayuwa da kanwarta Yarinyar da bai ta'ba tunanin zai aureta ba. Ya kai minti ashirin zaune a palon kafin ya mike cikin rashin kuzari ya nufi d'akin da yake tsammanin tana ciki..... A hankali Ya murd'a handile d'in d'akin yana so ya bud'e kofar sai yaji ta a rufe ya murd'a sosai nan yaji alamun key a jiki! Dan buga 'kofar yayi da hannunsa. A furgice! ta mike zaune tana zare ido! Ya sake buga kofar dakin had'e da kiran sunanta! jin muryarsa yasa taja tsaki! ta koma ta kwanta. Cigaba yayi da kiran sunanta yana d'an bubbuga kofar a hankali Ta sake mi'kewa zaune murya na "rawa tace""Waye.""? Ajiyar zuciya ya sauke jin muryarta hankalinsa ya kwanta da yaji tabbacin tana cikin gidan, Yace.""Bud'e kofar ki kar'bi abinci kici.'' Kai tsaye tace""Bana ci."" ta koma ta kwanta! Tsaye yayi a" bakin 'kofar d'akin yana d'an tunani Ya sake dan buga kofar hade da kiran sunanta. "Tace""Abbah dan Allah ka kyaleni kayi tafiyarka wai dole sai naci abinci ni bana bukatar duk wani abu da" "zai fito daga hannunka."" Yace.""To naji bud'e kofar ina so nayi magana dake.""" "Tsaki taja tace""Ni ba zan bud'e maka 'kofa ba kawai kayi tafiyarka.'' Ajiyar zuciya ya sauke yace.""Okey" "shikkenan yanzu dai kin bani dama na koma inda na fito ko? kai tsaye tace""Eh hakan sai yafi min kwanciyar hankali."" Girgiza kansa yayi ya matsa daga jikin 'kofar, ledar dake hannunsa ya ajiye kan center teble ya juya ya fita daga palon, yana fita ya fito da key daga aljihunsa ya kulle kofar palon kai tsaye ya nufi inda motarsa take......." * MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~ *15* Kai tsaye da ya fita daga gidan Naja'atu gidansa na gwangwanzo ya nufa domin bashi da inda zaije in ba "nan din ba, maigadinsa na gidan ya bude masa kofa ya shiga da motarsa ya gyara Parking a nutse ya fito daga motar ya nufi cikin gidan, shuru palon da alama itama Halisan ta dade dayin bacci, kai tsaye bedroom dinsa ya nufa dan ganin kamar hakan shine maslaha koda ya shiga dakinsa bai jira wani abu ya zare jallabiyar jikinsa, yai saura daga shi sai singlet da gajeran wando ya kwanta kan gadonshi tare da rufe jikinsa da bargo, cikin ikon Allah bacci mai nauyi ya dauke shi Komai gajiya da dad'in bacci" "asubah nayi yake tashi saboda tsabar sabo da yayi da tashin asuba jikinsa har bashi yake lokaci yayi, karfe hudu da kwata ya tashi ya nufi toilet a gurguje ya daura alwala ya fito ya zura jallabiyarsa, dadduma ya hau yayi nafila(raka'atanilfijir) yana idarwa yayi addua yanda ya sawwa'ka kana ya mi'ke ya fita. Dakin Halisa ya nufa domin tashinta, ya tarar da ita tana sharar bacci, tsayawa yayi a kanta yana" "dan bubbuga bed din da kiran sunanta, Halisa firgigit ta tashi zaune tana kallonsa, cike da mamaki tace"" Yanzu ka shigo gidan ne.""? Girgiza kansa yayi yana kokarin fita daga dakin yace.""Ai anan na kwana" lokacin dana shigo kinyi bacci ki tashi kiyi sallah.'' Ya bud'e kofar dakin ya fita. Halisa ta shiga mamakin maganarsa to anan ya kwana garin ya akayi haka ta faru? to ko dai yarinyar nan "tayi masa tsiya ne? murmushi tayi ta mike farin ciki kamar me a zuciyarta ta nufi toilet cikin zuciyarta tana fad'in ""Lallai wannan babbar dama ce a gurina. Wajejen biyar da minti goma ya shigo gidan ya" "nufi dakin yaransa, nan yaga suna ta bacci basu tashi ba, tashinsu yayi yace suje suyi alwala suyi sallah. Ya fita daga d'akin, Halisa kuwa wanka tayi sannan tayi alwala ta fito tayi sallah a gurguje ko adduar kirki ba tayi ba ta mike daga kan daddumar, wata matsiyaciyar rigar bacci ta dauko bata da maraba da tsirara tasa a jikinta ta fesa turare kusan kala goma a jikinta, ta dauko maganin mata na matsi ta lakata a hannunta kafin tasa a gabanta sai da ta tofa maliki yaumi dini (Subahanallah) sannan ta cusa maganin a matantakar ta, ta mayar da maganin inda take 'boye shi, hijab d'inta ta zura a jikinta ta nufi dakin maigidan Abba Abbas na zaune a kan Sofa yana dan duba wayarsa ta shigo dakin, 'kamshin" "turaranta ya cika dakin, fuskarsa a sake ya amsa mata sallamarta, tazo ta zauna kusa dashi tana gaishe" "shi ya amsa a nutse yana tambayarta kwanan yara Tace"" Sun kwana kalau! Hijab din jikinta ta cire ta" "ajiye gefe, Ya tsira mata ido yana kallonta, gani yayi ta dawo 'yar yarinya domin rigar irin mai maida tsohuwa yarinya ce Halisa akwai breast sosai gasu manya manya gashi bata wani shayar da yawa ba shiyasa basu zube sosai ba, gabakidaya ji yayi hankalinsa ya tashi, dama daurewa kawai yake, idananunsa suka kad'a sukayi jawur, Ta sake matsawa jikinsa tana masa magana kasa-kasa, wai tambayarsa take mai yasa bai kwana gidan amarya ba Abbah Abbas da ya soma fita daga nutsuwarsa" "kai tsaye yace.""Kulle 'kofarta tayi shine dalilin da yasa na dawo nan."" Ta'be bakinta tayi ba tace komai ba ta shiga shashshafa jikinsa, hannunta ya ri'ke suka mike kai tsaye bed suka nufa. Halisa ta baje" "hajar ta sosai ta sakar masa jiki yayi abinda yake so da ita tana taimaka masa da sabbabin salon data tanade su dan samun damar mallakarsa, abinka da jarumin namiji ji yayi Halisan ta kasa isar sa gabad'aya yaji kamar an 'kara mata ni'ima da d'adi! gashi gabanta ya tsuke ya cika sosai sai zubar da ruwa yake, abinda bayayi a ranar sai da yayi sambatun surutai Abbah Abbas komai dad'in sex baya ta'ba yarda yayi wannan sambatun da iface-iface! a ganinsa duk shashancin ne meye abin ihu! sai dai yayi ta sauke numfashi yana sakin ajiyar zuciya. Basu saurarawa junansu ba sai kusan tara saura na safe," yara har sunyi wanka sun shirya sun fito palo sun zauna amma babu break fast....... "'Bangaran Naja'atu kuwa bayan fitar Abbah Abbas din daga gidan, sai ta shige cikin bargo ta kud'indine" "jikinta tana addua, daga zarar ta rufe idonta fuskar 'yar uwarta take gani, gashi bargon dake lullube a jikinta sai kamshin turaran Halimatun yake, cikin fitar hayyaci ta cire bargon daga jikinta ta mike da sauri ta bud'e kofa ta fita, kan kujera ta takure jikinta tana kuka, nan ma ta dinga ganin gilmawar Halimatun" tana jin sautin muryarta a kunnanta. "Hannu ta dora a kanta, tana kuka da fad'in ""Innalilihi wa'ina ilahi raji'un! na shiga ukuna!! ta mike a" "sukwane ta nufi dakin Abbah Abbas din cikin ikon Allah tana murd'a kofar dakin ta bude shiga tayi da gudu ta kulle dakin taje ta kwanta kan bed dinsa, ta rufe jikinta da bargonsa tana ta rawar jiki da addua hawaye kuwa kamar an bud'e famfo, haka ta kwana tana firgita da zabure-zabure, da asubah tayi sallah a dakin ta bude kofa ta fito kai tsaye kofar fita daga palon ta nufa, ta dinga murdawa kofar ta'ki bud'ewa" zubewa tayi bakin kofar ta had'a kanta da gwiwa tana ihu!! Abbah Abbas yayi mamaki tsayin lokacin da ya dauka yana tara da Halisa dan haka a gurguje ya samu yayi wanka ya shirya a gurguje ya fito palo ya same su suna break fast dan Halisa data fito Umarni ta bawa Saddiqa kan ta shiga ta dafa musu ko indomee ce... "Yaran na ganinsa suka shiga gaishe shi ya amsa fuskarsa cike da walwala, Ya kalli Mufida da fad'in "" Ina" "Mommyn ki.""? Tace.""Ba ta dade da shiga dakinta ba."" ba tare da yace wani abuba ya kama hanyar fita, gabadayansu suka ce Abbah adawo lafiya.'' Ya amsa musu a lokacin da yake kokarin fita." Lokacin da taji kamar ana 'kokarin bud'e 'kofar dakin zabura! tayi ta mi'ke tsaye hawaye duk ya bushe fuskarta ga jijiyoyin kanta da suka tashi alamun taci kuka ta koshi! kofar ta tsirawa ido gabanta na dukan uku-uku......Abbah Abbas ya bud'e kofar palon ya shigo Da gudu taje ta rungumeshi ta fashe da "kuka tana makyarkyata a jikinsa! hannu guda yasa ya dafe bayanta yana bin palon da kallo! Ba yau Naja'atu ta saba ri'ke shi ko ta rungumeshi ba, a duk sanda xata r'ike shi ko ta rungume shi a lokotan baya baya jin komai a cikin zuciyarsa da jikinsa, amma yau ji yayi jikinsa na wani irin rawa mussaman da yaji tudun breast d'inta a cikin kirjinsa ajiyar zuciya ya sauke mai zafi! ya d'an cire ta daga jikinsa, yana kallon fuskarta yaga duk tayi wujiga-wujiga ga alamun furgici nan a tare da ita! gyaran murya yayi kafin yayi magana, Yace.""Dota wato har yanzu baki daina kuka ba ko ki fad'a min abinda ke damun rayuwarki.""! Hanci ta sha'ka tana sake shigewa jikinsa da rarraba ido a palon murya a dashe tace.""Abbah Yaya Halimatu ce tazo tana yi min magana dan Allah ka taimaka min ka rabani da wannan rayuwar da nake cikinta ka mayar dani gida gaban iyayena wallahi ba zan iya zama a gidan nan ba ka taimaka min" "Abbah rayuwata na cikin garari da tashin hankali.""! Tana rirrikeshi take wannan maganganun" "Hannunta ya ri'ke ya dan sassauta muryarsa sannan yace.""Ki kwantar da hankalin ki Dota wanda ya" mutu baya dawowa kawai kinsa tsoro acikin zuciyarki shiyasa kika kasa samun nutsuwa a gidan Shuru "tayi tana goge fuskarta, yaja ta suka nufi bedroom dinshi, koda suka shiga dakin sai yaga shimfidar gadonsa a hargitse ga bargonshi a 'kasa, ya kalleta cikin nazari yace.""A dakin nan kika kwana ne.""? Hawaye suka wanke mata fuska tace.""Eh ko ina tsoro ake bani shine na shigo nan na kwanta to anan din ma ban daina firgita ba."" shuru yayi yana bin dakin da kallo, kafin yace.""Babu wani abin tsoro a cikin gidan nan ke kanki kin sani lafiya lau mukayi rayuwa a ciki ina ganin kamar kin sanya tunanin Halimatu a cikin ranki shiyasa kike furgita ina so ki kwantar da hankalinki ki nutsu ki san da cewar wanda ya mutu" "baya dawowa, fargaba da damuwar da kika sanya a ranki duk itace ta janyo miki firgita.""" "Girgiza kanta tayi tana ri'ke hannunsa tace""Abbah ba zan iya zama ba dan Allah ka mayar dani gidanmu" "ka dubi halin da nake ciki ka tausayawa rayuwata."" Ya dinga kallonta yana mamakin maganarta ya tausayawa rayuwarta to wane irin tausaya mata zaiyi bayan wanda yake mata, Yace.""Yanzu dai je kiyi wanka tukkuna naga alama ma kamar baki karya ba ko.""? Daga kanta tayi tace""Ba zan iya shiga dakin ba tsoro nake ji."" Kai tsaye yace.""To sai kiyi a toilet dina."" Tace""To kayana na dakin ai."" Yace.""Bari na dauko miki."" Fita yayi daga dakin, ta dinga zazzare idonta tana bin dakin da kallo, shi kansa dakin nasa tsoransa take ji, tana tsaye ya shigo hannunsa rike da riga da zani na atamfa super ire-iren kayan da yake d'inka musu, ya ajiye kan bed yace.""Baki shiga wankan ba."" Hanyar toilet din ta nufa salo-salo! ya bita da kallo mai tarin ma'anoni! bayan shigarta toilet din ya dauki bargon dake kasa ya mai dashi kan bed din ya xauna gefen bed din hade da kunna wayarsa yana dubawa, kawai yaji ihun ta daga cikin toilet din kafin ma yayi wani yun'kuri ta fito a guje jikinta duk kumfar sabula ta dauro towel dinsa yana kokarin fad'uwa daga jikinta, ya mike a gigice yana tambayarta ihu! take tana nuna masa toilet din, Ya rike hannunta yana tofa mata addua tangadi ta shiga yi tamkar 'yar maye ta tafi luuuu! zata fad'i! ba tare da 'bata lokaci ba ya ri'ke ta sosai a jikinsa, cikin tashin hankali da damuwa ya nemi gefen bed ya zauna da ita" "rungume a jikinsa, ji yayi jikinta na wani irin kyarma! yana rawa kamar wacce take cikin zazzabi mai zafi!" "babu shakka a firgice take, adduoi ya shiga tofa mata a jikinta yana me tsirawa fuskarta ido, a fizge suna" "dan kama da Halimatu kad'an, nan ya shagala da kallonta dan gani yayi tana nema ta rikid'e ta koma masa Halimatu.......Lokacin ne kuma ta dan samu nutsuwa ta bude idonta tana ambatar kalmar innalillahi wa'ina ilahi raji'un! Ta mike da sauri ganinta kwance lakadan a jikinsa ga towel din jikin ya sa'bule! brest dinta duk a waje! Da sauri shima ya gyara yanayin sa amma dai duk da haka kana kallonshi sai gane ya hau network, Yayi dan gyaran murya as'usul Yace.""Sannu ki dinga yawaita addua ina ganin tunda kin firgita da zaman side din nan zan sa a gyara miki Side din da ya kasance nawa sai ki koma can."" Gyara towel din jikinta tayi ta mike daga jikinsa, kayan ta dake kusa dashi ta dauka tana so tasa tana jin kunyarsa, Yace.""Ya zaki sa kayan bayan duk ga sabulu nan a jikinki."" Cikin rawar Murya tace""Ba zan iya komawa toilet din ba, dan ina wanka naji kamar ana kiran sunana."" Ya dinga kallonta abin na bashi mamaki! Mikewa yayi ya rike hannunta yace.""Muje na raka ki kiyi wankan."" Ma'kale kafad'a tayi tana komawa baya! Yace.""Zan tsaya har ki gama fa kuma bazan kalleki ba."" Hawaye ta share tace''Na hakura da wankan.""Ya girgiza kansa da fad'in ""A'a ai bai dace ba kina amarya ki zauna da datti ba zakiyi ba'ki fa."" Kallonsa ta dinga yi tana mamakin maganarsa, Tace.""Abbah ni d'in amaryar waye.""? Ya nuna kansa da hannu da fad'in ""Amaryata mana."" Taji wani irin ciwo da takaici a cikin zuciyarta, hawaye suka kece mata tace.""Kaico da wannan kalmar taka Abbah! Kaico da wannan maganar dake fitowa daga bakin ka, ni ba amaryarka bace 'Yar ka ce."" Tana gama maganar ta ta cire hannunta daga cikin nasa ta fita daga dakin, gabadaya ma ji tayi ta daina jin tsoron akan ta zauna a dakinsa yana kiranta da amaryarsa gwara ta fito" koma meye ya cutar da ita.... * MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ "~~~~~~~~~~~~~~~~ *16* Ya jima a dakin yana sa'kawa da kwancewa kafin ya fito palon, inda ya sameta" a takure a kan kujera har yanzu bata daina zubar da hawaye. Saboda jin haushin maganar data fad'a "masa yasa ya kama hanyar fita dan baya so ya zauna a gidan zuciyarsa ta tunzira shi a kanta, dan ya lura koda 'kuruciya a tare da ita to da akwai iskancin dan iskancin ma yafi yawa a tare da ita, gabad'aya ya lura ta raina shi kuma ta daina ganin girmansa, wannan d'abi'un da take masa na 'bata masa rai sosai da sosai! Yana dab da fita yaji ta ri'ke masa hannu, ya juyo fuskarsa babu walwala yana kallonta yace.""Me" "zanyi miki kuma.""? Cikin rawar murya tace""Dan Allah zan bika dik inda zakaje kada ka barni ni kad'ai" "wallahi ba zan iya zama ba."" Shuru yayi yana kallonta na minti biyu kafin yace.""Jeki dauko hijab din'ki.""" "Da sauri ta saki hannunsa Hijab dinta dake kan kujera ta d'auka tasa ya nuna mata 'kofar fita da hannunsa, da sauri ta fice tana sauke ajiyar zuciya, kwana d'aya tayi a cikin gidan jin ta take tamkar a cikin 'kaya, kulle 'kofar palon yayi yazo shigeta ya nufi motarsa....Bin bayansa tayi da saurin gaske, ta ma rigashi bude motar ta shiga ta zauna tana zazzare ido, sai da ya gama magana da maigadinsa sannan ya shiga motar, yana zama tace.""Jakar kayana na manta ban dauko ba kuma tana d'akin Yaya Halimatu.'' Ya kalleta cikin rashin walwala yace.""To meye amfanin daukar jakar kaya ke a tunaninki ina zan kai ki.""?" "Tace.""Na dauka zaka mayar dani gidan Baba Malam."" Girgiza kansa yayi yace.""Ba can zan kaiki ba zan kai ki gidan Halisa ku zauna da yara zuwa dare sai mu dawo gidan tare."" Fashewa tayi da kuka tace""Dan Allah ka daka mu dawo ni wallahi akan na zauna gidan nan gwara na zauna a gidan Anti Halisan yafi."" Yace.""Kina ganin zaki iya zama a gidan.""? Da sauri tace""Eh zan iya."" Ba tare da yace komai ba ya bud'e kofar motar ya fita, cikin gidan ya koma ya shiga, jakar kayanta dake dakin Halimatu ya dauko mata ya fito.Ganinsa dauke da jakar kayanta yasa ta sauke ajiyar zuciya,tana ganin gwara ta zauna a gidan Halisa akan ta zauna ita kadai a wannan uban gidan wanda ake bata tsoro, bayan mota yasa jakar, ya shiga ya zauna ya tada motar ya fita daga cikin gidan Tana ganin sun hau kan titi ta sauke ajiyar zuciya wacce" "ta sanya shi dan kallonta da gefan ido, ya dauke idonsa tare da maida hankalinsa gurin draving din da yake. Motar tayi tsit! na kusa minti goma kafin yayi gyaran murya a nutse ya ambaci sunanta! ta" "kalleshi tare da amsawa, Yace.""Ina so inyi miki wata tambaya bana son ki munafurce ni ko kuma ki 'ki fad'a min gaskiya."" Tayi shuru tana wasa da yatsun hannunta, Yace.""Me yasa bakya so kiyi rayuwar aure dani.""? Kallonsa tayi ya gyada mata kansa a nutse yace.""Amsa nake so ki bani bance kuma ki bani amsar da zata 'bata mun rai ba."" Tace""Saboda na dauke ka a matsayin mahaifina shiyasa nake ganin kamar haramun ne nayi rayuwar aure da kai."" Yace.""Waye ya fad'a miki haka? shiru tayi Ya cigaba da cewa"" Aure a tsakanina dake ba haramun bane Naja'atu, dan na ri'ke ki kin girman a hannuna hakan ba zai hanani na raya sinnar ma'aiki dake ba mutukar Allah ya kad'dara hakan a tsakanina dake, mutane nawa ne sukayi irin wannan auran na *MADADI* kuma auran yayi albarka, inaso ki sani da badan mutuwa ta raba tsakanina da Halimatu ba to da babu abinda zai sanya ni naji sha'awar auranki, na kwadaitu da auranki ne dan ina ganin kamar zaki maye min gurbin matata ta gurin kyawawan halaye gami da sadaukarwa, ashe ba haka abin yake ba, Allah yasa kun fito ke da Halimatu ta tsatso daya amma kuma halin kowa ya bambanta, shin meye aibuna da bakya so kiyi rayuwar aure dani? ko kina ganin ba zan iya dauke miki dukkanin bu'katunki ba ne? Shuru tayi kanta a kasa tana ta nazarin maganganunsa, Ya cigaba da cewa. ""Nasan babu irin sa'ke-sa'ke da zuciyar ki ba tayi miki a kaina, kina ganin kamar nazo da son" "zuciya a cikin al'amarin a matsayina na babba ba yaro ba na aure ki, kina ganin tamkar na cutar da rayuwarki ne tunda na hanaki auran saurayi wanda ya dace da rayuwarki ko ba haka bane"".? Kasa magana tayi, Ya cigaba da cewa"" Nasan kin san da cewar Annabi Muhammad (slw) ya auri Nana Ayshatu tana 'yar shekara tara, yayin da shi kuma yake da shekara Hamsin, to kuwa idan hakane aurena dake babu haramci a ciki tunda wanda akayi duniya dominsa ma ya auri 'yar 'karamar yarinya wacce bata kai matsayin shekarun da kike ba a yanzu, ina ganin ni na aikata sinna mai kyau tunda nayi irin abinda Annabi ya aikata."". Naja'atu duk jikinta yayi sanyi da maganganunsa, Ya cigaba da cewa"" Inaso ki san" "da cewar abinda kike tunanin wani saurayi mai tashen balaga zaiyi miki a zamantakewar aure to Matashin mutum kamata dan kimanin shekara hamsin zaiyi miki abinda yafi wanda kike tunanin shi saurayin zaiyi miki."" ajiyar zuciya ya sauke kafin ya cigaba da cewa"" Mafi akasari 'yan matan yanzu" abinda ke damunsu kenan.... ((('kalubale gare ku 'yan mata masu tashe saboda ku na zauna nayi "wannan littafin, dan akwai masu 'karamar 'kwa'kwalwar da za suce su baza su auri tsoho ba sai saurayi," "toh wallahi bari na fad'a muku a wannan zamanin ba'a tsayawa za'ben miji, idan kikace xaki tsaya za'be- za'be to zaki tsufa baki yi aure ba, idan magidanci mai mata yazo auranki idan har anyi binkice mai kyau a kansa an gane cewar yana tsaye a kan gidansa da kula da iyalinsa to ki lalla'ba ki shiga daga cikin, idan kin tsaya kince ke sai saurayi to zaki iya auran saurayin kuma ki kasa samun biyan bukatarki, Samarin yanzu duk 'yan bana bakwai ne kuma mafi akasari auran sha'awa suke daga zarar bukatarsu ta biya shikkenan zaki fuskanci kalubale, bance duka aka taru aka zama daya ba amma dai abinda yake faruwa na fad'a, idan kuwa kika auri wanda ya dan kwana biyu to shi yasan menene aure saboda ya dade a cikin inuwarsa zai ri'ke ki da kyau kuma duk wata soyayya da kike tunanin saurayi zaiyi miki to sugar Dady d'in da kika raina zaiyi miki wacce tafi ta saurayin domin shi tsohon hannu ne a harkar )))) Abba Abbas ya cigaba da cewa"" Abinda yake damun su kenan sai suce su baza su auri tsoho ba dan suna ganin kamar idan sun auri mai shekaru baza su more kuruciyarsu ba, wanda kwata-kwata ba haka bane sunyiwa abun mummunar fahimta ne, inaso ki zauna kiyi tunani mai kyau a kan wannan maganganun da mukayi dake," "Na farko ni ban haife ki ba, ballanta ki dinga ganin kamar kin aikata haramci dan kinyi mu'amular aure dani! Na Na biyu kuma wad'annnan abubuwan da kike yi sun soma isata idan baki gyara ba to zan dauki mataki a kanki, ni ba yaro 'karami bane ballanta ki dinga yi min iskancin da duk kika ga dama, a yanzu ni ina a matsayin mijinki ne ba Ubaba kamar yanda kike dauka a da to yanzu ba haka bane! Wallahi! duk ranar da na sake jin kin fad'i wata mummunar magana a kaina da aurana sai na 'bata miki rai! na dauka kuruciya ce ke damunki sai kuma daga baya na gane rashin arziki ne, to ni ba lusarin namiji bane ke zaki fadawa kowa hakan tunda kin taso a gidana kinga yanda nake zamantakewar aure da mataye na, suna bani girma suna mutuntuni babu wacce take fad'a min bakar magana ko kuma taja min tsaki! dan haka" "nake gargadinki ki kiyaye aikata abinda zai janyo miki 'bacin raina.""" "Tun kafin ya gama maganarsa ta rufe fuskarta cikin hijabi tana kuka, shima tunda ya gama maganarsa bai" "sake cewa komai ba ya cigaba da draving dinsa, daf da zai shiga cikin unguwar ne kira ya shigo wayarsa, koda ya duba sai yaga numbar Halisa a nutse ya daga wayar, Tace""Abban Mufida ya kuma ka fita baka karya ba.""? Kai tsaye yace.""Naje duba Naja'atu ne yanzu ma dai ganin zuwa tare da ita ta kasa zaman gidan."" Da sauri tace.""Kamar yaya.""? Yace.""Idan nazo zanyi miki bayani."" Kashe wayarsa yayi dan ganin kamar zata 'kara masa wani 'bacin ran! Yana ta jin shashshekar kunanta sai damunsa take kawai dai yayi mata shuru ne yasan dole idan ta gaji zata daina. Halisa kuwa kasa'ke tayi da waya a hannu shin" me hakan yake nufi da zai dauko mata yarinya ya kawo mata gida! cika tayi ta batse ta hard'e a kan kujera tana jiran zuwansu......... Saboda yasan zai samu matsala daga gurinta yasa ya shiga gidan fuskarsa a murtuke dan baya so tayi masa rashin arziki ya lura ba tayi maraba da zuwan Naja'atun ba. Mussadiq na ganin Naja'atu tare da "Abbansu ya tashi a guje yaje ya rungumeta, Allah sarki yaro kenan har ya mance abinda tayi musu, tsugunawa tayi ta rungumeshi tana sumbatarsa a fuska, Abba Abbas kuwa bai tsaya ba kai tsaye dakinsa ya nufa, Halisa ta mike ta bishi tana huci!! Dama ya tsammaci shigowarta, ya tsira mata ido yana kallonta ganin yanda idonta yayi jajawur lokaci guda, Ri'ke 'kugu tayi tace""Nifa bangane ba meye amfanin kawo ita gidana naga harda jakar kayanta."" Yace.""Eh kamar yanda na fad'a miki a waya hakane tana jin tsoron zaman gidan ita kadai shine dalilin da yasa na daukota na kawo ta ta zauna nan kafin na yanke hukunci.""" "Murya na rawa tace""To ba sai ka kai mata su Saddiqa su taya zama ba, meye sai ka kawo min ita gida.""" "Yace.""Ina tunanin ko ta ganta tare dasu Saddiqar ba zata samu nutsuwar da ake bukata ba."" Tace""To naji" "a'ina kake shirin ajiyeta."" Cikin jin haushin titsiyen da take masa yace.""A duk inda nayi ra'ayi gidana ne ai."" Ganin ya fusata! yasa ta dan sassauta tace""Sai dai a gyara mata d'aya sashen ta zauna dan ni bana jin zan iya zama tare da ita."" Yace.""Ai dama ba'ace dole ki zauna da ita ba tunda ita tafi so ta zauna anan ke yanzu zanyi duk yanda zanyi cikin satin nan a gyara miki inda zaki zauna a can gidan."" Girgiza kanta tayi tana 'kas-'kas! da cingum! din bakinta tayi wani murmushi tace""Ba zai yiwu ba! ai na fad'a maka ba zan amince da wannan rabe raben gidan ba, nima ina nan babu inda zanje."" Daga mata hannu yayi yace.""To magana ta 'kare kada nan gaba kice min zaki koma can dan ba zaki koma wallahi."" Tace.""Ai duk inda kake ina nan idan ka tattara ka koma can nima zan tattaro nawa nawa na biyo bayanka."" Shuru yayi mata ya zauna gefan gado, ta juya ta fita tana fadin ""Bari na kawo maka kayan break din."" Tana fita ta gansu zaune a kujera sun kewaye ta har da Mufida sai murna sukeyi tamkar sunga wata sabuwar hallita, ita kuma sai murmushi take musu. Halisa taja tsaki cikin tsawa tace""Ke Mufida me kike anan zo nan ki" "taya ni 'aiki."" Yarinyar ta mike da sauri! Halisa ta nuna mata hanyar kicin tana fad'in ""Bana son shashanci ni kun wani zauna kuna dariyar banza."" Naja'atu dasu Saddiqa suka bita da kallo tana kokarin shiga kicin tana surutai Bayan shigewar Halisan, ta kalli Su Saddiq tana nazarinsu, kwana biyu da bata gansu ba" "sai taga kamar sunyi rama ta rike hannun Mussadiq tare da fad'in ""Kayi rashin lafiya ne.""? Girgiza kansa yayi yace."" Yaya Naja'atu kema kin dawo nan kenan na dauki akwatin kayan ki na kai miki dakinmu.""? Kanta ta d'aga masa idanunta na kawo ruwa, da sauri yaron yaje ya shiga jan jakar kayan Saddiqa ta mike taje tana taimaka masa, Naja'atu binsu tayi da kallo hawaye ya zubo mata tausayi yaran suka bata, tana ganin ko dan saboda su zata dinga adduar Allah ya sanya mata dangana domin ta zauna tare da dasu Halisa ce ta fito daga kicin hannunta ri'ke da tire jere da kayan tea ko kallon inda Naja'atun take" "ba tayi ba tayi ba ta nufi dakin maigidan, Naja'atu ita dai binta da kallo kawai take.........." "Yana zaune 'kasan kafet ta shiga dakin, ajiye tiren tayi ta zauna tana kokarin had'a masa tea din yace.""Ki" "bawa Naja'atu abinci dan bana tsammanin taci wani abu tun jiya."" Kallonsa tayi kamar za tayi magana kuma sai ta fasa, ta hada masa tea kana ta zuba masa farfesun kayan cikin rago wanda yaji magani! ta mike ta fita daga dakin Saddiqa ta kalla tace""Ke Saddiqa ki shiga kicin ki girka muku abinda zaku ci" "dan ni ba baiwar kowa bace.""! tana gama maganarta ta shiga dakinta......" "Saddiqa ta mike da sauri tana kallon Naja'atun tace.""Don Allah Yaya Naja'atu kada ki kulata.""" "Murmushin takaici tayi tace.""Jeki yi aikin ni ba'a gabana take ba ballanta na tanka mata."" Saddiqa ta sauke ajiyar zuciya ta wuce kicin din, mikewa tayi ta nufi dakin su Saddiqar nan ta tarar da Mussadiq yana ta jera mata kayanta a cikin wardorbe dinsu, Tace""Mussadiq daka bar kayan ma a jakar da yafi."" Yace.""Ai akwai guri a wardrobe din shiyasa nake shirya miki kayanki a ciki."" Zama tayi tana bin dakin da kallo, gado uku ne kananu irin na 'yan boarding Mussadiq yace.""Yaya Naja'atu zan baki gado na ki" "kwanta kafin Abbanmu ya kawo miki naki."" Tace""To nagode Mussadiq."" ya mike da sauri yana fad'in ""Bari ma naje na fada masa."" Kallo ta bishi dashi har ya fita daga dakin Dakin Abban nasu yake kokarin" "shiga Halisa ta hangoshi tsawa ta buga masa da fad'in ""Me zaka shiga kayi.""? Yace.""Zan fad'awa Abbanmu ne cewar Yaya Naja'atu bata da gado."" Cikin tsawa! tace""To sarkin iyayi da rawar kai ai ya fika sani."" Abbah Abbas din ne ya fito daga dakin nan Halisa ta gyara yanayin fuskarta Tace.""Gashinan wai yana so ya shiga yayi magana da kai shine nace masa kana cin abinci sai ka fito tukkuna."" Ya kalli" "Mussadiq din a nutse yace.""Menene.""? Mussadiq yace.""Abbah Yaya Naja'atu bata da gadon kwanciya" "amma kayanta sun samu guri a wardrobe d'in mu."" Murmushi yayi yace.""Gaskiya Magaji kana son Yaya" "Naja'atu sosai kada ka damu zansa a kawo mata gadonta itama."" Murmushi yaron yayi yace.""Nagode Abbah."" Cike da farin ciki ya nufi dakin nasu yana so yaje ya fad'a mata abinda Abban nasu yace. Abbah Abbas fita yayi daga gidan ya tafi sabgoginsa sai yamma likis ya shigo unguwar kuma" "bai shiga gidan ba sai bayan sallahar isha'i, Halisa yau ma ta cancad'a kwalliya kamar itace amaryar tana zaune a palo ita da yaran suna kallo kamar jiya, ita kuwa Naja'atu ta kasa zama a palon tana d'aki ta takure kanta sai neman Salim take a waya bata shiga. Hannu bibbiyu Halisa ta kar'be shi, ta bashi" "abinci yaci kamar koda yaushe ya dawo palon ya zauna nan yaga babu Naja'atu a gurin, Ya kalli Mussadiq da fadin ""Ina Yaya Naja'atu."" Mussadiq yace.""Tana dakinmu nace ta fito muyi kallo ta'ki."" Kai tsaye yace.""Je ka kirata."" Yaron ya tashi da sauri! ita kuwa Halisa shan kunnu tayi ta wani tamke fuskarta. Da" "hijab a jikinta suka fito ta zauna kan kujera kanta a kasa tace""Abbah Sannu da zuwa."" Ya amsa yana nazarinta yace.""Me kike a daki ke kad'ai bayan kowa na palo."" Shuru tayi, Ta kalli Halisa a nutse yace.""Inaso nayi magana daku a dakina."" Mikewa yayi ya nufi dakinsa."" Halisa ta mike tabi bayansa, ita kuwa Naja'atu gyara zama tayi dan bata fahimci maganarsa ba, Minti biyar da shigar Halisa dakin nasa Kira ya shigo Wayarta koda taga numbarsa sai gabanta ya yanke ya fad'i! ta dauki wayar Yace.""Ki shigo dakina zanyi magana daku."" a raunane tace""To."" Kashe wayarsa yayi, Halisa kam sai jijjiga kafa take ta cika ta batse sai wani 'kas-'kas take da cingum din bakinta, Ya kalleta cikin 'bacin rai yace.""Malama ki cire wannan cingum din na bakin ki."" Ta daina 'kas-'kas din tayi ta dauke kanta. Da 'kyar ta iya mi'kewa ta" "nufi d'akin nasa yayin da yaran suka bita da kallo, Saddiqa dai duk tafi su hankali ta gane Yanzu Yaya" Naja'atu dai-dai take da Anti Halisa a gidan to dan ta shiga dakin Abban nasu ba abun mamaki bane....... "*GA MASU BUKATAR KARANTA BOOK DIN ZASU TURA #300 SINGLE, VIP GROUP #600 GA ACCONT" D'IN DA ZA'A TURA KUDIN.......0542382124.....BINTA UMAR GTBANK. IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA KIYI MIN MAGANA TA WHASAP DA WANNAN NUMBAR......07084653262 IDAN KIN SAN BA BIYAN KUDIN LITTAFIN NAN ZAKI YI BA DON ALLAH KADA KI KIRA WAYA TA KO KIYI MIN WATA MAGANA TA WHASAP* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA SO KU BIYA KUDIN LITTAFIN ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS. 90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE.* * MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~ _*Aunty Binta wai dan Allah me yasa duk littafin ki kike bawa maza Power akan mata ni dai duk na karanta novls din 'ki ban ta'ba ganin wanda kika bawa mace power ba* _ _*MAFI A KASARIN TAMBAYAR DA MUTANE KEYI MIN KENAN WAI ME YASA NAKE BAWA MAZA POWER! "A LITTAFIN NA, TO GA AMSA, BANI NA BAWA MAZA POWER (IKO) BA ALLAH NE YA BASU, NAMIJI IN DAI SUNANSA NAMIJI TO KOMAI 'KAN'KANTARSA SAI YA JAGORANCE KI KODA KUWA KE KIKA HAIFE SHI, TO BALLANTA NAMIJI A CIKIN GIDANSA TO AI NI KO LOKACIN DA NAKE KARATUN LITTAFIN HAUSA DAGA NA FARA KARANTA LITTAFI NAGA AN BAWA MACE POWER A KAN MIJINTA NAKE DAINA KARANTAWA DAN NA TSANI LUSARIN NAMIJI WANDA BAYA IYA JAGORANTAR GIDANSA, MEYE AMFANIN POWER MACE A GIDANTA IDAN YA KASANCE KINA JUYA MIJIN KI TO ME KENAN AKAYI? AI DUK GIDAN DA KUKA GA MACE NA MULKI A CIKINSA TO TA KAUCE HANYA NE, NI DUK MACEN DAKE MULKI A GIDAN AURANTA TANA JUYA MIJINTA YANDA RANTA YAKE SO WALLAHI BATA BURGENI SABODA NASAN 'KARSHEN TA NADAMA! MATA SU ZAUNA A 'KARKASHIN MAZAJEN SU KAMAR YANDA ALLAH YACE, SU KUMA MAZAN SU KULA DA DUK WASU HAKKO'KIN MATAYEN SU, AMMA BA WAI INA FIFITA NAMIJIN NOVEL AKAN MACEN NOVEL BA INA SO INA NUNA MUKA ABINDA YAKE FARUWA A" ZAHIRI SHINE NAMIJI KO MAI 'KAN'KANTARSA JAGORA NE *_ *17_18* "Kanta a 'kasa ta shiga dakin da sallama a bakinta, Shi kadai taji ya amsa sallamar dan ko Halisa ta amsa" ita dai ba taji ba. "Kusa da Halisan ta zauna tare da sunkuyar da kanta 'kasa, dakin ne yayi shiru na tsayin minti uku kafin" "yayi gyaran murya kamar yanda ya saba idan zaiyi magana yace."" Gabad'ayan ku nasan kunsan abinda yasa na tara ku anan ko.""? shuru sukayi babu wacce tayi magana." "Ya kalli Halisa a nutse yace.""Tun kafin na kawo miki Naja'atu gidan nan mun gama magana dake ina" "fatan zaki kar'bi yarinyar nan hannu biyu ki dauke ta a matsayin *'ya* ba kishiya ba, wannan kad'ai za kiyi min ki nuna min ke mai kaunata ce."" Halisa ta d'ago kanta da sauri ta kalleshi, lallai sai ta ri'ke yarinyar a matsayin *'Ya* ba kishiya ba sannan zai gane ita mai kaunarsa ce maganar ma mamaki ta bata" "sosai kuma ta 'kara tabbatar da cewar namiji bashi da kunya, komai 'kan'kantar kishiyarta yaushe zata" dauke ta a matsayin *'Ya* wannan magana ma bai mai yiwu bace. To shima dai da ya fad'i maganar yasan abune da ba zai ta'ba yiwu ba dan ya riga yasan yanda Halisa take da masifar kishi ai da wuya ta ri'ke yarinyar a matsayin *'Ya* ko *'Yar uwa*. Hankalinsa ya mayar kan Naja'atu ya dan tsira mata ido na minti biyu kafin ya kira sunanta. Da sauri ta d'aga kanta tana kallonsa da idanunta da suka soma kawo ruwa. Ganin ita yake kallo yasa tayi saurin sunkuyar da kanta gabanta na fad'uwa! "Yace.""Ke ma d'azu kafin na kawo ki cikin gidan nan mun gama magana dake kuma ina fatan dukkanin" "abinda na fad'a miki sun shiga kunnan ki kiji ki kuma shiga hankalin ki, zaman aure kika shigo kiyi a gidana ba shirme da shashanci ba, wannan da take zaune tafi kar'fin raini a gurinki."" Yafada yana nuna" "mata Halisa, bata kalleta ba sai sake sunkuyar da kanta 'kasa da tayi" "Ya cigaba da cewa""Duk ina sane da rashin kunyar da kike mata a lokotan baya! bakya ganin girmanta duk" "irin maganar da tazo bakin ki fad'a mata kike bakya gaisheta a duk inda zaku had'u! tsaki! harara duk babu wanda bakyayi mata, to duk nasan da hakan nake kyale'ki koda ita Halisan zata kawo 'karar ki ina bata hakuri saboda a samu zaman lafiya ina kuma nuna mata ke yarinya ce idan kika kara hankali zaki daina. Halisa tayi hakuri da halayen ki a baya, dan haka a yanzu kada naji kada na gani kin zageta ko" "kin fad'a mata bakar magana ko kuma kinyi mata tsaki! tsakaninku mutunci da mutunta juna inaso ki dauki Halisa a matsayin Uwa abokiyar shawararki wannan kad'ai zakiyi min nasan cewar ke d'in tarbiyar Halimatu ce."". Tsit dakin yayi bayan gama maganarsa Halisa tamkar ta zuba ruwa a 'kasa tasha" "dan farin ciki taji dadi sosai yau da ya nunawa yarinyar matsayinta a gurinsa, ashe duk yana sane da iskancin da yarinyar ke mata a baya amma bai ta'ba magana ba, ji tayi duk wani haushinsa da take ji ta daina, sai wani murmushi take tana jijjiga 'kafa. Ita kuwa Naja'atu kanta a kasa ta kasa dagowa dan" tasan idan ta dago 'kwallar dake kokarin zubowa daga idananunta zata tona asirin zuciyarta. 'Dan "kashingid'a yayi kan bed din yana kallon Halisa babu alamun wasa a fuskarsa yace.""Yarinyar nan zata cigaba da zama anan dakin! tunda ya kasance d'akuna uku ne to bai kamata ta kwana cikin yara ba idan yaso ni nabi da'ki-d'aki! kafin komai ya daidaita."" Halisa ba haka taso ba amma sai tayi kokarin danne kishinta tace""To shikkenan hakan ma yayi dai-dai ai."" Yace.""To tunda kece uwargida sai ki shirya yanda" "al'amarin zai kasance.""" "Cikin ya'ke! da danne wani mugun kishi tace""Kwana biyu zaka dinga yi kamar dai yanda kake yi lokacin" "Halimatu."" Gemunsa ya shafa yana d'an murmushi yace.""Ai na dauka ko zaki sanja tsari ne shiyasa na tambaye ki.""? 'Yar dariya tayi tana ta'be baki tace""Kwana bibbiyu shine tsari mai ma'ana idan kuma kafi son kwana d'ai-d'ai to."" Ya kalli Naja'atu had'e da kiran Sunanta! A firgice! ta kalleshi dan ita bata san" wainar da suke toya ba tana can tunanin ya za'ayi ta fece daga gidan. "Yace.""Ke a ganinki kwana nawa-nawa zan dinga yi a tsakaninku.""? Murya na rawa tace""Ban gane" "maganar ba."" Mikewa zaune yayi yana kallonta yace.""Muna maganar raba kwanan girki ne a tsakaninku shine nake tambayar ra'ayin ki."" Shuru tayi wasu lafiyayyun hawaye suka wanke mata fuska wai yau" itace Abbah Abbas ke tambayarta maganar kwanan girki. "Ganin tayi shuru yasa ya kalli Halisa yace.""Kwana bibbiyu din shi zamu dauka kamar yanda kika" "ce.""Mikewa tayi tana fad'in ""Hakan yayi! to ni dai sai dai nace Allah ya bamu alkairi."" Hanyar fita ta nufa zuciyarta kamar ta babbake! Kallo ya bita dashi kafin yace.""To Allah ya tashe mu lafiya idan kin fita kisa yara su tashi daga kallon da suke suje su kwanta haka."" Ai fad'ar wannan magana da yayi sai ya 'kara tunzura ta a fusace! ta bud'e kofar dakin ta fita tare da doko kofar da karfin gaske Tana fita palon ta" raraka yaran d'akinsu sai masifa take tana zaginsu kamar sune sukayi mata laifi Mussadiq da Saddiqa a tsorace suka bar gurin. Innalilihi wa'ina ilaiji raji'un! kawai take ta ambata bayan fitar Halisa daga dakin gabadaya Jinin jikinta ya "daskare hatta da kafafunta jinsu take sunyi mata nauyi da sanyi tana ji kamar ba a jikinta suke ba. Gyaran muryarsa taji kafin taji ya kira sunanta, amsawa tayi tana kallonsa ya iya kiran sunanta" tamkar a bakinsa a ka rad'ashi. "''Kinci abinci ko.""? Yafada yana mata wani kallo na 'kasan ido! 'Daga kanta tayi tana mai dauke idonta" "daga kansa, Yace."" To shiga toilet ki dauro alwala kizo muyi nafila ta godiya ga Allah."" Mi'kewa tayi salo- salo ta nufi toilet d'in Minti biyar ta fito daure da alwala ya mike ya shiga toilet din shima ya dauro" alwala ya fito. Nafila sukayi raka'a biyu kamar yanda Annabi ya koyar da sababbin ma'aurata! Abba Abbas ya jima hannunsa a saman kanta yana addua kafin ya cire ya d'aga hannunsa sama nan ya jima yanayi wa Allah "kirari, daga bisani ya rufe adduarsa da fatihatulkitabi suka shafa ita dashi, mikewa yayi daga kan abun sallahr ya dauki key motarsa dake kan drowar taga ya bude dakin ya fita." "Zukud'un!! tayi bayan fitarsa daga d'akin, ita yanzu abun ma mamaki yake bata gami da tsoro! da gaske" "dai sai tayi zaman aure dashi, tunda gashin nan har ya zaunar dasu tare da matarsa yana kawo mata tsare-tsarensa harda kashedi da gargadi kada ta zagi matarsa, lallai Abbah Abbas yayi masifar bata mamaki! to ita yanzu ba wannan ne ma yake sake furgitata ba sai kawo ta dakinsa da yayi, to me zaiyi mata? bata da mai bata amsa! mikewa tayi da saurin gaske ta nufi kofar fita, cikin ikon Allah kuwa tana" jan kofar ta bude! palon ta fita tana zazzare ido! tv a kashe yaran duk sunje sun kwanta. Kujerar data zauna a dazu nan ta nufa ta duba wayarta zama tayi kan kujerar ta shiga lalubar numbar Salim Lokacin shi yana ma can gidan kallo hayaniya ta hanashi ya daga wayar sai ihu suke shida abokansa sunci 'kwallo. Text ta tura masa tana hawaye tace. _Salim anya kuwa kana sona kuwa? tun jiya nake kiran wayarka baka dauka ba ashe dama duk soyayyar da kake min karya kake Kada fa ka manta kai kad'ai nayi wa alkwarin mallakawa kaina da komai nawa "dan Allah kada ka bari Abba Abbas ya samu nasara a kanmu dan gani nan a gidansa a cikin dakinsa ya kulleni kasan hakan da yayi yana nufin abubuwa da yawa, dan haka dan Allah ka daure kayi wani abu akan wannan al'amarin.""_" Tura masa tayi tana adduar Allah yasa ya duba ya bata amsa. Salim shida abokinsa suna cikin mota "bayan fitowarsu daga gidan kallo ya dauko wayarsa yana dubawa, ganin Kira da text din Naja'atu yasa yaja tsaki! text din ya shiga dubawa! bayan ya gama karantawa ya nunawa abokinsa, shima ya karanta, dariya yasa ya bashi hannu suka tafa yace.""Amma gaskiya yarinyar nan na sonka da yawa, yana da kyau ka fara gudanar da aikinka dan na lura dattijon nan zulamamme ne! ya samu 'karamar yarinya sai 'barin" "jiki yake kada ka barshi ya lashi zumar nan ta dad'in rai.""" "Salim yayi wani murmushi yana shafa siririn sajensa yace.""Ai wallahi sai na d'and'ana masa d'aci! da" "bakin cikin daya jefa ni a ciki dan haka bari kaga ni."" Sai kawai ya shiga kiran wayar Naja'atun, da sauri ta dauki wayar ta kara a kunnanta." "Salim ya wani narkar da murya cikin sigar yaudara da janye hankali a kasalance yace.""My Princess bani" "da lafiya zuciyata ta kusa ta daina aiki yini nayi ina aman jini! soyayyarki ina tsammanin itace ajalina! na kasa daga wayarki ne saboda ni kadai nasan irin masifar da zan shiga idan naji sautin muryarki, to amma ganin wannan text din naki na yanzu ya firgitani sosai har naji sha'awar na kira ki a waya na gargade ki kan cewar komai rintsi kada ki kuskura ki mallakawa wannan tsohon jikinki kada ki bari ya kusanci inda kike my princess ni kad'ai nasan irin yanda nake jin fleengs a duk sanda na tuno zubin hallitarki hakika na jima ina kwadayin na ganni ina tsotsar bakin ki! sannan babu babban abinda yake d'aga mun hankali kamar breast dinki na jima ina mafarki gasu a hannuna ina wasa dasu ina tsotsa ina lailayasu a hannuna! dan Allah my princess kada ki bari wani yayi amfani da damata duk rintsi duk wuya kiyi min wannan" "alfarmar.""" "Tunda yake maganar take 'kan'kame wayar a kunnanta tana sauke ajiyar zuciya tsigar jikinta na tashi, ji" tayi gabadaya jikinta ya rikice ta dinga jin sha'awar Salim din na taso mata. Murya a dushashe "tace""My prince kada ka damu zan kula maka da kaina da jikina nayi maka alkawarin babu mai mallakata" "sai kai kuma insha Allahu zan fito daga gidan Abba Abbas da budurcina muyi auranmu tinda shari'a bata rahamta mana ba.""" "Salim ya sakeyin 'kasa da murya yace.""Yawwa my princess nagode kwarai da soyayyarki gareni nima" "insha Allahu zan cigaba da yi mana kokarin dan ganin bukatarmu ta biya."" Ajiyar zuciya ta sauke tana kokarin magana, taji alamun bude kofar palon..........Da sauri ta mike ta nufi dakinsu Saddiqa da wayar a kunnanta tana magana 'kasa-'kasa tace""Salim gashinan ya dawo zan kashe wayar yanzu."" Yace.""To shikkenan my Prince. "" Kashe wayar yayi ya kalli abokinsa dake draving sai kawai suka kwashe da dariya" "kamar wasu shashashai! Kamalu yace.""Gaskiya Salim ka iya tuggu! yarinyar nan fa gabadaya ta mato a" "kanka duk maganar daka fada mata da sauri take amsawa kamar wani ubanta."" Salim ya shafa sajensa" "yana dariyar mugunta yace.""Ai na fada maka dama gangar jikinta kawai ya aura, amma zuciyarta na tafin hannuna."" Yafadi maganar yana nuna hannunsa." "Abbah Abbas ya shigo hannunsa ri'ke da ledoji guda uku, kulle kofar palon yayi kai tsaye ya nufi dakinsa" a hannunsa rike da ledojin dake hannunsa. Jim yayi yana bin dakin da kallo sai kuma ya ajiye "ledojin hannunsa kasan kafet ya nufi toilet, dan kwankwasa kofar yayi yana kiran sunanta, shurun da yaji ne yasa ya dan tura kofar toilet din yana dubawa, ganin bata ciki yasa yayi saurin fita daga dakin, kai tsaye dakinsu Saddiqa ya nufa domin yasan tana can dan babu wata hanya da zata samu ta fita daga" gidan tunda kafin fitarsa sai da ya rufe kofar palon da key. "Yana shiga ya hangota kwance kusa da Mussadiq Ya tsaya daga bakin kofa tare da yin gyaran murya," "mikewa tayi a zabure tana kallonsa, Yace.""Ya zaki zo ki takure kanki ki anan bayan kin san ko shi Mussadiq din gadon na iya yi masa kad'an."" Kasa tayi da kanta tana wasa da hannayeta, Ya juya tare da" "fad'in ""Ki taso daga cikinsu ki dawo dakina ki kwanta ko bakiji abinda nace d'azu ba.""?" "Murya na rawa tace"" Abbah dan Allah ka kyaleni na kwanta a cikinsu sai nafi iya bacci. girgiza mata" "kansa yayi yana lumshe ido yace.""Ba zaki takurawa kowa ba ki taso kawai.""" "Da sauri tace""Sai na kwanta a 'kasan kafet babu damuwa.'' Yace.""Idan baki taso ba zanzo na daukeki da" "kaina bana son gaddama."" Ganin yayi maganar cikin rashin wasa sai ta tsorata! da sauri ta sauko daga gadon Mussadiq ta biyo bayansa suka fita daga dakin." "Suna shiga dakinsa ya nuna mata ledojin da ya shigo dashi yace.""Ki dauki guda d'aya akwai kazar" "amarcinki a ciki kada nan gaba ace ana bina bashi.""" "Naja'atu ta dinga kallonsa le'banta na rawa, babu shakka mutumin nan da gaske yake abinda ta fada" kenan a zuciyarta. Tana kallonsa ya nufi toilet ta dinga girgiza kanta tana sake takure jikinta cikin kujera wai shin me yake shirin faruwa ne? Ganinsa ya fito daga toilet daure da towel iya 'kugu! faffad'an kirjinsa mai cike da yalwar gashi a waje sai yasa 'yan hanjinta hautsinawa! cikinta ya wani murd'a mata! da mugun sauri ta sunkuyar kanta a 'kasa! ashe haka yake da 'kirar mazantaka gani tayi kirjinsa a cike dam! ga jikinsa a murd'e! cikinsa a shafe tamkar wanda baya cin abinci! Karkarwa jikinta ya shiga yi gumi na yanko mata daga ko wace kusurwa ta jikinta.... "*GA MASU BUKATAR KARANTA BOOK DIN ZASU TURA #300 SINGLE, VIP GROUP #600 GA ACCONT" D'IN DA ZA'A TURA KUDIN.......0542382124.....BINTA UMAR GTBANK. IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA KIYI MIN MAGANA TA WHASAP DA WANNAN NUMBAR......07084653262 IDAN KIN SAN BA BIYAN KUDIN LITTAFIN NAN ZAKI YI BA DON ALLAH KADA KI KIRA WAYA TA KO KIYI MIN WATA MAGANA TA WHASAP* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA SO KU BIYA KUDIN LITTAFIN ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS. 90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE.* * MADADI!! * _(Ba Haram Bane!!)_ *NA* *BINTA UMAR ABBALE * ~~~~~~~~~ *MANAZARTA WRITES ASSOCIATION * _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ ~~~~~~~~~ *LAST FREE PEGE* *19_20* "'Dauke kanta tayi lokacin da taga yana kokarin sanya gajeran wando, ta tsirawa 'kasan kafet ido gabanta" "sai duk uku-uku yake, muryarsa taji ta dokin kunnanta inda yake cewa""Ta tashi taje tayi wanka tazo ta kwanta, ba tare da tayi kuskuran kallonsa ba ta mike salo-salo ta nufi bandakin, to koda ta shiga toilet din ma kasa yin komai tayi ta jingina jikin bango(garu) tana tunani yanzu idan Abbah Abbas yace zai kar'bi sadakinsa ya za tayi? wani irin tsoro ne ya shige ta, taji gabad'aya gwiwowinta sunyi sanyi! ita yanda ma za'ayi ta kwanta gado d'aya dashi take tunani gashi ta lura dashi sai wani abu yake yi tamkar bai damu da halin damuwar da take ciki ba. Da kyar ta d'an sirka ruwa yayi d'umi tayi wankan, ta" wanke bakinta kamar dai koda yaushe kafin ta kwanta sai tayi brush ta daura towel jikinta ya tsane tsaf "sannan ta mayar da kayan jikinta ta fito, kwance ta same shi saman gado babu komai a jikinsa sai gajeran wando ga fitilar dakin a kunne! simi-simi ta nufi kan kujerar data ta bari, sunanta taji ya kira cikin" "ma'koshi, tsayawa tayi ba tare data juyo ba, Yace.""Ba kiyi wankan bane.""? a sanyaye tace.""Nayi.""" "Yace.""To cire hijabin kizo ki kwanta."" Tace.""Abbah kayi hakuri zan kwanta kan kujera."" Mikewa zaune yayi yace.""Tunda nake da Halimatu bamu ta'ba raba shimfida ba saboda haka bana so mu fara haka dake," kizo ki kwanta a makwancin ki Ni babu abinda zanyi miki.'' yafada yana nuna kusa dashi. Hawaye suka zubo mata tayi tsaye tana kallosa gami da d'umbun mamakinsa. "Ganin ta'ki zuwa yasa ya mi'ke ya nufi inda take, cikin gaggawa tayi 'kasa da kanta dan gabadaya ji tayi" ilahirin tsigar jikinta na mi'kewa sakamakon ganinsa babu kaya a jikinsa. "Yana zuwa ya ri'ke hannunta yaja ta suka nufi bed din, zaunar da ita yayi ya zauna yana kokarin cire mata" "hijab din jikinta, ta ri'ke hannunsa tana girgiza masa kanta bakinta sai rawa yake tana so tayi magana amma tana gudun yayi mata fad'a." "Bai saurareta ba sai da ya cire mata hijab din yabi jikinta da kallo, Atamfar d'azu ce a jikinta, d'inki kuma" mai nauyi ne da dogon hannu gashi garin ana zafi dalili kenan daya sanya shima bai kwanta da riga a "jikinsa ba, Yace.""Ki dan cire koda rigar jikinki ce sai kiyi daurin kirji da zanin dake jikinki zaki fi jin dadin kwanciya.""" "Cikin rawar murya da rawar baki tace""A'a ai bana kwanciya babu riga a jikina komai zafi zan iya kwanciya" "a haka."" Girgiza kansa yayi ya raba 'kafafunsa ya jawo ta yasa a tsakiyar sa yana fad'in akwai cutuwa ki kwanta da riga a jikinki. kawai sai ya shiga kokarin cire mata rigar. Rirri'ke hannunsa take tana fad'in" """Allah zan iya kwanciya da riga a jikina dan Allah kada ka cire min riga Abba. Bai saurareta ba sai da ya" "cire mata rigar jikinta yayi saura daga ita sai breziya ganin haka yasa tayi saurin sa hannayenta duk biyun ta rufe kirjinta dasu, hawaye na zubo mata! kokarin mikewa zaune take a jikinsa ya hanata kafafunsa ya hard'e da nata sosai ya matseta a jikinsa, ya kwanta rigingine itama ta kwanta rigingine duk rabin jikinta na jikinsa, bargo ya janyo ya rufe musu jikinsu ya d'ora hannunsa guda saman cikinta dai-dai" cibiyarta.....Naja'atu ihu! ne kawai bata kurma ba amma hawaye tuntuni yake gudana a fuskarta.. Addua yake so yayi musu amma ya gagara yi dan gabadaya hankalinsa tashi yayi jikinsa yayi wani irin "sanyi wata irin sha'awar yarinyar ce ta taso masa, gabad'aya a yanda ya tsara shine ba zai taki yarinyar ba sai an dan kwana biyu tukkuna yana so ya nuna mata kulawa ne ya kuma nuna mata cewar abinda take tunanin baza ta samu ba dangane da auranta dashi to ba haka bane dalilin da yasa kenan ya shirya" tsaf! domin ya siye zuciyarta da kalolin soyayyarsa. "Rintse idonsa yayi yana sauke wata zazzafar ajiyar zuciya, gaskiya da wuya ya iya daurewa dan gabadaya" "hankalinsa ya tashi jinta a cikin jikinsa, ba tare da yayi tunanin komai ba kawai ya shiga wasa da hannunsa a saman fatar cikinta yana d'an shafa ramin cibiyarta. Hannunsa da yake yawo a jikinta tayi" "saurin ri'kewa 'kam! tana wani irin kuka tace""Abbah dan Allah ka bari dan Allah.""!! Shuru yayi yana" "sauke ajiyar zuciya, ita kuma ta kama hannunsa ta ri'ke kamau! tana sheshsheka! Lumshe idonsa yayi" "yana adduar Allah yasa bacci ya daukeshi ya huta, amma yasan da 'kyar yau ya iya rintsawa sakamakon azababbiyar sha'awar dake taso masa." Ita kuwa jin ya daina shafa jikinta yasa ta sauke ajiyar zuciya amma dai duk da haka bata sakar masa "hannu ba yana d'amke a cikin nata, a wautar ta wai so take yayi bacci sai ta sake shi ta kuma bar masa gadon Kawai sai taji ya mike zaune da sauri ya burkitata 'kasan gadon, rintse idonta tayi ganinsa yayi" mata rumfa zai danneta! """Wayyo Allahna.""! Tafada muryarta na hard'ewa, hannunsa yasa a saman fatar le'banta yana shafawa a" hankali a hankali! Tsira masa ido tayi jikinta sai karkarwa yake. Gani tayi duk ya koma wata kala idanunsa sunyi jawur! duk da ya rage hasken fitilar dakin bai hanata hango tsabar sha'awarta a cikin 'kwayoyin idonsa ba!! Ganin tana yi masa wani irin kallo ne yasa ya kashe dusasheshen hasken da ya bari a take d'akin yayi "duhu lokacin ne kuma Allah ya bata damar ture shi ta mike zaune da sauri tana laluben hanyar sauka, hannunta ne ya sauka kan jikinsa, taji ta ri'ke wani abu mai tauri da kwari a hannunta! a gigice ta saki ta" dira kasan bed d'in tana makyarkyata. "Kamota yayi da saurin gaske ya mayar da ita ya kwantar, still ya sake yi mata rumfa da jikinsa. Hucin" numfashinsa ne ya dinga dukan fuskarta hakan ya tabbatar mata da cewar fuskarsa na dab da tata! ta dinga kuka tana kauda kanta! Saukar fuskarsa taji a tsakanin wuyanta yana sakar mata wasu zafafan kesses (Parsonality) Wanda yayi bala'in rikirkita mata lissafi....... A take tsigar jikinta ta shiga tashi sakamakon jin yanda yake goga mata gashin fuskarsa a jikinta sai tsikarinta yake yi tana jin 'kaikaiyi! "Bud'e baki tayi da kyar tace.""Ab Abbah please ka bari ba girman ka bane bana jin dadin wannan abin" "da kake mun.""" Kamar ta 'kara tunzarashi dayin abinda yake yi ya cigaba da goga mata gefan fuskarsa a fuskarta da "wuyanta, a jiyar zuciya ta shiga saukewa tana kauda kanta had'e da tutture fuskarsa. Cikin dubara" "irin tashi ya samu nasarar had'a bakinta da nasa ba tare da tayi tsammani ba kawai sai jin bakinta tayi a cikin nasa yana tsotsa tamkar mai tsotsar alawa! ta dinga kokarin cire bakinta ta kasa saboda ya riga ya ri'ke da nasa! Wasu hawayen bakin ciki da takaici ne suka shiga zubo mata, *Wai yau Abbah Abbas shine" ke kissing d'inta baki da baki kai wannan rana ba zata ta'ba mancewa da ita ba* Shi kuwa wani irin sha yake wa bakinta kamar zai shanye mata ruwan bakinta tsotsa yake yana sa "harshensa a sa'ko da lokonan bakinta har wani tallafo kanta yake yana kyarma da rawar jiki, kai!! bai ta'ba jin baki mai sugar irin nata ba wani irin za'ki yawun bakinta ke dashi Da 'kayar ya cika" mata harshe aikuwa gabadaya da le'bunanta da harshen suka d'umame da radad'in zafi sakamakon jin ba'kon abu da sukayi suka dinga yi mata zafi da zugi! kuka take tana dukan kirjinsa had'e da turje-turje da kafafunta! Cikin wani irin hali ya sauke daga kanta ya samu gefen gadon ya zaune had'e da dafe kansa! Gabad'aya yarinyar ta tayar masa da hankali gashi yana ganin ba zai samu biyan bukatarsa ba a gurinta. Mi'kewa zaune tayi tana kuka tana laluben zaninta domin ta daura a jikinta wannan karon ma a cinyarsa "ta d'ora hannunta, jin kamar gashi-gashi yasa da sauri ta cire hannunta! tana matsawa baya! can lokon gadon ta makure jikinta ta janye bedshirt din ta rufe jikinta dashi tana hawaye." "Sautin kukanta ne ya cika masa kunne, ya dan juyo a hankali yana kallon bayansa, duk da akwai duhu a" "dakin bai hanashi hangota a can 'kuryar gado ba, ya dan shafa kansa cikin wani irin hali na damuwa gami da bukatuwa ya mike ya nufi toilet domin ya tsarkake jikinsa. Har ya fito daga toilet din bai daina jin" "sheshshakar kukanta ba, sai ya kunna fitilar dakin a take dakin ya gauraye da haske." "Rintse idonta tayi da saurin gaske tana sake matse jikinta guri guda, bed din ya hau, sai ta zabura tana" "rawar jiki tace""Abbah dan Allah kayi hakuri kada kayi min komai.""" Ganin yanda take ta makale jikinta a jikin bed din yasa ya dan janyo hannunta aikuwa ta 'kwala 'kara! had'e da fizge hannunta ta sauka daga bed din tana kare jikinta da bedshirt din hannunta. "Ranshi ne ya 'baci da abinda take yi kawai sai ya rabu da ita ya kai hannu ya kashe hasken dakin," kwanciyarsa yayi ya rufe kafafunsa da blankent. Ita kuwa kan Sofa ta lalla'ba taje ta zauna tana me tsirawa bed ido gani take kamar zai biyo ta kan "kujerar................Abbah Abbas bacci ne ya dauke shi bacci mara dad'i baccin da ya sanya shi mafarkai barkatai. Naja'atu kuwa yanda taga dare haka taga rana sai gefin asuba bacci ya soma fizgarta, jin motsin" tashinsa yasa firgigit ta mike zaune tana zazzare ido. Yana kunna hasken dakin ya mike ya nufi toilet ya daura alwala kamar dai yanda ya saba ya gabatar da nafila kafin ya wuce massalaci Sai da ya fita sannan ta sauke ajiyar zuciya ta mike da sauri taje ta duba rigarta tasa ta dauki hijabinta ta zura da sauri ta fita daga dakin. "Dakin su Saddiqa ta nufa koda ta shiga dakin sai ta gansu duk a kwance basu tashi ba, taji dadin hakan" "da sauri ta nufi toilet din dakin, ta tub'e kayan jikinta, ruwa ta hada tayi wanka kana tayi brush sai ta daura alwala ta fito A gurguje ta shirya ta tsaya kan Saddiqa tana tashinta, gabadayansu suka tashi" "tace""Ku tashi kuje kuyi alwala.""" "Saddiqa ce ta fara tashi ta nufi toilet din, ita kuma ta gyara dadduma ta tayar da sallah." Bayan ta idar da sallar kwanciya tayi kan daddumar ta takure jikinta daga zarar ta tuno da abinda ya faru a tsakaninta da Abbah Abbas sai gabanta ya yanke ya fad'i! har yanzu le'bunanta zafi suke mata idan ta tuno da yanda ya dinga shan bakinta tsigar jikinta duk sai ta mike. "Mussadiq ne yazo ya zauna kusa da ita yana gaisheta, ta mike a sanyaye tana amsawa, Saddiqa da" Mufida ma suka gaisheta a nutse ta amsa musu. 'Dakin ya shigo hannunsa ri'ke da wani "maidaidaicin carbi, Naja'atu tayi saurin sunkuyar da kanta 'kasa kwata-kwata bata so ta had'a ido dashi." "Ya tsaya daga bakin kofa yana fadin ""Ashe kun tashi."" Mussadiq yace.""Eh Yaya Naja'atu ce ta tashe mu.""" "Ya d'an kalleta da gefan idonsa, ya kauda kansa yana amsawa gaisuwar 'yayansa, juyawa yayi zai fita yaji muryarta tana gaishe shi, ba tare da ya Juya ba ya amsa, ya bude kofar dakin ya fita." "Gabad'ayan su suka mike zasu fita tace""Ina zakuje.""? Saddiqa tace""Zamuje mu gaisa da Mommy ne.""" shuru tayi tana kallonsu suka fita daga dakin.. "Lokacin da suka shiga gaishe da Halisa yana tsaye a dakin suna magana, ya bisu da kallo har suka fita" "yana mamakin ina ita Naja'atun wato ba taji maganarsa ta jiya ba kenan? a tunaninsa zata biyo yaran suzo gaishe da Halisan tare, Inda ita kuma sam ba tayi tunanin hakaba saboda ba gaishe da Halisa ne a gabanta ba abinda ke gabanta shi ya dameta.........Ya kalli Halisa a nutse yace.""To yanzu nawa kike ganin" zasu isa.? "Mikewa tayi daga kan daddumar da take zaune tana kokarin cire hijabin da tayi sallah dashi tace""To ka" "zauna mana sai nayi maka lissafi."" Jim yayi kafin ya zauna! dan yana sane ya'ki zama a dakin saboda yasan halin da yake ciki na sha'awa baya so taja ra'ayinsa ya aikata wani abun da ita a cikin hakkin wata." "Zama tayi kusa dashi tana nanikar jikinsa, ya kalleta babu yabo babu fallasa yace.""Kiyi min bayanin nace" "kamar nawa ne zai isa da zaki siyo mata sutturun da suka dace.""" Fuskarsa ta shafa da hannunta ta kai bakinta kan kuncinsa ta manna masa kiss! tana me d'ora hannunta "a cinyarsa, ganin irin abinda take masa ne yasa ya gane abinda take nufi! Yace.""Kin san dai ba'a cikin kwanakin ki kike ba ko.""? Marairaicewa tayi tace""Haba ai kaima kasan ba zab iya bari har sai nan da" "kwana shida ba wallahi, ni dai gaskiya a bukace nake.""" "Kallonta ya shiga yi yana mamakin maganarta, yace.""To nima bani nake da kaina ba sai kije ki tambayi" "mai hakki idan ta baki aro na shikkenan.""" "'Bata rai tayi tana sake shigewa jikinsa tace""Allah ya kiyaye na tambayi yarinyar nan wani abu kaine kake" "da iko da kanka kuma kafi kowa sanin halin da nake shiga idan ina cikin wannan halin dan haka ni ba zan iya sauraran komai ba sai na samu biyan bukatata."" Kallonta kawai yake dan shi ya rasa ma abinda zai ce mata, yana jinta tana ta shashshafa jikinsa tana masa salo iri-iri to abinka da wanda dama yake a bukace" "a take ya bada kai bori ya hau, suka shiga biyawa junansu bukata..." Gabad'ayansu har ita suka fito palo suka zazzauna suna hira kar'fe takwas shuru basu ga gilmawar masu "gidan ba, tara ma tayi shuru, basu fito ba, A hankali ta kalli Mussadiq tace""Ko Abbanku ya fita ne.""? Yaron ya girgiza kansa da fad'in ""Wallahi ban sani ba dazu dai da muka shiga gaishe da Mommy na ganshi a dakin.""" "Shuru tayi tana nazarin maganar yaron, ta kalleshi cikin sanyin jiki tace""Kana jin yunwa ko.""? Kai ya" "d'aga mata, mi'kewa tayi ta kalli Saddiqa da Mufida tace""Kuzo ku nuna min kicin din na had'a muku break fast."" Suka mike da sauri suna murna, tare suka shiga kicin din nan suka shiga aiki kowanne ta bashi abinda zai taimaka mata dashi Halisa ta samu abinda take so sosai ta ri'ke wuta ta'ki" barinsa ya huta shi kuma jinta zam-zam! ya dinga d'imautar dashi ya kasa hakura da ita suka dinga abu daya kamar jaraba koda yake dama can sun saba tunda jajayen sawun su. Sai kusan goma da rabi ya "fito daga dakin, lokacin su har sunyi break dinsu suna zaune dai a palon suna hira wanda take saka musu baki jefi-jefi Ido suka had'a ita dashi lokacin da ya fito daga dakin Halisan duk sai ya diririce! lokaci" "guda ta gane rashin gaskiyarsa kuma ta gane abinda suka dade sunayi a dakin, wace irin magana ce za'ace an shiga daki sama da awa uku anayi ai da akwai alamun tambaya. 'Dauke kanta tayi sam" "bata wani ji ciwo ba dan ba wai sonsa take ba ballanta taji haushin abinda sukayi mata, cigaba tayi da dan dudduba wayarta dake hannunta, Shi kuma da sauri yake kokarin shiga dakinsa. Mussadiq" "yace.""Yawwa Yaya Naja'atu ga Abban namu ya fito dama nace miki bai futa ba.""" Da sauri ta kalli yaron tana d'an hararasa! Shi kuma Abbah Abbas din tsayawa yayi yana kallon Mussadiq "din yace.""Waye yazo nema na.""? Shuru tayi, Mussadiq yayi karaf yace."" 'Dazu ne Yaya Naja'atu take tambaya ta wai ko ka fita saboda munji shuru bamu ga ka fito daga dakin ka ba shine nace mata kana" "dakin Mommy.""" Naja'atu taji kamar ta kwad'awa yaron mari! kada fa Ya d'auka ko sonsa take shiyasa take tambayarsa "Shi kuwa Abbah Abbas murmushi yayi yana dan shafa gemunsa ya kalleta a nutse yace.""Ina tare da" "Halisa muna tattauna magana mai muhimanci insha Allah anjima zakuje tare dake da ita ki za'bi irin kayan da kike so domin ita na wakilta ta had'a miki lefe."" Tsakaninsa da Allah ya fad'i maganar dan shi" yana ganin meye a ciki dan Halisa ta had'a mata lefe ai duk a zaman d'aya! Ita kuwa Naja'atu maganar ce ta girmi tunanin ta wannan ma ai rainin hankali ne da zaice Halisa ta had'a "mata lefe kuma har ya iya fad'a mata da bakinsa, zuciyarta tace mata ""To ke meye abin damuwa ai ba sonsa kike ballanta na dan yace Halisa ta had'a miki lefe kiji haushi!!! "" Eh duk da ba sonsa nake ba amma ai hakan bai dace ba abin kamar yazo da cin fuska a ciki, to idan ya kasance tana sonsa kuma haka zai dinga d'ora kishiyarta kan al'amuranta abinda ba zata iya jurewa ba kenan don ita ba Yaya Halimatu bace. Dauk'e kanta tayi ba tare da tace masa komai ba, shi kuma yanayin yanda yaga ta nuna sai" "yaji wani farin ciki ya lullu'beshi yana addua Allah yasa yarinyar ta soma sonsa. Yana shiga daki, Ita" "kuma ta shiga fad'a da zuciyarta ganin kamar tana so ta takura mata gurin ganin kamar anyi mata rashin adalci a gidan zuciyarta sai ingizata take akan ta dauki mataki ta bishi daki ta tambaye shi me tsaya yayi a dakin Halisa har tsayin awa uku alhalin yasan a cikin kwanakin auranta yake, sannan kuma tace ita bata yarda Halisa ta had'a mata lefe ba!.....Allah mai iko! abinda zuciyarta keta sa'ka mata kenan duk ta kasa samun nutsuwa a gurin sai kallon kofar dakin nasa take tana tununin taje ko kada taje? Mikewa tayi ba tare da dogon nazari ba ta nufi dakin nasa har tasa hannu zata bude kofar sai kuma ta fasa, ta juya cikin" sanyi jiki ta nufi dakinsu Saddiqa kwanciya tayi ruf da ciki kawai ta tsinci kanta da fashewa da kuka. *Tofah! Ko kukan me Naja'atu take? Ita da take ikirarin bata kaunar Abbah Abbas din to meye najin haushi dan ta ga ya dad'e a dakin matarsa? Lallai akwai alamun tambaya dangane da Al'amarin Akwai-Akwai_Akwai!! Rikita_Rikita anan agaba! Wai shin ya zata kaya ne a tsakanin Abbah Abbas da Amaryarsa? Shin zai samu nasarar kar'bar budurcinta ko kuwa? Salim zai kyale Naja'atu tayi rayuwar aure da Mijinta Kuwa? Wane Babban kuskure Naja'atu zata tafka anan gaba? Meye makomar Yaya Ramlatu da Halisa? akwai sauran labari anan gaba!!!! Ga duk wanda yake da ikon biyan kudin littafin nan ya biya ya karanta #300 ko #600 basu isa su biya kudin littafin nan ba Koda yake ai 'KARYA ce amma dai ni nasan 'karyar tawa tana Tasiri a wani gurin dan haka da kai da ke ina so duk ku biyo ni domin a cigaba da tafiyar daku Single #300 Vip #600 Babu tsada Kada ki nuna ganin 'kyashin biyan kudi ki karanta kice bari ki bari idan an sato ki kiranta Allah ya isa! Idan anyi magana kice kema "gani kikayi an turo shiyasa kika karanta, to duk wanda ya'ki sharar massalaci zaiyi ta kasuwa! *" *Masu had'a min decoment na books daga zarar na gama bazan ce komai ba sai dai na ro'ki Allah ya tattara muku zunuban da na d'auka gurin rubuta littafin ya d'ora muku a kanku Shikkenan sai a raba mana zunubin tare daku kun rage min nauyi.* *Masu tambayar wai ni bana littafin free ne sai na kudi: Amsa To farkon littafina Nana Khadija Free ne "zagi da 'korafi gami da rashin hakuri irin na redars yasa na mayar dashi na kudi, tun daga haka shikkenan na daina littafin kyauta amma akwai book dina RUWAN DARE free ne book1 yana nan yana yawo a groups ga duk mai bukatar karantawa sai ya tambaya a groups insha Allah idan na gama rubuta littafin MADADI zab cigaba da typing d'insa RUWAN DARE free ne bana kudi bane! idan na gama Madadi zan" cigaba da rubuta muku shi * *Masoya masu sahihiyar kauna Ina alfahari daku * "*GA MASU BUKATAR KARANTA BOOK DIN ZASU TURA #300 SINGLE, VIP GROUP #600 GA ACCONT" D'IN DA ZA'A TURA KUDIN.......0542382124.....BINTA UMAR GTBANK. IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA KIYI MIN MAGANA TA WHASAP DA WANNAN NUMBAR......07084653262 IDAN KIN SAN BA BIYAN KUDIN LITTAFIN NAN ZAKI YI BA DON ALLAH KADA KI KIRA WAYA TA KO KIYI MIN WATA MAGANA TA WHASAP* *MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA SO KU BIYA KUDIN LITTAFIN ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS. 90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE.* Mdd *21* "Halisa kuwa bayan fitar maigidan daga dakin, cikin farin ciki ta d auki wayarta ta shiga kiran Yaya" "Ramlatu, duk ta shaida mata abinda ke faruwa, ta fada mata cewar maigidan ya bada kud'i kimanin dubu" dari biyu yace wai a siyawa amaryarsa kayan lefe masu kyau sannan yace ma idan basu isa ba ta fada "masa. Yaya Ramlatu taja tsaki! tace""Ko dubu dari ba za'a kashe mata ba gurin had'o lefen komai 'kananu za'a siya mata dan haka idan kin tashi tafiya kasuwar ki biyo ta gidana mu tafi tare."" Halisa tace""Eh to da cewa yayi wai muje tare da yarinyar ta duba abinda takeso."" Yaya Ramlatu tace""Ki san dubarar da zaki masa ki fito ke kad'ai meye wani dole sai anje da ita."" Halisa tace""Zan nuna masa yarinyar ta zauna ta kula da yara insha Allah za'a siyo mata komai mai inganci."" Yaya Ramlatu tace""To ke kuma nawa ya baki kudin naki kayan."" ? Murmushi tayi tace.""Nima dubu dari biyu ya bani kamar nata kuma yau da daddare yace zai shigo min da mukkulin sabuwar motata."" Yaya Ramlatu ta rangad'a bud'a tace""To Alhamdullhi babu shakka kwalliya ta soma biyan kudin sabulu dan haka idan zaki zo kada ki manta da al'kawarinmu" "dake.""" "Halisa na dariya tace""Haba Yaya Ramlatu ai 'Yar halak ce ni insha Allah zan kawo miki."" Cikin farin ciki" "Yaya Ramlatu tace""To Allah ya 'kara mallaka miki mijinki a hannuki."" Halisa ta amsa da amin tana cike da farin ciki ganin ta kowane 'bangare tana samun biyan bukata. Cikin shararriyar kwalliya ta fito palon" "ta samu yaran suna zaune a palo suna kallo, ba tare da tace musu komai ba ta nufi dakin maigidan, shima lokacin yana kokarin fitowa cikin shirin fita, ganin uwar kwalliyar da taci tana kamshin turare sai ya 'bata fuska yace.""Keda zaki shiga kasuwa kuma meye nayin kwalliya harda shafa turare."" Tayi fari da ido kamar yanda ta saba idan za tayi masa magana tace""Wallahi shaf na manta ban fad'a maka ba yau ne bikin sunan 'Yar yayata data haihu a unguwar Gaida to inaso in fara zuwa can kafin naje kasuwar."" Yace.""Anya kuwa sai dai ki za'bi d'aya dan idan kin tafi suna da zuwa kasuwa lokaci zai 'kure baki dawo gida ba."" Da sauri tace""Shine ai nace mai zai hana ita Naja'atun ta zauna ta kula da yaran tunda amarya ce bai kamata ace daga zuwanta ta fara yawo ba insha Allah zamuje tare dasu Shamsiyya zan siyo mata komai mai kyau wanda ake yayi."" Yana gyara zaman hularsa a kansa yace.""Wannan shawarar taki tayi" "kyau dan gabadaya banyi tunanin hakan ba okey muje sai na ajiye ki a gidan bikin.""" "Farin ciki ya cika mata zuciya, ta juya tana wata irin tafiya irin ta manyan mata." "Tsakiyar palon ya tsaya yana kallonsu, ya kalli Mussadiq da fadin""Ina Yaya Naja'atu.""? Yaron" "yace.""Tund'azu data shiga daki bata fito ba mybe bacci take."" Ba tare da yace komai ba ya nufi dakin yaran." Ruf da ciki ya sameta bayan ta gama kukanta bacci ne ya dauketa a haka. Ya tsaya kanta yana k'are mata kallo. Halin da ya shiga lokacin da yake kiss d'inta jiya kawai yake tunowa yarinyar nada wani sirri na mussaman a tare da ita. Hannu yasa ya dan shafi gefan fuskarta yana kiran sunanta Ta bud'e idonta wanda kuka da bacci ya mai dasu wani iri! shi kuwa ai ji yayi tsigar jikinsa ta tashi ganin yanda idanunta suka jirkice kamar wacce take ciki sha'awa. Gyaran murya yayi kamar yanda ya saba ya sake kiran sunanta. "Mikewa zaune tayi tana goge fuskarsa had'e da d'an zum'bura baki ta'ki kallon inda yake tsaye. Yace.""Za" mu fita tare da Halisa zaki zauna tare da yara kafin ta dawo da nace zakuje tare domin ki duba abinda kike so sai kuma yanzu take ce min zata je bikin suna ina ganin ke sai ki zauna tare da yaran a gida kafin "Allah yasa ta dawo."" Fuskarta ta goge tana kallon kasan gadon da take zaune tace""Nifa Abba daka bar" "kudinka bana son wani lefe kayan da nake dasu ma sun isheni.""" "Cikin d'an mamaki yace.""Saboda me? ai hakkinki ne dole nayi miki tunda inada iko."" Kamar ta fad'a" "masa mara dad'i sai dai tayi shuru tana d'auke kanta, tayi al'kawarin ko an siyo kayan ba za tayi amfani dasu ba." "Agogon dake daure a hannunsa ya dan kalla sha biyu shaura na rana ya nufi kofar fita yana fad'in ""Sai" "mun dawo ki kula da kanki da yara."" Wani irin kallo ta bishi dashi har ya fita daga dakin taja tsaki mai karfi ta koma ta kwanta." "Halisa a bakin titi tasa ya ajiyeta tace ya sauketa zata shiga da 'kafa, nan ya 'kara jaddada mata cewar" kada ta kai dare tayi ta gama duk abinda za tayi ta koma gida da wuri. ta amsa masa kamar gaske tana d'aga masa hannu "Tana ganin motarsa ta wuce ta tari a daidaita sahu ta shiga kai tsaye unguwar gwangwanxo ta nufa," "dama tun kafin taje ta shaidawa Ramlatu gata nan a kan hanya dan haka a shirye ta tarar da ita ba kuma tare da 'bata lokaci ba suka dauki hanyar gidan 'Yar Sa'adu! koda suka isa gidan cike yake da manyan mata masuji da kansu, kamar dai koda yaushe 'Yar sa'adu na zaune kan kujerarta mata sun kewaye ta suna ta d'aga magungunan mata suna dubawa ita kuma tana musu 'karin bayani a kan maganin, 'Yar Sa'adu na ganin su Halisa ta rangwada guda ta gyara zamanta tana dariya ta kalli Halisa da fad'in ""Kaga Uwargidan Alhaji Abbas Lallai tunda naga kina kyallin goshi akwai magana ai dama nace sai kin dawo da" kafafunki.'' Halisa ta bata hannu suka tafa suna kyalkyala dariya! suka zazzauna suna gaisawa da juna. "'Yar Sa'adu tace"" Aikuwa kun taki sa'a dan jiya aka kawo min kaya daga Zindar gasu nan masu kyau ne" "sosai sai da kudi?"" Yaya Ramlatu ta d'aga wata madaidaiciyar roba wacce take cike da wani abu shi ba black ba browan ba."" 'Yar Sa'adu tace""Wannan maganin dake hannunki sunansa sai maigida Ihu!! da kuwwa! idan kika mallaki maganin nan kin wuce takaici wallahi duk abinda kikace yayi miki sai yayi miki.""" "Da sauri Halisa ta kar'bi maganin tana dubawa! dariya tasa tace ""Lallai maganin nan za'aje dashi koga" "yanayin hoton dake jikinsa, Namiji da mace ne tsirara suna sex wani irin style mai ban mamaki! budewa tayi ta d'an dangwalo maganin a hannunta ta lasa! taji wani za'ki!! fauuu! a bakinta, tsigar jikinta sai da ta tashi ta rintse idonta." "'Yar Sa'adu ta bawa ta kusa da ita hannu suka tafa! tana dariya tace"" 'Yar gari taji sabon abu a bakinta ai" "nake fad'a miki Halisa yanda kikaji za'kin maganin nan haka kema zaki dinga za'ki da dad'i mutukar kina amfani dashi, kuma amfanin maganin nada yawa dan yana 'kara karfin sha'awa sosai idan ma mijinki baida karfi yana saurin kawowa to wallahi karfin wannan maganin sai ya mayar dashi tamkar ayu kullum yana ma'kale dake." "Halisa tace""A'a ni mijina baida wannan matsalar sai dai na siya dan biyan bukatar kaina dan haka yanzu" "nawa ne maganin.""?" "'Yar sa'adu ta gyara zamanta tana 'kas-'kas da cingum din bakinta tace""Dubu dari ne kacal amma tunda" "ke costomar ce ki bada dubu casa'in da biyar na cire miki dubu biyar."" Yaya Ramlatu tace""Haba dai 'Yar Sa'adu ki sake yi mata ragi kin san fa yanda garin yake kuma kinga komai tsadar magani Halisa bata ta'ba" "gandar siya kuma kin san idan taji dadinsa in ya kare zata dawo ta siyi wani.""" "'Yar Sa'adu ta kalli ta kusa da ita tana 'bata rai tace""Hajiya Mairo dan Allah nawa na siyarwa da matan da" "suka fita yanzu wannan maganin.""?" "Hajiya Mairo tace""Dubu dari ashirin.""! 'Yar Sa'adu ta kalli Halisa tace""Kinji dai da kunnanki dubu dari da" "ashirin na siyar dashi amma ke nace ki bada dubu casa'in da biyar kina neman ragi.""? Halisa tayi shuru tana nazari gabadaya kudin data fito dasu dubu dari biyu da hamsin ne har kudin kayan lefan Naja'atu kuma a ciki ta dauki dubu dari ta bawa Yaya Ramlatu dama tun kafin su fito sun gama yanke shawarar dubu dari kacal zasu kashe gurin had'awa Naja'at lefe, yanzu abinda ya rage a hannunta dubu ar'bain da" takwas ne tunda sunyi kudin mota da sauran. "Ta kalli Yaya Ramlatu tace""Ina ganin kudin kayan yarinyar nan zan bada dan gaskiya bazan bari maganin" "nan ya wuce ni ba.""" "Yaya Ramlatu tace""To kin tanadi abinda zaki fad'a masa idan kin koma gida.""? Murmushi tayi tace.""Sosai" "kuwa ni nasan karyar da zanyi masa. Yaya Ramlatu tace""Tom shikkenan."" Halisa ta zuge zif din jakarta ta fito da kudi ta shiga lissafawa.........." Bayan fitar masu gidan Naja'atu ta dan dauki lokaci a dakin a kwance tana tunane tunanen mafita a "gareta gabadaya ta rasa wane mataki zata dauka, ta kira wayar Salim sau curin masaki yaki dagawa, sai da taci kukanta ta koshi sannan ta fito palon a lokacin da Saddiqa take kokarin shiga dakin domun ta tambayeta abunda zasu dora na abincin rana Ganin yanda idanun antina nata sukayi fululu yasa" "jikinta yayi sanyi ta kalleta a sanyaye tace""Dan Allah Yaya Naja'atu ki daina kuka da damuwa ki kwantar" "da hankalinki wallahi Abbanmu zai kula dake ki daina damuwa.""" "Dan kauda kanta tayi cikin kokarin bagarar da maganarta tace""Waye ya fada miki kuka nake bacci nayi fa" "shiyasa idona yayi ja."" Saddiqa dai ba yarinya bace ballanta ta dauki maganarta sai dai kawai ta bar maganar a yanda ta fada tace""To shikkenan dama shigowa nayi na tambaye ki me zai mu d'ora na abinci.""? kai tsaye tace ""Muje kicin din sai muyi aikin tare."" Kai tsaye kicin din suka nufa tare." "Mussadiq ne ya shigo kicin din hannunsa rike da wayarta yana fadin ""Yaya Naja'atu Abbanmu na kiran" "wayarki."" Goge hannunta tayi ta kar'bi wayar tana dubawa, miss call dinsa ta gani, ajiye wayar tayi ta cigaba da aikinta." Kimanin minti biyar da fitar Mussadiq daga kicin din wani kiran ya sake shigowa kamar bata so ta daga "wayar, Yayi mata sallama ta amsa ciki-ciki Yace.""Ya gida ina fatan babu matsala.""? ""Umm."" Tace Yayi shuru na minti biyu kafin yace.""Ina fatan kunci abinci."" nan ma bata bashi cikakkiyar amsa ba. Ranshi ya 'baci yace.""Ki bude baki kiyi min magana meye wani umm! Tace""Gashi muna girkawa."" Yace.""To haka nake so ki gaishe min da yaran sai na dawo."" Shuru tayi masa yana kashe wayar ta ajiye tare da jan 'karamin tsaki! da sauri Saddiqa ta kalleta sai kuma tayi saurin dauke kanta ta cigaba da aikin dake gabanta sam ba taji dadin tsakin da akayi wa Abbanta nata ba kawai dai tayi shuru ne dan bata da yanda" za tayi. To Halisa da Yaya Ramlatu a gidan 'Yar Sa'adu suka lalace! sai bayan la'asar suka bar gidan kai tsaye suka "nufi kasuwar dubai ta jakara, nan suka shiga katin dan jummai suka shiga siyan atampopi da lesuna masu saukin kudi suka je gurin masu undar wear suka siyi masu saukin kudi takalma da jaka guda uku 'yan dubu daya da dari biyar sai mayafai hudu masu sharara da saurin lalacewa, kayan make up marasa kyau da ar'ha suka siya, Gabadaya basu kashe dubu saba'in ba gurin siyayyar ana shirye-shiryen kiran sallahr" magariba suka fito daga kasuwar. "Abbah Abbas tun misalin shida na yamma ya dawo gida, lokacin Naja'atu da Saddiqa sun gama komai" "hatta da abincin dare sun shirya tsaf koda ya dawo yaga gidan nashi tsaf yaran ma tsaf tsaf sai farin ciki ya kamashi dama ko lokacin Halimatu haka d'abi'ar su take kafin ya dawo gida sun gama komai zai dawo ya ga komai cikin kyau da tsari, sai dai kuma koda ya duba Halisa yaga bata dawo ba sai ranshi ya 'baci sosai! ya fito daga dakin nata da waya a hannunsa, lokacin ita kuma hayaniyar abubuwan hawa tasa ta kasa jin kiran da yake mata a waya. Cikin 'bacin rai ya shige dakinsa domin daura alwalar sallar" magariba. "Har yaje massalaci ya dawo Halisa bata shigo gidan ba, fitowa yayi daga cikin gidan ya tsaya a harabar" gidan yana sake kiran wayarta a rayuwarsa ya tsani matarsa tayi dare a waje Lokacin da yake kiran "wayar a lokacin mai adaidata ya sauketa ita da kayan data siyo, ta dan bubbuga gate din gidan maigadi" "ya bude mata, ganinta yasa da sauri ya bude karamar kofa ta fito ya dinga daukar kayan yana shiga dasu" "cikin gidan, shi kuwa Abbah Abbas jin tace masa gata nan shigowa yasa ya kashe wayarsa ya tsaya a gurin yana jiran shigowarta, Halisa ganin yanda fuskarsa take a murtuke yasa gabanta ya fad'i! a take ta shiga marairace fuska! ta bude baki za tayi masa magana kawai ya rufe ta da fad'a! takaici ya cika mata zuciya a gaban maigadi yake niyyar tozarta ta kawai sai ta wuce shi ta nufi cikin gidan, aikuwa hakan ya fusata shi! ya bi bayanta ciki nan ya sake rufeta da fad'a a gaban yara! duk suka mi'ke tsaye! suna kallonsu, Halisa duk kunya ta isheta ta kalli maigadi dake ajiye ledojin kayan data siyo tace ya fita! shima" da sauri ya fice yana mamaki! ashe haka ubangidan nasa yake da masifa. Ita kuwa Naja'atu dariya ne kawai ba tayi ba ta dinga kallon Halisa tana rantse-rantse da kokarin kare "kanta shi kuma ya'ki sauraranta sai da ya gama fad'ansa sannan ya bar gurin a fusace!! Halisa bayan barinsa gurin ta shiga rarraba idanunta a palon kawai sai taga yaran sun zuba mata ido har da wacce ta tsana a idonta ma sai taga kamar yarinyar dariya take. Cikin tsawa! tace""Dan ubanku kallon me kuke" "min? munafukan yara kawai.""! Da sauri suka shiga fad'in ""Mommy sannu da zuwa."" Ko kallonsu ba tayi ba ta watsawa Naja'atu harara! fuuuu ta wuce dakinta kamar zuciyarta zata tsage! babu shakka dole ta taka masa burki a gidan dan ba zata yarda ya dinga ci mata mutunci a gaban yara ba. Naja'atu kuwa" dariyar dake damunta ce ta su'bce mata sai tayi 'kasa da kanta tanayi tana d'an duba wayarta ta yini cikin takaici amma wannan abun da ya faru ya wanke mata zuciyarta *Na 'Dan samu sukuni nayi Typing duk da bashi da tsayi sosai Vip gruop afuwa idan baku samu da daddare ba kuyi hakuri dan Allah kuyi min adduar Allah ya bani ishashshiyar lafiya insha Allahu na warware sosai zaku samu yanda kuke so kamar yanda nayi muku al'kawari Nagode* *Littafin na kudi ne. Koda zaki ganshi a gruops to na sata ne idan kinaso ki biya ki karanta ga yanda abin yake* Vip Gruop #600 Normal Gruop#300 Accont: 0542382124..Binta Umar Gtbank Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar. 07084653262 *BINTA UMAR ABBALE* BHRBN *22* Halisa na shiga d'akinta ta shiga band'aki a gurguje tayi wanka ta fito daure da alwala sallah tayi ba tare da tayi doguwar addua ba ta mike daga kan daddumar ta fito palo tana muzurai Naja'atu na ganinta "tayi kasa da kanta dariya na nema ta kufce mata, ashe ta ganta tana 'kunshe dariya kawai sai ta shiga cusa mata ashar dama zagi bayayiwa Halisa wahala kamar 'yar maguzawa haka take, Tana kumfar baki gami da hayaniya tace""Mahaukaciya ni da zaki dinga yi min dariya?me kika gani na dariya a jikina?" "Naja'atu tace""Allah ya baki hakuri ni wallahi bake nakewa dariya ba ina hira da friend dina ne a waya! 'Kwafa tayi ta girgiza kanta da fad'in ""Zan gyara miki zama a gidan nan dan ni ba'sarki bace ballanta na ki raina ni."" Shuru palon yayi babu wanda yayi magana, Halisa cikin tsawa! da masifa ta kalli Saddiqa" "tace""Ina fatan kun girka abinda zakuci dan cikin ku babu wanda zanyi wa wani girki a yanzu dan na gaji.""" "Saddiqa tace""Eh Mommy munyi abinci Yaya Naja'atu ce ma tayi."" Tsaki taja tace""To ku taso ku dauko" "wad'ancan kayan ku kaisu dakin Abbanku."" Da sauri suka mike suka shiga kwasar ledojin kayan data siyo," sai da suka gama shiga da kayan dakin sannan ta shiga ta same shi zaune a kan Sofa da Loptop a kan cinyarsa "Jikinta a sanyaye ta zauna kusa dashi, tunda taga fuskarsa a murtuke tasan har yanzu bai huce ba." "Tace""Wallahi tsautsayi ne ya ritsani dani a maimakon ka fara tambayar dalilin da yasa nayi dare kawai sai" ka rufe ni da masifa a gaban maigadi da yar. Hannu ya d'aga mata tun kafin ta karasa maganar "yace.""Tunda dai ni ban isa na fad'a miki magana kiji ba to kije zan dauki mataki a kanki kin sani sarai na tsani kuje unguwa kuyi dare a waje ki fita tun safe ba zaki shigo gidanki ba sai bayan sallahr isha'i mai" "kikeyi a waje sai kace namiji.""" """Dan Allah kayi hakuri wallahi ba haka naso ba na fada maka tsautsayi ne ya ritsa dani a gidan bikin da" "naje wasu mata da ba'asan daga ina suke ba suka shigo gidan to kasan abinka da taro babu wanda ya damu dasu aka cigaba da harkoki dasu ashe 'barayi ne, na ajiye jakata kan gadon Maijego na tafi nayi alwala kawai na dawo na tarar da zif din jakar a bude sun kwashe rabin kudin daka bani nayi wa yarinyar" "nan siyayya."" Cikin rawar murya ta 'karashe maganar tana goge hawaye." Daina duba Loptop din yayi ya tsaya kawai yana kallonta. sai ta sake fashewa da kuka ta cigaba da cewa """Wallahi sama da 'kasa aka neme su aka rasa, sai daga sannan kowa ya farga ya fara duba jakarsa ashe bani kadai sukayi wa sata ba har da wasu amma dai tawa tafi muni.""" Shuru yayi yana nazarin maganarta jikinsa na bashi anya kuwa da gaske take? ganin yanda take kuka duk "ta koma kalar tausayi yasa ya amince da maganarta yace.""To yanxu a'ina kika samu kudin da kikayi wannan siyayyar bayan kince an sace.""" "Tana goge fuska tace""Ai ba duka suka kwashe ba sun bar min dubu cas'in da biyu shine bayan mun gama" "jajantawa junanmu na dauki Shamsiyya ta rakani muje kasuwar Dubai ta jakara na siyo mata atampa guda biyar les uku mayafai uku jaka da takalma uku sai undis da kayan make up, ajiyar zuciya ya sauke yace.""Allah ya 'kara kiyayewa daga yanzu sai ki san da wanda zaki dinga zama a cikin taro kuma ki kiyaye ajiye jakarki a'koina.""" "Hawaye ta goge tana sake 'kas'kantar da kanta kamar gaske tace""Insha Allah na kuma gode daka" "fahimce ni yana da kyau kuma ka duba kayan."" Yace.""Kada ki damu zan duba idan na gama abinda nake."" Yafada hankalinsa na kan loptop din cinyarsa. Halisa ganin yana aiki yasa ta mike ta fita daga" dakin zuciyarta wasai taji dadi da karyarta ta samu gurbi a zuciyarsa. ko kunya babu ta zauna a gurun "cin abinci ta cika cikinta da girkin Naja'atu mai dadi da gamsawarsa, ta mike ta nufi dakinta domin ta kira Yaya Ramlatu a waya ta fada mata yanda sukayi da maigidan." "Mussadiq ya kalli Naja'atu da hankalinta gabadaya yake kan wayarta, yace.""Yaya Naja'atu gobe ne za'a" "koma makaranta ko.""? A nutse ta kalleshi tace""Eh mana ai kunsha hutu sosai gobe kowa da kowa zai koma."" Mufida tace""Wallahi bana son a koma makarantar nan mutum ya tafi tun safe sai yamma akwai" "gajiya.""" "Tana 'yar dariya tace""Mufida in banda abinki waye kika ga ya ta'ba gajiya da neman ilimi ai kudi da ilimi" "mutum har ya mutu nemansu yake."" a dan sanyaye yarinyar tace""Hakane kuma anti.""" Naja'atu ta cigaba da charting d'inta tana murmushi Salim ne yake kashe mata jiki da hirarar soyayya! "voice note ya turo mata, ta mike ta nufi dakinsu Saddiqa dan tana jin tsoro ta bud'e a gabansu suji tasan Mussadiq da bin'kwakw'kwafi ita kuma Saddiqa da kishin Ubanta." "Ruf da ciki ta kwanta ta bude voice note din muryasa mai kashe mata jiki taji yana cewa""My Princess ina" "fatan kin wuni cikin koshin lafiya kuma ina fatan baki manta da al'kawarinmu dake ba.""" Itama gyara muryar ta tayi ta amsa masa da cewar tana nan lafiya kuma al'kawarin da tayi masa yana nan insha Allahu shine zai mallaki komai nata. Salim yaji dadi sosai da amsar data bashi kawai sai ya "sake gyara kwanciya a katifarsa ya shiga sakar mata zantukan batsa! masu muni! abin ya dinga bata mamaki da kunya dan tunda suke da Salim bai ta'ba yi mata irin wannan zantukan ba sai yanzu! Duk ya kashe mata jiki tana so tace ya daina ta kasa fad'a masa, kawai idan ya turo mata voice note din sai ta bude ta saurara tana lumshe idonta! wani idan ta bude kasa hakuri take sai ta bashi amsa! haka ta dinta mutsu-mutsu a kan bed din tsigar jikinta na tashi, sai ta dinga jin wani irin Feeling na taso mata. Abubuwan da Abba Abbas yayi mata a daran jiya su ta dinga tunawa tana sake jin maganganun" da Salim din keyi mata na sake tasiri a ranta da gangar jikinta. "Shigowar yaran ce tasa tayi saurin mi'kewa zaune tana dan daidaita yanayin ta, a sanyaye ta kalle" "Mussadiq tace""Zaka kwanta a gadon ka.""? Yaron yace.""Eh amma ki kwanta Ni sai na kwanta a kasan" "kafet. A sanyaye tace""Nagode Mussadiq."" Saddiqa ta kalleta tace''Yaya Naja'atu ya naganki wani iri ko baki da lafiya.""?" "Da sauri ta shafa fuskarta tana kauda kanta daga kan Saddiqar tace""Me kika gani lafiya ta lau bacci ne ya" "fara daukana."" Saddiqa tace""Ayya. juyawa tayi ta shiga dauko kayan baccinsu. ita kuma Naja'atun ta mi'ke simi-simi ta nufi toilet, tsayawa tayi a toilet din gabanta sai faduwa yake, hakika zantukan da Salim yayi mata sun masifar tayar mata da hankali gabadaya ma ji tayi ta rasa abinda ke damunta, jikinta babu" kuzari tayi wanka ta fito da kayan jikinta har yanzu tana jin feeling na damunta "Mussadiq ne ya mika mata riga da wando cotton yace.""Yaya Naja'atu gashi na dauki miki kayan baccin" "ki."" Kar'ba tayi ta zauna gefan gadon tana fadin ""Nagode Musaadiq ku kwanta domin ku tashi da wuri.""" Kwanciya sukayi kowanne na adduar bacci. "Shuru tayi tana takure jikinta gabadaya ma ta kasa sanya kayan bacci abin duniya ya isheta, wayar ta" "dauka tasa airpix a kunnanta ta kunna voice din Salim din tana saurara tana wani lumshe idonta. Kawai taji kira ya shigo wayar da sauri ta duba dan ita duk a tunaninta Salim din, gabanta ya" "fadi ganin numbar Abba Abbas, 'kin daga wayar tayi tana kallonta ta katse wani kiran ya sake shigowa," nan ma sai da ta kusa katsewa sannan ta dauka kamar wacce ta tashi daga bacci tayi magana. Taji muryarsa radau a kunnanta Wai ta kawo masa abinci da yake 'bacin ran Halisa bai bari ya zauna yaci abincin ba sai yanzu da ya gama aikinsa. "A sanyaye tace"" Yana daining abincin ai."" Yace.""Ai na sani cewa nayi ki kawo min daki okey.""" """To tace a sanyaye, ya kashe wayarsa....Kayan da Mussadiq ya dauko mata tasa ba tare data daura" "dankwali ba ta zura hijab a jikinta ta fita. Abincin dake jere a daning ta shiga dauka tana kaiwa dakin," "ya fito daga toilet yaga tana kokarin fita, yace."" Zo ki duba kayan ki gasu nan a ajiye.""" "Ta dawo ta dan zauna gefan kujera ba tare da ta ta'ba kayan ba, shi kuwa zama yayi kasan kafet ya" "tankwashe kafafunsa, yana jira ta zuba masa abincin, ganin ta tsirawa guri guda ido tana tunani yasa ya girgiza kansa kawai ya shiga zuba abincin da kansa, har ya kammala cin abincin bata duba kayan ba sai kallon guri guda take Sunanta ya kira yana kallonta, tayi saurin sauke ajiyar zuciya ta kalleshi sai" "kuma ta sunkuyar da kanta kasa, Abbah Abbas yana da wani irin kwarjini a idon mutane shiyasa bata iya had'a ido dashi sosai Babu wasa a cikin maganarsa yace.""Nace ki duba kayan ki gasu nan ki futar da" "wanda kike so a d'inka miki sai Halisa ta bawa telan dake mata dinki yayi miki.""" Ta 'bata fuska tana zum'bura bakinta ta tsani ya dinga yi mata maganar Halisa. Kayan ta jawo ta shiga "dubawa, al'amarin ya bata mamaki sosai, kaya marasa kyau duk kalar 'yan 'kauye shine za'ace kayan lefanta wallahi babu abinda za tayi amfani dashi a cikin kayan." "Cire hannunta tayi daga kan kayanta. Yace.""Ina fatan sunyi miki.""? Hawaye ne suka wanke mata fuska" "cikin shagwaba tace""Ni wallahi babu abinda yayi min aciki kayan duk masu arha ne gasu kalar 'yan kauye.""" "Dariya ta bashi yayi kadan yana mata wani irin kallon kasan ido yace.""To aike ma 'yar kauyen ce kuma" "meye laifin Halisa anan ai tayi kokari ki dai yi hakuri ki duba wanda za'a dinka miki a ciki.""" "Sosai take kuka tace""Wallahi dai-dai da undis ba zan sa a cikin kayan nan ba na hakura kawai abawa" "mabukata.""" "Dariya yayi sosai yace.""Lallai su Naja'atu manya mata to shikkenan tunda kayan basuyi miki ba na" "amince za'a bawa mabukata kamar yanda kika so, ina kike so kije kiyi siyayyar kayan lefan ki.""" "Hanci ta sha'ka tana goge hawayen fuskarta tace""Kawai ka barshi."" Yace.""Ai ba za'ayi haka ba na fada" "miki dole nayi miki sutturu tunda hakkin ki ne.""" "Shuru tayi tana sake goge fuskata, yace.""Kwashe kayan abincin nan kizo kiji wata magana."" Kallonsa tayi" "taga yana mata wani irin kallo, duk sai taji wani irin kasala ya kamata, ta mike da rashin kuzari a tare da ita ta shiga kwashe kayan abinci Shi kuma ya shiga dudduba kayan da Halisa ta siyo, duk da ba wani" "sanin kayan mata yayi ba ya gane kayan ba masu kyau bane, murmushi yayi ya had'e kayan a ledojinsu ya matsar dasu gefe guda. Naja'atu kuwa tsayuwa tayi a kicin tana tunani shin ta koma dakin ko kada" "ta koma tana jin tsoron ta koma ya sake danneta irin jiya, ajiyar zuciya ta sauke ta shiga tunanin" zantukan Salim na d'azu! tabbas da Abbah Abbas zai kwatanta mata irin soyayyar da Salim yace zai dinga yi mata da taji dad'i a yanzu dan babu abun da take muradi sai hakan. Har tayi nufin shiga dakin su Saddiqa kawai sai ta fasa ta bude dakin Abba Abbas din ta shiga. Yana "bandaki yana wanka ta zauna gabanta na faduwa, tunda ya fito ta sunkuyar da kanta 'kasa, ta kasa daga kanta ta kalleshi, Abbah Abbas din ne yake gigitata duk sanda za taganshi babu kaya a jikinta jikinta hausinewa yake." "Har ya gama shiryawa kanta na kasa tana wasa da hannuwanta, Kawai dakin ne taga yayi duhu! da sauri" "ta dago kanta tana kalle-kalle, inuwarsa ta hango yana zuwa inda take, da sauri ta mike tsaye! tana so ta sanja guri, ya dam'ke hannunta. Kafin tayi wani yunkuri taji ta a cikin kirjinsa, ajiyar zuciya ta sauke" "tana sake shigar da kanta cikin kirjinsa, kamshin turaran jikinsa ya sake hautsina mata tunani, Abbah Abbas kam yayi mamakin yanda ta yarda ya rungumeta yasa hannunsa kan mazaunanta yana shafawa, had'e da sakar mata kiss a wuyanta, ji tayi 'kafafunta na rawa, ya rik'eta sosai suka nufi gadon, hijab din" "ya cire mata ya shiga hautsina gashin kanta yana sassanawa, sai ajiyar zuciya yake saukewa." Abin mamaki Naja'atu kasa aikata komai tayi jikinta duk ya saki ta dinga shigewa jikinsa tana fitar da numfashi mai sauti "kwanciya yayi ya d'ora ta samansa, sosai ya rungumeta ya cigaba da shashshafa sassan" "jikinta. Gefan fuskarsa yake goga mata a fuskarsa da wuyanta, lokaci guda ta rikice masa wata irin" "runguma take masa tana kiran sunanshi. da fadin ""Abbah! ka bari dan Allah."" Tana fad'in maganar kuma tana sake ri'ke masa wuya, shi kuwa cigaba yayi da goge mata fuskarsa yana so ya had'a bakinsa da nata yau ma yana so yasha bakinta dan gaskiya jiya shi kadai yasan dadin da ya kwasa." "Koda ya samu nasarar hada bakinsa da nata bata damu ba, sai ma luf da tayi tana ji yana sarrafa bakinta" "yanda ransa yake so, ba taji zafin jiya ba sai dai har yanzu ba taji dadin da akeji ba sai dai ta lura shi yana jin dadi koga yanayin yanda yake sucking din harshen ta da le'bunanta kamar wani matashin saurayi Gabadaya Abbah ya fita daga hayyacinsa, ya cire bakinsa daga nata ya mi'kar mata da" "kafafunta, dogon wandon jikinta yake kokarin cire mata, Ta yunkurin mikewa, ya hanata, takure jikinta tayi tana rawar jiki! ita da kanta taji sauyi a 'kasanta dan pant dinta tana jin danshi ga wani 'kaikayi da gurin ke mata, Tana jinshi ya cire mata dogon wandon yayi saura daga ita sai pant! Kunya ce ta rufeta tabbas data na da k'wanjin hana shi aikata abinda yake mata da ta hana shi, amma inaa! zuciyarta da" gangar jikinta suna bukatar abun. Abbah Abbas hannu yasa a kan pant din ya dan shafa! ta zabura tana makyarkyata! had'e da had'e "cinyoyinta, ya d'an bud'e kafafunta yasa kansa a gurin ya sumbata, ai ji tayi kamar ta kurma ihu!!! Kafin ta dawo hayyacinta taji saukar hannunsa kan brest dinta." "Ai sai ta gigice tana tutture hannunsa, dan gabadaya ji tayi tana nema ta suma! 'Dago ta yayi ta mike" "zaune, cire rigar yake kokarin yi ta dinga ture hannunsa tana kuka! wai shin ya za tayi ne? Shi kuwa bai fasa ba sai da ya cire rigar breziyar ma ya 'balle ta ya jefar lafiyayyan breast din'ta cikkaku masu kyau da kyartawa suka wanke masa ido duk da cewar akwai duhu a dakin bai hanashi ganinsu ba. Hannuwanta" "duk biyun tasa ta rufe breast din tana hawaye da rawar murya take fad'in ""Abbah ka bari bana so dan" Allah ka rabu dani! baka cancanta da wannan al'amarin ba a tare dani.'' Ita take surutanta dan gabadaya shi hankalinsa ma baya tare da jikinsa so yake kawai yaji yana sucking "din Brest din a bakinsa. Yana cire hannunta tana sake mayarwa tana kuka had'e da tureshi," "Ya mayar da ita ya kwantar yayi mata rumfa, kauda kanta take tana jin kunyar abunda ke faruwa shi" kuwa ya dinga jiyo da fuskarta yana bata kyawawan kesses masu inganci! numfashi ta shiga saukewa "tana sake rufe kirjinta da hannunta, hannunsa yasa da karfi ya cire hannunta dake kirjinta, breast din" dake gefan bakinsa shi ya shiga lasa da harshen sa yana kokarin kama nipple d'in! "Ihu! ta kurma! da karfi! yayi gaggawar rufe mata bakinta da hannunsa, lallai Naja'atu bata da hankali" zata tona masa asiri a gida ga yaransa. Jin yana shan breast dinta sai dik wani alkadari nata ya karye "sakin jikinta tayi ta daina rufe kirjin nata, hakan ya bashi damar kama d'aya breast din ya shiga murza nipple din yana sucking din dayan da bakinsa." Wani irin ruwa taji na zuba daga 'kasanta gashi ya dameta da motsi da 'kaikyayi ta dinga motsa cinyoyinta tana sakin nishi Abbah a ranar ya firgita mata tunani da kalolin soyayyarsa masu wahalar "samu, ita dashi duk ta wannan hanyan suka samu satisfaction Sai bayan ya sauka daga bed din ne" "kuka yaci karfinta ta toshe bakinta da hannunta ta dinga yi cikin zuciyarta tana fad'in ""Salim kayi hakuri nima ba laifina bane amma komai rintsi zan kiyaye ba zan bari ya kar'be maka budurcina ba.""" "Tana ganin ya fito ta mike tana kare fuskarta da bedshirt ta nufi toilet tayi wankan tsarki, koda ta fito ma" "kasa kallonsa tayi ta lalubi kayanta tasa can kan kujera ta nufa ta kwanta. Muryarsa 'kasa yace.""Ke" "meye haka zaki koma nan ki kwanta."" shuru tayi masa wasu hawayen na zubo mata." "Sunanta ya kira Tana jinsa ta share, Ya mike yazo ya tsaya kanta! yana cewa taje ta kwanta, rufe" "fuskarta tayi da hijab dinta ta kud'indine jikinta tana fad'in ""Dan Allah ka kyaleni Abba tunda dai bukatarka ta biya shikkenan ni ka rabu dani na kwanta anan yafi min .""" "Bai saurareta ba ya dauke ta cak ya nufi bed din da ita, hijab din ya cire mata, ya dora ta samansa yana" "shafa bayanta a hankali a hankali, ita kuma sai ajiyar zuciya take saukewa, tana lumshe idonta, cigaba yayi da shafa gashinta da sassan jikinta yana dan kiss din gefan fuskarta da wuyanta, a haka bacci ya dauketa, ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya rufe musu jiki da bargo sannan ya shiga karanto adduar" kwanciya bacci.. *ASUBAH TA GARI AMARYA DA ANGO* *Littafin na kudi ne! Idan kingan shi a gruops to na sata ne idan kina bukatar ki biya ki karanta to ga yanda abin yake* Vip #600 Normal#300 accont: 0542382124..Binta Umar Gtbank...Idan katin waya zaki turo kiyi min magana ta whasap da wannan numbar...07084653262 *BINTA UMAR ABBALE* Mdd *23* "Yana tafiya masjid itama ta fito daga dakin, a dakin su Saddiqa tayi sallah sannan suma ta tashe su sukayi" "sallahr, Yauma kamar jiya tare suka shiga kicin da Saddiqa suka shiga shirya abinda za'a karya dashi a gidan, Halisa ta fito daga dakinta cikin hijabi kai tsaye dakin maigidan ta nufa ba tare da tayi tunanin komai ba ta tura kofar dakin ta shiga fuskarta babu walwala, jiya da mugun bakin ciki ta kwana dan har sai da ta zubar da hawaye sakamakon abinda kunnanta yaji ye mata a daran jiyan, koda yake ai itace ta jawowa kanta damuwa, dama hausawa nacewa kazantar da baka gani ba tsafta ce haka kawai sabida tsabar gulma tazo tana musu la'be aikuwa duk ihun! da Naja'atun da dinga yi a kunnanta kusur-kusur d'in da suka dinga yi shine yayi masifar tashin hankalinta, tasan halin mijinta da jaraba baya d'aga kafa a wannan gurin gani take ma ai tuntuni ya gama sanin yarinyar, takaicin haka yasa ta kwana da ciwon kai" mai tsanani! "Tana shiga dakin ta ganshi yana cire bed shirt din dake shimfide a kan gadon, karaf idanunta ya sauka" kan milk din breziyar Naja'atu wacce ta manta garin sauri bata dauka ba. Wata irin 'kayar kishi tazo ta tokare mata a makoshi! "Da kayar ta zauna kan Sofa tana gaisheshi, ya amsa fuskarsa a sake ya d'ora da fad'in ""Yau ban shigo na" "tashe ki ba na makara ne shiyasa dana fito kai tsaye na wuce masjid ina fatan kin tashi lafiya.""?" "Halisa aka wani marairace fuska tace"" Gaskiya ban tashi lafiya ba dan kwana nayi kaina yana ciwo yanzu" "ma abinda na shigo na fada maka kenan."" Yace.""To yanzu ya kike so ayi kina so nace ki shirya kije asibiti ko? wai shin me yasa ke bakya gajiya da yawo.""?" "Tace""Haba Alhaji kawai saboda jin dadi sai na 'kir'kirarwa kaina cuta wallahi da gaske nake bani da" "lafiya."" Murmushi yayi yace.""Halisa kenan to Allah ya baki lafiya idan kuma rashin lafiyar ta alheri ce ni dama haka nake so.""" "Ta'be bakinta tayi tace""Wacece ni? ai na barwa matar so tazo ta haihu wacce Allah ya bani ma Allah" "yasa mata albarka."" 'Bata rai yayi yace.""Wai ke meya sa kullum kike abu irin na yara! wannan ai shashanci ne ! yanzu idan Allah ya baki haihuwar sai kice bakya so.""" "Cikin kissa da karyar da kai tace""Wallahi inaso sosai kuwa ai gani nayi kana ta wani zumudi da rawar jiki" "akan yarinyar nan duba fa kaine kake gyara makwancin da kuka kwanta ita meye amfaninta dama ai tuntuni bata laifi a gurinka."" Cike da kishi ta fadi maganar." "Ya 'bata fuska sosai yana kallonta yace.""Kada ki sakeyi min magana makamanciyar wannan, dake da ita" "duk d'aya kuke a gurina, Naja'atu yarinyar ce akwai abubuwan da za tayi a yanzu wanda dole ayi mata uziri kafin tayi hankali ke kuma kin fita hankali tunda kin fita shekaru abinda zakiyi daban da wanda za tayi, kuma kina maganar ina gyara gado, ke sau nawa kina kwana a dakin ki fita ki barshi haka ni zan cire" "zanin gado nasa wani, dan haka idan zakiyi magana ki dinga sara kina duban bakin gatari" Halisa ta dinga kallonsa tana kokarin danne hasalarta! kawai taga ya sunkuya ya dauke breziyar Naja'atu dake 'kasa ya ajiye a gefen bed din ya nufi toleit abunsa. Mikewa tayi a fusace! ta fita daga dakin tana wani irin huci!!! Kicin ta nufa dan anan ta jiyo motsinsu. "Suna tsaka da aiki ta daka musu tsawa! Saddiqa ta juyo a firgice tana rawar baki ta fara gaisheta, ita" kuwa Naja'atu ko gezau ba tayi ba ta dai tsaya da aikin da takeyi tana kallonta sai wani hayaniya take tana fuffuka! """Malama fito min daga kicin babu abinda kuka iya sai shashanci duba dan Allah duk kun cikawa mutane" "gida da k'auri!! soya doya kawai kamar kina soya kan uwarki.""!! Naja'atu ta kalleta da sauri tana mamakin zagin da tayi, to wa take zagi a cikinsu ita ko Saddiqa ai ko Saddiqa ta zaga ba zata bari ba sai ta rama." "A nutse tace"" Ni mutum idan ya zage ni wallahi ba zai min ciwo ba saboda nasan bani yake zagi ba kansa" yake zagi kuma dai dan Allah mutum idan ya girma yasan ya girma mtssww!!! ta karasa maganar tana jan dogon tsaki! "Halisa ta fusata sosai tace""To mara kunya mara mutunci ai dama kin saba yi min rashin kunya ohoo!" "yanzu dai kin ramawa Saddiqa zagin da nayi mata kenan."" Ta'be bakinta tayi tace""Eh tunda abinda kika fahimta kenan hakane."" Hanyar fita ta nuna mata da fad'in ""Zoki fice min daga kicin 'Yar iska mara" "mutunci masu mugun hali.""" """Wallahi kece mara mutunci kuma ni ba 'yar iska bace dan iska yasan kansa, mugun hali kuma kanki kike" "gorantawa tinda duk cikin danginmu ba'a ta'ba haifa mana d'an shege ba.""" Jin tana nema ta 'ballo mata ruwa yasa ta shiga kicin din tana d'ura mata ashar! tana ingizata wai sai ta "fita, Naja'atu 'yar taurin kai tace"" Wallahi ba zata fita sai ta gama abinda take." Saddiqa ganin abin na neman ca'bewa sai ta fita daga kicin din tana share hawaye kai tsaye dakin "Abbansu ta nufa tana kuka. ""Dan abu takazan ki a gidan ubanki muka goya d'an shege kinji yarinya" "da sharri."" Halisa tafada tana kokarin doke mata baki, ita kuwa fizgewa tayi ta matsa gefe tana gyara wuyan rigarta tace""Haba anti Halisa komai 'boye-'boyen ku mun sani Wannan Shamsiyyar sai da tayi cikin shege kafin ayi mata aure yanzu haka d'an data haifa yana gidanku gurin mahaif Kafin ta 'karasa" "halisa ta kaiwa bakinta duka! ta kauce da sauri tana fad'in ""Allah ya isa wallahi.""! Karaf! a kunnansa lokacin da yake kokarin shigowa kicin din shida saddiqa, Halisa na ganinsa ta fashe da kuka tace"" Yanzu Naja'atu ni kikewa Allah ya isa me nayi miki kawai daga na shigo kicin inayi muku sannu da aiki ashe zaki iya zagin Halimatu.""? Abbah Abbas ya dinga kallonta da 'bacin rai a tare dashi yace.""Rashin kunyar taki" "ashe har ta kai haka? Yanzu baki duba girmanta ba kike zaginta wato kin manta maganar mu dake ko.""" "Kuka tasa tace""Wallahi ba haka bane dik abinda ta fad'a 'karya takeyi ai ga Saddiqa nan a gabanta akayi" "komai kuma ka tambaye ta kaji, haka kawai muna aikinmu ta shigo tana zagin mu wai bamu iya komai ba" "mu fita mu bar mata kicin dinta, shine nace ta bari mu 'karasa ta'ki bari tazo tana dukana."" Itama ta 'karashe maganar tana kuka had'e da ri'ke bakinta." "Abbah Abbas dik sai ya rasa ma maganar wa zai dauka, Halisa ta goge hawaye kamar gaske tace""Tunda" "fitina da sharri zaki dinga yi min a gida to zaki bar min gidana dama ni kikazo kika samu a gidan, dan bazan zauna dake ba watarana kisa hannu ki dake ni da girma da komai ni ba'sa'ar ki bace ballanta na nayi kishi dake, Halimatu ce dai-dai dani, dan haka ni a matsayin kanwa na dauke ki ba kishiyasa ba to" "tunda abin ya zama haka zaki bar min gida ki tafi naki ko kuma ni na bar miki gidan.""" Tana gama maganarta ta fita daga kicin din tana goge fuskarta "Halisa na fita ya juyo kanta tana rab'e jikin bango (garu) tana matse fuskarta, fad'a ya shiga yi mata" "wanda yake nuna mata cewar ya yarda da duk maganganun da Halisa ta fad'a tunda gashi da kunnansa yaji lokacin da take yi mata Allah ya isa! Sunkuyar da kanta 'kasa tayi tana hawaye tana jinsa sai fad'a yake mata wai lallai idan tana son zama dashi to ta zauna lafiya da kowa a gidansa, taji kamar tace masa ai dama ba sonsa take ba da zaiyi wannan maganar ko yanzu akan 'kaya take ya saketa ai babu dole, kwarjinsa ya hanata cewa komai kawai sai ta fita daga kicin din da gudu ta nufi dakin su Saddiqa tana kuka! Ya bita da kallo mamaki wato yana mata fada ta mai dashi soko ta barshi a tsaye, girgiza kansa yayi ya nufi palon Ita kuwa Halisa taga lokacin da Naja'atun ta shigo palon tana kuka, sai farin ciki ya" "cika mata zuciya dama tasan da wuya ya'ki daukar maganar da tayi, Gani yayi duk yaran sun shirya cikin uniform ya kalli Saddiqa yace."" Yi sauri ki fito muku da bresk fast di n kafin Salim din yazo."" Saddiqa da" Mufida suka nufi kicin din da sauri sune suka shirya gurin cin abincin tsaf! yaje ya zauna gurin cin abincin "tare da yaransa, Saddiqa ta had'a masa tea ta zuba masa doya wacce zata isheshi, Albarka yasa mata ya" "dauki cup din tea yana sha, yana neman numbar Salim a wayarsa." "Salim na draving yaja tsaki kafin ya dauki wayar, Yace""Afuwa Kawu ganinan kan hanya."" Yace.""Okey kayi" "sauri kada kasa su makara ko."" Yace.""Insha Allah nan da mintina biyar zan karaso dan na shigo unguwar."" ""Okey."" Yace ya kashe wayarsa ya maida hankalinsa gurun abincin dake gabansa..." Halisa ce ta fito daga daki tana wani salo-salo idanunta sunyi jawur! zama tayi kusa da kujerar Saddiqa ta "dafa kanta cikin kissa tace""Sannu da aiki Saddiqa ."" A dan tsorace ta amsa da ""Yawwa Mommy."" Kallonta yayi yace.""Zamu fita tare yanzu za muje hospital mafi kusa a dubaki dan bana son zama da lalura."" Ta sake marairaicewa da fadin ""Wallahi ba kaji yanda nake jin jiki ba gashi yarinyar nan ta 'kara mun wani" "'bacin ran.""" "Yace.""Ai laifin ki ne tunda kin san halinta me yasa zaki biye mata kuyi ta cacar baki a gaban yara duk" "ranar data zage ki a gaban yaran nan mutunci ki ya zube wallahi gwara ki kama kanki.""" "Da sauri tace""Dan Allah ka bar wannan maganar da kake kamar baka san halinta ba kafin na fad'i d'aya" "ta fad'a min goma ni wallahi ban shiga kicin din da wata manufa kawai dai ta raina ni ne shiyasa bata ganin girmana amma yanzu na yanke hukunci kawai ta bar min gidana shi yafi amfani idan kuma lallai a gidan nan zata zauna to a gyara mata d'aya side din taje can ta 'karata.""" "Yace.""Sai an kwana biyu tukkuna abinda dai nake so dake anan shine ki cigaba da hakuri kuma kina" "kokarin ri'ke girmanki idan kin kama mutuncinki na tabbata komai rashin kunyarta ba zata zage ki ba. Halisa shuru tayi tana jijjiga 'kafafunta, Saddiqa ce ta had'a mata tea ta zuba mata soyayya doya da" "wainar 'kawai akai tace ""Mommy gashi kiyi break ."" Cikin ya'ke tace""Nagode Saddiqa Allah yayi muku" "albarka."" Duka suka amsa da amin harda shi," "Salim ne yayi sallama ya shigo hannunsa rike da key na mota, Yaran ne duk suka mike suna gyara zaman" "jakar makarantarsu, Salim ya shiga rarraba ido a palon Naja'atu kawai yake so yayi tozali da ita, da bai ganta ba sai ya nufi dannig area d'in yana wani shafa kansa kai daka ganinsa kaga munafiki Hannu ya" "mikawa Abba Abbas suka gaisawa yana wani risinawa kamar mutumin kirki! Ya gaishe da Halisa, tana" washe baki ta amsa tana tambayarsa Yaya Ramlatu. "Abba Abbas ya mike hade da daukar wayoyinsa dake kan teble din, ya kalli Salim da fad'in ""Ka kai yara" "skullu daga bisani sai ka biyo ni kasuwar daga baya zamuje hospital da Halisa bata jin dadi."" Salim yace.""Ayya Sannu Big Aunty ashe ba kiji dadi ba Allah ya sawwak'e yasa kaffara ne."" Halisa ta mi'ke tana" "dan ya mutsa fuska tace""Wallahi kuwa "" ameen ya rabbi idan ka koma gida ka gaishe min da Yaya."" Ya" "amsa da za taji insha Allahu.........Gabadaya suka fita harabar gidan yaran suka nufi motarsu ta makaranta, shi kuma Salim din ya dan tsaya suna magana da Abba Abbas din kafin yaje ya shiga motar da sauri yaja motar ya fita daga gidan, Halisa ta kame a gidan gaba tana jira ya shigo kawai sai taga ya juya da nufin komawa cikin gidan, cike da mamaki take kallonsa, to me zai komar dashi kuma! 'kwafa tayi ranta ya 'baci babu shakka gurin yarinyar zaije, mtsssw! an girma kamar ba a girma ba a dinga abu irin na yara abinda ta fada kenan a fili tana jan tsaki!. Ganinshi zai dawo cikin gidan yasa tayi saurin" "sakin labulan window din data la'be tana le'kensu, da sauri ta nufi toilet ta kulle kofa. Kai tsaye daya" "shigo d'akinsu Saddiqa ya nufa saboda yasan tana ciki Koda bai ganta a dakin ba, sai yayi tunanin tana" "toilet, ya karasa bakin toilet din yana k'wank'wasawa! da kiran sunanta, tana jinsa tayi masa shuru mugun haushinsa take ji shiyasa ma bata so ta kalli fuskarsa, Abbah Abbas haka ya 'karaci buga kofar toilet din ya hakura, dan ya kai minti goma sha biyar yana tsaye yana aikin buga kofa da kiran sunanta bata saurareshi ba, ransa a 'bace ya fita daga dakin Halisa kuwa cika tayi tai fam! ta dinga hura hanci" "takaici da bakin ciki kamar su kasheta, haka ita dashi sukayi tafiyar kowa ransa a 'bace!" *Littafin na kudi ne! Koda zaki ganshi a gruops to na sata ne idan kina so ki biya kudin littafin to ga yanda abin yake. * VIP #600 Normal #300 Accont:0542382124...Binta Umar gtbank..Idan katin waya zaki tura kiyi min magana ta whasap da wannan numbar 07084653262 *BINTA UMAR ABBALE* BHRBN *24* "Tana jin fitarsa daga dakin ta fito daga toilet din, zama tayi k'asan kafet ta had'a kai da gwiwa abin" "duniya duk ya isheta, ta kai minti ashirin a zaune tana sa'kawa da kwancewa kafin ta yanke shawarar mi'kewa ta dauki hijabinta tasa, hanyar fita ta nufa, Gidan Abbah Magaji za taje dan ba za tayi zaman kad'aici ba gabadaya gidan girma yayi mata ta dinga jin tsoro na shigarta. Koda maigadi yaga zata fita" baice mata komai ba dan shine ma ya bude mata karamar kofa ta fita yana yi mata adawo lafiya. Tana "kokarin shiga gidan Abbah Magaji Salim ya shigo da mota, tsayawa tayi har yayi parking ya le'ko da kansa yana d'aga mata hannu wai taje, dama sabida ita ya dawo gidan bayan ya ajiye yara a skull, cikin zumudi gami da farin cikin ganinsa ta nufi inda motar take, Ya bude mata ta shiga ta zauna kusa dashi" "tana fara'a da fadin ""Wallahi naji dadin ganinka.""" "Ya saki wani murmushi yana shafa sumarsa hade da yi mata shegen kallonsa yace.""Na shigo gidan tun" "dazu ina ta rarraba ido banga sanyin idaniya taba, shiyasa na kasa wucewa kasuwa kamar yanda mijinki ya bukata nace sai na dawo nayi tozali dake."" Tana murmushi tace""Ina dakin su Saddiqa ban san kazo gidan ba.""" "Yace.""Ina fatan dai wani abu bai shiga tsakaninki da wannan dattijon ba."" Gabanta ne ya fadi ta kalleshi a" "sanyaye tace""Babu wani abu da ya shiga tsakaninmu ai nayi maka al'kawarin kai zan mallakawa kaina."" munafikin murmushi yayi yace.""Nagode Princess yanzu inaso ki d'an yi min abinda zai d'ebi min kewarki idan naje kasuwa."" Tace""Ban gane abinda kake nufi ba."" Kallon kasan ido yayi mata yace.""Haba baby sai nayi miki bayani dalla-dallah ashe har kin manta hirarmu ta jiya da irin amsar da kika bani, yanzu fa kika gama cewa jikin ki da komai naki nawa ne to inaso ki d'an fara gwada min soyayyar da kikeyi min a zahiri."" Cike da mamaki take kallonsa dan ta fahimci inda maganar sa ta dosa, shuru tayi ta kasa magana, kawai taji ya kama hannunta ya rike yana shafawa, Da sauri ta cire tana d'an hararasa tace""Idan sai na rungume ka ko nayi maka kiss sannan zaka gane kaunar da nake maka gaskiya ce, to kuwa sai dai kada ka yarda dani da son da nake maka koda nake cewa komai nawa naka ne ai ba ina nufin mu aikata haramci ba inaso bayan na rabu da wannan 'kaddararran auran muyi aure da kai mu mori junanmu shine abinda nake nufi."" 'Bata fuska yayi yace.""Dan kiyi kissing d'ina ko kin rungume ni ai ba wani abu bane amma tunda kince haka shikkenan."" Cikin rashin walwala ya 'karasa maganar, Tace''Gaskiya kayi hakuri ba zan iya ba."" Cikin fusata yace.""Okey fita a motar nan na tafi inda zani dama duk karya ce ba wani sona" "kike ba da kina sona ba zaki tsaya jayayya dani ba.""" "Ganin ya fusata! yasa jikinta yayi sanyi murya na rawa tace""Dan Allah kayi hakuri ka gane abinda nake" "nufi bana so ranka ya 'baci.""! Yaja tsaki mai tsayi da fad'in ""Bacin rai kuma wane iri ai raina ya gama 'baci dake.""" "Tace.""To kayi hakuri my love kada kayi fushi dani zuciyata zata shiga wani yanayi mutukar kana fushi da" "ita.""" "Ta'be bakinsa yayi yace!.""Ai kin bani mamaki wallahi amma babu komai ina ganin zan hakura dake na" "fara duba 'yan matan da suke sona sai na fitar da gwanata a cikinsu."" Jin ya fad'i haka sai hankalinta ya" "tashi murya na rawa tace""Dan Allah kada kayi min haka my Prince. "" Fuskarsa ya mi'ka mata da fadin"" Okey oya kiss me idan kina sona.""" Ta dinga dawurwura kafin ta kai bakinta fuskarsa ta manna masa kissi da sauri ta cire bakinta tana jin "nauyi da kunyar abinda tayi, murmushi yayi yana shafa gurin da tayi masa kiss din ya kalleta yana wani lumshe idonsa yace.""Allah ya nuna min ranar da zan had'a bakina da naki ina mutukar so naji ina tsotsar wannan lips din naki masu kyau da daukar hankali."" Yana kokarin kai hannusa kan le'bunanta yake maganar, ba ta bari ya kai hannunsa fuskarta ba ta bude motar da sauri ta fita daga ciki gabanta sai faduwa yake Salim ya kalleta cike da mamaki! kamar xaiyi magana kuma sai yayi murmushi yana" "girgiza kansa ya kunna motar had'e da daga mata hannu da fadin ""Zan kira ki a waya idan anjima akwai" "labarai masu dadi ina so ki tanadi amsar da zaki bani.""" "Hannunta ta d'aga masa tana ya'ke tace""To shikkenan sai na jika."" Motar yaja ya bar gurin ita kuma da" sauri ta nufi gidan Abba Magaji tana waiwayen bayanta kamar wata mara gaskiya. Salim yana "draving yana duba wayarsa yana sakin wani shegen murmushi ashe lokacin da take kiss d'insa ya saita camera......Hoton ya fita sosai kamar dama da son ranta hakan ya kasance fuskarsa da murmushi itama tata fuskarsa a sake duk wanda yaga hoton zai fahimci cewar masoya ne, ba tare da 'bata lokaci ba ya d'ora hoton a fuskar wayarsa domin yana so Allah ya nunawa Kawun nasa hoton ya gani yasan dole" ransa zai 'baci ! idan ya tambaye shi shi kuma yana da amsar da zai bashi. "Aunty Maryam na zaune a palo ita kadai yaran duk sun tafi makaranta kawai taji sallamar Naja'atun," "cike da mamaki take kallonta har ta 'karaso inda take ta zauna kujerar kusa da ita tana gaisheta, Aunty Maryam ta amsa mata cike da kulawa tace""Naja'atu me ya fito dake ina fatan dai lafiya.""" "Murya na rawa tace""Lafiya lau Anty gidan ne shuru su Saddiqa sun tafi skull Anty Halisa da Abba sun fita" "a tare ni kuma tsoron gidan nake.""" "Anty Maryam tace""Ayya ai sai a hankali zaki saba ina fatan maigidan ya san zaki zo nan.""" Shuru tayi tana wasa da hannunta. "Anty Maryam tace""Be sani ba kenan naga kinyi shuru.""" "Tace""Ai na dauka babu wani abu dan nazo tunda koda can muna zuwa da Yaya Halimatu."" Anty Maryam" "tace''Eh duk da haka dai yana da kyau ya san zaki zo itama marigayi ya kafin ta fita zuwa wani guri ai tana fad'a masa ko baki san yanzu haka mala'iku na tsine miki ba.""" "A sanyaye tace""Na sani anty."" Tace""To amma kin sani kika take.""! Shuru tayi dan bata da abinda zata ce," "Anty Maryam tace""Yanzu ki kira wayarsa ki fada masa gaki anan gidan nasan ba zaiyi fad'a ba."" zum'bura baki tayi gaskiya ba tajin zata iya kiran wayarsa dan ba 'karamin haushinsa take ji ba." "Anty Maryam tace""Dake nake magana fa kodai har yanzu baki saduda kin kar'bi auran ba."" Fashewa tayi" "da kuka tace""Dan Allah anty ki kyaleni ni bazan kira wayarsa ba saboda bashi da adalci.'' Cike da mamaki antyn take kallonta tace""To ikon Allah wane iri rashin adalci yayi miki kuma.""?" "Hawaye ta goge tace""Anty duk da bana sonsa da auransa ya dace ya bawa Anty Halisa ta had'a min lefe" baki ga banzayen kayan data siyo min ba kuma wallahi nasan tana sane tayi haka dan ta bani haushi! sannan kuma d'azu tazo tana zagina harda dukana a baki a maimakon ya tambayi ba'asi kawai sai ya "dauki laifi ya d'ora mun.""" "Anty Maryam tayi shuru tana nazarin maganar, tabbas komai akace Halisa ta aikata ba zata musa ba" "saboda dama tasan halinta, Halimatu tasha wahala a hannunta, dalili kenan da ya sanya basa shiri da juna da ita gasu dai ma'kota kuma mazajensu abokan juna ne amma kowa sabgarsa yake a tsakaninsu babu jituwa ko ta kwabo Cikin rarrashi tace""Kiyi hakuri da Halisa nasan dai kin san hakurin da" "Marigayiya tayi da ita to kema inaso ki kwatanta ko kifi nat. ""Gaskiya anty ba zan iya ba wallahi.'' Ta" katse tun kafin ta 'karasa maganar. "Anty Maryam tace""Ke me yasa bakya tsawa a baki shawara ne? Halisa bata da kirki macace muguwa mai" "shegen kissar tsiya babbar macace ma ya ta iya da Halisa ballanta na ke! ki tsaya ki saurare ni da kyau! yanzu fushi ke ba naki bane! kamata yayi lokacin da yake fadan sai ki bashi hakuri ki fad'a masa yanda abun yake ba kiyi zuciya ba, kinga yanzu ita bukatarta ta biya ta had'aku fad'a sun ma fita unguwa tare dashi babu abinda ya dameta, to gobe ma haka zata sake miki ke kuma gaki mara wayo sai kiyi fushi ki" "tsaya girman kai ke ba zaki bada hakuri ba to ba haka ake zamantakewa ba.""" "Tana kuka tace""Anty nayi yunkurin fad'a masa abinda ya faru ya'ki saurarata shiyasa nima na bashi guri.""" "Anty Maryam tace""Yanzu dai magana ta wuce kodan gaba kada ki sake aikata hakan idan wani abun ya shiga tsakaninki da Halisa yazo yana miki fada ki bari ya gama tukkuna sai ki fada masa abinda ya faru" "kada ki sake bar masa gurin bai dace ba.""" "Cike da mamaki take kallonta tace""Anty sai na zauna kawai ya dinga yi mun fada alhalin ba laifina bane.""" "Anty Maryam tace""To meye yau da gobe da kansa zai gane gaskiya dan me yasa Halimatu ta ciri tuta a gurinsa nasan har ya mutu ba zai mance da ita ba saboda tayi masa ladabi da biyayya.""" Girgixa kanta ta shigayi gaskiya da kamar wuya wai gurguwa da auran nesa Halimatu daban Naja'atu daban kowa da Halinsa. murya na rawa "Tace""Anty Maryam wallahi Allah shine d'aya har yanxu bana jin son mutumin nan a cikin zuciyata to ya" "za'ayi na iya zaman gidansa."" Anty Maryam tace""A hankali zaki ji sonsa na shiga zuciyarki ballantana Alhaji Abbas yayi duk macan da zata ganshi zata so ya zama mallakinta ke na fahimci tsufansa ne bakya so kuma ke kike abunki 'yan mata nawa ne suke neman irinshi su aura 'yan matan da suka fiki kyau da" "komai ma gasu nan suna yawo a gari amma ke kin samu kina wasa da damarki.""" Shuru tayi tana nazarin maganar anty maryam din itafa sam ba taga wani abun rubibi a gurin dattijo irin "wannnan ba, kawai mace idan tana so ta more rayuwarta to ta auri dai-dai da ita amma auran tsoho a" "ganinta duk tauyewa rayuwa hakkine. Anty Maryam tace ""Ki kirashi a waya ki fada masa bana so ya" samu labarin kina zuwa gidan nan yayi miki fada kinga nima zaiga laifina da nake barin ki kina zama. "Wayar ta dauka ta nemo numbar tashi, dan dai kawai anty maryam din ta dage ne amma da wallahi ba" zata fada masa ba. Wayar tashi na hannu Salim dan haka da yaga kiran Naja'atun sai ya katse! "ya'ki kai masa, Naja'atu ta sake kiran wayar a karo na biyu Salim ya'ki dagawa wayar tayi ta ringing har ta" "katse!! Ta kalli anty Maryam din tace"" Ya'ki dagawa."" Anty Maryam tace""Watakila yana tare da mutane anjima sai ki sake kiransa.""" Dan ta'be bakinta tayi ta shiga whasap tana dubawa. Anty Maryam mikewa tayi ta nufi kicin tana "mamakin 'kuruciyar yarinyar yanzu meye abin gudu a dangane da auran ta da Abokin mijin nata, babu shakka kuruciya ce ke damunta kuma idan Halisa ta gane akwai rashin jituwa a tsakaninsu to ita kuma tabbas ta samu hanyar da zata cigaba da shiga tsakaninsu." "Sai bayan sun fito daga sallahar azahur ne ya samu sararin 'kar'bar wayoyinsa dake hannun Salim, ya" "zauna gurin zamanshi yana duba wayar, a lokacin yaga miss call din Naja'atun, da sauri ya shiga kiran wayar yana fatan Allah yasa lafiya dan baiyi tsammanin kiran wayarta ba, Lokacin da yake kiran wayar ita kuma tana bedroom din anti maryam tana sallah, Anti Maryam ta daga wayar a nutse tayi masa sallama. Jin muryar anty maryam yasa shi mamaki yace.""Maryam ce ko.""? Tace""Eh wallahi nice ai" muna tare da Naja'atu tun safe ta shigo tace kunje unguwa yara kuma sun tafi skull wai tana jin tsoron "zaman gidan shine nace ta kira wayarka ta fada maka to kuma ta kira baka samu dagawa ba.""" "Ajiyar zuciya ya sauke yana hamdala a zuciyarsa yace.""Wayar bata hannuna a lokacin okey babu" damuwa bayan sallahr la'asar sai kisa ta ta koma gida tunda ina tsammanin ma yanzu Halisa ta dawo dan dama asibiti na ajiyeta na wuce kasuwa. amma tunda tana son zama dake idan anyi la'asar kisa ta ta koma gida. "Anty maryam tace""To insha Allah."" Sallama sukayi anty maryam ta juyo tana kallonta tace''Kinji ashe" "lokacin da kika kira wayar bata hannunsa, yace babu komai idan kinyi sallah la'asar sai ki koma gidan.""" "zama tayi kusa da ita ba tare da tace komai ba, anty Maryam ta mike tare da fadin ""Bari na kawo mana" "abinci muci akwai wasu abubuwa da zan baki idan kika mayar da hankali zasu taimake ki."" kicin ta nufa, Naja'atu ta bita da kallo tana tunanin wane abubuwa ne zasu taimaketa." Halisa kuwa bayan ta gama ganin likita gidansu ta wuce kuma sai da ya gargade ta kan lallai data gama da asibiti ta koma gida amma saboda ita mai kunnan 'kashi ce ta tafi gidansu......Sai da tayi sallahar la'asar sannan tayi sallama da mahaifiyarta Anty maryam ta fito daga bedroom dinta hannunta rike da bakar leda guda biyu ta zauna kusa da "Naja'atun tana bud'ewa ta kalleta a nutse tace"" Wannan garin magani ne na mata mai kyau nice ma na had'a abina da kaina idan kin koma gida ki d'ebi cokali biyu kisa madara da ruwa kisha haka zaki dinga yi kullam, maganin zai taimaka miki Wannan kuma gumba ce itama kisa mata madara ki dama sai kisha," "duk da cewar ke amarya ce amma hausawa nacewa idan kana da kyau ka 'kara da wanka, idan kinga" amfanin maganin nasan zaki sake nemansu a gurina. "'Karba tayi ba dan za tayi amfani dasu ba, ta mike tana gyara hijab dinta, tace""Nagode anty sai anjima.""" "Anty maryam ta mike tana sake jaddada mata yanda za tayi amdani da maganin, har bakin gate ta rakata sannan ta koma cikin gidanta." "Tana fitowa daga gidan ta watsa maganin dake hannunta a kwata, babu abinda zai sa tayi shaye-shayen" maganin mata alhalin ba son auran take ba.......... Halisa ta rigata shigowa gidan koda ta duba gidan taga ba tanan jiki na rawa ta nemi wayar maigidan "tana fad'a masa wai Naja'atu bata gidan tun safe! Kai tsaye yace mata ya san bata gidan ta kwantar da hankalinta."" Jikinta ne kuma yayi sanyi jin abinda yace. Naja'atu ta shigo ta sameta zaune a kujerar" "palo, kallon juna sukayi babu wanda yayi wa dan uwansa magana a cikinsu, Naja'atu kai tsaye dakinsu Saddiqa ta wuce cike da damuwa gami da jin tsanar masu gidan a cikin zuciyarta. Halisa tsaki taja" mai karfi cikin takaici da tsanar yarinyar ta nufi dakinta haka suka zauna babu wacce tayi tunanin d'ora "girkin dare a cikinsu.....Karfe shida shaura yaran gidan suka dawo daga skul, Abbah Abbas kuma sai daf" "da magariba ya dawo ya shigo ya tarar da palon babu kowa, yaran suna cikin dakinsu tare da Naja'atu ita kuwa Halisa saboda tasan sharrin data shirya tana d'akinta a kwance a kan bed wai ita mara lafiya...." *Littafin na kudi ne. !* "Koda zaki ganshi a groups to na sata ne, idan kina so ki biya kudin karatu to ga yanda abun yake." VIP Group #600 Normal #300 Accont:0542382124....Binta Umar gtbank. Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar. 07084653262 *BINTA UMAR ABBALE* Mdd *25* Ganin har an fara kiran sallahr magariba ne yasa bai saurari kowa a gidan ba ya nufi dakinsa ya daura "alwala ya nufi masjid din dake daura da gidansa, bai shigo gidan ba sai bayan sallahr isha'i, har yanzu babu kowa a palon, idanunsa ne ya sauka gurin cin abinci yaga kan daning din wayam! babu komai mamaki ya kama shi,girgiza kansa yayi ya nufi dakin Halisa sai kawai ya tarar da ita a kwance a bed ta" rufe jikinta sai makyarkyata takeyi. "A kanta ya tsaya yana kiran sunanta, ta dan bude ido tana kallonsa a sanyaye tace""Sannu da zuwa."" ya" "amsa yana dan nazarinta kafin yace.""Wai jikin ne har yanzu.""? Tace""Eh wallahi ai kana saukeni a asibiti zazzabi mai zafi ya rufe ni da kyar ma na dawo gida."" Yace.""Ina fatan likita ya dubaki sosai ina result din.""? Tace.""Bani da ciki kawai dai zazzabi da ciwon kai mai zafi ya kamani ya dai d'ora ni akan magani gasu can kan drowar dan ban fito daga asibitin ba sai da na tsaya na siya."" Yace.""Allah ya sawwa'ke sai ki mayar" "da hankali gurin shan maganin."" Tace.""Yanzu ma so nake nayi sallah naci abinci sai nasha maganin.""" "Yace.""Bana tsammanin akwai abinci dafaffe a gidan nan dole sai na sake fita yanzu." "A sanyaye tace ""Kafin na kwanta sai da na had'a Naja'atu da Allah kan ta shiga kicin din ta d'ora abinci ko" "dan saboda yara wallahi kallo ban isheta ba, karshe ma tsaki taja ta barni a gurin Ranshi ya 'baci sosai!" "babu shakka duk abinda akace ta aikata ba zaiyi musu ba, gidansa da abinci amma saboda tsabar rashin mutunci tana so ta tona masa asiri da girmansa da komai ya dinga yawon restaurant. Halisa na ganin" ya juya zai fita da rai a 'bace sai ta saki murmushi tana adduar Allah yasa yayiwa yarinyar hukunci mai tsauri! "Lokacin da ya shiga dakin yaran tana sallah, Yaransa suka shiga yi masa sannu da zuwa ya amsa babu" "cikakkiyar walwala a tare dashi, yace suje palo yanzu zai fito zasuje unguwa tare, da sauri suka fita suna murna." "Tsaye yayi bakin kofar dakin yana jiran ta idar, ita kuma tun kafin ta idar da sallahr gabanta ke faduwa, ta" "lura da masifa ya shigo dakin, a sanyaye tayi sallama ta kalleshi baki na rawa tace"" Abbah sannu d Hannu ya daga mata a fusace! yace.""Me ya hanaki girki a gidan nan.""?" "Shuru tayi tana tunanin amsar da zata bashi, gaskiya ba zata ce ga abinda ya hanata girki ba kawai dai ta" "shagala tare dasu Saddiqa kuma ta dauka Halisa za tayi, Ganin tayi shuru yasa ya rufe ta da fad'a Yace."" Kin san Halisa na kwance babu lafiya me yasa ba zaki shiga kicin ke kiyi aiki ba, kuma ta fad'a min cewar tace kiyi abinci kin ja mata tsaki kin bar gurin, a gidana da abinci da komai amma saboda kina so ki tozartani ki sauke min tukunya kisa ni yawon gidan siyar da abinci To wallahi duk ranar da haka ta sake" "faruwa sai na 'bata miki rai tunda ke kin zama mara jin magana to zamu sa 'kafar wando d'aya dake. Kuka take ta ma kasa cewa komai, lallai a yaushe sukayi haka da Halisa? babu shakka maganar" "aunty maryam ta fito Halisa shaid'aniya ce, ita wallahi data san ba za tayi girkin ba da ita sai tayi, kuma da yake wannan maganar ai tunda tazo gidan itace take girki amma sabida yaje anyi masa famfo yazo yanayi mata fad'a yama 'ki tsayawa ya saurari ta bakinta, yana fita daga dakin ta zame ta kwanta kan daddumar tana cigaba da tsiyayar da hawayen bakin ciki Wannan auran dashi gwara babu a gurinta" ya zame mata ala'ka'kai da masifa. "Mussadiq kawai ya d'auka a cikin yaran nasa sukaje sukayi take away, ranshi duk a 'bace! ya tsani da" girmansa da komai a ganshi yana yawon gidan abinci a ganinsa hakan kamar zubewar mutumci ne.......Koda Mussadiq ya kai mata nata koro shi tayi tace ya fita da ledar bata so Yaron ya fito da ledar take away din a hannunsa yana satar kallon Abban nasu dake zaune a kan kujera yana cin abinci Kusa "dashi ya zauna jikinsa a sanyaye, Ya kalleshi a nutse yace.""Ya ka dawo da ledar abincin.'' Murya na rawa yace.""Tace na fita dashi bata so."" Murmushi yayi yace.""Jeka ajiye mata a gabanta ka fito ka kyaleta. Yace.""Abbah tsoron masifar Yaya Naja'atu nake kada ta dokeni dan na lura tana cikin fushi mai" "tsanani."" Yace.""Idan ta doke ka zan rama maka."" Mussadiq yayi jim! yana nazarin maganar abban nasa, mikewa yayi ya sake nufar dakin a karo na biyu Hankalinta na kan wayarta taga yaron ya dire mata" ledar ya ruga a guje ya fita daga dakin Tsaki taja ta ture ledar daga gabanta tayi rantsuwa sai dai ta kwana ba taci abinci ba dan ba zata ci abinda ya siyo ba. Kwanciya tayi kan gadon Mussadiq ta bude "whasap tana dubawa, voice note din Salim yafi ashirin wanda ya turo mata." Da sauri ta bud'e tana saurara! murmushi ta dinga yi tana lumshe idonta gabadaya jikinta ya mutu domin zantukan da Salim yake mata na yau sun sha bambam dana jiya! gabadaya ma mantawa tayi da 'bacin ran da take ciki shauki da sha'awa duk sun dame ta "Gani tayi ya turo mata hoto da sauri ta bude, gabanta ya yanke ya fadi ganin hotonsu a cikin mota" "lokacin da take masa kiss a fuska, da sauri ta tambaye shi ya akayi ya dauki hoton bata sani ba? rokonsa ta shigayi akan ya goge kada ya bari Abbah Abbas ya gani Yace"" Ba zai goge ba itama ya turo mata ne" dan sabida yana so ta d'ora shi a fuskar wayarta saboda yana so Abbah Abbas din ya gani Tace My prince idan Abbah yaga hoton nan dani da kai asirinmu zai tonu dan Allah kada ka bari yaga hoton nan ni zan fika shiga tashin hankali kuma duniya za tayi tur damu. "Yace.""My Princess kece kike tsoron ya gani! ni ko d'ar! ba nayi wai dan yaga hoton nan dan saboda na" "tanadi amsar da zan bashi koda zai kalubance ni, ke kuma munufar d'ora hoton nan a fuskar wayarki shine nasan idan ya gani jikinsa zaiyi sanyi zai gane cewar bafa kya sonsa zuciyarki tana tare dani, hakan zai sa yaji sha'awar auran ya fita daga ransa tunda na fahimci shi mutum ne mai kishi idan bukatarmu ta biya ta dalilin hakan kinga sai ya sawwake miki ki fito muyi auranmu."" Shuru tayi tana nazarin maganganunsa! Eh ta amince da wannan shawarar ta Salim zata sa hoton a fuskar wayarta har Allah yasa wanda akayi dominsa ya gani! tasan duk ranar da yaga hoton kamar yanda Salim din ya fada jikinsa zaiyi sanyi, sannan zai shiga cikin kunci da damuwa kasancewarsa mutum mai kishin kansa, to sai dai bata da amasar da zata bashi idan ya turketa da tambayar akan me yasa tana matsayin matarsa ta d'ora hotonta da wani akan wayarta. Sai Tace""Salim ina jin tsoro yaga hotonmu ni da kai idan kai kana" da amsar da zaka bashi ni bani da amsar da zan bashi.'' "Salim yayi murmushi yace.""Idan yazo yana miki magana kice masa ai hoton ya dad'e tun kafin a daura" "muku aure dashi yake, idan yace to me yasa kika sa a wayarki sai kice kin kasa cirewa shiyasa kika barshi." "Mirmushi tayi tace""Wannan shawarar tayi wallahi aikuwa yanzu zan sa hoton a wayata Allah yasa ma" "idan ya gani yayi zuciya ya sakeni."" Salim yace.""Ameen ya Allah."" zan kashe data yanzu zamuje gurin" "kallon boll da abokina kada kiyi bacci da wuri idan na dawo inaso muyi hirar dare wacce tafi ta yanzu dadi.""" "Murmushi tayi tace""To sai ka dawo idan kuma nayi bacci sai gobe mu had'u! Yace.""To shikkenan ki kula" "da kanki sosai kada ki barshi yayi gangancin ta'ba min wani 'bangare daga jikin ki."" Tace""Kada ka damu my lov ni takace har abada."" Salim yayi murmushi jin dadi bukatarsa na biya ta kowane fanni yana sake siye zuciyar yarinyar da salon soyayyarsa. Yace.""Okey kiss me please. "" Dariya tasa tace ya za'ayi nayi maka kiss ta waya. Yace idan kinyi zanji a kunnena da gangar jikina."" Murmushi tayi tace""Kai dai ka fiye zolaya wallahi! sai anjima."" ta fada tare da kashe wayar tana murmushi, gaskiya Soyayyar da Salim keyi" "mata na burgeta sosai shiyasa kullum take kara kaunarsa, shi kuwa Abbah Abbas babu abinda ya iya sai" fad'a komai fad'a da rashin uziri ga mutum! ai ba tajin zata ta'ba iya zama dashi tunda shi ya zama mijin tace komai Halisa ta fad'a masa dai-dai ne a gurinsa babu binkice zai hau kai ya zauna yazo yayi tayi mata tsawa! Tana kwance tana juye juye yunwa duk ta isheta amma saboda tsabar cutar kai ta'ki daukar abinci taci Su Saddiqa suka shigo dakin da niyyar kwanciya dan goma na dare tayi Abbansu yace su kashe kallon da suke suje su kwanta. "mikewa zaune tayi tana kallonsu, nan ta hangi" Mussadiq sai 'buya yake a bayan Saddiqa ta lura tsoronta yake ji shiyasa ya kasa tunkaro gadonsa da "take zaune, murmushi tayi tace""Kai Mussadiq daina 'buya ni babu abinda zanyi maka kaje ka saka kayan baccinka kazo mu kwanta yau a gadonka zan kwanta."" Murmushi yayi yace."" Nagode Yaya Naja'atu." "Saddiqa ce ta bashi kayan baccinsa yasa yazo ya dauki pillow guda daya yace.""Yaya Naja'at ke kika kwanta kan gadon ni bari na kwanta kasan kafet."" Tausayi yaron ya bata tace""Anya Mussadiq ban so kaina ba kuwa kazo ka kwanta ai gurin zai ishemu."" Girgiza kansa yayi ya kwanta kasan kafet yana fadin""Na bar miki ki dinga kwanciya har sai sanda Abbah ya kawo miki naki."" Murmushi tayi tana girgiza kanta tace""Nagode yarona Ubangiji Allah yayi maka albarka."" yaron ya amsa da amin yana jin dadin yau ya farantawa Yaya Naja'atu rai Ta kalli Saddiqa dake kokarin kwanciya tace""Ki kashe fitilar dakin," "Saddiqa tace""Yaya Naja'at wai da gaske kike anan zaki kwana yau.""?" "Harararta tayi tace""Ke wannan wace irin magana ce? da a ina nake kwana to.""? Saddiqa kamar za tayi" magana sai kuma taja bakinta tayi shuru ta kwanta tare da rufe jikinta da bargo tana tunanin wani abu Itama kwanciya ta gyara had'e da kashe wayarta gabad'aya! yau tayi alkawarin ba zata je dakinsa ba ballanta ya samu damar latsa mata jiki bayan ya gama yi mata fada. To shima Abbah Abbas din a "nashi bangaran bai wani damu ba dan ganin bata zo dakin nasa ba, sai kawai yayi shirin kwanciya bacci kamar yanda ya saba ya fito daga dakin nasa ya nufi na Halisa ya tarar da ita tana bacci dan bayan taci abincin da ya siyo musu kwanciya tayi bacci ya dauketa ko sallahr magariba da ishai ba tayi ba, tashin ta yayi ya tambaye ta shin tasha magani? tace tasha sai yayi mata sallama ya fita daga dakin, a maimakon ta tashi taje tayi alwala tunda da akwai sauran lokaci sai kawai ta koma ta kwanta da k'udirin gobe sai ta" "had'a sallolin gabadaya ta rama a lokaci daya, sai kace wacce ranta yake hannunta." "Dakin yaran ya nufa! ya tarar sun kashe fitila sai ya kunna wayarsa yana haskasu, Ganinta kwance kan" gadon Mussadiq tana bacci shi yana 'kasa sai ransa ya 'baci! wannan ai abin kunya ne ta saukar da yaro daga makwancinsa ita ta kwanta(ina fatan baku manta da mutumin naku ba a gurin son 'ya'ya) Kasa hakuri yayi kawai ya shiga tashinta! ta mike zaune da sauri tana kallonsa! fuskarta ya haska sosai "yace""Sauko ki bashi gurinsa ya kwanta.""! Ba tayi musu ba ta sauka daga gadon ta tsaya a gefe. Ya sanya" "hannu ya cicci'bi Yaron ya kwantar dashi a gadon, ya rufeshi da bargo ya tsaya kansa yayi masa addua" "duk tana tsaye tana kallonsa ya nufi gadajen sauran 'yayansa suma yayi musu addua ya nufi kofar fita daga dakin! ta dinga jin zuciyarta na wani iri tafarfasa itama ai haifarta akayi da zai dinga nuna mata 'ya'yansa masu daraja ne taji kamar ta fitar masa daga gida dan a rayuwarta ta tsani wulakanci da tozarci Daf da zai fita yaga ledar take away d'inta ya tsaya yana dubawa, alamu sun nuna yanda take" "haka take ba'a ta'ba komai na ciki ba, domin ya gazgata yasa ya sunkuya ya dauki ledar yana dubawa," aikuwa babu abinda taci a ciki. "Juyowa yayi yana sake haskata da hasken wayarsa yace.""Me yasa baki ci abinci ba.""? Kai tsaye tace""Bana" "jin yunwa.""? jimm! yayi yana nazarin maganarta yasan karya takeyi kawai tayi fushi ne saboda yayi mata fada, yace.""Sabida kinyi laifi anyi miki fada shine zakiyi wa kanki horo da yunwa."" shuru tayi ba tare da ta tanka masa ba..........Ganin ta'ki cewa komai yasa ya girgiza kanshi ya kama hanya ya fita daga dakin, yasan dai yunwa ba kanwar lasa bace lokacin da zata nemi abinci babu wanda zai sani, shi dai ya sauke nauyin dake kansa, Koda ya shiga dakin nasa bai sa key a kofar ba barinta yayi a bude wai ko zata shigo" ta kwanta......gajiya yayi da jiran shigowarta dakin bacci mai nauyi ya dauke shi... *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a group's to na sata ne idan kina so ki biya kudin karatu to ga yanda abin yake. VIP Gruop #600 Normal gruop#300 Accont: 0542382124 Binta Umar gtbabk idan katin waya zaki turo kiyi min magana ta whasap da wannan numbar 07084653262 *BINTA UMAR ABBALE* BHRBN *26* "Da safe yaran suka tashi cikin walwala da farin ciki, Naja'atu kuwa kwana tayi cikin 'kunci da takurewar" "zuciya kafin ma tayi bacci sai da taci kukanta ta koshi sannan.......... dalilin kukan da tayi yasa ta tashi da jan ido Mussadiq yaron da ya damu da ita sosai shine ya dameta da tambayar mai ya samu idonta yayi ja, tace masa ciwo yake mata, yaron ya yarda da maganar data fad'a ita kuwa Saddiqa jinta kawai tayi da kunne ta riga ta gane kuka ne ya mayar mata da ido kamar jan gauta. Tana cikin taimakawa" "Mussadiq gurin sanya takalminsa ya shigo dakin, yana sanye da jallabiya ba'ka mai yankakken hannu, as'usul hannusa da k'aramin carbi yana ja. Yaran suka shiga rige-rigen gaishe shi ya dinga amsawa cikin" "sakin fuska, da kulawa. Kanta a kasa ba tare data d'ago ba tace""Ina kwana."" Ya amsa lokacin da yake kokarin fita daga dakin, yaran ne suka biyo bayansa kai tsaye suka nufi dannig domin karyawa, sai dai me? babu komai a kan dannig din Abin ya bashi mamaki sosai ya kalli Saddiqa yace.""Baku had'a break" "bane.""? Tace''Ai bamu tashi da wuri ba shiyasa."" shuru yayi takaici kamar yasa zuciyarsa ta buga, yace.""Yi maza kije ki dafa muku indomee kafin Salim din yazo."" Da sauri ta nufi kicin din...Dakin Halisa ya nufa, ya tarar da ita tana sallah! sai bayan da ta idar sannan yace.""Ashe bayan na fita komawa kikayi kika kwanta wai me yasa kike wasa da sallah ne.""? Ya kalli agogon hannunsa yana kallonta babu faraa a fuskarsa yace'' dubi lokaci bakwai da kusan rabi kina kwance baki yi sallah ba bayan kuma kin san da cewar yara" "zasuje makaranta.""" "Cikin 'kosawa da maganarsa tace""bayan nasan yara zasuje makaranta to me zanyi musu ? Saddiqa ta iya" "komai idan ma ita Naja'atun ba za tayi ba ai Saddiqar sai ta dafa musu abinda zasu ci da wanda zasu tafi dashi tunda kasan ni ba lafiya ce dani ba."" Yace.""Duk da haka me zai hana ki 'kokarta ki shiga kicin d'in kiyi wani abun."" Shuru tayi masa domin itafa ba zata dinga katsewa kanta bacci ba ta tashi tana wani hidimar yara. Yace.""Tunda dake da Naja'atun duk kun zama 'yan kanku zan sa a kawo min mai aiki" "wacce zata dinga kulawa da yarana, ke kina ganin kyashin kulawa dasu tunda ba ke kika haifesu ba ita kuma tana fama da kuruciya da rashin hankali okey ku cigaba da abinda kuke zan dauki mataki."" Yana" kare maganarsa ya fita daga dakin. "Kicin din ya nufa Allah sarki sai ya shiga taimawa Saddiqar cikin tausayinsa tace""Abba kaje ka huta zan" "iya komai."" Girgiza mata kai kurrum yayi ya cigaba da feraye dankali yana sawa a ruwa. Hawaye ta" "goge tace""Dan Allah Abbah kaje ka huta wallahi zan iya ka bari."" Tafada tana kar'bar wukar hannunsa," "da sauri ta zuba indomee din ta cigaba da fareye dankali yana tsaye yana kallonta, tausayi yaran suke" bashi! gabadaya basu san wani abu damuwa ba a lokacin da mahaifiyarsu take raye babu abinda ta gaza "musu tana sauke hakkinsu dake kanta ta kowanne 'bangare, babu shakka Allah baya barin wani dan wani yaji dadi." "Naja'atu ce ta fito palon ta samu Mufida da Mussadiq a zaune a kan kujera, gurin cin abincin ta kalla taga" "babu komai a kai tace""Ke Mufida ba kuyi break bane.""? Mufida tace""Eh Mommyna bata da lafiya shine Abbanmu yace .""Yaya Saddiqa ta dafa mana indomee."" Sai taji tausayin yaran ya kamata da sauri ta nufi kicin din...Turus! tayi ganinsa tsaye a jikin drowar kicin suna magana da Saddiqa wacce take aikin soya" dankali. "Kanta a 'kasa ta shiga kicin din sosai, shi kuma ganin ta shigo kicin din yasa ya fita ba tare da yace komai" "ba. A gurguje suka gama had'a abin karyawa, Saddiqa ta shirya musu dannig din suka zauna suna" "karyawa, Halisa ta fito daga dakinta ko kunya babu ta zauna gurin cin abincin, ita kuwa Naja'atu barin gurin tayi cike da takaicin abinda Halisan keyi a gidan Salim ne ya shigo wanda yayi dai-dai da" "fitowar Abba Abbas din daga da'ki! musabaha sukayi da juna Salim kamar wani mutumin kirki sai sunkuyar da kansa yake yana tsokanar Mussadiq Abba Abbas ya zauna kan kujera yana kallonsa yace.""Idan ka kaisu skull din ka wuce kasuwa kawai sai misalin sha biyu sai kazo ka dauke ni.""" "Yace.""Kawu ina fata dai lafiya.""? Yace.""Lafiya lau zan dan huta a gida ne kafin lokacin.""" Salim ya lura Kawun nasa kamar yana da damuwa farin ciki ne ya cika masa zuciya yana addua Allah yasa hoton jiya ya gani ya d'aga masa hankali Hanyar fita ya nufa yana karkad'a key din mota yaran suka bi bayansa cikin sauri. Halisa tana gama break din mikewa tayi ta dawo kusa dashi ta zauna hade da d'ora kanta a kafadarsa. "Tace""Na fahimci tun jiya kake cikin damuwa kayi hakuri dan Allah ni dai duk abubuwan nan da suke" "faruwa ba'a son raina ba dan da inada lafiya da babu abinda ba zanyi ba, kuma magungunan dana shane suka kashe min jiki shiyasa ban tashi da wuri ba amma insha Allah hakan ba zata sake faruwa ba.""" Wannan maganganun na Halisa sun wanke masa zuciya sai ya daina ganin laifinta gabad'aya ya dauki laifin ya d'orashi kan kan Najaatu Halisa shigewa jikinsa ta cigaba dayi tana dan matsa masa "ga'bobin! jikinsa lokaci guda jikinsa ya mutu! kasala da sha'awa suka saukar masa sai kawai ya gyara zamansa kan kujerar hakan ya bata damar hawa jikinsa sosai tana cigaba matsa masa jiki jallabiyarsa take kokarin cire masa.... dai-dai lokacin Naja'atu a fito daga dakin, ganin abinda ke faruwa yasa gabanta ya fad'i! gabadaya ma su basu san ta fito ba dan Halisa ta samu nasarar cire masa jallabiyarsa shi kuma ya rungumeta 'kam! yana sansana jikinta had'e da sumbatar wuyanta. Ji tayi kafafunta na rawa! da" sauri ta juya domin komawa dakin hawaye na nema ya zubo mata!! Abbah da Halisa shafe-shafen su sukayi a palon kafin su nufi daki domin biyawa kansu bukata. Zama tayi ta zabga tagumi!! daga zarar ta tuno lokacin da yake sumbatar wuyan Halisa sai gabanta ya "fad'i tsigar jikinta duk ta tashi, zazzafar soyayyar da yake mata ta dinga dawo mata a 'kwa'kwalwarta! wani irin kishin Halisa ya cika mata zuciya, mike tayi ta shiga zagaye dakin so take ta fita amma tana jin tsoron kada ta fita taje taga abinda zai tarwatsa mata zuciya." Hawaye ta dinga sharcewa tana kai kawo a dakin...Yanke shawarar fita tayi ta tarwatsu!! kawai taga basa "palon sai jallabiyarsa da dankwalin les din Halisa! Tsaye tayi kan doguwar kujerar da suka tashi, ta dinga kallon kujerar kamar su take kallo! a fusace! ta dauki jallabiyar tasa da dankwalin Halisan ta watsa su" bakin kofar dakinsa! Zama tayi ta rufe fuskarta da hannayeta ta shiga rera kuka! zuciyarta na wani irin bugawa! yanzu me "sukeyi a daki! Ta bude fuskarta da sauri tana kallon kofar dakin nasa, taji kamar taje ta 'balle kofar! hanci ta sha'ka! a fusace! ta mi'ke ta nufi dakin su Saddiqa ruf da ciki ta kwanta kan gadon Mussadiq ta dinga kuka tana dukan pillo..........Ta jima cikin wannan yanayin kafin ta sake mikewa ta fita palon Ikon" "Allah har yanzu suna ciki basu fito ba, agogon dake kafe a bangon palon ta kalla taga kusan goma da wani abun sunyi awa d'aya da rabi da shiga dakin Cikin kyarmar jiki ta nemi guri ta zauna tana" fuskantar kofar dakin da suke ciki. Halisa tana can maganin 'Yar Sa'adu na aiki Eh lallai babu shakka maganin yaci kudinsa dan gabadaya Abbah Abbas ya rikice sai faman sasakar Halisa yake kamar babu gobe yi yake tamkar zai farketa ya kawo kusan sau uku amma ya kasa hakura! Halisa tun tana taimaka masa har ta daina dan ta galabaita sosai! bata ta'ba tsammanin maganin aikinsa ya kai hakaba! Amma saboda ta cuzgunawa Naja'atu ta'ki saduda ta kwaci kanta bashi take yana ci sai kace jaka. Naja'atu tana zaune tsuru a palo motsi kadan ta kalli agogo sha daya tayi ga sha biyu ta kawo kai babu "labarin masu gidan, cikin karaya da sarewa ta mi'ke tana rangaji zata nufi daki Yaya Ramlatu ta" "rangad'a sallama a palon Da sauri ta tsaya tana kallonta, Yaya Ramlatu ganin yarinyar a firgice yasa ta" "daka mata tsawa tace""Ke meye kika, tsaya kina kallona sai kace baki sanni ba.""" "Ji tayi hawaye naso su zubo mata sai dai ta daure bata bari sun zubo ba cikin rawar baki tace""Yaya" "Sannu da zuwa ga guri zauna.""" "Yaya Ramlatu tace""Da kece kike nuna min gurin zama kaji yarinya da iyayi mtssw ina matar gidan take.""?" tafada tana rarraba idanunta a palon. "Cikin kokarin danne damuwarta tace""Tana daki."" Yaya Ramlatu ta mike ta nufi dakin Halisan tana" "surutai......Tsaye tayi tana jiran fitowar Yaya Ramlatun, ta fito ranta a bace tace"" Kince tana daki to yana duba banganta ba ashe na zama abokiyar wasanki." "Girgiza kanta tace""A'a kiyi hakuri mybe to tana dakin Abbah."" Ramlatu tace""Maijin naku bai fita bane.""?" "Da sauri tace""Ya fita tun safe."" Tsaki! Ramlatu taja ta nufi dakin Abbah Abbas din kawai ta shiga bugawa da karfi tana kiran sunan Halisa." "A firgice Halisa ta shiga tureshi tana fad'in ""Abban Mufida muryar Yaya Ramlatu nake ji a gidan fa.""" "Abbah Abbas ko sauraranta baiyi ba ya cigaba da abinda yake sam Ramlatu bata isa ta hanashi yaji dadinsa ba. Ita kuwa Halisa kuka wiwi ta shiga yi dan ta riga ta gama galabaita gabanta duk ya, tsage" "sai zugi yake mata, tunda take dashi bai ta'ba yi mata irin wannan hawan ba." Yaya Ramlatu ta dinga buga kofa tana surutai da kiran Sunan Halisa. Ganin ba'ayi magana ba yasa ta "juyo kan Naja'atu dake tsaye! kawai ta gaura mata mari a fusace! tace""Ashe dama baki da mutunci? kawai kin sani inata buga kofa bayan ba kowa a dakin Naja'atu na hawaye tace""Wallahi suna ciki" "kinga rigar Abba da dankwalin Anty Halisan ma.""" Tafada tana nuna mata kayan dake yashe a bakin kofar dakin Yaya Ramlatu ta shiga bin kayan da "kallo sai kuma ta saki murmushin mugunta taje ta nemi kujera ta zauna ta zuge jakarta ta dauko goro tana ci Ganin Naja'atun ta'ki barin kofar dakin yasa ta buga mata tsawa da fad'in ""Dan ubanki" tsayuwar me kike musu a kofar daki munafuka kawai ashe kin san abinda sukeyi shine kika sani ina buga "musu kofa.""" "Cikin kokarin son ta san abinda sukeyi din tace""Ni ban san me sukeyi ba kawai dai sun shiga daki tun safe" "shine nima hankalina ya tashi.....Yaya Ramlatu tace""To sinna suke rayawa dan haka sai ki kwantar da hankalin ki zasu fito idan sun gama. Naja'at za tayi magana sai ga Halisa ta bude kofar dakin ta fito a" "firgice sai wata iriyar tafiya take tana cizar le'bunanta!!! a firgice! Yaya Ramlatu ta mi'ke ta iske inda take tana tambayarta menene! Halisa hawaye suka wanke mata fuska! ta rike hannun Yaya Ramlatun tace""Muje d'aki Yaya Al'amarin yafi karfina."" Cikin tashin hankali Yaya Ramlatu ta ri'ke hannunta suka nufi dakinta Halisa sai cire 'kafa take da kyar tana tafiya a hankali a hankali Yaya Ramlatu sai rirrike take Naja'atu taji dadi ganin Halisan cikin halin ciwo a fili tace ""Allah shi 'kara alhakina ne ya kama ki," murmushi tayi ta bar gurin. Halisa da kyar ta zauna gefen bed tana rintse idonta sai hawaye ya shiga zubo mata ita kadai tasan radadi da zugin da gabanta ke mata. "Yaya Ramlatu tace""Wai me ya faru ne ni kin sani cikin fargaba da tashin hankali Murya na rawa Halisa" "tace""Ya Ramlatu dan Allah taimaka ki jona min ruwan xafi na shiga gabana kamar an tsaga da reza haka nake jinsa.""" "Yaya Ramlatu ta ri'ke baki tana kallonta tace""Kamar yaya na jona miki ruwan zafi sai kace wata maijego" "ko amaryar da aka karbi budurcinta zakiyi ruwan zafi."" Halisa tace""Yaya Ramlatu duk wannan maganar bata taso ba tunda kikaji na fadi haka to akwai matsala.''" "Ya Ramlatu tace"" To Allah ya kyauta! kettle ta dauka ta shiga toilet ta jona ruwan zafi a ciki ta fito ta" "tsaya kan Halisan tana tamayar ta, Halisa tace""Maganin nan ne na gurin Yar Sa'adu ashe haka yake da karfi sau biyu fa kacal nasa amma tunda ya fara abu daya bai saurara ba ya kawo yafi sau biyar."" Yaya Ramlatu ta rike bakinta tana girgiza kanta tace""Aifa lallai dole kiji jiki ta'b! to ai sai ki ajiye maganin idan ya kama da cutarwa a ciki ko kuma ki dinga sa kad'an ina dalili."" Halisa ta sha'ki hanci tace""Ai gabad'aya ma maganin zubar dashi zanyi dan ba zan zauna na kashe kaina a banza ba."" Yaya Ramlatu tace""Haba ke kuwa abun zunzurutun kudi zaki zubar."" A dan hasale Halisa tace""To ko na baki kina so ne.""? Da sauri tace""Oo rabani da wannan shirme ni bashi ne a gabana ba.( Halisa ya kamata ki nutsu ki gane Yaya Ramlatu na ingizaki kina siyan abinda zai cutar dake da kudinki me yasa ita bata siya tayi amfani dashi sai ke mara hankali ki ta siyan abu baki san yanda akayi aka had'ashi ba ki dinga cusawa a matuncinki dan cutar kai) Tace""To kawai tunda nace zubarwa zanyi ki kyaleni ba zan kara sawa a gabana ba ballanta" "'kaninki ya kashe ni."" Yaya Ramlatu ganin Halisa ta fusata! sai ta sassauta murya tace""Allah ya kyauta to" "tashi kije kiyi ruwan d'umin Allah ya kiyaye gaba.""" Halisa ta mike a hankali ta nufi toilet. Naja'atu kuwa wanka tayi a gurguje ta shirya ta fito palo ta zauna so take taga da wane ido Abba Abbas "din zai kalleta dan tasan a cikin hakkinta ya shiga daki ya share awa kusan hudu yana abinda bai dace ba. Aikuwa ganinsa tayi ya fito shar dashi kamar wani matashin saurayi, Yana sanye da farin yadin" piltex cotton anyi mishi aiki da bakin zare wuya da hannu! sai yayi amfani da hula mai duhu! kafafunsa na sanye da takalmi mai gidan yatsa ba'ki yayi kyau sosai yana ta kamshin turarensa. Lafiyayyar "harara ta watsa masa wacce ta dauki hankalinsa sosai ya tsira mata ido yana mamakinta, Gani yayi ta" murguda bakinta ta dauke kanta tana motsa bakinta. "Sai ya karaso inda take tsaye a nutse ya tsaya a kanta yace.""Ke lafiyarki kuwa.""? Ta kalleshi tana sake" "murguda baki Sai abin ya bashi dariya yace""Da alama kina bukatar ganin likita kwa'kwalwa."" Fashewa" "tayi da kuka tace""Abbah a gaskiya abinda kake baya dacewa wai dama haka addini yace kuyi."" ? tafada tana me tsira masa idonta, dama tayi al'kawarin sai ta d'aga masa hankali kamar yanda ya d'aga mata. Kallonta ya shiga yi yana mamakin maganarta, ta goge hawayen fuskarta ta cigaba da cewa''" Kana shiga daki ka kulle kofa a cikin kwanakin aurena da musulunci ya bani da wane ido kake tunanin "zan kalleka kaifa ba yaro bane sai ka dinga shiga hakkina.""" Ya saki baki kawai yana kallonta sosai maganganunta suka bashi mamaki!! Mikewa tsaye tayi da wayarta "a hannunta tace""Dan Allah idan kasan ba za kayi adalci a tsakaninmu ba to ka sawwake min tunda dama baka d'ora min idda ba sai naje na auri wanda zai kula dani "" Kasa cewa komai yayi kawai ya zuba" "mata ido yana kallonta. ita kuma ganin jikinsa yayi sanyi sai taji dadi ta ra'ba ta jikinsa zata bar gurin, turata yayi ta koma kan kujerar ta zauna! wayar hannunta ta fad'i kusa da kafafunsa, hankalinsa ne ya dauke gurin hoton dake fuskar wayar tata. Da sauri ya sunkuya ya dauka yana dubawa! ganin abinda" "ke wayar yasa hankalinsa yayi masifar tashi, ya nuna mata fuskar wayar da fad'in ""Waye wannan.''? duk da yasan waye kawai tsintar kansa yayi da tambayarta, tace"" Salim ne.""? Wani bahagon mari ya kifa mata yana tsuma! yace.""Yaushe kukayi wannan hoton.? ashe munafurtata kuke.''? tana kuka tace""Wannan hoton ya dad'e tun kafin muyi aure da kai yake."" Cikin tsawa! yace.""Karya kike wannan hoton bai jima ba ashe baki da mutunci naja'atu kina so ki zubar min da mutuncina ko.? Tace""Na fada maka wallahi hoton ya dade tunda baka yarda ba shikkenan."" A fusace ya doka wayar da bango (garu) ta fad'i kasa duk ta farfashe! tsuganawa yayi ya tsince sim card din ya karyasu ya watsar a gurin, ya kalleta da jan ido yace."" Tunda kin zama shaid'aniya to zanyi maganinki kin janyo duk wani tausayinki da nake ji na daina sai na mai dake cikakkiyar mace mai lasisi a gidan auranta zaki zauna da tsoho har karshen" rayuwarki...... Dakinsa ya nufa cikin tsananin bacin rai!! ita kuma ta had'a kai da gwiwa tana kuka sam bata dauka zai fusata hakaba gashinan garin neman gira ta rasa ido ya fasa mata waya ya karya mata sim! babban tashin hankalinta a yanzu shine ta wace hanya zata dinga saduwa da masoyinta. Tabbas da tasan zai dauki matakin lalata mata wayarta daba ta nuna masa hoton ba. Salim ya dade da shigowa palon "amma bata sani ba sai da ya kira sunanta sannan a furgice ta dago kanta tana kallonsa, ta bude baki kenan za tayi masa magana Abbah Abbas din ya fito daga dakinsa hannusa da rike da wayoyinsa, ganin Salim a tsaye a kanta ya sake tunzura masa zuciya cikin gawurtacciyae tsawa mai had'e da zazzafan kishi yace.""Kai mai kake anan.""? Gabadayansu suka firgita suka juyo suna kallonsa, Salim yace.""Kawu nazo daukar ka kamar yanda kace karfe goma sha biyu na dawo na kai kasuwa to ina shigowa sai na tarar da" "ita tana kuka shine nake tambayarta ko wani abune ya faru.""" "Wani banzar kallo ya watsa masa kafin yace.""Malam bani key din mota ka tafi naka guri bana bukatar na" "sake ganinka cikin al'amurana.""" "Salim yace.""Subahanallahi Kawu mai ya faru kuma idan laifi nayi maka ka gafarce ni kasan dan adam ajizi" "ne.""! Yace.""Ban nemi wata magana da kai ba key na mota nace ka bani ka fita ka bani guri."" Salim ya'ki bashi key din ya tsaya yana rokansa gafara! A fusace! yace.""Zan dauki mataki mai tsauri a kanka idan baka bani key ka fice min daga gida ba."" Salim ya bude bakinsa zaiyi magana Yaya Ramlatu ta fito daga dakin Halisa hankali a tashe ta 'karaso gurin tace"" Me yake faruwa ina jin anata hayaniya."" Salim ya karasa kusa da mahaifiyarsa cikin rawar baki ya shiga fada mata abinda ke faruwa. A sanyaye ta kalli dan" "uwan nata dake tsaye yana huci!! tace""Duk da dai ban san abinda ya had'aku ba ina rokon ka yafe masa" kasan dan adam ajizi ne ba wai na hakana kayi masa hukunci ba salim kai kake da iko dashi cikin ko wane "hali.""" "Ajiyar zuciya ya sauke yace.""Bana bukatar ke kisan me yayi shima kuma bana bukatar yaji abinda yayi" "daga bakina tunda nasan yasan abinda ya aikata min na ha'ince wannan dalilin ya sanya ni yunkurin cireshi daga cikin sabgogina saboda ya kasance maha'inci.""" "Yaya Ramlatu ta fashe da kuka tana kallonsa tace""Wai shin me yayi zafi ne? dan Allah ka fada min abinda" yayi maka kake jifansa da wannan mugayen maganar Naja'atu ya kalla cikin takaici da bacin rai "yace.""Yaya Ramlatu tunda nace abar maganar to a barta shine yafi amfani.""" "Tace""Aikuwa ba za'a barta ba dan naga ka kalli waccar munafukar yarinyar watakila duk sharrinta ne.""" "Shuru yayi mata, sai kawai ta shiga zagin Naja'atun tana fad'in duk iya asiri da surkulle na ubanta to bai isa ya raba tsakanin hanta da jini ba.""" Naja'atu abu biyu ya had'e mata a duniya ta tsani taji ana zagin iyayenta ji tayi kamar ta rama sai dai tayi shiru ta sunkuyar da kanta tana ta kuka gami da yanke shawarar da zata fisheta. Abbah Abbas ganin "al'amarin na Yaya Ramlatu na nema ya wuce gona da iri sai ya dakatar da ita yace.""In dai akan ya kori Salim ne take wannan abu to ya janye maganarsa dan haka magana ta mutu."" Fadin hakan yasa ta sassauta ta nemi guri ta zauna tana haki! ita kuwa Naja'atu mikewa tayi tana kuka ta shige dakinsu Mussadiq Yaya Ramlatu ta bita da kallon banza da fadin ""Aikin banza gayyar tsiya masu raba" zumun Daga mata hannu yayi yace.''Dan Allah ki daina wannan maganar bata dace ba ni sukayi wa laifi "ita da Salim din kuma na yafe musu."" Salim baiso ya fadi hakaba yaso ayi ta tak'are a gurun, amma dai duk da haka yaji dadi da yasa masa 'bacin rai a zuciyarsa. Sai ya karyar da kai cikin sassauta mirya" "yace""Kawu kayi hakuri duk da baka fada min laifina ba amma na dauka ina neman afuwarka kuma insha" "Allahu ba zan sake ba.""" "Ba tare da ya tanka masa ba ya kama hanyar fita, sai yayi saurin rufa masa baya yana d'agawa" mahaifiyar tasa hannu. *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a gruops to na sata ne idan kina so ki biya kudin karatu ga yanda abin yake. VIP Gruop#600 normal gruop#300 Account: 0542382124... Binta Umar gtbank. idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* Mdd *27* Salim da sauri ya 'karaso bakin motar yasa hannu ya bude masa motar hade da matsawa gefe guda yana "wani sunkuyar da kansa tamkar wani mutumin kirki, Abba Abbas ya shiga motar ya zauna har yanzu fuskarsa a murtuke take, da sauri salim ya rufe motar ya zagaya ya bude mazauninsa ya zauna sannan ya kunna motar suka fita daga gidan Motar shuru tayi kowa na sa'ke-sa'ke a cikin zuciyarsa, Abbah" "Abbas kamar zai daure maganar azuciyarsa sai ya kasa gyaran murya yayi babu wasa cikin maganarsa yace.""Kai!! wannan hoton da nagani cikin wayar Naja'atu yaushe kukayi dauke shi."" Salim yaji gabansa ya fad'i! cikin dakiya da kokarin kare kansa yace.""Kawu wane hoto ne kake magana akansa."" ? A dan fusace! yace.""Kai bana son rainin hankali malam ya ina tambayarka kana tambayata wato matata kake bibiya ko.""? Salim yace.""Subahanallahi Kawu wannan wace irin magana ce kakeyi ina ni ina matarka Kawu ai wutsiyar ra'kumi tayi nesa da 'kasa ni wallahi yanzu kunyarka ma nake ji idan na tuna wai na ta'ba soyayya da Naja'atu. Abbah ya daga masa hannu da fad'in ""Ba cewa nayi kayi min wasu zancan" "banza ba ina tambayarka hoton da nagani a cikin wayar matata yaushe kukayi shi.""?" "Cikin rawan murya Salim yace."" Wallahi Kawu ban fahimci inda maganarka ta dosa ba kayi min bayani" yanda zan fahimta saboda nasan ni a yanzu tsakanina da Naja'atu gaisuwar mutunci ce tunda ta zama matarka ai dole na girmamata to kawu ina zan ganta ma ballanta na muyi hoto tare. "Abbah Abbas yaji zuciyarsa ta danyi sanyi saboda jin maganar da Salim din yayi, Gyara zamansa yayi" "yace.""Wani banzan hoto nagani kai da ita a cewar ta tun kafin aure ya shiga tsakanina da ita yake kuma saboda shashanci da rashin sanin hakkin aure ta dauki hoton ta dora a fuskar wayarta shiyasa hankalina ya tashi na d'ora zargina gabadaya a kanku kai da ita.""" "Salim ya dinga girgiza kansa cikin sanyin murya yace.""Hakika munyi hotona masu yawa da naja'atu a" "lokacin da muna soyayya to amma daga lokacin dana tabbatar da cewar tafi karfina sai duk nagoge hotonanta dake cikin wayata Kawu ka yarda dani wallahi bazan ta'ba cutar da kai ba.""" Ajiyar zuciya ya sauke! yanzy yaji sanyi cikin ransa domin kalaman Salim din sunsa ya gazgata maganarsa kan cewar tsakani da Allah yake zaune dashi kuma a tsakaninsu babu cuta babu cutarwa. Yaya "Ramlatu kuwa tana ganin maigidan ya fita sai ta mike tabi Naja'atu dakin ta dinga zazzaga mata masifa tana zagin iyayenta da fad'in ""Insha Allahu sai Allah ya tona musu asiri kuma duk asirin da Baba malam" yakewa zuriarsu da yardar Allah kansu zai koma. "Naja'atu kasa hakura tayi tace"" Yaya Ramlatu mu bama asiri muna zama da mutum da zuciya daya duk" "wanda kikaji yana maganar anyi masa asiri to bai yarda da kansa ba Amma ni da iyayena da Allah muka dogara kuma shine zai shige mana gaba. Yaya Ramlatu tace""Eh lallai wuyanki ya isa yanka yarinyar" nan to dan ubanki Malam Sani!!! Halimatu ma bata iya karawa dani ba ballantana ke karan kad'a miya da har nake magana kina mayar min da martani to ni sai na sabauta miki rayuwa wallahi Tana kuka "tace""Dan Allah kiyi hakuri na fada miki abinda yake zuciyata ne kuma ni ba rashin kunya nayi miki ba."" Yaya Ramlatu ta gaura mata mari a zafafe tace""Dan uwarki kin tsaya gaba da gaba dani kina fada min" "maganar da ranki yake so amma kice ba rashin kunya kike min ba to Ubanki kike min kome.""?" "Halisa ta turo kofar dakin ta shiga tana dan ya mutsa fuska tace""Wai me faruwa ne? tun dazu nake jin" hayaniya. Yaya Ramlatu ta shiga wassafa mata abinda ya faru. "Tsaki taja ta kalli Naja'atun tace""Yaya Ramlatu sharrin yarinyar nan yafi kala d'ari komai akace tayi ba" "zanyi mamaki ba nima nema suke su rabani da 'yata mufida, tunda tazo gidan nan Mufida ta daina zuwa inda nake sai na kwana na yini bansa ta a idona ba tana nane dasu sun lashe mata kurwa.""" "Yaya Ramlatu tace""Ai sai kiyi gaggawar dauke yarinyar ki dan kada su koya mata mugun hali na gado.""" "Naja'atu na tsaye tana jinsu suna ta zaginta iyayenta da kakaninta, sai da suka gaji dan kansu suka fita daga dakin." Cikin kuka da tashin hankali ta nemi hijabinta tasa ta kama hanya ta fita daga gidan tana kuka kamar "ranta zai fita. Aunty Maryam taga ta fad'o mata gida tana kuka, a gigice ta mike ta tare ta tana" "tambayarta abinda ke faruwa, Naja'atu rungumeta tayi tana kuka tace""Aunty Maryam kun kassara min rayuwata kun cutar dani ba zan iya wannan rayuwar ba, gidan Abbah Abbas yafi karfina dan haka wallahi tallahi zan yankewa kaina hukunci da ba zaiyi wa kowa dad'i ba."" Aunty Maryam tace""Innalilihi wa'ina ilahi raji'un! Naja'atu nutse ki fada min abinda ke faruwa ashe duk kin manta shawarwarin da na baki" "jiya.""" "Tace""Aunty Maryam wane shawarwari zanyi amfani dasu kullum a gidan a cikin laifi nake Halisa tayi ta yi" min sharri a gurinsa sai ya dauki maganarta ba zaiyi binkice ba yazo yay tayi min fad'a! Yanzu haka Yaya Ramlatu na gidan kafin na fito ta zage ni ta mare ni yafi sau uku me nayi mata zata dinga dukana nima fa "ba'ason raina akayi auran nan ba da zasu dinga takurawa rayuwata.""" "Aunty Maryam jikinta yayi sanyi tace""Gaskiya Yaya Ramlatu abunda takeyi bata kyautawa, kawai da" "girmanta da komai ta dinga zuwa gidan k'aninta tana lalata masa zamantakewar gida, wallahi haka Halimatu tasha wahalarsu, kiyi hakuri ki koma dakinki idan Abba Magaji ya dawo zan fad'a masa abinda" "ke faruwa gaskiya dole ya samu abokinsa yayi masa magana.""" "Tace""Anty Maryam babu inda zan koma gidan Baba malam ma zan tafi.""? Anty Maryam ta rufe baki cikin" "tsoro tace""Dan Allah daina wannan maganar kina so ki janyo min fada gurin mijina kenan idan kika tafi gidan baba malam zasu d'ora laifin akaina ki daiyi hakuri insha Allah komai zai daidaita. Naja'atu shuru" kawai tayi tana sauraran maganar da Anty maryam din keyi har abada bata jin zata iya zaman aure a gidan Abbah Abbas dole ta nemawa kanta mafita dan tana ji tana gani ba zata 'kare rayuwarta cikin kunci da masifar kishiya ba. Aunty Maryam ta dinga rarrashinta gami da bata shawarwari masu amfani wanda idan da zata daukesu "to ba karamin taimakonta zasuyi ba, amma ina! hausawa na cewa wanda yayi nisa baya jin kira dan gabadaya Naja'atu a cikin zuciyarta bata da niyyar zaman aure a gidan Abba Abbas burinta kawai ta samu damar da zata sanya ta kufce daga hannunsa. Sai da tayi sallahar la'asar a gidan Abba Magajin" "sannan Aunty maryam ta lalla'bata kan ta tafi gida insha Allahu zata sanar da Abba Magaji duk abunda ke faruwa a gidan abokin nasa, Naja'atu kamar gaske tayi mata sallama ta fito daga gidan, kai tsaye sai ta mi'ki titi ta dingi tafiyar 'kafa kofar na'isa ta nufa gidan Baba Malam dan tayi rantsuwar ba zata koma gidan ba, ta riga ta fito kenan Baba malam na zaune kan dadduma a dakalin gidansa ya hangota" "ta karyo kwanar gidan, idonsa yasa mata yana so ya tantance itace ko ba itace ba, sai da ta kusa zuwa kusa dashi sannan ya gazgata, ganin da yayi mata a firgice yasa hankalinsa ya tashi jikinsa yayi sanyi sosai! ita kuma tana zuwa sai ta zube gabansa ta bude bakinta za tayi magana kuka yaci karfinta, cikin taushin murya yace.""Tashi ki shiga ciki komai yayi tsanani maganinsa Allah."" Ta mike kamar mara lafiya ta nufi cikin gidan Baba Talatu na bakin rariya tana d'auraye kwanuka taji sallamarta da sauri ta juyo tana" "kallonta tare da amsa sallamar da tayi Itama ganin yanda ta shigo firgai firgai ya tashi hankalinta, sai" ta mike daga inda take ta karaso kan tabarmar da Naja'atun ke zaune tana tsiyayar da hawaye. Zama "tayi kusa da ita tare da fadin ""Naja'atu daga ina kike wannan zuwan naki bana alkairi bane.""! Kukanta ne ya sake tsananta ta rike hannun mahaifiyar tata tace"" Baba daga gidan Abbah Abbas nake tunda kuka kaini kuka ajiye ake azabtar dani wahalar yau daban ta gobe daban, Yaya Ramlatu tazo har gidan tayi mun duka ta zageni ta tsine muku ta kira ni mayya babu irin cin mutunci da zagin da ba tayi mun ba, wannan dalilin ya sanya ni bar musu gidan dan bana so na zauna a gidan ta tunzura zuciyata na rama" zagin iyayena da take ace nayi mata rashin kunya. "Baba Talatu tace""Haba Naja'atu har yaushe aka kai ki dakin mijin naki da zaki zo da wannan maganar wai" "shin me yasa ke baki da hakuri ne? shin ba zakiyi koyi da 'yar uwarki ba, Halimatu har ta kwanta dama bata ta'ba zuwa gidan nan ta kawo 'karar mijinta da 'yan uwansa ba tana hakuri cikin ko wane hali kuma tana biyayyar aure amma ke kwana uku kacal kinzo gida shin ko dai kina so ki zubar mana da kima da" mutunci ne a unguwa. "Girgiza kanta ta shigayi tace""Baba akwai cutuwa a cikin wannan auran da kuka 'kulla domun kuwa ta" kowane 'bangare babu sassauci ni ake zalinta kwana uku kacal da nayi a gidan na fuskanci ba gidan zama bane Halisa sai abinda tace akeyi kullum cikin yi min sharri take a gurin Abbah sai yazo yayi tai min fada bani da laifi Baba kuma kin san kowa da halinsa a gaskiya ni ba zauna wani ya dinga zagin iyayena nayi "shuru ba dan iyaye ba sufi iyaye ba.""" Baba Talatu tayi shuru jikinta duk yayi sanyi da maganganun Naja'atun babu shakka duk d'a nagari ba zai so a dinga zagin iyayensa a gabansa ba. Baba malam ne ya shigo gidan ya zauna gurin zamansa yana "kallonsu sunyi jugum! ya kalli Naja'atu da fad'in ""Auta kada kice min yaji kikayi kika zo gida."" Baba Talatu tace""Aikuwa dai abinda tayi kenan Cikin damuwa yace.""To akan me? Ashe ke ba zaki kyautata hakurin" "da 'yar uwarki tayi a dakin mijinta ba.""! Baba Talatu tace""To abun ne gaskiya da akwai matsala kuma kasan kowa da halinsa ba lallai ne Naja'atu ta kauda kanta daga kan abinda Ramlatu zata zo tayi mata ba, idan baka manta ba kasan haka Halimatu ta sha fama da Ramlatu wallahi ni na rasa wace irin macace" "wacce kullum girma take amma tana sake lalacewa da rashin hankali.""" "Baba Malam yace.""Duk wani abu da Ramlatu zata zo tayi miki a gidan mijinki idan bada mijinki kuka" "samu sa'bani ba to komai mai sauki ne! ban lamunce ki dinga dauko kafarki kina zuwa gida akan abinda bai kai ya kawo ba, shin dan Ramlatu ta zage ni ko ta zagi mahaifiyarki sai me? mutukar baki bude baki kin rama ba to kanta take zagi! dan haka daga yau sai yau kada Ramlatu ta sake zuwa gidan mijinki wani sa'bani ya shiga tsakaninki da ita ki d'auko 'kafa ki zo gida, yin hakan zai janyo miki 'bacin raina.'''!! Tayi shuru hawaye nata zirara a fuskarta dama tasan da wuya baba malam ya kyaleta ta zauna masa a gida gashi 'kiri-'kiri yana nema ma ya d'ora laifin a kanta. Yace.""Tun kafin gari yayi duhu ki tashi ki koma" dakin 'ki farin cikina a duniya shine inga kin zauna lafiya tare da mijinki saboda haka kije ki cigaba da hakuri insha Allahu zaki ci riba anan gaba. Mi'kewa tayi tana 'kokarin zura takalminta takaicin duniya ya isheta wai iyayenta da suka haifeta sun kasa gane abinda take ji a cikin zuciyarta da anyi magana sai suce tayi hakuri idan hakuri na kisa a ganinta to da tuni ya kasheta. Koda ta fita daga gidan kai tsaye gidan Alhaji ta nufa dan yanda Yaya Ramlatu ta kuntata mata to itama sai ta janyo mata fad'an iyayenta. Hajiya na zaune a palo tana jan carbi Naja'atun ta shiga da sallama kasa kasa a bakinta "Kallo guda Hajiya tayi mata ta fahimci akwai damuwa, Naja'atu zama tayi kujerar da take kallon hajiyan" "tana share hawaye...Hajiya ta ajiye carbin hannunta a nutse ta kalleta tace""Naja'atu tunda na ganki a furgice nasan babu lafiya ki fad'a min abinda ke faruwa.""? wasu sababbin hawaye ne suka zubo mata, murya na rawa ta shiga fad'a mata abinda ke faruwa da irin sharrin da halisan ke mata da kuma yanda Abbah Abbas din ke dauka yazo yayi mata fada ba tare da yabi ba'asi ba, sannan ta fada mata zagi da" dukan da Ramlatu tazo har gida tayi mata. "Hajiya shuru tayi takaici kamar ya fasa mata zuciyarta, ita kam ta rasa yaushe Ramlatu za tayi hankali" "wallahi da girmanta da komai ta dinga daukar kafa tana zuwa gidan yara tana shashanci to babu shakka wannan karon zata fuskanci bacin rai daga gareta. Tace""Kiyi hakuri kinji ko Naja'atu hakika nasan anyi" "miki ba dai-dai ba amma na roke ki kiyi hakuri ki kwantar kuma da hankalin ki tunda dai kin kawo min 'karar Ramlatu da Abbas to ni kuma zan hukunta miki su saboda haka yanzu ma ba zaki koma gidan ba, har sai shi Abbas din yazo a gabanki zanyi masa fadan kan abinda yake yi ba dai-dai bane."" Naja'atu taji dadi sosai da yanda Hajiya ta goya mata baya sai kawai ta gyara zamanta a palon ta zauna suna dan ta'ba hira da hajiyar..........Abbah Abbas kullum suka taso daga kasuwa kafin su nufi gidajensu shi da Abokinsa Abba Magaji sai sun shiga kofar na'isan sun gaisa da iyayensu wataran ma a can suke sallahr magariba kafin su tafi gida, to yau ma kai tsaye da suka taso daga kasuwar kai tsaye can suka nufa. Ganinta" a zaune a kusa da hajiya ya bashi mamaki sosai! ita kuma sauri tayi ta dauke kanta tana zum'bura bakinta. Hajiya ta amsa sallamarsa ya shiga palon a nutse ya zaune kan kujerar dake fuskantar hajiyar "yana gaisheta, Hajiya ta amsa kadar kadahan! tunda yaga haka sai yasha jinin jikinsa. Ya kalli Naja'atu" "yana tsuke fuska yace.""Ke! wa kika tambaya kan cewar zaki zo nan.""?" "Hajiya tace""Ai zamanta a gidan baida amfani tunda ka kasa ri'ke amanarta, sannan ka bawa matarka da" "'yar uwarka lasisin dukanta da zaginta gami da hanata sakat! a cikin gidan.""" "Sai ya kasa gane inda maganar mahaifiyar tasa ta dosa."" Yace.""Hajiya bangane ina maganarki ta dosa" "ba."" Tace""Ai dama ba zaka gane ba sai na ganar da kai, to wannan yarinyar dai 'karar ka ta kawo min kancewar kuna azabtar da ita kai da matarka sannan kuma yau Ramlatu taje har gidan ta doketa.""" "Maganar ta bashi mugun mamaki! kamar shi da girmansa da shekarunsa a kawo shi 'kara gaban iyayensa," "Ya dago kansa yana kallonta sai yaga kanta na kallon wani guri sai faman zum'bura bakinta take, tunda yake da Halimatu da Halisa tsayin shekarun da sukayi a tare babu wacce ta ta'ba kawo 'kararsa gaban iyayensa sai wannan yarinyar gaskiya ya jinjina al'amarin sosai! amma babu komai idan ma raini ne ya" soma shiga tsakaninsu to dama ya dauki alkawarin yau yake so ya fitar da raini a tsakaninsa da ita. "......Hajiya ta cigaba da cewa""Wannan dalilin ne yasa nace ba zata koma gidan ba sai kazo naji ta bakin ki," "shin me yasa a duk sanda Halisa zata kawo magana baka tsayawa kayi bunkice zaka hau kai ka zauna kazo kana yin abinda ya dace.""" "Rashin abinda zaice ne yasa yace.""Ayi hakuri Hajiya.""" "Tace""To Dan Allah daga yau ka zama mai adalci a tsakanin matanka idan wani abu ya faru a tsakaninsu" "ka daina dora laifi a kan mutum daya ka dinga yin binkice tukkuna.""" "Tace.""Insha Allah Hajiya to amma ni abinda ke bani mamaki anan shine har yaushe akayi auran da har" "za'a fara kawo 'kara duka fa yau kwananta hud'u a gidan kuma iya bakin kokari inayi a tsakaninsu.'' Hajiya tace"" To nidai ga abinda tazo ta fada min kuma nasan wannan matar taka babu abinda ba zata aikata ba dan haka kaja mata kunne ita in banda abinta ai kamata yayi ta dauki naja'atu a matsayin kanwarta ba kishiyarta ba kuma itama Ramlatu zata zo ta sameni har gida, idan ta dinga zuwa gidanka tana lalata maka zamantakewar matanka to tun wuri ka taka mata burki tunda har yanzu taki tayi hankali."" Yace.""Ba zan hanata zuwa gidana ba domin suna zumunci da Halisa amma zanyi bunkice sosai kan maganar da ita Naja'atun tazo ta fad'a miki idan na tabbatar da gaske ta doke ta to ni kuma zan" "nuna mata rashin jin dadi na.""" "Hajiya tace""To Allah ya sa'ba halaye dama nace idan tayi sallah taci abinci sai ku tafi.'' Agogon dake" "daure a hannunsa ya duba ya mike da fad'in ""Bari na hau sama mu gaisa da Alhaji."" Kafin ma ya rufe bakinsa ya hango shi yana sakkowa daga benansa, Alhaji Sama'ila ya sauko ne d'aure da alwala da nufin zuwa massalaci, gaisawa sukayi da Abba Abbas d'in dama ita Naja'atu har dakinsa taje ta gaisheshi, ita kuwa Hajiya 'kin fada masa abinda ke faruwa tayi saboda ba wata cikakkiyar lafiya ce dashi ba Abbah" Abbas da mahaifinsa a tare suka nufi massalaci domin gabatar da sallar magariba... *Littafin na kudi ne...!* Koda zaki ganshi a gruops to na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu to ga yanda abin yake. VIP #600 normal#300 Account: 0542382124..Binta Umar gtbank...Idan katin waya zaki turo kiyi min mgn ta whsap da wannan numbar. *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* BHRBN *28* "Sai bayan ishai ya shigo gidan, a lokacin itama tayi sallah taci abinci tana zaune suna hira da Hajiyan, ba" "tare da ya zauna ba ya kalli hajiyan da fad'in ""To hajiya sai da safe."" Hajiya ta kalli Naja'atu da fad'in ""Tashi kuje ki kara hakuri insha Allahu zakici ribar hakurinki.""ta kalli Abba Abbas din da fad'in "" Kai kuma ina fatan kaji abunda na fada maka ko."" Yace.""Naji hajajju Allah ya shige mana gaba."" Ta amsa da ameen."" ya juya ya fita, ita kuma ta mike a sanyaye tasa takalmanta hajiya tace""To Allah ya tsare insha Allah zansa a kawo ni gidan naku."" Tace."" Tom Hajiya sai kinzo."" Kafin ta fita sai da ta shiga dakin hajia Rabi kishiyar Hajiyar tayi mata sallama Hajiya Rabi ta bata kayan islamic irin na mata masu kyau. ta" kar'ba tana godiya tayi mata sallama tabi bayansa. "Tare ta gansu da Abba Magaji a jikin mota suna magana, gabanta ya fadi ganin Abba magaji duk sai ta" "tsorata kai a sunkuye tana kokarin bude mota tace""Abba Magaji ina wuni."" Ya amsa fuskarsa a sake, dan shi gabadaya bai san wai yaji tayi ba tunda shi Abbah Abbas din bai fada masa komai ba. Bude mota" tayi ta shiga tana zazzare ido addua take Allah yasa Abbah Abbas din ya shigo su tafi dan gabadaya jikinta yayi sanyi tasan da Abba magajin yasan abinda ta aikata sai ya 'bata mata rai. Motsin bude motarsa taji sai ta nutsu tayi kasa da kanta gabanta na fad'uwa. Ya shiga motar ya zauna ba tare da kalleta ba a nutse yaja motar suka bar gurin gabadaya hankalinsa nakan draving din da yake "bai ko kalli inda take zaune ba. ita kuma ganin yanda ya sha kunu ne yasa duk tsoro ya cika mata zuciya. kire ne ya shigo Wayarsa dake gaban aljihunsa, ya dauka yana dubawa yaga Halisa ce, ya kara wayar a kannunsa tare da amsa sallamarta, tace""Abbah Mufida yau shuru baka shigo gida da wuri ba nace Allah" "yasa dai lafiya sannan kuma ina so na fada maka cewar yarinyar nan Naja'atu tun safe bata gidan nan.""" "Yace.""Kada ki damu gani nan tare da ita taje gidan Alhaji ne."" Halisa tace""Au! to ai da da zata tafi sai ta" "fad'a mana nida yara duk hankalinmu ya tashi wallahi.""" "Yace.""Nima bata fad'a min saboda tana da iko da kanta na dawo daga kasuwa na sameta a can."" Halisa" "tace""Ikon Allah."" Yace.""Ganinan shigowa yanzu."" Cikin kissa tace""Allah ya kawo ka lafiya."" Kashe wayarsa yayi a mayar aljihu ya cigaba da draving dinsa Naja'atu taji ciwon yanda ya banzatar da ita" "tana ganin ai kamata yayi ya rarrasheta tunda ita akayiwa laifi amma saboda bata da wata daraja a gurinsa laifinta ma yake gani Itama sai ta dinga kauda kanta tana kallon hanya, tana kuma kokarin" mayar da hawayen dake so ya zubo mata. Dai dai asibitin Hasiya bayaro yayi parking ya fito ya tsallaka titi naga ya nufi wani ke'bantaccen gurin "gasa kaji da sauransu ya jima a ciki kafin ya fito hannunsa rike da ledoji masu dauke da sunan gurin, tana ganin zuwansa ta juyar da kanta ya bude motar ya shiga ya zaune, 'kin juyowa tayi har ya tayar da motar suka bar gurin fuskarta na kallon hanya sai zumbura baki takeyi, a haka sukaje gidan babu wanda" ya kula dan uwansa. "Yana parking ta bude motar tayi gaba, ya girgiza kansa tare da fitowa daga motar yabi bayanta da ledojin" a hannunsa. Halisa da yaran suna zaune a palo suna kallo kamar dai koda yaushe yaran suka iske inda yake suna "masa sannu da zuwa, mussadiq ya kar'bi ledojin hannunsa yana kokarin kai masa daki, yace.""Bani guda d'aya sauran naku ne kowa ya dauki daya."" Mussadiq yace.""Mungode Abbah."" Mussadiq Ya mikawa kowa nasa, Halisa kuwa mi'kewa tabi bayansa dakin." Naja'atu kuwa dama data shigo gidan babu wanda ta kula kai tsaye daki ta nufa..tana jin wani irin kunci "na dawowarta gidan a duniya ta tsani ta budi ido ta ganta a gidan ji take tamkar tana kurkuku! Mussadiq ya shiga dakin da ledarta a hannunsa a sanyaye yace.""Yaya Naja'atu ga naki."" Girgixa kai tayi tace''Jeka hada ka cinye naci abinci gidan hajiya."" Yace.""Yaya Naja'atu gidan Hajiya kikaje me yasa bakije dani ba.""? Murya na rawa tace""Ka bari idan zan sake zuwa zai je da kai."" Yace.""To nagode amma dan Allah ki kar'ba kici ni ba zan iya cinyewa duka ba."" Tace.""To ka ajiye gobe sai ka tafi dashi skull."" Yace."" Uhum!uhm ni dai nafi so kici hankalina zaifi kwanciya."" Kar'bar ledar tayi ta bude tana dubawa, taga gashashiyar kaza da sauran kayan ciye ciye. Tace""To zauna muci tare."" Yace.""To bari na dauko nawa."" Da sauri ya fita" daga dakin. "Halisa kuwa cikin kissa da kisisina ta dinga bugun cikin Abbah Abbas din, saboda tana so tasan dalilin da" "yasa yarinyar tafiya gidan Hajiya, shi kuwa ba tare da tunanin komai ba ya fada mata dalili Ta ri'ke" "bakinta tana jimantawa tace""Amma gaskiya yarinyar nan bata kyauta ba, yanzu kamarka zata kai 'kara gurin hajiya! hummm! gaskiya ta bani mamaki kuma a yanda kake kauntarta da nuna kulawarka a kanta bai kamata tayi maka hakaba, kuma wallahi karya take Yaya Ramlatu bata doketa ba sharri kawai tayi mata! dan haka kada ma kace zaka tunkari Yaya Ramlatu da wannan maganar idan haka ta kasance Yaya Ramlatu zataga kamar kafi kaunar matarka a kanta kuma kasan karfin zumunci yafi gaban a hadashi da" "komai. ni a ganina yarinyar zaka hukunta ba wai ita Yaya Ramlatun ba.""" "Yace.""Koma dai menene insha Allahu ya kusa zuwa karshe, sannan bana daukar wasu abubuwan da" yarinyar nan take da zafi dan saboda nasan akwai karanci shekaru a tare da ita gaba kadan idan ta kara "hankali ba zatayi ba. Ta'be baki tayi tace""Babu wani kuruciya tsabar iskanci ne wallahi.' Ajiyar zuciya ya" "sauke ya kalleta da fad'in ""ki duba cikin rigar dana cire ki dauki key din motarki."" Halisa ta ru'kun'kume shi tana dariya."" Shima dariyar yake yana mamakin murnar da take, Halisa ta dauko key din tana ta washe bakinta, mikewa yayi yace.""Gobe zan kaiki ki d'auko motar a inda na siya miki."" Tace""To nagode sosai Allah ya saka da alkairi."" tare suka fito daga dakin, ya zauna a gurin cin abinci Halisa ta had'a masa abincin data girka wanda ta barbade shi da maganin mallaka, shi kuwa kamar koda yaushe yayi bisimillh" sannan ya soma cin abincin ba tare da ya kawo komai a cikin ranshi ba. Naja'atu kuwa bayan sun gama cin abinci da Mussadiq wanka tayi tasa doguwar riga mai botira ta gyara "gashinta hula tasa sannan ta dauki hijabinta tasa ta nemi guri ta kwanta, abinda duniya ya isheta, 'yar wayar dake d'ebe mata kewa babu, ita kuma ba zata fita palo ta zauna a cikinsu ba tasan a irin wannan lokacin yana zama a palon tare da yaransa, fuskarsa ma bata son gani gabadaya wata irin tsanarsa takeji a cikin zuciyarta. Bacci ne ya soma fizgarta taji shugowar yaran zasu kwanta zaune ta mike tana kallon" "Mussadiq yana kokarin daukar pillow tace""Zo ka kwanta a gadonka."" Sauka take kokarin yi. Yaron ya" "ajiye pillow a kasan kafet kamar yanda yayi jiya yace.""A'a Yaya Naja'atu ki kwanta ke.""" "Tana kokarin yin magana Mufida ta shigo tace""Yaya Naja'atu wai kije inji Abbanmu."" Taji wani fad'uwar" "gaba ya rikota mata, tace""Yana ina.""? Yarinyar na kokarin sa kayan baccinta tace''Yana palon."" Ajiyar zuciya ta sauke taji dadi ai ta dauka yana dakinsa ne shiyasa gabanta faduwa." "Kai tsaye palon ta nufa. Loptop ta sameshi yana dubawa Ta dan tsaye daga nesa da fad'in ""Abbah gani.""" "Ba tare da ya kalleta ba yace.""Zo ki zauna muyi magana."" Jim! tayi kafin taje ta zauna!" "Cigaba yayi da duba loptop dinsa ya bawa banza ajiyarta. Tace""Abba ina jinka zanje na kwanta."" Shuru" "yayi mata ya cigaba da abinda yake, sai kawai ta yunkura zata mike. ya dago tare da kwatsa mata tsawa yace.""Idan kika tashi sai na 'bata miki rai a gurin nan."" Da sauri ta koma ta zauna tana kallonsa..Gani tayi yayi kicin kicin da fuska ya rufe Loptop din ya juyo yana kallonta, lokaci guda taji gwiwarta tayi sanyi Abbah Abbas nada masifar kwarjini mutukar ka hada ido dashi Yace.""Wa kika tambaya kika fita.""?" "shuru tayi tana kallonsa. Cikin wata tsawar yace.""Ba magana nake miki ba.""?" "Baki na rawa tace""Babu kowa na fita daga gidan ne domin a ganina kamar hakan shine yafi alkairi.''" "Yace.""Saboda baki san meye aure ba shiyasa kike fad'ar haka ko? shuru tayi tana jin wani gumi yana" tsatstsafo mata a jikinta. Ya cigaba da cewa''Saboda baki da kirki kamar ni zaki kai 'kara gurin Hajiya to "me kike tunanin zai faru dan kin kaini 'kara.""?" "Shiru tayi yace.""Naja'atu ban ta'ba tsammanin haka halinki ba sai yanzu gabad'aya na gane baki kaunata" "bakya kuma kaunar zama tare dani shin bakya tunanin aurena shine alheri a tare dake! me nayi miki kike nuna 'kiyayyarki 'karara a kaina.""" "Hawaye suka zubo mata tace""Abbah har abada bana 'kinka kawai dai na fad'a maka tun farkon al'amarin" "nan ni ba zan iya rayuwar aure da kai ba.""" "Yaji wani d'aci! a magwaronsa, da kyar ya had'iyi yawu yace.""Why! Naja'atu Why! meye laifina? wane" "aibu ne dani me narasa na mazantaka da bakya sona.""!! Tace""Abba da zan iya tursasa zuciyata ta soka da tuni na tursasata kodan iyayena su samu nutsuwar da suke bukata sai dai kash! bani nake da zuciyata ba itace take dani Abbah nayi nayi na sama maka gurbi a cikin zuciyata na kasa, kullum kamar ana 'kara" "mata 'kiyayyarka haka nake ji a zuciyata.""" Wannan maganar ta soke shi sosai da sosai kuma bai ta'ba tsammanin yarinyar zata iya kallon tsabar "idonsa ta furta masa kalmar 'kiyayya 'karara ba! sosai ya fusata! yarinyar ta kaishi bangon ma'kurar 'bacin rai! ya mi'ke da jan ido loptop din ya ajiye saman kujera ya tsaya kanta yayi mata rumfa, sai gabanta ya tsananta fad'uwa! ta tsira masa ido le'banta na rawa! so take tayi magana amma ta kasa, hakika yanayin data ganshi yayi masifar firgitata, kafin tayi aune ya dauke ta ya sa'ba a kafad'arsa ya" ri'keta sosai saboda kada tayi zillo! hanyar dakinsa ya nufa ita Wani mahaukacin ihu! ta kurma!! tare da dunkule hannunta tana dokansa a bayansa. Ihunta! yasa "Halisa ta fito daga dakinta a guje! sai dai bata samu nasarar ganin kowa a palon ba dan tuni sun shiga dakin sai saurin rufe kofar taji, da sauri ta kalli kofar dakin Wani irin takaici ne ya turnuketa tsaki taja" ta nufi dakinta. """Abbah dan Allah kayi hakuri iya gaskiyata na fad'a maka bana jin zan iya mallaka maka wani abu nawa" tuntuni na fad'a maka maslaha a garemu ga sawwake min dan gaskiya ba zaka ta'ba jin dadin zaman aure dani ba tunda bana sonka. surutan da takeyi kenan tana zillo hade da dukan bayansa da hannayeta. "Fitilar dakin ya kashe kai tsaye ya nufi bed din da ita, kwantar da ita yayi! da sauri tayi yunkuri mikewa" "zaune, ya d'ora mata nauyinsa! gabad'aya ya sakar mata jikinsa a jikinta yana fitar da wani irin numfashi na tsantsar bakin ciki da 'bacin rai! shin ta ina zai fara ne? Gabad'aya ji yayi kansa ya kulle! Maganganun yarinyar sunyi masifar kassara masa gabobin jikinsa...Kuka ta dinga yi tana janyo numfashi da kyar!" "Abbah ya danneta sosai ta kasa katabus! sai da ya tabbatar ta galabaita sannan ya dan daga ta, kai tsaye duguwar rigar jikinta ya fara kokarin cirewa, ta dinda rirrike hannunsa tana masa magiya, ko sauraranta baiyi ba ya cire rigar ya jefar dama bata sa breziyya ba, da sauri tasa hannu ta rufe breast d'inta tana kuka gami da tureshi da kafafunta. Hakan bai dameshi ba, kawai ya dora hannunsa kan pant din" "jikinta yaja da mugun karfi, pant din ya yage a take ta kankame jikinta tana ihu! da hannunsa ya tura ta ta fadi saman gadon kawai ya d'ora hannunsa a gabanta yana laluben ramin! Ta dinga wani irin abu kamar zata shid'e tana kiran innalilhi wa'ina ilahi raji'un! cinyoyinta sai kyarma suke Baiyi mata da" sauki ba dan yana samun nasarar samun ramin ya tura d'an yatsansa na tsakiya da karfin gaske! Sai kawai ta zube kan bed din tayi lakwas tana makyarkyata da kiran sunan Allah wani irin zafi taji yana ratsa mata jiki Wasa ya shigayi da hannunsa a gurin yana kokarin bud'e hanyar ita kaman ai ta riga ta gama galabaita sai karkarwa jikinta yake tana kuka. Hannunsa ya zare daga ciki Ya cire jallabiyar jikinsa hade da gajeran wandon yayi tik! gabadaya ya tattarota ya rungume a jikinsa yana sakar mata wasu zafafan kesses masu hautsina lissafi!. Jin fatar "jikinsa na gogar tata sai ta sake shiga rudani! ta samu gefan wuyansa ta gartsa masa cizo tana kuka! a maimakon hakan da tayi ta kwaci kanta sai ma ta sake ingizashi, ya kai bakinsa kan Brest dinta da shiga sha yana tsotsar nipple d'in yana ta sauke wani gawurtaccen numfashi Duk da tana jin dad'in abin bai" "hanata dukansa ba tana yakushi da Allah ya isa, dan yanzu ta daina yi masa magiya da hadashi da Allah" jefansa kawai take da munanan kalamai saboda bata da kunya. "Ba dan ransa yaso ba ya cire bakinsa dake kan brest din ya mayar kan bakinta, rufe mata bakin tsiwar" yayi ya shiga sarrafashi yanda ransa yake so Al'amarin yafi karfinta sai tayi lakwas dan gabadaya jikinta ya mutu banda hawaye babu abinda take. Yana kissing dinta baki da baki yana sake ya mutsa "mata jikinta da salon soyayyarsa har ya samu tayi sanyi ta saduda damar da ya samu kenan ya dinga wasa da gabansa a gabanta a har Allah ya bashi sa'a ya shigeta, wanda kafin ta bar hakan ya kasance sai da ta wahalar dashi mutuka amma dai ya samu nasarar huda jikinta ya shiga sosai inda ita kuma ta kama joystick dinsa ta ri'ke tamau da padlock d'in jikinta! ya wani gigice! ya d'imauce jinsa a cikin wata duniya ta mussaman yasa ya kusa zaucewa, ya dinga aiki babu ji babu gani dan gabadaya ma ya manta cewar da yarinya kankanuwa yake wacce bata san kan harkar ba! Bugunta ya dingayi yana sakin nishi da ajiyar zuciya!! Naja'atu daina kukan fili tayi sai na zuciya dan gabadaya kasa tantance a inda take tayi azabar ta isa har tayi yawa, Abbah Abbas yaki sassautawa ta ko wanne fanni yanayi yana shan bakinta da breast" dinta duk ya zama sakarai komai nata ya zama abin so da rububi a gurinsa. *To Yau fa Naja'at taji maza bari muga bakin rashin kunya zai mutu ko kuwa! * *Littafin na kudi ne...!* Koda zaki ganshi a gruops to na sata ne idan kina so ki biya kudin karatu ga yanda abin yake. VIP Group #600 Normal #300 Account: 0542382124 Binta Umar gtban..Idan katin waya zaki tura sai kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* BHRBN *30* "Yana ganin Dr Sa'adatu ta fito daga dakin, sai ya mike yana kallonta, kai kana kallon yanayin daya nuna" "zaka fahimci cewar yana bukatar karin bayani daga bakinta, Dr Sa'adatu tayi murmushi cikin nutsuwa tace""Yallabai ka kwantar da hankali amarya bata ji ciwo ba kamar yanda kake tunani, lafiya gurin yake amma dai duk da haka yanzu zamuje pharmacy da kai akwai magungunan da zata d'ansha zasuyi dauke mata rad'idi da zugin da gurin yake mata.""" "Ajiyar zuciya ya ajiye yace.""To alhamdulilalhi bari na dubata na fito."" Dr tace""To babu damuwa.""" "Fuskarta dauke da murmushi ta samu Guri ta zauna tana kallonsa ya nufi dakin, sai taji tana sha'awar ina ma itama takasance a matsayin matarsa, dan ta lura shi din mutum ne shi mai tsananin kula da iyalinsa ta kowanne bangare, addua tayi a matsayinta na bazawara kan Allah ya bata miji kwatankacin" sa. "Naja'atu kuwa bayan fitar Dr daga dakin, zanin jikinta ta kwance ta bude cinyoyinta gabad'aya ta d'an" "zame pant d'inta ya sauka dai-dai cinyoyinta a hausarta wai gurin ta bude yasha iska a ganinta rufewar da tayi shine yake sanyawa yana k'ara yi mata zafi Aikuwa yana shigowa da abinda yayi tozali kenan," Tsigar jikinsa ce ta wani tashi sai yayi Saurin kauda kanshi jiki a mace ya 'karasa bakin bed din ita kuwa sai jan zaninta take tana kokarin rufewa had'e da dauke kanta sam bata san kallon fuskarsa. Ya "jima a tsaye a kanta yana kallonta tana ta kici-kicin jan zani ta rufe sai ya sunkuya yayi mata rumfa numfashinsu ya dinga had'uwa! goshinta ya sumbata cikin taushin murya yace.""Sannu kinji ko zai daina yi miki zafi insha Allah! kuma naji dadi sosai Dr tayi min bayani cewar baki samu matsala ba yanzu zamuje tare da ita domun a kawo miki magani wanda zai taimaka miki gurin dauke zafin da gurin yake. Ba tace masa uffan ba sai ma wasu hawaye da suke kokarin zubo mata, sam bata so tana sha'kar" "numfashinsa gashi ya wani sunkuya mata a jiki....Jin bakinsa tayi kan le'bunanta yana lasa da harshensa," tayi gaggawar juyar da kanta tana jin mugu-mugun mamakin abinda yake mata gaba'daya ma ta lura dashi ya manta matsayinsa a gurinta abinda ya ga dama shi yake yi. "Tsayuwarsa ya gyara yana kallonta da idanunsa da suka soma risinawa yace.""Me kike so na kawo miki" "kici nasan dole kina bukatar abinci.""" "Uffan ba tace masa ba...Yace.""To tunda ba za kiyi min magana ba idan na dawo zan maimaita abunda" "nayi jiya ."" Tayi saurin kallonsa bakinta na rawa! girarsa ya daga mata yana so ya tabbatar mata da maganarsa. da kyar tace""Koma me ka siyo zanci dan Allah kada ka kuma wani abu dani zan iya" "mutuwa."" Yayi murmushi yana shafa gemunsa had'e yi mata kallon 'kasa-'kasa yace.""Bana jin zan iya yi miki alkawarin abinda kike so yana da kyau ki zama jaruma mai daukar ko wacce irin lalura wannan" "abun ba zai sanya ki mutu ba sai dai ma ya 'kara miki lafiya.""" Wannan maganar da yayi tasa taji wani tsoronsa ya shigeta Murya na rawa tace Dan Allah kayi hakuri "kada ka 'kara yi wallahi ba zan iya ba."" Tausayi ta bashi ganin har ta soma hawaye kuma ya hango tsantsar tsoronsa a kwayar idonta, sai yace.""Daina kuka ba zan sake ba shikkenan ko."" Tace""To ka rantse da Allah."" Maganar sai ta bashi dariya yace."" Ba sai na rantse ba tunda nayi miki alkawari shikkenan ki" "kwantar da hankalinki ki daina kuka.""" "Kanta ta shiga d'agawa tana kallonsa wai so take ta tabbatar da gaskiyar maganarsa, shi kuwa hularsa" "dake saman kansa ya gyara ya kama hanyar fita daga dakin tare da fad'in ""Sai na dawo ko."" Kallo tabishi dashi tana jin tsana da tsoronsa na sake 'karuwa a cikin zuciyata, hakika da tana da inda za taje ta fake" to data gudu gabad'aya sun nemata sun rasa... "Halisa da Dr din ya samu a palon suna hira, yana fitowa Halisa ta kura masa ido zuciyarta na tafarfasa!" "Shi kuwa nan da nan ya daidaita nutsuwarsa cikin dakewa ya kalli Dr Sa'adatu da fadin ""Muna iya tafiya yanzu.""" "Dr ta kalli Halisa tana dan murmushi tace""To madam Allah ya bamu alkairi."" Ciki ciki tace""Okey."" ya" "kalleta tare da karantar yanayin da take ciki, yace.""Zan dan futa sai na dawo."" Iskar da yake ma bata" "kalla ba dan wani irin mugun haushinsa takeji ganin yanda yake ta wani rawar jiki ko maganar zuwa kasuwa ma bayayi.""" "Suna fita ta mike ta nufi dakinta, ta dauki wayarta ta shiga sanarwa da Yaya Ramlatu halin da ake ciki.""" "Yaya Ramlatu tace""Halisa ki rabu dani naji da bakin cikin dake damuna! Halisa tace""Me ya faru dake Yaya.""?" "Yaya Ramlatu tayi 'kwafa! cikin tsabar bacin rai tace""Mutsiyaciyar yarinyar nan Naja'atu itace ta kai" "'karata gurin Alhaji da Hajiya yau da safe sai ganin d'an aike nayi, koda naje gidan Alhaji baiyi min da sauki ba rufeni yayi da fad'a sosai hajiya har da cewa duk sanda na sake zuwa gidanku bata yafe min ba.'" "Halisa tace""Lallai al'amarin Malam Baba yayi tsanani! to nima nan a cikin matsala nake dan gabadaya na" "kasa gane kan maigidan tun jiya daya kwanta da yarinyar ya zama sakarai sai rawar jiki yake yi yama kasa zuwa kasuwa gabadaya ya lalace a gindin yarinyar. Yaya Ramlatu tace""To ke yanzu wane mataki zaki" "dauka dangane da faruwar hakan.""? Halisa tace""Kawai so nake na samu malamin da zaiyi min aiki akansa" "gabad'aya a zare masa sha'awarta a zuciyarsa ko kuma idan yaje zai sadu da ita gabansa ya mutu ya'ki aiki.""" "Yaya Ramlatu tace""Wannan aikin ba mai wuya bane mutukar zaki futo da kudi ni kuma zan baki goyon" baya dan nima abinda yarinyar tayi min yasa gabadaya na sake tsanarta. "Tace""Wallahi idan zan samu malamin da zaiyi min wannan aikin ko nawa ne zan biyashi."" Yaya Ramlatu" "tace""Shikkenan yanzu zan kira 'Yar shagamu a waya zan fad'a mata duk abinda ke faruwa, nasan zata kaimu inda bukata zata biya."" Halisa ta sauke ajiyar zuciya tace ""To sai naji daga gareki Yaya Ramlatu nagode."" Sallama sukayi da juna kowanne ya kashe wayarsa cike da mugun nufi" "Bayan fitarsa daga dakin bacci mai nauyi ne ya dauketa, sai ji tayi ana shafa mata tafin kafafunta had'e" shara'bar 'kafafunta. Bude ido tayi da sauri ganinsa zaune dab da ita yasa ta zabura! da sauri zata mike zaune! ya ri'ke "hannunta cikin lafazi mai dadi yace""yi hankali kisa nutsuwa kada ki fama ciwon naki."" Maganar tasa yasa ta tuna abinda ke da akwai." A hankali ta saukar da kafafunta kasa tana so ta mike tsaye ya kama hannunta suka mike tare. kamar me koyon tafiya suka nufi toilet brush tayi suka fito tare. zama tayi gefan bed tana jin yanda cikinta ke murd'a mata yunwa takeji sosai Idonta ne ya sauka kan ledar Osis daya shigo dashi. dauka yayi ya "mika mata da fadin""kici abinci sai kisha magani ko.""" "Kar'ba tayi tana kokarin sauka kasan kafet, shi kuma sai ya shiga duba maganin da Dr ta bashi abinci" "taci sosai ta had'a da lemo mai sanyi lokaci guda ta dawo cikin hayyacinta. ganin ta samu nutsuwa sai ya mika mata maganin da ruwan dake hannunsa, kamar zata fashe da kuka ta kar'ba tana jujjuya maganin a hannunta, a rayuwarta ta tsani had'iyar 'kwaya. Yace.""Kisha mana kin tsaya kina kallonsa."" 'Daya bayan d'aya tasha maganin tana wani ya mutsa fuska." "Ya dan sassauta murya wanda idan ba ita d'in ba babu me ji yace""Yanzu sai shiga ruwan zafi ko.'' ?" Tsintar kanta tayi da kallonsa domin ita wallahi abinda yake mata mamaki yake bata tsakanin jiya da yau duk ya sanja magana ma idan zaiyi mata da wata irin murya ta mussaman yake mata babu abinda yake bata haushi dashi sai munafikin kallon da yake mata ta 'kasan ido......kawai ta shiga bin bayansa da kallo a lokacin da yake kokarin shiga toilet din. "Minti goma ya fito yana kallonta yace""Zo muje ki shiga ko."" Ta mike a hankali dan itama tana so ta shiga" ruwan zafin ko ta samu saukin wani abun. "Ya nufeta yana tattare hannun rigarsa yace""Ki cire kayan jikinki sai ki daura towel sai kinfi sakewa."" Kafin" tace wani abu ya sata a jikinsa yana kokarin kwance mata zani! "Da sauri tace""Zan iya cire kayana dan Allah kyaleni.""" "Girgixa mata kai yayi ya cigaba da kwance daurin da tayiwa zanin jikinta yanayi yana sumbatar wuyanta," ji tayi tsigar jikinta ta soma tashi sakamakon gemunsa da yake goga mata fatar jikinta. Jin yana kokarin cire zanin gabadaya yasa ta dan ture fuskarsa dake wuyanta ta matsa gefe tare da jan "zanin saman kirjinta ta daure! sosai sannan ta cire rigarta sai ta kwance dankwalin dake kanta ta rataya a wuyanta, kai tsaye toliet din ta nufa ta barshi a tsaye a gurin Ya dan jima a tsaye a inda yake yana" kokarin saisaita kansa kafin ya samu gefen bed din ya zauna yana jiran fitowarta. Tunda ta fito yake "mata wani irin kallo na ma'kurar kurrula. ita kuma ji tayi kafafunta na rawa gabanta kuma na faduwa, ta" "dauka ya gaji da jiran fitowarta ya fita daga dakin, shiyasa ta share kusan mintina ar'ba'in a ciki ashe yana zaune bai fita ba." Kamar ta koma toilet din haka taji sai dai ta daure ta ta nufi bed din domin daukar rigarta tasa. hannunta ya fizgo da karfi sai kawai ta fada kansa! ya wani matseta sosai a jikinsa yana ya mutsa mata jiki Kuka take tana kokarin mikewa yana sake matseta hade da so ya kwance zanin dake daure a "jikinta. Tace""Abbah dan Allah kayi hakuri dan Allah kada ka sakeyi min irin na jiya ka duba 'kan'kantata" "ba zan iya ba.""" Bakinsa yasa a kunanta ya shiga tsotsa yana hura mata iskar bakinsa! lokaci guda jikinta ya rikice ta dinga "kyarma tana kiran sunansa, wannan soyayya ta Abbah Abbas ta mussaman ce kuma babu shakka Naja'atu karonsu na farko dashi ta tabbatar da cewar lallai maza ma suna suka tara. Gabadaya Abbah" Abbas bai bar mata komai a jikinta ba sai da yayi mata haihuwar uwarta tukkuna hankalinsa ya kwanta ya shiga sarrafa albarkatun jikinta mussaman breast dinta da sukayi masifar tsone masa ido sha yake hade da murzasu tamkar zai tsinke mata nippels. Sun dauki kimanin mintina ar'ba'in cikin wannan yanayi kafin ya samu da kyar ya samu satisfaction duk ya 'bata mata jikinta da uban sperm dinshi mai yawan gaske "Tana kuka tana komai ta mike zaune da kyar tana duban jikinta, wannan abin da ya zuba mata a jikinta" yayi masifar bata haushi wannan ai kazantace! kamar ta rufeshi da duka haka ta dinga ji. "Juyawa tayi ta ganshi yayi rashe-rashe a bed din yana fitar da wani irin numfashi, ga katuwar joystick" dinshi a tsaye kyam tana kallon rufin dakin Cikin gigita da mugun tsoro ta tashi daga gurin hannunta rike da zaninta da ya cikwikwiye tana kokarin daurawa a jikinta ta kama hanyar futa daga dakin tamkar wata zautacciya!! ta'bdijam! ai ba zata zauna ya turmushe da wannan katuwar abar tasa ba. Tana fita "sukayi ido hudu da Halisa dake zaune a palo tana kallo..Halisa ganin yarinyar ta fito daga dakin a gigice yasa ta bita da wani irin kallon mamaki! ikon Allah ashe yana nan bai fita ba, ita wallahi duk daukar da takeyi ya fita tunda ta dade zaune a palon ba taji motsinsa ba..Naja'atu na shiga dakinsu Saddiqa sai ta" mike cikin zafin zuciya ta nufi dakin nasa. "Kwance ta same shi da ido a rufe, Allah yasa ya rufe jikinsa da bargo amma dai duk da haka tana ganin" girmansa ya bayyana da alama yarinyar wuya taji yasa ta fece ta barshi! koda yake itama lalla'bawa take dan har yanzu bata dawo normal ba """Abbah Mufida lafiya kuwa.""? Jin muryar Halisa yasa ya bud'e idonsa da sauri! halin da yake ciki yasa ya" kasa magana sai kawai ya fizgota ta fada samansa...Halisa a gigice ta fizge jikinta gabanta na fad'uwa! ina zata yarda ya sake ragargazata bata huce ba tukkuna! "Ya bita da wani irin kallon sha'awa da fadin"" Halisa ina cikin yanayi na bukatar taimakon ki."" da sauri" "tace"" Gaskiya babu abinda zan iya yi maka dan nima ba wai na gama jin dai-dai bane so kawai ka kira amaryarka ka biya bukatarka."" Da sauri ta kama hanya ta fita daga dakin, duk san sex da take da kuma son ta kuntatawa Naja'atu ba zata bari ya hau kanta ba tasan yanda yake a rikice haka idan ya hau to saukarsa sai abunda Allah yayi. shiyasa tana shiga dakinta tasa key ta barshi a jiki domin tana tunanin zai iya biyo ta. Abbah Abbas ya mike cikin tangadi kamar wani bugagge ya nufi dakin Halisa dan a ganinsa" "itace kadai zata iya dashi sai dai me key yaji a jikin kofar ya dinga murza key din dakin yaki budewa, ransa a bace ya nufi dakinsu Saddiqa babu yanda zaiyi dole ya sauke bukatarsa kan yarinyar idan ba" hakaba zasu iya yin asararsa dan baya jin zai iya kaiwa dare a raye... "Allah sarki naja'atu tana takure a kuryar gado taga ya shigo dakin, sai ta mike zumbur tana kallonsa......" Ya mayar da kofar ya rufe da key kai tsaye ya durfafi inda take. Ihu! ta dinga kurmawa!! tana bashi hakuri! malam bahaushe yace wanda yayi nisa baya jin kira Abbah Abbas kama 'yar mutane yayi ya turmushe ya shiga biyawa kansa bukata.. *Littafin na kudi ne..!* Koda zaki ganshi a gruops to na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu to ga yanda abin yake. VIP#600 Normal#300 Account: 0542382124...Binta Umar gtbank.. Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* Mdd *29* Abbaha Abbas gabad'aya ficewa yayi daga cikin hayyacinsa sakamakon jinsa a cikin wata duniya ta "mussaman duniyar da bai ta'ba riskar kansa a cikinta ba, hakika yanzu ya tabbatar da cewar ko wacce mace da irin baiwar da Allah yayi mata Naja'atu tana da baiwa ta mussaman wacce ba ko wace mace keda irinta ba Yarinyar ta gamsar dashi fiye da tunaninku, duk da kasancewar ya samu cikakkiyar gamsuwa a tare da ita sai ya kasa zare jikinsa daga nata, yana jin yanda joystick din nasa ke sake mi'kewa a cikin jikinta tana sake nuna masa da cewar bata k'oshi ba, sai ya dan motsa jikinsa yayi kamar zai zare joystick kawai sai yaji kamar an ri'ke masa shi a gurin, ya saki wani irin nishi yana lumshe idonsa!! wai shin me ya ri'ke shi ne? wanda yasa ya kasa fita daga ramin yabi nane a jikin 'yar mutune sai kace cingum! Shi kansa mamakin kansa yake so yake ya cire amma ya kasa saboda shi kadai yasan irin zumar da yake ji a cikin jikinsa......sake motsawa yayi ya dafa bed d'in da duk hannuwansa kamar zai cire sai ya kasa" kawai ya cigaba da aiki Naja'atu ta rirri'ke damtsensa tana ihu! na fitar hankali da kiran sunan "iyayenta da sunan Yaya Halimatu....Girgiza kansa kawai yake yana cizar lips dinshi yana ganin babu abinda zai dakatar dashi daga abinda yake yi dan shima shi kadai yasan halin da yake ji a cikin jikinsa bayan haka kuma yana ganin kamar laifin sa bane tunda itace ta ri'ke masa joystick ta'ki sakinsa..........Wannan al'amari dake faruwa a tsakaninsu yafi a gaban a had'ashi da komai! Naja'atu ta sadakar da cewar karshenta ne yazo dan yanda take jin joystick din Abbah Abbas din har cikin cikinta dalilin da ya sanya kenanan wani mahaukacin amai ya dinga taso mata, ta dinga rirri'ke cikinta tana tureshi yana sake danneta da bugunta, duk ya had'a zufa!! shima ya k'agauta ya samu satisfaction" shiyasa ya maida hankali sosai dan ganin bukatarsa ta biya. Yana bugunta tana yunkurin amai! duk da ya fahimci halin da take ciki hakan bai sa ya daina abinda yake ba. Sai da ya tabbatar da ya samu cikakkiyar gamsuwar da yake bukata sannan da sauri ya zare jikinsa dan baya so ta sake kulleshi kamar yanda tayi masa da farko "Cikin mawuyacin hali ya sauka, tayi wani irin yunkuri sai amai ya wanke masu jikinsu da shimfidar gadon," "Cikin rashin kuzari ya lalubi jallabiyarsa yasa ya mika hannu ya kunna bedlamp nan yaga aika aikar da yayi gabadaya shimfidar gadon tayi kaca-kaca da amai da jinin budurcin Naja'atu da yayi fatata fatata dashi!! Idanunsa ya rintse! yana kiran sunanan Allah! Ya bude da sauri jin tana wata iriyar sha'kuwa! kafin ma yayi wani yunkuri ta bingire a gurin.! A gigice ya tallafota yana kiran sunanta, bakinta a bude" idanunta a lumshe numfashinta sai fita yake da sauri da sauri ga zuciyarta sai bugawa take. Ya mike a jigace! ya nufi fridge ruwa ya dauko ya bude tare da tallafota ya shiga shafa mata ruwan a "fuskarta da jikinta, yana shafa mata ruwan yana tofa mata addua gabadaya nadama da tausayin yarinyar ne suka lullubeshi, hakika yasan shi kansa ya aikata abinda ba shikkenan ba, amma ya ya iya da abinda yafi karfinsa shima yana ganin kamar ba laifinsa bane nata ne tunda ita ta ri'ke shi! shiyasa gabad'aya ya" kasa sarrafa kansa da tunaninsa kawai ya dinga biyewa zuciyarsa da abinda take so. Ya jima rungume da ita yana dan shafa mata ruwa had'e da tofa mata adduoi cikin ikon Allah ta daina "abinda takeyi, jikinta yayi wani irin sanyi sai uban hawaye dake zurara daga idonta" Kamar 'kwai haka ya kwanta da ita ya mike cikin tararrabi gami da kunyar abinda ya aikatawa yarinyar na "rashin imani ya nufi toilet ya jona ruwan zafi a kettle yana tsaye ruwan yayi ya juye ya sake sa wani, ya fita daga toilet din, tana kwance kamar gawa babu abinda yake motsi a jikinta haka yaje ya tarairayota ya nufi toilet din da ita yana me tsirawa fuskarta ido, hakika yarinyar ta bashi tausayi sosai da sosai Koda ya sata a cikin ruwan zafin bata motsa ba sai ma sake bud'e kafafunta da tayi tana jin" "yanda ruwan ke ratsa mata jikinta, har yanzu ta kasa tsayar da hawayen dake zubo mata." Hankalinsa gabadaya na kanta ya samu yayi wankan tsarki ya fita a gurguje ya sanyo kayansa ya dago toilet din Sai kawai ya tarar da ita tana gyangyadi a cikin bawon alamun sun nuna ta dan samu "sassaucin abinda takeji Ya sanya hannu ya dagota, ta bude idonta da sauri tana kallonsa, ganinsa yasa" wasu masifaffun hawaye na tsantsar takaici da bakin ciki suka kufce mata. kafafunta suka shiga kyarma "tana nema ta koma cikin ruwan, ya rungumeta yana lashe hawayen dake zuba daga idonta, cikin wata iriyar murya da bai san shi kasa yana da ita ba yace.""Ki garface ni Naja'atu."" Bude idonta tayi da sauran kuzarin da ya rage mata ta tureshi daga jikinta ta kama hanya zata fita, yayi saurun rike hannunta a sanyaye yace.""Komai kikayi dai-dai ne amma kada ki fita baki tsarkake jikinki ba.""" "Tsayawa tayi tana shakar hanci! shi kuma ya wani tsirawa bayanta ido, ji yayi yana nema ya fad'i" sakamakaon Kallon kurrular da yake mata. Ya jawo hannunta hade da tsugunar da ita gaban ruwan "wankan da ya tanadar mata yace.""Kiyi wanka idan ba zaki iya ba sai na taimaka miki." Ba tare da tace komai ba ta dauki niyya a zuciyarta ta shigayin wankan tanayi tana kukan bakin ciki Abbah Abbas ya samu galaba a kanta ya rabata da budurcinta yanzu me zata cewa da Salim! idan ta tuno wannan al'amarin sai taji tamkar ta mutu ta huta da bacin rai. Towel ya mika mata bayan ta gama wanka ta dinga kokarin daurawa ta kasa saboda bata da kuzari sai ya "karba ya daura mata, ya dauketa suka fita daga dakin Dama ya cire bedshirt din yasa wani sai ya" "kwantar da ita a hankali ya rufe mata jikinta da bargo kana ya dauke bedshirt da ya 'baci ya nufi toilet dashi, kasancewar dare ya shiga sosai yasa ya bari da asubah ya wanke, alwala ya dauro ya fito har ya tsaya kan dadduma sai kuma yaje ta tsaya bakin bed din yana kallonta, Allah sarki Naja'atu bayan shigarsa toilet din bacci ne mai nauyi ya dauketa. Ajiyar zuciya ya sauke ya koma kan daddumar ya tada" sallahr nafila kamar yanda ya niyya ta. Bayan ya idar da sallar nafilar ya jima hannunsa a sama yana rokon ubangiji Allah ya sassautawa "yarinyar zuciyarta tayi hakurin zaman aure dashi, hakika yanda yake jinta a cikin zuciyarsa a halin yanzu yafi gaban kwatance, baya ta'ba tsammanin akwai abinda zai iya rabashi da ita shi dai babban burinsa shine yarinyar ta hakura ta zauna zaman aure dashi na har abadah Bai tashi daga gurin ba sai da yaji" ana kokarin tayar da sallahr asubahi sannan ya nufi massalaci domin gabatar da sallah Koda ya dawo kai tsaye dakin nasa ya nufa domin gabadaya hankalinsa nakanta nan ya tarar da ita tana ta bacci ya dan gyara mata kwanciyarta kana ya fita. Dakin yaransa ya nufa ya tarar dasu sun tashi sunata shirye- "shiryen makaranta, ya tsaya ya gaisa dasu sosai sannan ya nufi dakin halisa! takaici ne ya rufeshi ganinta kwance tana bacci dan alamu ma sun nuna ba tayi sallah ba. Cikin bacin rai ya buga mata tsawa mai" "tafe da kiran sunanta. mikewa tayi a zabure tana amsawa! Yace."" Wai ke me yake damunki ne a" "rayuwa.""? Da sauri ta kalli agogon bango taga bakwai saura! Sai ta wani langwabe kai tace""Wallahi da zazzabi na kwana shiyasa jikina duk ya mutu.'" "Yace.""Ai dama ke bakya kunyar karya kiyi ta janyowa kanki lalura okey kiyi maza ki tashi kiyi sallah ki" "shiga kicin kada kisa su makara. Tace""Kayiwa Naja'at magana mana."" Kai tsaye yace.""Bata da lafiya.""" "Halisa shuru tayi tana nazarin maganarsa kishi kamar ya kasheta tasan tunda yace haka to aikin gama ya gama! sai ta wani sha kunnu tace""Ai wannan rashin adalci ne ita kace bata da lafiya to nima ai ba lafiyar ce dani ba."" Ganin zata raina masa hankali yasa yayi mata jan ido hade da fadin kada ta sake ransa ya 'baci ba zataji da dadi ba. Hakan da yayi sai ya tsorata dan a duniya ta tsani bacin ransa, ta mike ta nufi toilet domin daura alwala. Yana tsaye ta idar da sallar ya tasa a gaba har kicin din sai da yaga ta soma" aiki sannan ya fito daga kicin din. Lokacin da ya shiga dakin nasa naja'atu ta tashi sai dai tana kwance tayi tayi ta mike zaune ta kasa jikinta duk yayi tsami daga zarar ta motsa kafarta za taji gabanta yana wani radadi kamar an barbada barkono. "Yana shigowa ta rufe idonta gabanta na faduwa, zama yayi yana kokarin cire bargon dake lullube a" "jikinta, ashe towel din dake daure a jikinta ya kwance gabadaya jikinta a bude yake." Tsirawa gabanta ido yayi ya dan sa hannu yana bude cinyoyinta idonsa ne yake masa gizo yana ganin kamar ta samu rauni a gurin Jin yana ta wage mata cinyoyi yasa ta ture hannunsa tana takure jikinta hade da sake rintse idonta. Gaskiya bai yarda ba dole ya dauko likita mace tazo ta duba masa ita. "Sunanta ya kira tayi shuru kamar ba taji shi ba..Yace.""Tashi ki shiga ruwan zafi kiyi wanka sai likita tazo ta" "dubaki ko kin samu rauni."" Wannan maganar da yayi sai tasa hankalinta yayi mugun tashi itama jikinta na bata gurin da akwai rauni dan zafin da take ji yafi gaban a kwatantashi Tana jin motsin tashinsa" "daga gurin ta bude idonta, taga ya nufi toilet kafin ya fito sai da ya wanke bedshirt din ya baci da sauran abubuwan da suka bata sannan ya had'a mata ruwan wanka ya fito yana goge hannunsa da karamin towel, ganin bata tashi ba yasa ya sukunya ya dauketa ya nufi toilet din da ita, Naja'atu da kyar ta iya tsugunawa gaban ruwan wankan tana rintse idonta da cizan lips tayi wankan tsarkin ganin tana karkarwar jiki yasa ya dauki soso sa sabulu yayi mata wanka tas ya daura mata babban towel wannan karon hannunta ya rike dan baya son yaga tana lanjarewa a hankali a hankali suka fito daga toilet din, ya" zaunar da ita gefan bed din da sauri ya nufi dakin su Saddiqa domin dauko mata kayan sawa. "Mussadiq ya tambaya inda kayan nan ta yake, yaron ya dauko mata doguwar riga ta shadda yana" tambayar Abban nasu Naja'atun Abbah Abbas kasa cewa yaron komai yayi ya karbi kayan ya fita daga dakin Halisa na shirya dannig taga ya fito sai wani rawar jiki yake ya nufi dakin nasa da kayan naja'atu "a hannunsa tsaki taja mai karfin gaske! a fili tace""Allah ya kyauta mutum namamajo! gurin ta bari cike da" takaici da bakin kishi. "Da kansa ya shirya mata jikinta ya zauna kawai yana kallonta, ita kuwa kallonta da yake yasa wata" "sabuwar 'kiyayyarsa ta sake bijiro mata, dauke kanta tayi tare da jan tsaki kasa kasa ta dan gyara ta kwanta. Abbah Yaji tsakin da tayi mishi kuma baiji ciwo ba shifa yanzu duk abinda yarinyar za tayi ba zai" ga laifinta ba domin babban burinsa shine ta zauna dashi ya cigaba da kasancewa cikin ni'imar da Allah yayi mata. "Ya mike cikin rashin kuzari ya sauya kayan jikinsa, key ya dauka ya fita daga dakin Halisa da Yaran na" "zaune a danning suka ga zai futa. Cike da takaici Halisa tace""Ina kuma zakaje ba kayi break fast ba." "Yaje ""Yanzu zan dawo zanje na dauko likita ne tazo ta dubata."" Shuru tayi tana ta'be bakinta, ya kalli" "Mussadiq da fad'in ""Idan kun gama break din ku shiga ku duba Yaya Naja'atu bata da lafiya."" Sukace to Abbah sai ka dawo." Fita yayi da saurin gaske Halisa yana fita ta mike ba tare da tunanin komai ba ta nufi dakin nasa. Naja'atu sai ganin mace tayi a kanta. "Halisa ta 'bata rai sosai tace""Yanzu ke baki ji kunya da nauyin abinda kikayi ba.""?" "Cikin wani irin yanayi take kallonta kafin tace""Me nayi wanda zai sa naji kunya.""? Kai tsaye Halisa" "tace""Kin kasance gado daya da mutumin da ya rike ki tamkar 'yar cikinsa ai ana barin halas dan kunya." Tsaki! taja ta kalleta kallon raini dama kuma a ciki take da ita dangane da irin sharrin data dinga yi mata "saboda haka sai tace""Kece jahila wacce kika fi fifita al'ada akan halas d'in da kike maganar sa, shikenan saboda Abbah ya ri'ke ni kamar shi ya haifeni sai na fasa rayuwar aure dashi! to bari kiji rayuwar aure da Abbah yanzu na fara ki rubuta ki ajiye Abbah Abbas ya zama ni na zama shi yanzu babu sauran wata" "magana dai-dai nake dake.""" "Halisa ta d'aga mata hannu a fusace! tace""To mara kunya ba cewa nayi ki zageni ba naga kina wani tada" "jijiyar wuya."" Maganar sai ta bata dariya tace""Ba dole na tada jijiyar wuya ba naga ai kina nema ki shiga abinda bai shafeki ba ina ruwanki da abinda ke tsakanina da mijina ko kuma ni kinga ina sa miki ido akan" "harkokin da kike a cikin gidan nan.""" "Halisa taja tsaki mai karfin gaske tace""Banza mara kunya kawai idan namiji ne gashinan kaki nan ki" "cigaba da bashi yana ci watarana sai kinyi kuka da idanunki."" Tace""Eh naji ko kukan jini zanyi babu ruwanki mijina ne."" Halisa ta fusata sosai ta dinga ji kamar ta turmushe yarinyar kawai sai ta fice! fuuuuu! tana wani irin huci! gaskiya zama bai kamata ba dole ta bazama gidajan malam dan taga alamar yarinyar nan zata kaita ta baro Ita kuwa Naja'atu Halisa na fita taja tsaki tace""Banza mahaukaciya kawai sai" "kace ance mata son mijinta nake zata zo tana yiwa mutane hauka! hawaye ta goge tana gyara kwanciyarta yaran suka shigo ta dan saki fuskarta tana amsa gaisuwarsa, Mussadiq kuwa ganinta kwance a bed din abbansu sai abun ya bashi mamaki yace.""Yaya Naja'atu yau a dakin Abbanmu kika kwana" ashe.'? "Da sauri tace""A'a na shigo nayi masa shara ne sai na kwanta ina hutawa."" Da yake baida wayo sai ya" amince da maganarta sukayi mata sallama suka fita. To Abbah Abbas tare suka shigo gidan da Dr Sa'adatu babbar likita ce dake aiki a asibitin nasarawa dake kano da yake anan file dinsu yake shida iyalinsa. Fitowa yayi daga dakin domin ya bawa Dr damar yin aikinta fargabarsa da damuwar sa shine kada Dr tace masa gurin ya samu matsala shine babban abinda ke fadar masa da gaba.. Cike da kunya Naja'atu ta kwanta Dr ta shiga dubata. Dr Sa'adatu ta Umarce data saka wandonta "bayan tagama duba gurin, cikin sanyin jiki ta mayar da pant dinta ta gyara zamanta gabanta na wani irin faduwa tsoron abinda Dr din zata fada take." "Dr tace""Kanwata me yasa kika 'ki bawa mijinki cikakken had'in kai a lokacin da yake kokarin kar'bar" "budurcinki.""? Hawaye suka wanke mata fuska tace""Dr ba laifina bane wallahi yafi karfina ne."" Dr ta girgiza kanta tana dan murmushi tace""Babu namijin da yake fin karfin mace Kanwata Alhaji bai fi karfinki ba kece kika dinga matse jikinki har kika janyowa kanki shan wahala Na duba na gani gabanki ya dan" "tsatstsage amma ba sosai ba zan baki magani sannan ki dinga shiga ruwan zafi sau uku a rana."" Tace""To amma dai gurin bai samu matsala ba ko.""? Dr tace''Babu wata matsala da ya samu ko yanzu oga zai iya hawa yayi aiki akai idan yana bukata."" Da sauri tace""Dan girman Allah ki rufa min asiri kada kisa yaji" "wallahi da zafi.""" "Dr tasa dariya tace'""Haba k'awata meye abin tsoro ai yanzu kuma kin wuce wannan gurin bana so ki" zama raguwa a gidan mijinki ki daure idan yazo da bukatarsa ki kar'beshi hannu biyu. Girgigiza kanta ta shiga yi tana goge fuska ita yaushe zata iya da wannan masifar gabadaya ma tsoronsa takeji a cikin zuciyarta. "Dr ta mike da fadin"" ina fatan kin dauki shawarwarin dana baki."" Daga kanta tayi kawai dan saboda dr ta" fita ta bata guri! saboda maganar da tafada ta sanya tana jin haushinta sai kace wata dabba wacce bata san ciwon kanta ba zata sake yarda yayi wani abu da ita ai kome za'ayi sai dai ayi ba zata sake bari yayi ba. Dr ta kama hanya ta fita daga dakin tana mamakin halin kuruciyar yarinyar. *Littafin nakudi ne...!* Koda zaki ganshi a groups to na sata ne idan kina so ki biya kudin karatu ga yanda abin yake. VIP Gruop #600 Normal #300 Account: 0542384124...Binta Umar gtbank. Idan katin waya zaki tura to kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar 07084653162 *BINTA UMAR ABBALE* BHRBN *30* "Yana ganin Dr Sa'adatu ta fito daga dakin, sai ya mike yana kallonta, kai kana kallon yanayin daya nuna" "zaka fahimci cewar yana bukatar karin bayani daga bakinta, Dr Sa'adatu tayi murmushi cikin nutsuwa tace""Yallabai ka kwantar da hankali amarya bata ji ciwo ba kamar yanda kake tunani, lafiya gurin yake amma dai duk da haka yanzu zamuje pharmacy da kai akwai magungunan da zata d'ansha zasuyi dauke mata rad'idi da zugin da gurin yake mata.""" "Ajiyar zuciya ya ajiye yace.""To alhamdulilalhi bari na dubata na fito."" Dr tace""To babu damuwa.""" "Fuskarta dauke da murmushi ta samu Guri ta zauna tana kallonsa ya nufi dakin, sai taji tana sha'awar ina ma itama takasance a matsayin matarsa, dan ta lura shi din mutum ne shi mai tsananin kula da iyalinsa ta kowanne bangare, addua tayi a matsayinta na bazawara kan Allah ya bata miji kwatankacin" sa. "Naja'atu kuwa bayan fitar Dr daga dakin, zanin jikinta ta kwance ta bude cinyoyinta gabad'aya ta d'an" "zame pant d'inta ya sauka dai-dai cinyoyinta a hausarta wai gurin ta bude yasha iska a ganinta rufewar da tayi shine yake sanyawa yana k'ara yi mata zafi Aikuwa yana shigowa da abinda yayi tozali kenan," Tsigar jikinsa ce ta wani tashi sai yayi Saurin kauda kanshi jiki a mace ya 'karasa bakin bed din ita kuwa sai jan zaninta take tana kokarin rufewa had'e da dauke kanta sam bata san kallon fuskarsa. Ya "jima a tsaye a kanta yana kallonta tana ta kici-kicin jan zani ta rufe sai ya sunkuya yayi mata rumfa numfashinsu ya dinga had'uwa! goshinta ya sumbata cikin taushin murya yace.""Sannu kinji ko zai daina yi miki zafi insha Allah! kuma naji dadi sosai Dr tayi min bayani cewar baki samu matsala ba yanzu zamuje tare da ita domun a kawo miki magani wanda zai taimaka miki gurin dauke zafin da gurin yake. Ba tace masa uffan ba sai ma wasu hawaye da suke kokarin zubo mata, sam bata so tana sha'kar" "numfashinsa gashi ya wani sunkuya mata a jiki....Jin bakinsa tayi kan le'bunanta yana lasa da harshensa," tayi gaggawar juyar da kanta tana jin mugu-mugun mamakin abinda yake mata gaba'daya ma ta lura dashi ya manta matsayinsa a gurinta abinda ya ga dama shi yake yi. "Tsayuwarsa ya gyara yana kallonta da idanunsa da suka soma risinawa yace.""Me kike so na kawo miki" "kici nasan dole kina bukatar abinci.""" "Uffan ba tace masa ba...Yace.""To tunda ba za kiyi min magana ba idan na dawo zan maimaita abunda" "nayi jiya ."" Tayi saurin kallonsa bakinta na rawa! girarsa ya daga mata yana so ya tabbatar mata da maganarsa. da kyar tace""Koma me ka siyo zanci dan Allah kada ka kuma wani abu dani zan iya" "mutuwa."" Yayi murmushi yana shafa gemunsa had'e yi mata kallon 'kasa-'kasa yace.""Bana jin zan iya yi miki alkawarin abinda kike so yana da kyau ki zama jaruma mai daukar ko wacce irin lalura wannan" "abun ba zai sanya ki mutu ba sai dai ma ya 'kara miki lafiya.""" Wannan maganar da yayi tasa taji wani tsoronsa ya shigeta Murya na rawa tace Dan Allah kayi hakuri "kada ka 'kara yi wallahi ba zan iya ba."" Tausayi ta bashi ganin har ta soma hawaye kuma ya hango tsantsar tsoronsa a kwayar idonta, sai yace.""Daina kuka ba zan sake ba shikkenan ko."" Tace""To ka rantse da Allah."" Maganar sai ta bashi dariya yace."" Ba sai na rantse ba tunda nayi miki alkawari shikkenan ki" "kwantar da hankalinki ki daina kuka.""" "Kanta ta shiga d'agawa tana kallonsa wai so take ta tabbatar da gaskiyar maganarsa, shi kuwa hularsa" "dake saman kansa ya gyara ya kama hanyar fita daga dakin tare da fad'in ""Sai na dawo ko."" Kallo tabishi dashi tana jin tsana da tsoronsa na sake 'karuwa a cikin zuciyata, hakika da tana da inda za taje ta fake" to data gudu gabad'aya sun nemata sun rasa... "Halisa da Dr din ya samu a palon suna hira, yana fitowa Halisa ta kura masa ido zuciyarta na tafarfasa!" "Shi kuwa nan da nan ya daidaita nutsuwarsa cikin dakewa ya kalli Dr Sa'adatu da fadin ""Muna iya tafiya yanzu.""" "Dr ta kalli Halisa tana dan murmushi tace""To madam Allah ya bamu alkairi."" Ciki ciki tace""Okey."" ya" "kalleta tare da karantar yanayin da take ciki, yace.""Zan dan futa sai na dawo."" Iskar da yake ma bata" "kalla ba dan wani irin mugun haushinsa takeji ganin yanda yake ta wani rawar jiki ko maganar zuwa kasuwa ma bayayi.""" "Suna fita ta mike ta nufi dakinta, ta dauki wayarta ta shiga sanarwa da Yaya Ramlatu halin da ake ciki.""" "Yaya Ramlatu tace""Halisa ki rabu dani naji da bakin cikin dake damuna! Halisa tace""Me ya faru dake Yaya.""?" "Yaya Ramlatu tayi 'kwafa! cikin tsabar bacin rai tace""Mutsiyaciyar yarinyar nan Naja'atu itace ta kai" "'karata gurin Alhaji da Hajiya yau da safe sai ganin d'an aike nayi, koda naje gidan Alhaji baiyi min da sauki ba rufeni yayi da fad'a sosai hajiya har da cewa duk sanda na sake zuwa gidanku bata yafe min ba.'" "Halisa tace""Lallai al'amarin Malam Baba yayi tsanani! to nima nan a cikin matsala nake dan gabadaya na" "kasa gane kan maigidan tun jiya daya kwanta da yarinyar ya zama sakarai sai rawar jiki yake yi yama kasa zuwa kasuwa gabadaya ya lalace a gindin yarinyar. Yaya Ramlatu tace""To ke yanzu wane mataki zaki" "dauka dangane da faruwar hakan.""? Halisa tace""Kawai so nake na samu malamin da zaiyi min aiki akansa" "gabad'aya a zare masa sha'awarta a zuciyarsa ko kuma idan yaje zai sadu da ita gabansa ya mutu ya'ki aiki.""" "Yaya Ramlatu tace""Wannan aikin ba mai wuya bane mutukar zaki futo da kudi ni kuma zan baki goyon" baya dan nima abinda yarinyar tayi min yasa gabadaya na sake tsanarta. "Tace""Wallahi idan zan samu malamin da zaiyi min wannan aikin ko nawa ne zan biyashi."" Yaya Ramlatu" "tace""Shikkenan yanzu zan kira 'Yar shagamu a waya zan fad'a mata duk abinda ke faruwa, nasan zata kaimu inda bukata zata biya."" Halisa ta sauke ajiyar zuciya tace ""To sai naji daga gareki Yaya Ramlatu nagode."" Sallama sukayi da juna kowanne ya kashe wayarsa cike da mugun nufi" "Bayan fitarsa daga dakin bacci mai nauyi ne ya dauketa, sai ji tayi ana shafa mata tafin kafafunta had'e" shara'bar 'kafafunta. Bude ido tayi da sauri ganinsa zaune dab da ita yasa ta zabura! da sauri zata mike zaune! ya ri'ke "hannunta cikin lafazi mai dadi yace""yi hankali kisa nutsuwa kada ki fama ciwon naki."" Maganar tasa yasa ta tuna abinda ke da akwai." A hankali ta saukar da kafafunta kasa tana so ta mike tsaye ya kama hannunta suka mike tare. kamar me koyon tafiya suka nufi toilet brush tayi suka fito tare. zama tayi gefan bed tana jin yanda cikinta ke murd'a mata yunwa takeji sosai Idonta ne ya sauka kan ledar Osis daya shigo dashi. dauka yayi ya "mika mata da fadin""kici abinci sai kisha magani ko.""" "Kar'ba tayi tana kokarin sauka kasan kafet, shi kuma sai ya shiga duba maganin da Dr ta bashi abinci" "taci sosai ta had'a da lemo mai sanyi lokaci guda ta dawo cikin hayyacinta. ganin ta samu nutsuwa sai ya mika mata maganin da ruwan dake hannunsa, kamar zata fashe da kuka ta kar'ba tana jujjuya maganin a hannunta, a rayuwarta ta tsani had'iyar 'kwaya. Yace.""Kisha mana kin tsaya kina kallonsa."" 'Daya bayan d'aya tasha maganin tana wani ya mutsa fuska." "Ya dan sassauta murya wanda idan ba ita d'in ba babu me ji yace""Yanzu sai shiga ruwan zafi ko.'' ?" Tsintar kanta tayi da kallonsa domin ita wallahi abinda yake mata mamaki yake bata tsakanin jiya da yau duk ya sanja magana ma idan zaiyi mata da wata irin murya ta mussaman yake mata babu abinda yake bata haushi dashi sai munafikin kallon da yake mata ta 'kasan ido......kawai ta shiga bin bayansa da kallo a lokacin da yake kokarin shiga toilet din. "Minti goma ya fito yana kallonta yace""Zo muje ki shiga ko."" Ta mike a hankali dan itama tana so ta shiga" ruwan zafin ko ta samu saukin wani abun. "Ya nufeta yana tattare hannun rigarsa yace""Ki cire kayan jikinki sai ki daura towel sai kinfi sakewa."" Kafin" tace wani abu ya sata a jikinsa yana kokarin kwance mata zani! "Da sauri tace""Zan iya cire kayana dan Allah kyaleni.""" "Girgixa mata kai yayi ya cigaba da kwance daurin da tayiwa zanin jikinta yanayi yana sumbatar wuyanta," ji tayi tsigar jikinta ta soma tashi sakamakon gemunsa da yake goga mata fatar jikinta. Jin yana kokarin cire zanin gabadaya yasa ta dan ture fuskarsa dake wuyanta ta matsa gefe tare da jan "zanin saman kirjinta ta daure! sosai sannan ta cire rigarta sai ta kwance dankwalin dake kanta ta rataya a wuyanta, kai tsaye toliet din ta nufa ta barshi a tsaye a gurin Ya dan jima a tsaye a inda yake yana" kokarin saisaita kansa kafin ya samu gefen bed din ya zauna yana jiran fitowarta. Tunda ta fito yake "mata wani irin kallo na ma'kurar kurrula. ita kuma ji tayi kafafunta na rawa gabanta kuma na faduwa, ta" "dauka ya gaji da jiran fitowarta ya fita daga dakin, shiyasa ta share kusan mintina ar'ba'in a ciki ashe yana zaune bai fita ba." Kamar ta koma toilet din haka taji sai dai ta daure ta ta nufi bed din domin daukar rigarta tasa. hannunta ya fizgo da karfi sai kawai ta fada kansa! ya wani matseta sosai a jikinsa yana ya mutsa mata jiki Kuka take tana kokarin mikewa yana sake matseta hade da so ya kwance zanin dake daure a "jikinta. Tace""Abbah dan Allah kayi hakuri dan Allah kada ka sakeyi min irin na jiya ka duba 'kan'kantata" "ba zan iya ba.""" Bakinsa yasa a kunanta ya shiga tsotsa yana hura mata iskar bakinsa! lokaci guda jikinta ya rikice ta dinga "kyarma tana kiran sunansa, wannan soyayya ta Abbah Abbas ta mussaman ce kuma babu shakka Naja'atu karonsu na farko dashi ta tabbatar da cewar lallai maza ma suna suka tara. Gabadaya Abbah" Abbas bai bar mata komai a jikinta ba sai da yayi mata haihuwar uwarta tukkuna hankalinsa ya kwanta ya shiga sarrafa albarkatun jikinta mussaman breast dinta da sukayi masifar tsone masa ido sha yake hade da murzasu tamkar zai tsinke mata nippels. Sun dauki kimanin mintina ar'ba'in cikin wannan yanayi kafin ya samu da kyar ya samu satisfaction duk ya 'bata mata jikinta da uban sperm dinshi mai yawan gaske "Tana kuka tana komai ta mike zaune da kyar tana duban jikinta, wannan abin da ya zuba mata a jikinta" yayi masifar bata haushi wannan ai kazantace! kamar ta rufeshi da duka haka ta dinga ji. "Juyawa tayi ta ganshi yayi rashe-rashe a bed din yana fitar da wani irin numfashi, ga katuwar joystick" dinshi a tsaye kyam tana kallon rufin dakin Cikin gigita da mugun tsoro ta tashi daga gurin hannunta rike da zaninta da ya cikwikwiye tana kokarin daurawa a jikinta ta kama hanyar futa daga dakin tamkar wata zautacciya!! ta'bdijam! ai ba zata zauna ya turmushe da wannan katuwar abar tasa ba. Tana fita "sukayi ido hudu da Halisa dake zaune a palo tana kallo..Halisa ganin yarinyar ta fito daga dakin a gigice yasa ta bita da wani irin kallon mamaki! ikon Allah ashe yana nan bai fita ba, ita wallahi duk daukar da takeyi ya fita tunda ta dade zaune a palon ba taji motsinsa ba..Naja'atu na shiga dakinsu Saddiqa sai ta" mike cikin zafin zuciya ta nufi dakin nasa. "Kwance ta same shi da ido a rufe, Allah yasa ya rufe jikinsa da bargo amma dai duk da haka tana ganin" girmansa ya bayyana da alama yarinyar wuya taji yasa ta fece ta barshi! koda yake itama lalla'bawa take dan har yanzu bata dawo normal ba """Abbah Mufida lafiya kuwa.""? Jin muryar Halisa yasa ya bud'e idonsa da sauri! halin da yake ciki yasa ya" kasa magana sai kawai ya fizgota ta fada samansa...Halisa a gigice ta fizge jikinta gabanta na fad'uwa! ina zata yarda ya sake ragargazata bata huce ba tukkuna! "Ya bita da wani irin kallon sha'awa da fadin"" Halisa ina cikin yanayi na bukatar taimakon ki."" da sauri" "tace"" Gaskiya babu abinda zan iya yi maka dan nima ba wai na gama jin dai-dai bane so kawai ka kira amaryarka ka biya bukatarka."" Da sauri ta kama hanya ta fita daga dakin, duk san sex da take da kuma son ta kuntatawa Naja'atu ba zata bari ya hau kanta ba tasan yanda yake a rikice haka idan ya hau to saukarsa sai abunda Allah yayi. shiyasa tana shiga dakinta tasa key ta barshi a jiki domin tana tunanin zai iya biyo ta. Abbah Abbas ya mike cikin tangadi kamar wani bugagge ya nufi dakin Halisa dan a ganinsa" "itace kadai zata iya dashi sai dai me key yaji a jikin kofar ya dinga murza key din dakin yaki budewa, ransa a bace ya nufi dakinsu Saddiqa babu yanda zaiyi dole ya sauke bukatarsa kan yarinyar idan ba" hakaba zasu iya yin asararsa dan baya jin zai iya kaiwa dare a raye... "Allah sarki naja'atu tana takure a kuryar gado taga ya shigo dakin, sai ta mike zumbur tana kallonsa......" Ya mayar da kofar ya rufe da key kai tsaye ya durfafi inda take. Ihu! ta dinga kurmawa!! tana bashi hakuri! malam bahaushe yace wanda yayi nisa baya jin kira Abbah Abbas kama 'yar mutane yayi ya turmushe ya shiga biyawa kansa bukata.. *Littafin na kudi ne..!* Koda zaki ganshi a gruops to na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu to ga yanda abin yake. Mdd *31* Abbah Abbas bai saurarawa yarinyar mutane ba sai da ya tabbatar da cewar ya samu cikakkiyar "gamusuwar da yake bukata sannan ya sauka daga kanta, tana kwance laga-laga tana fitar da numfashi sama-sama hawaye duk ya bushe a saman fuskarta ga wani irin bushewa da ma'kogwaronta yayi babu abinda take bukata sai ruwa mai masifar sanyin gaske Rintse idonta tayi ta Takure jikinta guri" guda jikinta na wani irin rawa. Gabadaya ji tayi duniyar ta fita daga ranta ta dinga jin inama tabi "yayarta ta huta da wannan azaba da Abbah Abbas ke gana mata, sabida rashin hakuri da kawaici a dakin 'yayansa kan gadon d'ansa ya haike mata itakam har duniya ta nad'e ba zata ta'ba mancewa da wannan rana ba. To shima nasa bangaran tunanin da yake yi kenan, gabadaya idanunsa ne suka rufe shiyasa ya" "kasa sarrafa kansa amma shi kansa yasan yayi abin kunya..hannu ya mika Ya dauki gajeran wandonsa yasa a jikinsa kana yayi gyaran murya da fadin ""Tashi a cire bedshirt din a sa musu wani.shuru tayi masa" tamkar da dutse yake magana. "maganar ya sake maimaitawa, ta dan motsa a hankali ta mike zaune tana kare kirjinta da siket" dinta. Kunyar hada ido yake da ita shiyasa ya kauda kansa kafin yasa hannu ya janye bedshirt din kudindine shi yayi a hannunsa kana ya kama hanyar fita daga dakin Yana fita ta sauke ajiyar zuciya ta daddafa kamar mai koyan tafiya ta nufi toilet domin tayi ruwan dumi ta kuma tsarkake jikinta.. Abbah Abbas kam kai tsaye da ya shiga dakinsa toilet ya nufa da bedshirt yasa shi cikin washing "marching ya wanke tas ya shanya a toilet din, Yana wanka yana tunanin kasancewar sa da yarinyar gabadaya ma ya rasa yanda zai kwantata yanda yake ji idan yana sex da ita! Halimatu nada tata baiwar hakama Halisa itama tana da tata! amma yayi imani da cewar baiwar dake tattare da Naja'atu ta" mussamance yana tunanin idan zai kwana a kanta yana aikin abu daya ba zai gaji ba. A gurguje ya shirya jikinsa tsaf ya fito palo dai-dai da lokacin da yaran suka dawo daga skull biyar da rabi na yamma kenan. "Halisa na kicin tana aiki ya shiga ya sameta kallonsa tayi tace""Sai yanzu zaka fita kenan.""? fuska a tsuke" "yace""Abinda kikayi kin kyauta kenan? Da sauri tace""Me nayi maka ?"" Gyada kansa yayi yace."" Kin mayar dani sakarai ko? okey tunda yini guda kin sani na haikewa 'yar mutane to ki taimaka ki d'anyi mata farfesu ko zataji dadin bakinta." "Wani kallo ta watsa masa tace""Wallahi bazan yi mata ba idan ka damu taci ka shigo kayi mata wannan" ma ai cin fuska ne kayi yini kana sasakar 'yar mutane kaji dad'in ka sannan ka sani aikin wahala to ina gama aikin da nakeyi zan bar kicin din nan dan babu wani farfesu da zanyi mata. "Yace.""Kema ai a lokacin ki haka nasa Halimatu tayi miki."" Da sauri tace""Halisa daban Halimatu daban ni" dai ba zanyiwa kishiya bauta ba idan zata fito taci abincin da kowa zai ci to idan ba zata ci ba to sai ka siyo mata farfesun. "Yace."" Naja'atu ba kishiyar ki bace kanwarki kice, tunda ban isa na saki kiyi abuba za kiga abinda zai" "faru."" Jin haka yasa jikinta yayi sanyi ta bishi da kallo yana kokarin fita tace"" To wai da kake wannan maganar farfesun me zanyi mata.""?" "Yace.""Duk wanda kikayi nasan zaiyi mata dadi."" Ta sake jin wani sabon kishin na sukan zuciyarta" "daurewa tayi tace"" shikkenan zanyi.'' Ba tare da yace komai ba ya fita daga kicin din." "Cike da takaici Halisa ta dinga k'walawa Saddiqa kira, yarinyar na tsaka da cire uniform ta nufi kicin din a" "gigice! cikin hantara! tace""Ki bude freezar ki dauko kaji guda biyu kizo ki dora a wuta."" Tace""To mommy bari nasa kayana." "Muguwar tsawa ta buga mata da fad'in ""Dan ubanki zakiyi abinda na saki ko kuwa.""? Da sauri yarinyar ta" bude freezar ta fara kokarin ciro kazar da take a daskare...Wu'ka ta jefa mata dan har sai da ta kusa "sauka a kafarta tace"" Dauka kiyi dubara ki ciro da wannan wukar."" Saddiqa ta sunkuya ta dauki wukar tasa tana ta kokarin dauko kazar..cikin tsautsayi wukar ta shar'be mata hannu!" Yarinyar ta cillar da wukar gefe guda tana hawaye jini kuwa tuni ya soma zuba. "Halisa hankalinta ne ya tashi, sai ta shiga yi mata fada wai garin ya akayi ta bari wukar ta yanketa." "Saddiqa tace""Wallahi mommy ban san lokacin ba." "Hankali a tashe ta rike hannun yarinyar suka fita daga kicin din, jinin dake zuba ya firgitasu gabadaya" dan da gudu Mussadiq ya ruga ya fadawa Naja'atu abinda ke faruwa. Da sauri ta fito palon nan ta tarar da Halisa rike da hannun Saddiqar tana kokarin daure mata da yanki sai cewa take kada ta fadawa Abbansu ita tasa ta aiki. "Naja'atu tace""Ke Saddiqa Ya akayi kika yanke haka."" Saddiqa na share hawaye tace""Naje ciro kaza a" "freezar ne.? Cike da mamaki tace""Kawai sabida zaki dauko kaza sai ki yanke.""" Saddiqa ta kalli Halisa tsoronta takeji shiyasa ta kasa fadawa Naja'atu abunda ya faru.. Gurin ta karaso rai a bac'e ta kar'bi hannun tana dubawa gani tayi naman tafin hannunta ya fito yayi "jajur! ta kalli Halisa da fad'in ""Saboda mugunta zakice tayi shuru kada ta fadawa babanta so kike kenan hannunta ya lalace! duba fa yanda naman gurin ya fito." "Halisa tace"" Ke kada ki fada min maganar banza mana ai ba sabida wani abu nace kada ta fada masa" "saboda nasan kin san halin masifarsa mussaman a kan 'ya'yansa gabadaya ranmu zai iya 'baci ta dalilin haka.""" "Tace""Ranki ne dai zai 'baci amma ya zama dole a fada masa domin ya kaita asibiti."" Halisa taja tsaki mai" "karfi ta bar gurin tana fadin""Ai sai kiyi ta fad'a masa."" Kicin din ta koma ta cigaba da aiki tana tararrabi da" tunanin abinda zai faru mutukar Saddiqa tafada masa dalilin yankewarta da wuka to tasan ranta sai ya 'baci! A hankali ta zauna kan kujera ta zaunar da Saddiqar kusa da ita tana duba hannun nata! sosai yarinyar ta samu rauni amma saboda tsabar son zuciya irin na matar uba wai take cewa yarinyar tayi shuru kada ta fadawa babanta yanzu idan da Mufida 'yarta hakan ya faru da ita ai ba za tayi shuru ba. 'Kwallah ta goge tunawa da tayi da Halimatu! ta kalli Mussadiq da Mufida dake tsaye jikinsu duk yayi "sanyi dan Mussadiq ma kuka yake..Tace""Ke Mufida jeki dakin mamanki ki dauko min wayarta ki sako a cikin hijabi kada ki bari ta gani." "Mufida da sauri tace""To"" ta nufi dakin Halinsan Halisa na kicin Mufida ta shiga ta dauko wayarta ta" "kaiwa Naja'atun, ta kar'ba tana kokarin saka numbarsa sunansa ya fito Halisa tayi serving da Abban mufida." "Abbah Abbas na can kofar na'isa gidan hajiya kiran wayar ya sameshi, Jin muryar Naja'atu cikin wayar" "Halisa sai abin ya bashi mamaki! kafin ya tambayeta cikin rawar murya ta sheda masa abinda ke da akwai...Ya kashe wayar cikin damuwa ya fadawa Hajiya abinda yake faruwa! tace""Ikon Allah to kayi maza kaje a kaita asibiti a duba kuma ayi mata allurar nan dan gudun shigar ciwo.'' Ya mike tare da fad'in ""Insha Allah Hajiya sannan dan Allah kada ki manta da maganar mai aikin da mukayi ina bukatar mace dattijuwa mai hankali gami da tsabta."" Hajiya tace""Insha Allahu zan fad'awa Jummai ta duba maka a" "kurkusa ai masu aiki ba zasuyi wahala ba.""" Kafin ya isa gidan magariba tayi dan haka sai da ya tsaya a massalaci yayi sallah tukkuna ya shiga gidan "nasa, lokacin zafin ciwon har ya zuba mata zazzafi! Naja'atu da yaran duk sun shiga damuwa ganin Saddiqar sai rawar d'ari takeyi Koda yaga yanayin jikin 'yar tasa sai hankalinsa ya tashi, ya shiga" tambayar ba'asi! Halisa na tsaye a baki danning jikinta duk yayi sanyi. "Naja'atu tace"" Dawowar su kenan daga makaranta naji Anty Halisa na kwala mata kira dan ko uniform" "bata cire ba gasu nan ma a jikinta, ina ciki a kwance Mussadiq yazo yake fada min wai ga Saddiqa can ta yanke jini na zuba shine dana fito naga Aunty Halisa na daure mata hannunta da yanki kuma tana cewa" kada a fad'a maka! "Ya kalli Halisa yana so yaji karin bayani daga bakinta, sunkuyar da kanta tayi kasa dan bata da abin da" "zata ce! ganin alamun rashin gaskiya a tare da ita yasa Yace.""Ki fada min dalilin daya sa Saddiqatu ta yanke a hannunta." "Cikin inda inda gami da rashin gaskiya tace""Kasan ka fita ka barni ina aiki a kicin to ganin yamma tayi" "yasa na kirata nace ta dan taimaka min shine ban san ya akayi ba naji ta rike hannunta tana kuka wai ashe wuka ce ta yanke ta.""" "Yace""Saddiqa ya akayi shin maganar da Halisa tayi gaskiya ne? Saddiqa tace""Eh mommy tace""Na dauko" "kaza a freezar to dana kasa daukowa sai ta bani wuka tace wai nayi dubara na dauko da ita.""" "Ya dinga kallon Halisa zuciyarsa na wani irin turiri! yace.""Ashe dama saddiqatu nasa aiki bake ba.""?" "Tace.""Wallahi ba'a sa. Kafin ta rufe bakinta ya bata kyakykyawan mari a fuska!" Palon yayi tsit!! Halisa kuwa kunyar duniya ta isheta sai ta sunkuyar da kanta kasa tana jinsa yana ta "zazzaga mata fad'a hawayen takaici ne ke kokarin zubo mata a fusace! ta bar gurin...Yaja tsaki mai karfi ya kalli Naja'atu da fuskar 'bacin rai! Yace.""Tashi maza ki dauko hijabi muje asibiti da ita.""" "Hakanan ta daure ta tashi tana tafiya salo-salo itama ba wani kwari ne da ita ba, tsoron abinda zaije ya" "dawo yasa ta lallaba ta fito jikinta sanye da hijabi, ya sunkuya ya dauki Saddiqan dake kwance a kan kujera ya nufi hanyar fita, ta rufa masa baya." Saddiqa tasha wuya sosai dan har sai da akayi mata din'ki a bayan hannunta sannan aka wanke gurin Dr ya hada mata maganguna masu kyau! tana kuka Naja'atu na taya ta dan gabadaya kasa daurewa tayi sai take jin ciwon tamkar a jikinta. Dr ya gama aikinsa ya nad'e gurin da plasta kana ya hada mata magunguna masu kyau. "Halisa kuwa tana shiga daki zama tayi gefan gado tayi tagumi! tarasa abinda ke damunta, wai yau ita" "aka mara a gaban yara! lallai dole ta dauki mataki dan gaskiya abin yayi mata ciwo sosai! ita tarasa wane irin so yake wa yaran wanda baya iya sarrafa kansa, ga Mufida nan kwatakwata baya nuna damuwarsa a kanta komai Saddiqa da mussadiq!" Mikewa tayi ta bude wardrobe dinta ta dauki hijab ta dauko kaya kala uku jakarta ta dauka ta sa kayan ta dauki pose dinta da key din sabuwar motar daya siya mata fitowa tayi tana wani irin huci! sai taga Mufida da Mussadiq a zaune sunyi tagumi! "Tsawa mai karfin gaske ta bugawa Mufida tace""Tashi dan ubanki kin zabga tagumi sai kace wacce akace" "uwarki ta mutu.! Yarinyar ta mike a firgice tana kallonta tace""Mommy ina zakije na ganki da jaka.""" "Tace""Gidan Ubanki zanje.""! Yarinyar tayi tsuru tana kallonta, tace""Yi maza ki shiga dakinku ki dauko kayanki zamu tafi gidan Baba dan ba zan tafi na barki a cikin mayu ba.""" "Yarinyar ta shiga girgiza kanta tana fad'in ""Mommy dan Allah ki barni a gida tare dasu Mussadiq."" Wani" "irin mari ta kifawa yarinyar tace""Dan ubanki kinyi abinda na saki ko kuwa kina nacewa mutsiyatan yara zasu koya miki mugun hali to mutukar ni na haifeki babu ke babu so." "Yarinyar ta turje taki tafiya dauko kayan, halisa cikin rashin imani ta dinga marinta kamar ba ita ta" "haifeta ba, babu arziki Mufida ta ruga dakinsu a guje taje ta rufe kofa tana kuka...Halisa ta dinga dukan kofar tana fadin""Shikkenan sun lashe min kurwar 'yata! kai ubangiji Allah ya rabamu da mayen mutum..Mussadiq ya sunkuyar da kansa kasa yana goge hawaye! A fusace! ta kai masa rankwashi a" "kansa tana fadin""Na tafi na bar muku gidan shegu mutsiyata."" Fuuuu! ta wuceshi ta nufi kofar futa." "Mussadiq ya tashi yaje ya tsaya a bakin kofar dakin nasu yana kiran sunan Mufida da fadin""Ta bude kofar" "mommy din ta tafi...Mufida na kuka tace""Mussadiq bazan bude ba sai Abbanmu ya dawo tsoro nake kada mommy ta dakeni."" Mussadiq zama yayi bakin kofar dakin yana kuka hade da bin palon da kallo." Driving yake tana satar kallonsa ta mirror ganin fuskarsa tayi a hade tamkar tunda aka hallice shi bai "ta'ba dariya ba, ba tun yau ba tasan shi da masifar son 'ya'ya tayi mamaki ma da hukunci mari ne kawai ya shiga tsakaninsa da Halisa tabbas kowa yaji abunda ta aikata yasan bata kyauta ba, kuma ta nunawa duniya cewar ba zata iya ri'ke yaran tsakani da Allah ba. Ita kuwa sai take ganin to meye amfani kana" son mutum amma baka son 'yayansa. Gani tayi yay parking a gurin da suka ta'ba tsayawa yayi musu take away. Yauma gurin taga ya nufa ta "bisa da kallo har ya shige cikin gurin, sannan ta mayar da hankalinta kan Saddiqa dake bacci a bayan mota, hannu ta mika ta dan shafi wuyanta taji har yanzu da zafi amma ba kamar dazu ba, cikin zuciyarta tace""Allah ya kareku daga sharrin matar nan."" Hango shi tayi ya tawo hannunsa da ledoji kamar yanda ya saba, tausayinsa taji ya ratsa mata zuciya, Abba Abbas mutum ne shi mai zuciya da kula da iyalinsa komai suke bukata sai yayi musu da jikinsa da aljihunsa a tarihin rayuwarta a gidansa bata ta'ba d'aura zani dan 'kasa da dubu biyar ba manyan atampopi da lesuna yake dinka musu shadda kuwa komai tsadarta zai d'inka yasa a jikinsa suma ya d'inka musu, komai nasu mai kyau ne! Idan sallah tazo kuwa" haka zai kwashe su a mota suyi ta siye-siye wanda har sallah ta wuce basu gama amfani dasu ba. Gaskiya ta wannan bangaran ya ciri tuta tana jin da tana sonsa to babu abinda zai hanata ta kyautata "masa, sai dai kash ta rasa a wane matsayi zata ajiye shi a zuciyarta duk da cewar ya kar'bi abu mai muhimanci a gurinta hakan bai sanya ta ta karaya daga kudirin dake cikin zuciyarta ba, tayi alkawarin ba zata kare rayuwarta da auran tsoho ba dole ne ma ya sauwake mata tunda ya kawar da kulafucinsa a" kanta Ganin yana kokarin bude motar ne yasa tayi saurin dauke kanta daga kansa...Ya zauna mazauninsa tare da kunna motar suka bar gurin. BHRBN *32* "Mussadiq najin motsin shigowarsu sai ya mike da sauri yana me kallon kallon kofar shigowa, Naja'atu" "ganin yaron kamar a furgice yasa tayi saurin 'karasawa kusa dashi tana tambayarsa, sai kawai yasa kuka yana nuna mata dakinsu da hannunsa." "Tace""Menene kake kuka ina Mufida.""? Yace.""Tana daki ta kulle kofa wai tsoro take kada mommy ta" daketa alhalin kuma mommy din ta tafi unguwa yanzu. Da sauri tasa hannunta jikin kofar tana bugawa had'e da kiran sunan yarinyar. Mufida najin muryar Naja'atu sai tayi saurin bude kofar ta rungumeta tana kuka. Taja hannunta suka zauna kan kujera tana tambayarta. Yarinyar na fada mata abunda ya faru ya shigo palon ya tsince karshen maganar inda take cewa Mommynta ta tafi gidan Baba da jakar kayanta saboda tace ba zata bita ba shine ta doketa. Ba tare "daya nuna damuwarsa ba ya kalli Naja'atun yace.""Kije dasu daki suci abinci su kwanta amma ki tabbatar da cewar Saddiqatu tasha maganinta kan 'ka'ida.""" A sanyaye ta amsa masa kana ta mike cikin dauriya ta nufi dakin yaran suka bi bayanta. Zama yayi kan "kujera yana mamakin halin halisa wato saboda ya nuna mata kuskuranta shine tayi yaji, to kuwa babu shakka wannan karon zai nuna mata fushinsa da babu inda zai taka yaje idan ta gaji da zaman gidan ta" dawo da kafafunta. Halisa sai bayan ta fita daga gidan kuma sai ta shiga tunanin abunda zata fadawa iyayenta idan taje! duk "ranar da tayi yaji taje gidansu mahaifinta ba yayi mata da sauk'i! fada sosai yake mata kuma ya daina kawo cefane mai kyau a gidan a yini a kwana ana cin tuwo washe gari kuma a dama kunu asha ko kosai babu sai dai ta fito da kudinta tayi siyi abinda take so, bayan haka kuma shimfidar arziki bata da ita a" gidan sai da ta had'a summokara ta kwana a kai. Yanke shawarar zuwa gidan Yaya Ramlatu tayi dan saboda tasan mijinta ba mazauni bane kuma Yaya Ramlatu tana da spire na daki sai ta shiga ta zauna ta rantse ba zata koma gidan ba sai yazo da kafafunsa ya bata hakuri wannan shine abinda ta kudurta a cikin ranta. "Yaya Ramlatu na shirye-shiryen kwanciya kawai taji sallamar Halisa a gidan, tayi saurin daga labule ta fito" tana amsawa. "Halisa kece da daddaran ina fata dai lafiya.""? Halisa ta girgiza kanta cikin kunar zuciya tace""Mu shiga ciki" "Yaya.""" Yaya Ramlatu ta rike hannunta suka shiga dakin suka zazzauna. Halisa kafin ta fadawa Ramlatu abunda ya faru sai da taci kukanta ta koshi!. "Yaya Ramlatu tace""Ki daina kuka! kada ki jazawa kanki lalura idan baki manta ba dama na fada miki idan" "yarinyar nan ta shigo gidan to ki tabbatar da cewar auranki na tangal-tangal dan saboda ni narasa wane irin mutane ne su masu masifar d'afar tsiya idan suka rikewa mutum kurwa sai sun rabashi da kowa, amma babu komai ai mune maganinsu, dama dazu bayan mun gama waya dake na kira *'Yar Shagamu* a waya duk na sheda mata abinda ke faruwa tace""Babu matsala zata shigo gobe mu tattauna dan akwai wani malami da take saran kaimu gurinsa insha Allahu kukanki ya kare mutukar mun dangane ga wannan malamin, sabida haka zaki zauna tare dani muga abinda hali zaiyi nasan idan aikin malam ya" fara tasiri a kansa zai nemi duk inda kike. "Halisa tace""Nima dama shawarar dana yanke kenan da nayi niyyar tafiya gidanmu sai na tuna idan naje" can din wahala ce shiyasa na nufo nan domin muyi shawarar abinda ya dace.. "Yaya Ramlatu tace""In dai kin futo da kudi ai komai mai sauki ne."" Tace""Cikin jakata a yanzu bai fi dubu" bakwai ba amma na fito da Atm dina gobe zan fita na ciro kudin insha Allah. "Yaya Ramlatu tace""To Alhamdullhi bari na tashi na gyara miki shimfida ki kwanta."" Mikewa tayi ta shiga" kici kicin sauko da katifa. (Kai jama'ai wai shin ita Ramlatu wace irin mata ce) Sai da ta tabbatar da cewar yaran sunyi bacci tukkuna sannan ta mike a nutse ta shiga toilet kafin tayi "wanka sai da ta sake shiga ruwan dumi tukkuna sannan tayi wanka ta fito daure da zanin atamfar jikinta. Tana kokarin bude jakar kayanta domin dauko kayan bacci ya shigo dakin, gabanta ya fadi sai ta" "shiga addua kan kada Allah yasa yace tazo dakinsa ta kwanta. Yace.""Duk sunyi bacci kenan.""? Kanta a" "kasa ba tare da ta kalleshi ba tace""Umm."" Sai ya nufi gadon Saddiqa tare da tsayawa a kanta yana" dubata. Ganin haka yasa da sauri ta dauki hijabinta tasa ta fito da riga da wando irin na bacci ta ajiye a kusa da ita ta rufe jakar gabanta sai dukan uku uku yake. Ya jima yana kallonta yana mamakin abinda tayi to meye kuma na rufe jiki dan shirme! wane dare ne jemage bai gani ba! "Gyaran murya yayi, ta zabura! da sauri ta takure jikinta." "Yace.""Zaki kwanta anan ko kuma zaki zo muje dakina.""?" "Da sauri tace""Zan kwana tare dasu dan saboda Hannun Saddiqa."" Yace""Okey to zaki iya kwanciya kasan" kafet kenan.? "Murya na rawa tace""Eh babu damuwa.""! Yayi shuru yana kallonta da murmushi a fuskarsa tsaf ya gane" "gudunsa take kuma ta tsorata dashi sosai dama haka yake so yana so ta gane bambamcin aya da tsakuwa yasan yanzu zata gane tsufa ko yawancin shekaru ba zai hanashi kuzari ba, d'an shekara sittin" ma sai ya fishi fitina "Ganin ya kama hanyar fita daga dakin yasa taji wani irin sanyi a cikin ranta, yana fita ta mike da sauri" tasa kayanta ta dauki bargo da pillow ta shimfida kasan kafet ta kwanta. "Ta dauka ba zai dawo dakin ba shiyasa ta cire hijab din jikinta, kawai sai taji ya turo kofar dakin ya shigo" hannunsa rike da lallausan bargonsa Mikewa zaune tayi ta had'e gwiwoyinta guri guda taki kallonsa "Shima ganinta cikin kayan baccin yasa ya shagala da kallonta, yarinyar na masifar tafiya da imaninsa." Tsayuwar da yayi a kanta yasa ta dinga jin tamkar ta saki fitsari a wando tuni hawaye ya soma d'iga daga "idonta. A nutse ya tsuguna gabanta yasa hannunsa ya dago fuskarta, sai kawai yaga hawaye na zirara!" "Ya jima yana kallonta da mamaki a fuskarsa, yace.""Kukan me kikeyi.""? Girgiza kanta tayi tace""Babu" "komai.""? Yace.""Akwai dalili ki fada min ko tsorona kikeji."" Ta d'aga kanta tana me rike hannunsa dake tallafe da fuskarta tace""Abbah dan Allah kada ka 'kara wallahi ni kadai nasan abinda nake ji.""" "Yaji tausayinta ya kamashi, yace""Ba zan sakeyi ba sai gurun ya warke sosai amma kiyi min alkawari idan" "nazo zaki bani goyon bayan da nake bukata. Cikin rashin dubara da wayo tace""Allah nayi maka" "alkawari zan baka."" Yace""To nagode ina rokan Allah yayi miki albarka ya kuma barni tare dake sannan ya" "albarkace mu da zuria mai albarka.""" Shuru tayi ba tace amin ba babban burinta ya tashi ya bata guri. "Fuskarta ya tsirawa ido yana kallon karamin bakinta, ji yayi ba zai iya hakura ba dan haka sai ya shiga" "kusantar fuskarta da tasa, ta wani irintse idonta tana takure jikinta." Hawayen dake ziraro mata ya shiga lashewa yana dan tsotsar kumatunta cikin wani irin salo na mussaman! Tayi kasa'ke! sa'kon na ratsa mata jiki. kafin yasa bakinsa anata sai da ya tsotsi le'bunanta sosai sannan yayi dubarar kama harshenta ya shiga tsotsa tamkar alawa "Wani irin yanayi ta dinga ji a jikinta, jikinta ya mutu kasala duk ta dabaibayeta, sosai da sosai takejin" dadin kiss d'in! ta dinga mutsu mutsu tana so ta tsotsi harshensa ta rasa yanda za tayi dan da tayi yunkuri kamawa sai ya janye nata ya rike yake ta tsosa kamar zai tsinke shi hannunsa da ya riko fuskarta ta kama ta ri'ke tamau! tana wani lumshe ido hade da d'an gyara zaman da tayi Shi kuwa ganin ta saki jikinta bata turje-turje yasa ya cigaba da abinda yake yi cikin nutsuwa da kwanciyar hankali. A 'kalla! sun dauki kimanin mintina goma cikin wannan yanayi kafin su rabu da juna! idanunta dake "lumshe ta bud'e tana kallonsa, sai yayi gaggawar mikewa dan saboda yanayin kallon da tayi masa yayi masifar tayar masa da hankali" "Hanyar fita ya nufa, kamar shashasha ta bishi da kallo tana ji kamar ta dawo dashi su cigaba da abinda" sukeyi(Ikon Allah ) zamewa tayi ta kwanta hade da daukar bargon daya ajiye mata ta rufe jikinta har fuskarta tana matse cinyoyinta sakamakon jin wani irin abu da gabanta ke mata tasa hannu a hankali a hankali tana shafa lebunanta tana wani lumshe ido...Wani irin yanayi take ji a jikinta wanda ta kasa tantance na menene? (Naja'atu ta fara fahimtar abunda ke da akwai) Da kyar bacci ya dauketa cikin wani yanayi mara dadi kafin gari ya waye kuwa ta farka ya kai sau uku dan data rintse idonta zata ganta tare da Abbas din rungume da juna suna abubuwa masu dadi da wuyar mantawa. "Dalilin da yasa kenan da asubah ta riga kowa tashi a gidan, cikin kasala da mutuwar jiki ta nufi toilet ta" tu'be gabadaya kayan jikinta har pant bata bari ba dan tana jin danshi danshi a jikinsa shiyasa ta kasa yarda da tayi sallah haka ba tare da tayi wankar tsarki ba. Wanka tayi kafin tayi bursh ta daura alwala ta fito wanda yayi dai-dai da shigowarsa dakin domin tashinsu kamar yanda ya saba. Ganin ta fito daga toilet din ne ya sanya ya sauke ajiyar zuciya ba tare da yace komai ba ya juya ya fita. "Bayan ta kintsa jikinta sai ta shiga tashi yaran kamar koda yaushe, sai da ta tabbatar sun tashi sannan ta" "hau dadduma domin gabatar da sallah.............Yaran bayan sun idar da sallah cikin nutsuwa suka shiga gaisheta ta dinga amsawa cikin sakin fuska, ta kalli Saddiqa da fadin""Ya jikin naki?""? Saddiqa tace""Da sauki yanzu bana jin zafi sosai."" Tace ""Dama ai Dr yace"" zafin ciwon jiya da yau ne kawai insha Allahu idan kina shan magani zai warke."" Saddiqa ta mike ta nufi wardrobe dinsu da hannu daya take kokarin dauko musu inform tace""Ke maye haka? da ciwo a hannuki zakije skull.""? Saddiqa tace""Yaya Naja'atu kin san halin Uncle Aminu ko."" Tace""Komai halinsa dana sani dole ya daga kafa ki kwana biyu a gida hannuki" ya warke tukkuna. Suna wannan ta'kaddamar ya shigo dakin Sai suka shiga rige-rigen gaisheshi kamar dai koda yaushe. "Ya amsa a nutse yana tambayarsu, a nutse tace masa wai skull za taje a haka.""" "Ya kalli Saddiqan tare da fadin""Kiyi hakuri ki zauna a gida kwana biyu ki samu sauki sosai ni da kaina" zanje na na fadawa ancle din baki da lafiya. "A sanyaye tace""To shikkenan Abbah Naja'atu ya dan kalla yana so yayi magana sai kuma yayi shuru da" bakinsa yana sk yaga iya gudun ruwanta kama hanya yayi ya fita daga dakin kamar kuwa tasan "abinda yake cikin zuciyarsa, ta mike da sauri ta fito da niyyar shiga kicin nan ta sameshi a kan kujera" yana duba loptop. ganin ta nufi kicin din sai ya sauke ajiyar zuciya me sanyi yana rokon Allah ya tabbatar da zaman lafiya a tsakaninsu. Tsaf ta kammala musu break fast ta shirya daning din gwanin sha'awa duk yana zaune yana kallonta yanajin wani farin ciki a cikin zuciyarsa ganin ta tashi da kuzari kuma yanayin tafiyarta ya daidaita yaji dadin hakan sosai da sosai. Tare da yaran ta zauna suna break fast shi kuma yana zaune a inda yake da alama yana duba mihimun abu cikin loptop din dake gabansa. "Salim ne yayi sallama ya shigo palon, yana sanye da kananun kaya wanda sukayi masifar yi masa kyau!" "Salim dan gayu kwana biyu ya sakeyin fresh saboda yana samun kudi sosai gurin Kawun nasa, Salim" yanzu har bleecing yake yayi wani uban haske ga sumar kansa tasha gyara sai kyalli take. Naja'atu kasa dauke idonta tayi daga kansa sai murmushi takeyi wanda kana ganinsa kasan na farin cikin ganinsa ne.. "Shi kuwa Salim ganin tana nema ta tona musu asiri yasa yayi gaggawar kauda kansa daga inda take, kai" "tsaye gurin Abbah Abbas ya nufa ya ritsina tare da mika masa hannu da fadin""Barka da asubah Kawu.""" Cike da kulawa ya bashi hannu sukayi musabaha yana amsawa tare da tambayarsa "mahaifiyarsa...Yace.""Tana nan lafiya Kawu tace Ma na sake tuna maka da sa'konta.""" "Yace.""Kada ta damu insha Allah zan baka ka kai mata."" Yace.""To godiya take Kawu....Cikin basarwa Salim" "ya kalleta yana dan ya'ke yace.""Antyna barka da asuba ina fata kin tashi lafiya.""" "Naja'atu wani iri taji jin sunan daya kira dashi...Dauke kanta tayi tana 'bata fuska tace""Barka dai."" Hakan" da tayi sai ya faranta ran Abbah Abbas din yaji dadi data nuna rashin kulawarta a kan Salim din. "Salim ya kalli Mussadiq da fadin""Oya ku tashi mu tafi."" Mussadiq da Mufida suka mike sai ya kalli" "Saddiqa yace""Baby kefa?"" Tace""Ciwo naji a hannuna." "Abbah Abbas yace ""Yau saddiqa bata zuwa skull ta samu rauni a hannunta saboda haka idan kaje ka" shedawa ancle dinsu abinda ke faruwa. "Yace."" Insha Allah Kawu."" Lokacin daya kama hanyar fita tare da yaran Naja'atu binsa tayi da wani irin" kallo mamaki take sosai wai yau ita Salim ke kira da Aunty lallai Salim gaskiya ya bata mamaki. Mi'kewa tayi jikinta a sanyaye ta nufi daki ta kwanta! ganinsa yanzu ya sake tayar mata da hankali sai taji duk ta tsani komai na duniya Abbah Abbas din ma taji bata son kallon fuskarsa. Saddiqa ce ta shigo "dakin, ta zauna tana kallonta tare da fadin"" Yaya Naja'atu Abbanmu yace.""Wai ki bani magani na.""" "Harararta tayi tace""Kamar baki san inda maganin naki yake ba duba dan Allah da girmanki da komai ake cewa a baki magani kamar wata kankanuwar yarinya.""" Saddiqa ta shiga binta da kallo ganin yanda take mata magana a hasale! sai abin ya bata mamaki! cikin sanyin jiki taje ta dauki maganin tasha ta kwanta kan bed dinta...... Sai da ya gama abinda yake a tsanake tukkuna ya rufe loptop din ya mike ya nufi gurin cin abinci Komai gashinan a shirye a kammale cikin tsabta ba kamar tsarin Halisa ba da wani abun ma "idan tayi yake sashi tashin zuciya. Abinci yaci sosai irin wanda ya jima baici irinsa ba, ya goge bakinsa" da tissue kafin ya mike ya nufi bedroom dinsa domin kintsawa. Halisa bayan sun gama karya kummalo sai ta dauki wayarta tana dubawa gaskiya tayi mamaki sosai da "ko text bata bai turo mata ba, jikinta yayi sanyi sosai hankalinta ya sake tashi, ta azalzali Yaya Ramlatu ta shirye suje har gidan 'Yar shagamun su sameta." Babu arziki Yaya Ramlatu tayi wanka ta shirya a gurguje suka fito sunayi wa Sakina sallama. Binsu tayi da kallo har suka fita daga gidan bakinta bai daina yi musu adduar shiriya ba. *'Yar Shagamu* wacce taga jiya taga yau tsuhuwar kilaki ce ta gama yawan karuwancinta ta siyi gida "tana tara maza da mata suna she'ke ayarsu a gidan, ita kuma tana gefe ta kasa sigari da goro da shisha duk maiso yazo ya siya...." "Halisa da taga irin rayuwar da Yar shagamu takeyi a gidan sai data tsorata, tana zaune a tsakar gida daga" "ita sai breziyya da dogon siket ga maza 'yan bana bakwai sun kewaye ta.""" "Ramlatu da 'Yar shagamu ciki a daidaita sahu suka had'u shikkenan sukayi musayar numbar, tunda Yar" shagamu ta fahimci cewar Ramlatu yar son duniya ce sai ta makale mata suka kulla abota. sa'i da lokaci Yar shagamu na kawowa Ramlatu ziyara har gidanta itama Ramlatun tana zuwa gidan nata duk da kasancewarsa matattarar 'yan iska. Yar shagumu ta nufi dakinta cikin gaggawa ta sako wasu matsatstsun kaya da karamin mayafi ta fito tare da kallon wani dan daudu dake zaune gaban kayan "sana'arta tace""Kai sarai zan je unguwa ka kula min da kayana sosai kuma kada ka bawa kowa bashi kaji ko." "Cikin muryar mata yace.""Kada ki damu uwar dakina." "Yar shagamu tace""Ku tashi mu tafi."" Da sauri suka mike kowacce ta zira takalminta suka fita daga gidan." To kafin su nufi zauran malam din sai da Halisa ta tsaya a banki ta ciri kudi kimanin dubu dari "tukkuna............Wannan dai ba za'a kira shi da malami ba sai dai boka saboda yanayin kayan dake jikinsa da tarkacen kayan tsafin dake gabansa harda 'kokon kan mutum, ga wasu fatoci na dabbobin daji iri-iri a" manne a bangon dakin dake suke ciki... Yana bud'e bakinsa da niyyar magana wari! ya d'umame! gurin Halisa da Yaya Ramlatu da sauri suka sa hannunsu suka toshe hancinsu. Yar shagamu tayi saurin cire musu hannu tana girgiza musu kai wai kada su rufe. Boka ya kwashe da wata mahaukaciyar dariya kawai sai tsotsutsi marasa kyawun gani suka shiga zubowa daga bakinsa. Halisa da Ramlatu suka tsorata mutuka! sai jikinsu ya kama 'bari! ganin yana daukar tsotsutsin yana sawa a bakinsa yana taunewa! Halisa tsigar jikinta ta shiga tashi ta dinga dauke kanta saboda masifaffan aman dake kokarin kufce "mata. Cikin tsawa gami da yanayin hausarsa yace""Wacece Halisa a cikinku.""? Ai a furgice Halisa ta" "juyo inda yake tana kallonsa, Sai ya sake kwashe da wata dariyar yayin da tsotsutsin suka cigaba da zazzagowa daga bakinsa." "Cikin bada bada! yace""Rarrafo kizo gabana ki dinga d'ibar wannan tsotsutsin kina sawa a bakin ki kina" taunewa. Halisa taji cikinta ya karta gudawa na nema ta kufce mata! yau ta kawo kanta mahallaka. Boka ya zabga "mata razananniyar tsawa yace."" Nakadu yana kanki a tsaye idan baki bi umarinsa ba zaki tashi da shanyayyar 'kafa yanzu." "Yar Shagamu tayi maxa tace""Ayi mata afuwa ubana bata saba zuwa irin wannan gurin ba shiyasa." "Boka yace""To anyi mata afuwa. tayi maza tabi umarin da aka bata!" Yar shagamu ta zunguri Halisa da take ta faman zare ido kamar kace kyat ta ruga da gudu Ai kafin tayi aune taji mari tas! a kuncinta na hagu! kafin ta dawo hayyacinta boka ya soma wata iriyar jijjiga yana zabura hade da dukan tarkacen dake gabansa da jelar karan dake hannunsa. Yar shagamu ta fadi a "gurin tana makyarkyata da fadin""Halisa zaki janyo mana masifa da tashin hankali kiyi maza kafin boka ya dawo hayyacinsa kije kiyi abinda aka saki idan ba hakaba to dukkaninmu zamu shiga cikin matsala."" Jin haka yasa Yaya Ramlatu tsurewa da sauri ta shiga tura Halisa gaban bokan bakinta sai rawa yake kana" ganinta kasan tana cikin tashin hankali. Halisa ta gurfana gaban boka ta shiga kwasar tsutsa mai abun kyankyami tana sawa a bakinta tana taunawa cakal-cakal!! Boka ya daina jijjigar da yake ya dawo dai-dai yana wani irin huci!!! wani daddaud'an ruwan gumi na diga daga jikinsa. Hannusa ya dora saman kan Halisa yana wani sambatu kafin ya cire tare da daka mata tsawa wai ta matsa daga gurin Cikin mawuyacin hali Halisa ta matsa daga gurin tana jin yanda kanta ke wani irin sarawa. "Boka ya kallesu daya bayan daya kafin yace.""Wannan matar mai kama da bulunboti tana nema ta janyo" mana fushin babban aljini! yanzu kwana na ne kawai yake a gaba dan yanda ya ri'ke ni yana shan jinina da ban bashi hakuri ba to ba zai sake ni ba sai ya tabbatar da cewar na zaman mushe! kuma idan ya "gama dani kanku zai dawo.""" Sukayi masifar tsorata mussaman Yaya Ramlatu da taji fitsari na diga a wandonta "Wani koko ya dauko ya rike a hannunsa yana duba cikinsa, dariya yasa ya hannu ya dagawa Halisa wai" taje ya nuna mata abinda ke cikin kokon. Da sauri taje tana lekawa Abbah Abbas ne da Naja'atu suke magana a yayin da suke daf da juna! Kafin Halisa ta gama nazari taga Abbahn ya rungume Naja'atun a jikinsa yana shafa bayanta. "Boka ya ajiye kokan yana kallonta yace""Abbas da Naja'atu ko.""? Da sauri tace""Kwarai kuwa haka sunan" yake. Kinzo akan a taimaka miki domin a kashe masa mazakuta kada ya samu karsashi da kuzari a yayin "da yake tare da yarinyar hakane ko ba haka ba."" Tace""Hakane Boka! Yace.""Bukatar ki ta biya zamu tura" Aljana yar Zabira!! ta dinga shafe masa mazakutar a duk lokacin da ya tunkari yarinyar da niyyar auratayya. "Halisa tace""Alhamdullhi Allah nagode maka."" Boka yace""Maza ki gyara maganarki nan gurin ba'a kiran" "Allah yanzu zaki b'ata aikinki kice Kina godiya ga uban kafuran Aljanu."" Da sauri ta fadi hakan tana zare idonta..." "Boka yayi mirmushi mai muni ya kalleta da fadin""Sarkin Kafurai yace a fada miki labari mai dad'i nan da" "lokaci 'kan'kani ma yarinyar za'a neme ta a rasa karshe ma Auran ne zai mutu.""" "Wani irin sanyi ya sauka a zuciyarta da sauri tace""A mika min godiya gurin Sarkin sarakuna."" Boka" "yace.""Yana jinki gashinan a saman kanki."" Halisa tayi saurin waiwaya wa bayanta. Boka ya dinga" "mahaukaciyar dariya yana dan dukanta da jelar karan dake hannunsa yace""Idan kina so a bude miki ido" "ki dinga ganinsu kiyi min magana yanzu."" A tsorace ta matsa kusa da Yaya Ramlatu tana girgiza kanta." "Yar shagamu tace""To godiya muke ubana yanzu meye abin sadaka."" Shuru boka yayi yana kallon" "kusurwa! yakai minti biyar a haka yana ta gyada kansa tare dayin wasu surutai ya juyo yana kallon Halisa yace.""Ana bukatar jaririyar kyanwa(mage) mai launin 'baki da zaiba! Sannan ana bukatar kayan cikin kadangaru guda bakwai! sai gashin jikin Gurgun kare mai launin baki da jajayen ido, sannan kuma ana" bukatar bakar akuya mai dauke da karamin ciki. "Halisa tace""To shikkenan zan bada kudi sai ayi duk yanda za'ayi tunda ni dai bansan inda zan samu wasu" "abubuwan ba."" Boka yace.""Kada ki samu damuwa yanzu yanzu zamu tura aljanu su samo mana abubuwan bukata." "Halisa ta fito da kudi dubu dari cif ta ajiye gabansa, tace""gashinan Ubana ina fata ka dade kana kar'ko a" "duniya."" Boka yasa mahaukaciyar dariya da fad'in godiya nake kuna iya tashi ku tafi.""." Suka mike da sauri suka juya baya suna tafiya tare da sambatun kirari ga boka najadu mai aiki da kafuran aljanu...... *Ubangiji Allah kasa mufi karfin zukatan mu amin* *Ina taya d'aukacin al'ummar musulmi masoya Annabi Muhammad (Saw) murnar zagayowar ranar haihuwarsa ina rokan Allah ya karawa Annabi daraja da wasila fil jannati * *Ka/ki Daure ki bada sadaka a wannan rana domin Annabi! sadaka bata yawa bata kad'an! tufafi ko abinci ko wani abu makamcin haka* *Uwar gida karkiyi miyar nama ko ki soya kaji ki 'boye ki hana makotanki daure ki bayar dan Annabi! wanda kika bayar shine rabonki. Ina fatan dani daku mu kasance cikin walwala da farin ciki a cikin wannan rana mai albarka* *ALLAH YA MAIMAITA MANA * *33* Mdd "A mutukar gajiye suka dawo gida, Halisa ta nemi guri ta kwanta kanta nayi mata wani irin ciwo gabadaya" "yanayin jikinta ya sauya zuciyarta in banda tashi babu abunda takeyi, Ramlatu ta sami Sakina kishiyarta tana tambayarta abinci wai idan ta dafa ta basu zasuci." "kai tsaye Sakina tace""Nayi girki amma bashi da yawa mun cinye nida yara."" Tsaki mai karfi Yaya Ramlatu" taja ta bar gurun. Sakina kuwa cikin zuciyarta cewa tayi babu wani girki da zatayi musu tunda su din sun kasance masu sabon Allah tasan gantalinsu suka tafi na malamai shiyasa suka yi asubanci Yaya Ramlatu na kokarin hura wuta sai kawai taga Halisa ta fito a guje ta tsuguna bakin rariya tana ta kwara amai. Da sauri tazo ta tsaya a kanta tana yi mata sannu. Halisa ta dinga kakari tana rike kirjinta wani irin ba'kin amai take kai kanka ka ganshi sai ya tasar maka da "zuciya saboda muninsa, duk ta hada zufa! sai rike kirji takeyi." Da kyar Yaya Ramlatu ta riketa suka nufi daki. kafin su kai ga shiga dakin Halisa ta yanke jiki ta fadi a gurin.Wani irin abu ta shagayi kamar wacce farfadiya ta kama ta. Iya firgita Ramlatu tayi ta kai ta kawo a gurin tana kiran sunan Halisan gami da tattaba jikinta. "Sakina ta fito daga dakinta tana ganin Halisa a kwance tana turjiya sai hankalinta ya tashi, cikin zuciyarta" "tace""Dama kowa ya sayi rariya yasan zata zubar da ruwa koda Halisa bata da iskokai to gurin yawon bokayenta zata iya haduwa dasu." Ramlatu cikin tsoro ta matsa gefe guda tana zare ido tunda take da Halisa bata ta'ba sanin tana da iska "ba sai yau...Sakina ta tsuguna gaban Halisa ta shiga tofa mata adduoi tana shafa mata a fuskarta, cikin ikon Allah Halisa ta daina buge-bugen da takeyi a gurun bacci ya dauketa" "Sakina ta kalli Ramlatu a nutse tace""Wallahi Ramlatu kuyiwa kanku fada ku daina abinda kukeyi yanzu" "meye ribarku a duniya idan kun cutar da wani, ki duba fa ki gani Halisa aljanu takeyi kuma daka ganinsu" masu cutarwa ne me zai sanya ku dinga kai kanku ga halaka! me kuke nema a duniyar nan da gabadayan "mu zamu tafi mu barta.""" "Ramlatu ta daga mata hannu da fadin""Kinga Sakina ba wa'azi nace kiyi min ba, ko wane mutum da kika" "ganshi da akwai kashi a gindinsa kuma kina maganar mu daina cutarwa to wai wa muka cuta! idan ni macuciya ce ai ba zaki kai labari a gidan nan ba, dan haka dan Allah idan ba zaki fadi alkairi ba to kiyi shuru da bakinki."" Sakina tace""Alheri na fada miki ba sharri ba kuma dama ita gaskiya ai daci gareta kun gama da Halimatu yanzu kun dawo kan Naja'atu to ku sani duk abinda Allah ya hukunta zai faru a kan" mutum sai ya faru saboda haka wallahi ku guji haduwarku da Allah. Yaya Ramlatu jikinta ne yayi sanyi da kalaman Sakina gabadaya bata ta'ba tsammanin cewar sakina tasan "irin abunda sukeyi kan halimatu ba cikin borin kunya tace""Allah yasa dai aljanna ba a hannuki take ba ballanta na ki hanamu shiga." Sakina ta girgiza kanta cike da takaici ta bar gurun Yaya Ramlatu ta tsirawa Halisa ido tana kwance kasan simintin tsakar gidan lokaci guda ta fyad'e tayi "wani iri da ita, gaskiya itama jikinta yayi sanyi da aikin wannan bokan daka gani bashi da imani tana jin tsoro kada ya cutar mata da dan uwa." Jikinta a sanyaye ta nufi kicin taje ta dora abinci ta fito. Dakinta ta shiga ta dauki wayar Halisa ta shiga neman numbar 'dan uwan nata Abbah Abbas na kasuwa yaga kiran wayar kamar kada ya daga wayar sai kuma ya daure ya daga cike da tsare gira yayi sallama. "Sai kawai yaji muryar Yayarsa, bai damu ba saboda yasan kusancin dake tsakanin Matar tasa da Yayar" tasa "Yace.""Yaya barka da rana ina fatan kuna nan lafiya? Tace""Lafiyarmu kalau ya kasuwa.""?" "Yace.""Alhamdullhi dazu Salim yake sake tuna min da sa'kon ki insha Allahu zan bashi ya kawo miki yau." "Yaya Ramlatu tace""Ni ba wannan ne yasa na kira ka ba inaso na tambayeka me ya hada ka da Halisa.""?" "Kai tsaye yace.""Me tazo ta fad'a miki.""? ""Tace kana fifita yaranka a kanta kuma kana rashin adalci a" "gidanka."" Cikin takaici yace.""Yanzu tana ina.""? Tace""Gata nan muna tare da ita bama ta da lafiya.""" "Yace.""Me yake damunta.""? Kai tsaye tace""Iskoki take dan Allah Abbas ka rike matarka domin itace matar" rufin asirinka duk arzikin daka samu tare da ita ka samu bai kamata kana fifita 'ya'yanka a kan matarka ba. "Yace""Dan Allah Yaya ki daina wannan maganar Halisa muguwar makarciya ce itace take zalintar yaran" "nan amma tazo ta juya miki magana har yanxu ta kasa gane muhimancin rike maraya.""" "Ramlatu tace""To me yasa zaka ce lallai sai itace zata kula maka da yaran meye amfanin auran Madadi da" "kayi da Naja'atu.? Sai maganar ta bashi mamaki sosai wato saboda yayi auran Madadi sai akace Halisa ba ruwanta da 'Yayansa sai wanda ta haifa, Ganin Ko ya fahintar da yayar tasa ba zata gane ba yasa yace.""Mu bar wannan maganar dan Allah sabida ba zaki ta'ba fahintata ba Halisa kuma bani nace ta fita daga gidanta ba, idan taga dama ta dawo shikkenan idan tana ganin zaman gidanki yafi mata sai taje" tayi . "Yaya Tace""Ai shiyasa na kira ka domun na baka hakuri saboda nasan bata kyauta ba tunda ba kaine kace" "ta fitar maka daga gida ba, dalilin daya sa na yanke hukuncin dawo da ita bayan sallahr isha'i."" Yace.""To kin taimake ta dan nayi alkawarin babu inda zan taka naje domin dawo da ita, sannan kuma inaso ki gargade ta sosai koda ta dawo bana son tashin hankali a matsayinta na babba kullum itace mai tayar da" "fitina a cikin gidan."" Ya Ramlatu tace""Magana dai ta kare insha Allah zanyi mata fada.""" "Sallama sukayi da juna, ta kashe wayar ta fito nan ta tarar da Halisa ta tashi zaune tana ta soshe soshe" "sai gumi takeyi ta kalli Yaya Ramlatu da fadin""Me ya faru ne na ganki kwance a kasa a cikin rana."" Ramlatu tace""Iskar ki ce ta kayar dake! Halisa shuru tayi tana kallon guri guda, Ramlatu tace""Yanzu mukayi waya da Abbas da sauri tace""Me yace dake.""? Yaya Ramlatu tace.""Kin san halinsa da tsari gabadaya ya d'ora laifi a kanki! dan haka kada ki damu ki koma domin ganin yanda zamantakewar gidan" zata sauya na tabbatar da cewar kina komawa hankalinsa zai dawo kanki. """Humm! kawai tace ta fara kokarin mikewa jikinta duk yayi kura sabida birgimar da tayi a gurin Ya" "Ramlatu ta nufi kicin da fadin"" Bari na juye miki ruwan sanwar abinci dana dora a wuta sai kiyi wanka dashi ko kyaji dadin jikinki...Halisa ba tare da tace komai ba ta daga labulan dakin Ramlatun ta shiga taje ta zauna tare da zabga tagumi! duk ranar da iskarta ta tashi takan kasance cikin kunci da takurewar zuciya kuma gabadaya takan rasa kuzarin jikinta, shiyasa bata son abinda zai tayar mata da hankali yanzu ma ta tabbatar da cewar zuwanta gurin boka ne yasa suka tashi, to amma babu damuwa mutukar" bukatarta zata biya magana ta kare. "Ita kuwa Naja'atu a kwance ta wuni damuwa da bakin ciki sun cika mata zuciya, wai Salim ne ke kiranta" da antinsa wannan al'amari ya bata mamaki. "Sai kusan biyar da rabi na yamma ta shiga kicin domin shirya musu abincin dare, farar shinkafa da miyar" "kifi kawai tayi musu ta shirya daining din kana taje tayi wanka ta shirya jikinta zamanta tayi a dakin, su kuma yaran suna falo a zaune dan tunda suka dawo daga makaranta suka ga yanayinta sai duk jikinsu yayi sanyi a duniya sun tsani suga tana bacin rai duk sai suma su shiga damuwa mussaman mussadiq." "Tana zaune kan dadduma bayan ta idar da sallahr isha'i taji muryar maigidan tare da yaran, motsawa ba" "tayi ba ya shigo dakin da sallama a bakinsa. Kamar mai ciwon baki tace""Sannu da zuwa."" Yace""Sannu" "ina fatan kun wuni lafiya.""?" "A takaice tace""Lafiya kalau."" Yanayin yanda take amsa masa magana yasa ya fahimci cewar tana da" "damuwa, ba tare da ya sake cewa komai ba ya fita daga dakin, zumbura bakinta tare da barin kan daddumar taje ta kwanta kan bed cike da damuwa a zuciyarta." "Yaya Ramlatu da Halisa ne sukayi sallama suka shigo palon a tare, gabadaya yaran suka yi tsamo-tsamo" "jiki a sanyaye suka amsa sallamar. Halisa ta dinga bin palon da kallo tana ta'be bakinta, ita kuwa Yaya" ramlatu zama tayi kan kujera tana amsa gaisuwar yaran Halisa ta bude bakinta kenan za tayi magana ya fito daga dakinsa. Kauda kansa yayi daga inda take dan har yanzu bai daina jin haushinta ba. Ita kuwa Ramlatu na ganinsa sai yasa ta janyo Saddiqa tana duba hannunta tare da yi mata sannu da jiki! "Yarinyar ta dinga amsawa a tsorace, itama Halisan a sanyaye taje tana duba hannun yarinyar sai wani marairaicewa take kamar mutuniyar arziki" .....Shi kuwa ko kallonta baiyi ba yaje ya zauna suna sake gaisawa da yar uwarsa. "Halisa ta wani risinar da kai kamar mutuniyar kirki ta gaishe shi, amsawa yayi hankalinsa nakan mussadiq" inda ya umarce shi da yaje ya kira Naja'atu tazo su gaisa da Yaya Ramlatun Halisa kuwa ganin yana dauke mata kai duk sai jikinta yayi sanyi tana ganin anya kuwa aikin bokanta zaiyi tasiri a kansa ta lura yana da taurin kai da kuma dafa'i a jikinsa tayi yaji a maimakon ya tarairayeta ko kallo bata isheshi ba. "Koda Mussadiq ya gaya mata sa'kon Abban nasu cewa yaron yaje yace tayi bacci, yaron yayi jim yana" "tunanin maganar ta buga masa tsawa da fad'in 'Ka wuce daga kaina kaje kace nayi bacci."" Yace.""Yaya Naja'atu karya fa babu kyau dan Allah kizo ku gaisa kamar yanda Abbah yace." "Mikewa zaune tayi tana hararsa tace""Naji jeka gani nan zuwa."" Da sauri yaron ya fita daga dakin Sai" da tagama zamanta sannan ta mike ta fita. "lokacin ma yaya ramlatun ta mike da niyar tafiya. Ta dan risina murya a kasa tace"" Yaya sannu Ina wuni.""" "Ta'be bakinta tayi tace""Na wuni kalau ai da kin sani kinyi zamanki ma ba sai kinzo mun gaisa ba."" Shuru palon yayi dan yanda ta fadi maganar kowa ya fahimci a hasale take da abinda Naja'atun tayi...Hanyar futa ta kama Abban da Halisa suka bi bayanta. ita kuwa juyawa tayi ta koma daki babu wata damuwa a cikin ranta dan tun ranar da matar ta zagi iyayenta ta daina jin tsoronta ba za tayi mata rashin kunya ba amma kuma ba zata lamunci a dinga tozarta mata iyayenta ba Daki ta koma ta kwanta tana cigaba da tunanin mafita a gareta. 'Kawarta Munira dake can jos itace ta fad'o mata, tabbas da tana da waya to" "data kira Munira tunda tana da numbar ta tasan zata bata shawarwarin da zasu taimake ta amma ta daina zuwa ta kaiwa anty Maryam shawara sabida ta lura itama tana goyon bayan zamanta a gidan Abbah Abbas din shuru tayi tana sake nazarin yanda za'ayi ta sadu da Munira, tana ganin za tayi" dubarar daukar wayar Abba Abbas din ta kira ta tunda tana da numbar ta. wannan tunanin da tayi sai yasa ta samu sassauci a cikin zuciyarta. Halisa kam bayan sun raka Yaya Ramlatu sai tabi bayansa dakinsa ta shiga tana wani salo-salo ta rike "hannunsa kawai sai ta fashe da kukan kissa tana bashi hakuri wai wallahi ranta ne ya 'baci shiyasa ta yanke hukuncin bar masa gida amma insha Allahu ba zata sake kwatantawa ba."" Yace.""Idan kina ganin yin hakan shine mafita a gareki to sai ki cigaba da daukar mayafi kina tafiya ni dai ko yau na rabu dake idan nayi ra'ayi zan maye gurbinki da wata sabida haka wallahi duk sanda na nuna miki kuskuranki akan wani abu kika dauki mayafi kika fita to ki tabbatar da cewar kin fita daga gidana har abada."" Murya na rawa tace""Dan Allah ka daina wannan maganar insha Allah ba zan sake ba raina ne kawai ya baci shiyasa na tafi amma ka daina cewa zaka rabu dani har abada. Yace.""Ai na lura hakan kike so shiyasa nake sake" "jadadda miki."" Tace"" Kayi hakuri na daina magana ta wuce insha Allahu." Halisa sai da tasan yanda tayi ta wanke kanta a gurinsa sannan hankalinta ya kwanta. Abbah Abbas shi kadai yayi kwanciyarsa dan da Halisan da ita Naja'atun babu wacce ya tunkara ya rabu "dasu su samu nutsuwa tukkuna...Bangaran Naja'atu ma tayi mamaki sosai da ba taji yayi mata wata magana ba koda asubah da ya shigo tashinsu lafiyar Allah suka gaisa babu wani abu a tare dashi ya fita daga dakin, sosai hakan yayi mata dad'i dama bata so ya dinga ta'ba ta yana tayar mata da sha'awa tafi so suyi nesa da juna har Allah yasa su rabu Yini tayi cikin walwala dan har palo ta fito ta zauna tana" "kallo ita kuma halisa taci kwalliya kamar itace amaryar sai shige da fice take tsakanin kicin da dainng an shiryawa maigida girki iri-iri kuma sai jan Naja'atu take da hira, to itama ganin Halisan ta dawo da sigar son a zauna lafiya sai ta saki jikinta tana amsa mata jefi-jefi! Koda maigidan ya dawo ya gansu suna hira ga yaran suna zaune a kusa dasu, sai ya shiga mamaki sosai ikon Allah yau Halisa da Naja'atu ne a zaune a guri guda suna hira harda dariya! kyataccen murmushi ne a fuskarsa ya shiga kallonsu yana jin dadi Halisa da sauri ta iske inda yake ta kar'bi abubuwan dake hannunsa tana masa barka da zuwa, ita" kam naja'atu sunkuyar da kanta tayi ba tare da wata cikakkiyar kulawa ba tayi masa barka da zuwa. Ya amsa babu yabo babu fallasa ya kama hanyar dakinsa. Yau kwalliyar da Halisa tayi ta tafi da imaninsa sosai Halisa 'yar gayu ce gashi ta iya ado da d'inkunan banza atamfa ce a jikinta riga da sket amma anyi mata dinki banza dan gabadaya saman rigar net ne brest dinta duk a waje ga wani masifaffan kamshin turare da takeyi Halisa duk da ta san da cewar ba a cikin kwanakinta take ba hakan bai hanata bashi kulawa ba saboda tana so ta sake wanke kanta a gurinsa ta gane ba da asiri kad'ai zata tsaya ba dole sai ta had'a kissa da siyasa sannan bukatarta zata biya. A Nasa 'bangaran kuwa shima bai hanata tattalinsa ba dan sabida ganin wacce alhakin hakan ke kanta bata wani nuna yana da muhimanci ba a gurinta shiyasa ya kyale Halisan take cin karanta babu babbaka Naja'atu ganin sun kwashe sama da rabin awa a daki basu fito ba sai taji zuciyarta nayi mata sake'sake! dan sabida tasan baya dogon zango a daki yake fitowa yaci abinci amma yanzu sun kai minti talatin basu fito ba. Ranta ne ya 'baci! tayi d'if! a gurin yaran sai hayaniya suke mata akam..Koda suka fito kin kallonsu tayi tana dai kallonsu ta gefan idonta suka nufi gurin cin abinci yaran ma suka mike suka nufi gurin suka zauna. Ita kuwa ko motsi ba tayi ba a gurin ta tsirawa tv ido kamar kallo take nan kuwa mugun haushin "halisa ne ya cika mata zuciyarta. Halisa cikin kissa tace""Naja'atu ki taso muci abinci mana." "Shuru tayi kamar ba taji ba.Halisa ta daure ta sake yi mata magana, kai tsaye tace""Kin san bana cin" "sakwara wallahi naga kamar ita kikayi ko"" Halisa tace""Ayya wallahi na manta amma ai ba ita kadai nayi ba akwai jollop din taliya tare da dankali nasan za tayi miki." "Murmushi tayi kamar gaske tace""Wai gaskiya anty Halisa jollop din taliya bata dame ni ba dama dai da" "miya ce to da sauki.""" Mugun takaici ya turnuke Halisa sai kawai taja bakinta tayi shuru ta cigaba da zubawa yaran abincinsu. "Shi kuwa Abba duk yana jinsu baice musu komai ba, ya ajiye wayar da yake dubawa yayi bisimillah tare" "da fara cin abincinsa. Naja'atu mikewa tayi daga inda take zaune ta nufi d'akinsu Saddiqa, ta wutsiyar" "idonsa ya bita da kallo yana mamakin halinta sai ana zaune kalau da ita lokaci guda ta burkice jiya dai lafiya lau suka yini amma tunda aka wayi gari ya rasa gane kanta, abinci ma tayi masa k'aura saboda wani dalili nata." Bayan sun kammala cin abincin Halisa da yaran palo suka koma suka cigaba da kallon tv shi kuwa Abbah "Abbas dakinsa ya nufa, ko minti biyar baiyi ba a ciki ya fito, Halisa na kallonsa ya nufi dakin da take... girgixa kanta tayi cikin zuciyarta tace""Duk wannan kulafucin naka sai yarinyar nan ta zama haramiyarka." "Samunta yayi tana kuka yayi tsaye a kanta tare da kiran sunanta, hannu tasa tana goge fuskarta ta kasa" "dagowa ta kalleshi...Yace""Kin 'ki cin abincin Halisa duk da kokarin da take miki kin watsa mata 'kasa a ido to inaso yanzu ki fada min abinda kike so kici tunda dai nine bakya so na huta sai na fita na siyo miki." "Zumbura bakinta tayi tace""Bana bukatar komai sai abu daya kuma nasan ba zakayi min shi ta dadin rai" "ba."" Yace.""Ki fada min kome kike bukata insha Allahu idan ina da iko dashi zanyi miki.""" "Tace""Abbah tunda ka samu biyan bukatarka a kaina me zai hana ka rabu dani naje na auri dai-dai dani.""" "Yace.""Okey dama abinda yake damunki kenan kike ta nukufurci.? Dauke kanta tayi tana shakar hanci." "Yace.""Ki rubuta ki ajiye cewar ni Abbas banga abinda zai sanya ni na rabu dake ba ni dan halak ne! Ki sani abu daya zakiyi min a duniya na iya rabuwa dake kuma bana fatan kiyi min abun har abada dan haka idan zaki samu nutsuwa ki samu idan kina ganin zaki cigaba da tayar hankalinki gami da yiwa kanki horon yunwa to sai ki mayar da hankali ni dai nasan ko a lahira Allah ba zai tuhume da hakkinki ba tunda" "nasan ina iyakacin bakin kokarina.""" Yana kare maganarsa ya kama hanya ya fita daga dakin ranshi a tsananin bace! Halisa ganin ya fito ransa a 'bace! sai wani farin ciki ya saukar mata a zuciya ta girgiza kanta cikin ranta "tace""Insha Allahu kun dinga samun sa'bani kenan har mai afkuwa ta afku..Hanyar fita ya nufa ta bishi da kallo tare da dora kafarta kan daya tana girgizawa." Naja'atu kuwa yana fita daga dakin kwanciya tayi ta cigaba da share hawaye ta rasa wane irin mayen "mutum Allah ya hadata dashi, ance ba'a sonsa ba'a son zama dashi ya nace sai kace kaska aikuwa zata shuka masa rashin mutunci wallahi." "Sai bayan goma na dare ya dawo gidan lokacin duk yaran sunyi bacci Halisa da Naja'atun ne ba suyi ba," "kai tsaye dakin yaran ya nufa...tana kwance kasan kafet ta rufe kafafunta da bargo ta ganshi a tsaye a kanta, da sauri ta mike tana zare ido hade da gyara botiran rigarta da suka zube." "Babu wasa a fuskarsa yace.""Tashi ki tafi dakina ki kwanta a can."" Kallonsa ta shigayi bakinta na rawa! Ya" "buga mata tsawa yana nuna mata kofar fita da hannunsa, babu shiri ta mike da sauri tana neman hijabinta, ta dauka tasa ta fita daga dakin." Tana fita ya shiga bin gadajen yaran nasa daya bayan daya yayi musu addua kamar yanda ya saba kana ya fito tare da rufe musu kofa Yana juyowa ya ganta a rakube kamar kace kyat ta ruga da gudu...Hannunsa da babu komai a rike dashi ya nuna mata kofar dakinsa. Ta gane abinda yake nufi sai ta kama kuka tana sake matsawa wai ba zata shiga ba. "Tunkaro inda take yayi, da sauri ta 'buya bayan labule! yasa hannu ya janye labulen ya riko hannunta da" kyau! suka nufi dakin. "Turjewa ta dinga yi tana bashi hakuri! yaki sauraranta sai da suka shiga dakin tare, yasa key a jikin kofar" "sannan ya sakar mata hannunta. Abincin ta da ya shigo dashi ya ajiye mata da fadin""Ga abinci nan kici" domin yau babu abinda zai hanani naci abincin jikinkin ki tunda na lura bakya jin magana na daina tausaya miki. """Dan Allah Abbah kayi hakuri na fada maka abinda ke zuciyata ne dan saboda bana so mu zauna zaman" "'kiyayyar juna ni da kai wallahi har abada ba zan soka ba."" Dariya yasa yana kallonta yace.""To in banda abinki ke waye yake miki maganar so! ni nan ban danmu ki soni ba yarinya ki cigaba da 'kina har karshen" rayuwarki ni kuma zan cigaba da sonki da kuma kasantuwa tare dake. Ganin yanda ya mayar da abin wasa yasa ta tsuguna a gurin ta hade kai da gwiwa tana cigaba da kukanta. Barinta yayi a gurin ya nufi toilet yayi wankan sa tsaf ya fito ya shirya cikin kayan bacci ya zauna yana duba loptop dinshi Ita kuwa data gaji da kukan kwanciya tayi a gurin ba tare da ta dauki abincin taci ba. "Sha daya da rabi na dare ya gama abinda yake ya rufe loptop din ya mike iske inda take, sunkuya wa yayi" ya ciccibeta ya nufi bed din da ita. yana kwantar da ita ta farka sai ta mike zaune da sauri tana kallonsa. Bedlamp kawai ya kashe dakin yayi duhu sosai cikin gaggawa ta matsa karshen gago gabanta na faduwa! Hannunsa yasa ya lalubota kawai ya shiga kici kicin cire hijab din dake jikinta hannunta tasa tana "hanashi, ya murde hannayeta ya fizge hijab din..Rungume ta yayi sosai a jikinsa sakar mata nauyinsa...Soyayyarsa mai wahalar samu ya shiga gwada mata, kamar wacce take a bukace da al'amarin sai ta sakar masa jikinta sosai wanda hakan shima ya bashi mamaki sosai, jin tana sakin nishi hade da" tura masa brest dinta ya gane cewar ta kai inda ake so. Yasa hannunsa a gabanta yana shafawa gabadaya yaji gurin ya jike lafiyayyar ajiyar zuciya ya sauke yana wani makyarkyata ya raba kafafunsa a kanta ya kama hannunta ya dora kan joystick dinsa yana sauke ajiyar zuciya. Kasa rikewa tayi hannunta ya dinga kyarma! ta cire da saurin gaske. "Ya sake kama hannunta ya d'ora a kai. A dashe yace.'' Ki Kama ki rike sosai a hannuki."" Cikin rawar baki" "tace""Um!um! Abbah ba zan iya ba dan Allah ka sauka.""" "Yanayin yanda tayi maganar sai ya kara tunzurashi, ya matse hannunta dake kan joystick din nasa kawai" ya shiga murzawa! ta dinga jin wani irin santsi santsi a hannunta ga joystick din nashi na sake kumbura..Gabadaya rikewa tayi gabanta ya cigaba da zubar da ruwa yana mata kaikayi...Cigaba tayi dayi masa wasa suna ta sakin wani irin nishi!! Sauka yayi ya gyara cinyoyinta yasa kansa a gurin ya shiga lasar ruwan dake fito mata yana tusa harshensa a cikin gurin. Gigicewa tayi ta wani kankame! masa wuya tana makyarkyata hade da kiran sunansa. Wai wannan dadin yana so ya zautar da ita dan sai sambatun kiran sunansa take tana tsotsar lips dinta sai kaca mayya! Abba Abbas wani irin salo yake mata na fitar hankali wanda ya sanya ta dinga kuka tana rirrike shi bata so ya daina abinda yake mata sabida dadin da take ji ya wuce misali Daf da zata samu satisfaction ai gabadaya zautuwa tayi cinyoyinta suka dinga rawa tabi ta dinga yakushin fatar jikinsa tana shashshekar kuka kamar wacce ranta zai fita. Yana jin d'umin sperm dinta a bakinsa yayi saurin cire bakinsa ya saita joystick dinsa zai sa. Lanjarewa tayi ta lauye ta dawo tamkar lagwanin risho saboda laushi da kan'kanta!! Cike da wani irin yanayi na tashin hankali ya rike joystick din tasa yana jijjigata! *Ina so ku kar'bi labarin littafin nan a yanda yazo bana son 'korafi hakan zai iya dakusar dani ku cigaba da bina kuna bani kwarin gwiwa har Allah yasa na isar da sa'kon da nake so na isar a cikin littafin My "Dota Aunty zeey naga comment din ki Kinji maganar asiri jikin ki yayi sanyi, kada ki damu labarin zai" "tafi cikin tsari kuma zan nishadantar daku burina kawai ku cigaba da nuna kulawarku a kaina kuna sharhi kan littafin, kamar yanda kukayi kwanaki biyu da suka wuce naji dadin haka sosai Sannan kuma ina" neman afuwarku na rashin samun update sai biyu a rana wallahi abubuwa da yawa suka sha kaina gashi bani da cikakkiyar lafiya amma insha Allahu komai ya daidaita zan faranta muku rai* *INA MI'KO GAISUWATA GARE KI UWAR DAKINA HAJIYA SHAFA'ATU S YARI ALHERIN ALLAH YAZO INDA KIKE MACE MAI FARAR ANIYA* *Littafin na kudi ne!* "Koda zaki ganshi a gruops to na sata ne, idan kina bukatar biyar kudin littafin to ga yanda abin yake" Vip gruop#600 Normal gruop#300 Accont: 0542382124...Binta Umar gtbank...Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* BHRBN *34* Cikin wani irin yanayi na tashin hankali da damuwa ya shiga jijjiga joystick din nashi burinsa kawai yaga "ta mi'ke amma ina wani irin kwanciya tayi ta lan'kwame ta koma tamkar ta karamin yaro, lokaci kankani kuma ya dinga jin yanayin jikinsa na sauyawa jikinsa ya rikice da wani irin zafin zazzabi sai ya shiga makyarkyata kawai sai ya fad'i saman jikinta ya matse ta sosai a jikinsa yana wani irin nishi hade da takure jikinsa a nata. Naja'atu tsorata tayi da yanayin data ganshi tasa hannunta jikin wuyansa taji wani irin zafi! tsoro ne ya shigeta, a hankali take kiran sunansa ""Abbah"" Abbah' Da kyar ya amsawa da fadin''Rufe ni da bargo bani da lafiya."" Da sauri ta janyo bargo da hannunta tayi dubara ra rufe musu jiki" "tana jin yanda jikinsa ke wani irin kaf-kaf yana datse hakoransa, hawaye ta shigayi tana mamakin" wannan wace irin rashin lafiya ce data rufe shi lokaci guda. Dan juyawa tayi a hankali ta kalli fuskarsa taga ya rintse idonsa yana janyo numfashi da kyar. "Mikewa zaune tayi ta kunna bedlamp tana kallonsa, nan taga yasa hannunsa kan joystick dinshi ya rike," gurin a hankali ta kai hannunta tana so ta cire hannunsa daga gurin dan gaskiya ta tsorata da yanayin da ya shiga lokaci guda......'Kin bari yayi ta gani ya rufe gurin sosai! a sanyaye ta mike ta shiga toilet jikinta ta gyara tayi wankan tsarki ta fito ta sanja kayanta ta dawo bed din nan ta tarar dashi bacci ya daukeshi still hannunsa na rufe a gabansa Itafa so take taga abinda yake 'boyewa shiyasa ta kasa hakura sai dai tayi dubarar cire hannunsa daga "inda ya rufe, gabanta ne ya fad'in ganin yanda joystick dinshi ta zama 'yar mitsitsiya tamkar ta yaro karami! tsorata tayi da sauri ta rufe masa jikinsa ta kwanta tana mamakin al'amarin, Tunani takeyi to me ya janyo masa shiga irin wannan yanayi lokaci guda? Ta'be bakinta tayi ta sake juyawa ta kalli fuskarsa, dan tausayi ya bata ganin yanda ya koma wani irin abin tausayi, hannu ta mika ta kashe bedlamp din ta" dan ja bargo dake jikinsa ta rufe jikinta...Da kyar ta samu bacci ya dauketa. Abba Abbas kuwa wani irin mafarki yake yi wai gashi yana sex da mace mai siffar Naja'atu amma yayi "yayi yaga fuskar yarinyar ya kasa gani, sai dai kuma yayi masifar gamsuwa da yarinyar dan ji yayi yarinyar ma kamar tafi sauran matan duniya dad'i" Aikuwa ya tashi yaga jikinsa duk ya baci! mikewa zaune yayi ya rike kanshi hade da kiran sunan Allah! a fili! firgigit ta mike zaune tana kallonsa. Bedlamp ta kunna tana sake kallon yanayin sa...ganin ya rufe fuskarsa da tafukan hannayesa yana salati yasa ta sake tsurewa a sanyaye ta kira sunansa...Bai amsa ba kiran sunan Allah kawai yake dan gabad'aya jikinsa ya rikice masa ya rasa abinda ke damunsa. Bayansa ta dafa murya na rawa "tace""Abbah sannu baka da lafiya ko.""? Bude idonsa yayi ya kalleta, da sauri ta matsa baya gabanta na" "wani irin faduwa, gabad'aya an sauya masa hallinta a idonta." Jikinta na kyarma! ta sauka daga bed din ta kama hanyar fita daga dakin tana waiwayensa..Shi kuwa kallo ya bita dashi yana so yayi mata magana amma ya kasa a kunnansa aka kira sallah ka idar gabad'aya ya kasa tashi ya gyara jikinsa ballanta na ya samu damar gabatar da sallahr asubahi. Naja'at a firgice ta shiga dakinsu su Saddiqa ta samu guri ta zauna tana addua a zuciyarta tsoro da fargabar abinda ta gani shine ya dameta motsi kadan za taji gabanta ya fad'i! da kyar ta iya yin alwala tayi sallah ta tashi yaran domin suyi sallah. Abbah Abbas ya jima zaune yana ta addua a fili da zuciyarsa kafin Allah ya bashi sa'a ya mike cikin "tangadi ya nufi toilet din yayi wanka kana ya daura alwala ya fito ya kintsa jikinsa, lokacin gari ya soma haske dole a gida yayi sallahr sa, abinda bai ta'ba faruwa ba dashi, bayan ya idar da sallahr sai ya dauki al'kurani mai girma ya shiga karantawa, tunda ya fara karanta al'kuranin ya samu nutsuwa a tare dashi tunaninsa ya dawo daidai sai gabadaya ma ya manta abinda ya faru dashi a daran jiya, cike da kuzari ya" rufe al'kur'anin ya ajiye shi a gurinsa ya fita daga dakin Yana shiga dakin yaran Naja'atu tayi kasa da kanta bata son sake kallon fuskarsa sabida gudun ganin abinda ta gani a tare dashi dazu Tana jinsa suna gaisawa da 'ya'yansa ba tare da ta kalleshi ba ta gaishi ya amsa cike da kulawa kana ya fita daga dakin. Halisa na tsaye a bakin daning tana kokarin gyarawa yana fitowa suka hada ido! wani irin murmushi ya "sakar mata, Halisa ta shiga mamakinsa sai ita ta mayar masa da murmushin cikin kissa da kokarin janye" "hankalinsa tace""Yallabai barka da asubah."" Yana kokarin zama kujarar daning din ya amsa da ""Barka dai uwargida kin tashi lafiya.""?" "Dariya tayi tace""Lafiya kalau."" Kallonta ya shiga yi yana mirmushi yau gabadaya gani yayi Halisan ta dawo" sabuwa a gurinsa komai nata burgeshi yake..Ita kuwa tamkar ta zuba ruwa a kasa tasha saboda farin ciki. Break fast din ta hada masa suna hira..Su Naja'atu suka fito daga dakin ita da yaran...Daning din suka "nufa suka zauna...Halisa ta kalli Naja'atu cikin munafikin murmushi na samun nasara tace""Naja'atu an tashi lafiya.""?" "Sak tayi tana kallonta! lallai a kwai wata a kasa yau ita Halisa take gaisarwa basarwa tayi tace""Lafiya lau" anty Halisa. "Tace""Ya yara suka kwana.""? Ganin tambayar tayi kamar ta rainin hankali sai kace wata mai aiki zata" tambaye ta kwanan yara...dan haka kawai sai tayi mata shuru ta janyo fulas din tea tana tsiyayawa a cup.....Cikin nutsuwa take breakfast din tana kallon dramar da sukeyi ko kunyar yara basa ji sai jifan junansu suke da kallon soyayya ta lura gabadaya Abbah Abbas din hankalinsa na kan halisa gabadaya yanayin sa ya nuna ita kadai yake bukata. 'Bacin ran abinda suke yasa ta ajiye "Cup din hannunta ta mike ta bar musu gurin, Halisa ce kawai ta bita da ido shi kuwa bai ma san ta bar" "gurin ba, halisa kawai yake bukata wata muguwar sha'awarta ce take bijiro masa. Halisa mikewa tayi ta" nufi dakinta tana wata iriyar tafiya. Bayanta yabi da kallo yana jin yanda joystick dinsa ke sake "kumbura, Ba tare da yaja wani dogon lokaci ba a gurin yabi bayanta..........Yara kam suna gama break" fast din su dakinsu su koma domin yau asabar basu da zuwa makaranta..... Koda ya shiga dakin Halinsa samunta yayi kwance a bed babu komai a jikinta tayi wata irin kwanciya wacce tayi masifar tafiya da hankalinsa Ya sake jin wani irin karfi da kuzari a jikinsa jikinsa ya shiga mazari yana wani lumshe idonsa ya nufe ta. "Mikewa tsaye tayi ta shiga cire masa jallabiyar jikinsa, ta rungumeshi sosai a jikinta tana gogo masa" "manyan breast dinta a kirjinsa kan bed din suka zube gabadayansu, Halisa ta samu dama sosai ta cire masa gajeran wandonsa abun mamaki joystick dinshi ta mike sam'bal! dan kamar ma ta 'kara girma da kwarjini Halisa bata jira komai ba tasa a bakinta ta shiga tsotsa tana lumshe idonta..Wannan salon na" Halisa na masifar gigita masa lissafi shiyasa yake jin a zuciyarsa komai rintsi ba zai iya rabuwa da ita dan sabida tana yi masa abubuwan da suka dace. Halisa sai da ta rikita masa lissafi tukkuna ta bar shi ya "shigeta nan ma ta rike wuta sosai salo iri iri ta shiga masa! Aikuwa abinka da gwarzo mai nema ido a rufe nan suka lalace suka share awa uku suna abu daya, sai da suka samu cikakkiyar gamsuwa sannan suka saurarawa junansu. Aikuwa Halisa tasha mamakinsa dan kyautar kudi yayi mata masu yawa kuma" "yace.""Ta shirya zasu je umara sati biyu masu zuwa." Yana fita daga dakin nata ta dauki wayarta cike da tsantsar farin ciki ta kira Ramlatu ta fada mata cewar aiki yayi! tafada mata kyautar kudin da yayi mata da kuma maganar zuwa umarar da zasuyi. "Yaya Ramlatu tace""To alhamdullihi haka muke sai dai kuma baki fada min tsakaninsa da tsinanniyar" yarinyar nan ba. "Halisa tace""Ai tunda naga sun kwana tare da ita washe gari yana min rawar jiki na gane bai samu biyan" bukata ba a gurinta amma dai duk da haka zansa musu ido sosai na gani domin na gane halin da suke ciki. "Ya Ramltu tace""To shikkenan sai naga tukwicina ko."" Halisa tayi dariya da fadin""Ba ke kadai ba ma har" "*Yar shagamu* zan muku kyauta ta mussaman dama ni babban burina na mallaki zuciyarsa ya zama sai abinda nace masa alhmdullhi kwalliya ta soma biyan kudin sabulu.""" Halisa yini tayi cikin walwala da farin ciki yayin da ita kuma Naja'atu ta yini cikin damuwa da fargaba "daga ta tuno abubuwan da suka faru tsakaninta da Abbah Abbas a daran jiya sai gabanta ya fadi gabadaya ta rasa samun nutsuwa a gidan, dan zaman daki ma gagararta yayi ta fito palo ta zauna cikinsu" Saddiqa tayi zugum! sa'i da lokaci tsigar jikinta na tashi Walwalar da Halisa take a gidan itace take bata mamaki sai wani ji take dasu har da tambayarsu me zata "dafa musu na abincin rana..Kowa ya fadi abinda yake so banda Naja'atu dan cewa tayi bata bukatar cin komai..Halisa murmushin mugunta tayi ta wuce kicin cikin zuciyarta tace""Shegiya Idan kikaji wuya da" "kafarki zaki bar min gidana.""" Naja'atu kuwa na ganin yamma tayi lokacin dawowar maigidan daga kasuwa tashi tayi bar palon ta "shiga dakinsu saddiqa ta zauna tana tunanin abinda zai fisheta. Waya take so ta samu ta kira Munira tana ganin gobe dole ta shiga gidan anty Maryam ta dauki wayarta a boye ta kira Kawar tata, wannan itace shawarar data yankewa kanta. Mussadiq ne ya shigo yake fada mata Abbansu ya dawo, tace""To" "jeka naji."" Yaron ya kama hanya ya fita daga dakin, a maimakon taje tayi masa sannu da zuwa sai ta sake gyara zamanta dan bata tunanin zata je yi masa barka da zuwa taje taga abinda zai b'ata mata rai wani lokacin har mamakin kanta takeyi a duk sanda taga Abbahn da Halisa suna zaman lafiya gami da nuna kulawa a kan junansu take jin haushin hakan ta kasa gane me yasa hakan ke faruwa da ita.tunda ita dai" tasan ba sonsa take ba to me yasa take jin haushi idan taga yana mu'amular arzki da matarsa. "Har suka zauna gurin cin abinci Naja'atu bata fito ba, ya kalli Mussadiq cikin nutsuwa yace.""Jeka kira" "Yaya Naja'atu tazo taci abinci."" Halisa tayi saurin cewa""Wallahi tun dazu ta shiga daki ta kulle kanta ni kam na rasa abinda ke damun Naja'atu wallahi gabadaya yini mukayi cikin walwala amma banda ita, gabad'aya kafin na shiga kicin sai da na tambayesu abinda suke so na dafa musu da rana kowa ya fada" "amma banda ita a takaice dai haka ta yini da yunwa gashi abincin daran ma taki fitowa taci.""" "Takaici ne ya kama shi, shi kansa halin yarinyar ya soma bashi haushi duk abinda za'ayi mata ba'a" "burgeta, ya fahimci halisa na kokari a kanta kuma tana kokarin so su zauna lafiya da juna amma ita kullum cikin so ta tayar masa da hankali gida take." "Yace.""Ki kara hakuri da halinta Akwai kuruciya a tare da ita idan ta kara shekaru zata daina abinda take.""" "Halisa mirmushin munafurci tayi ta cigaba da had'a masa abincin, shi kuma Mussadiq ya shiga dakin nasu domin kiran Naja'atun" Fitowa yayi yana kumbura fuska yaron shima ya soma jin haushin abinda takeyi zama yayi gurin zamansa ba tare da yace komai ba. "Halisa tace""Ina naja'atun.""? Yaron yace.""Cewa tayi na fita na bata guri wai takoshi."" Abbah Abbas ransa" ya sake baci abincinsa ya cigaba daci sai da ya kammala tukkuna ya mike ya nufi dakin. "Kan dadduma ya tarar da ita a takure tunda ta idar da sallahr ishai ta kasa barin gurin, Allah Allah take" gari ya waye taje gidan anty maryam. "Ganinsa a tsaye a kanta yasa da sauri ta dago kanta tana rawar baki tace""Abbah sannu da zuwa."" Cikin" "tsare gira babu alamun wasa a tare dashi yace.""Tashi ki wuce kici abinci."" Mikewa tayi da sauri ta kama hanyar fita yabi bayanta yana masifar jin takaicin abinda yarinyar take masa gabadaya ta mayar dashi sakarai kamar yarinya 'kan'kanuwa kullum sai yayi ya'ki da ita kafin taci abinci...Halisa kuwa ganin sun fito tare sai ta daure ranta ta shiga tsokanar Naja'atu wai ta daure ta dinga cin abinci ko ta samu tayi ki'ba idan ba haka ba sai Saddiqa ta fita kumari! Naja'atu ko kallonta ba tayi ba sabida tsabar haushinta" da takeji ta nemi guri ta zauna tana cika da batsewa. "Zama yayi yana fuskantar ta yasa halisa ta hada mata abincin ya tura gabanta tare da fad'in ""Maza ki" cinye shi tas! "Kamar za tayi kuka tace""Abbah ina zan kai wannan uban abinci ai yayi min yawa."" Yace.""Kici ki koshi jiya" ai haka kika kwana da yunwa yau da rana ma baki ci abinci ba duk ba zai rasa gurbi a cikin ki ba. "Tace""Gaskiya ba zan iya cinye wannan abincin ba kwata kwata ma bana cin pride rice ni."" Yace.""Yau zaki" "koyi ci dan wallahi kinji na rantse ba zaki mayar dani d'an wahala ba ni kenan zuwa siyo miki abinci kina 'kin ci."" Halisa tasa dariya tace""To kai in banda abinka ai amarya bata laifi meye dan kayi mata hidima.'' Kai tsaye yace""Na gaji da hidimar wannan yarinyar Halisa hidimar akeyi mata amma bata gani saboda" "haka ni ba zan zama sakarai ba.""" Halisa tana dariya ta bar gurin. "Naja'atu cin abincin kawai takeyi zuciyarta na tashi dan gabadaya bata jin dadin sa a bakinta, da kyar" taci rabi! ya ajiye cokalin zuciyarta na tashi. "Tilasta ta yayi kan lallai sai ta cinye sauran, kuka ta dinga yi masa tana bashi hakuri da fadin""Idan ya" "tsananta mata za tayi amai yayi hakuri ya kyaleta, rabuwa yayi da ita ya mike ya bar gurin." Itama barin gurin tayi ta nufi daki tana kuka gabadaya zuciyarta tashi take tana jin yanda abincin ke taso mata kwanciya tayi tana share hawaye. Halisa kam shigar banza taje tayo ta baza tururruka masu kamshi da tayar da sha'awa ta fito palo ta "sameshi yana duba loptop kamar dai koda yaushe. Tunda ya ganta yaji 'kososhin kansa sun kwance, ya" rasa wane irin turare ne wannan da halisa take amfani dashi a duk sanda zai sha'ki kamshinsa yakan rasa nutsuwarsa gabadaya. Loptop din dake cinyarsa ta dauke ta a jiye gefe ta hau cinyarsa tare da sakalo wuyansa da hannuwanta. Fuskarsa ya dora a kirjinta yana shanshanawa tare dasa hannayensa a kan "mazaunanta yana matsawa, ajiyar zuciya suka sauke a tare. Naja'atu ta fito daukar lemo domin cikin" "firjin dake dakin babu kawai taga abinda sukayi saboda da akwai haske sosai a palo..Tsigar jikinta ne ya tashi ganin Abban Abbas din na tsotsar saman breast din halisa, gabadaya idanunta ne suka rufe ta juya da saurin gaske ta koma dakin ta rufe kofa jingina tayi da jikin kofar ta dafe kirjinta jikinta duk yayi sanyi kasala duk ta baibayeta! lokaci guda wata irin masifaffiyar sha'awa ta taso mata abinda Abbah Abbas" "keyiwa Halisa ya d'aga mata hankali sosai, zamewa tayi ta zauna bakin kofar tana takure jikinta." "Halisa kam sai da ta gama tayar masa da hankalinsa sannan ta cire jikinta daga nasa ta matsa gefe guda," "yasa hannunsa cikin fitar hayyaci ya janyota tare da matseta a jikinsa yana cigaba da shashshafa ta. Tace""Abban mufida ina ganin fa abinda muke kamar bai dace ba muna shiga hakkin yarinyar nan a" cikin kwanakin ta saboda haka yau fa sai dai kayi hakuri dan ba zan iya bari kayi komai dani ba kaje gurin matarka dan itama macece kuma tana da dik abinda kake bukata. Da yake baya cikin hayyacinsa sai "yace.""Halisa bana jin yarinyar nan zata iya daukata a yanda nake jin kaina sannan kuma bata da juriya" "irin taki ki barni na biya bukatata."" Tace""Gaskiya na gaji da kwasar zunubi, sai dai kayi hakuri sai gobe tunda dama goben zaka dawo dakina amma bana tunanin zan iya amincewa da bukatarka a yanzu." "Kafin yace wani abu ta fizge jikinta ta nufi dakinta, rufe kofarta tayi ya bita da wani irin kallo na rashin" mafita. Mikewa yayi yana had'a hanya ya nufi dakin yaran. "Har yanzu tana takure a jikin kofar taji ana kokarin turo kofar da sauri ta mike tsaye, ya bude kofar ya" "shigo, ganinta a tsaye yasa ba tare da yayi magana ba yaja hannunta suka fita daga dakin" Kai tsaye dakinsa suka nufa...Naja'atu a bukace take dan da'alama tana da sha'awa a kusa shiyasa ta "kyaleshi ya dinga ya mutsa mata jikinta tana ta fitar da numfashi tare da rirrikeshi, ita dashi gabadayansu sun kai makura gurin bukatuwa da junansu. Babban burinsu su samu biyan bukata, Abbah Abbas ganin" "abinda ya faru dashi jiya yasa yau bai manta da adduar saduwa da iyali ba.(Allahumma jannabunalshaid'ani wajannabunal shaid'ani wama raza'ktana) sai da ya karanta sai uku sannan ya saita jijiyarsa ya fara kokarin sawa cikin ikon Allah ta shiga kuma bata kwanta irin jiya ba, to sai dai kuma bayan ya daidaita komai yana kokarin ya fara sai yaji tamkar an bubbuga masa gorori a gwiwowinsa gabad'aya jikinsa ya mutu yayi wani irin sanyi, kasala ta dabaibaye shi, gefe guda kuma masifaffiyar sha'awar dake damunsa na sake azalzalarsa amma kuma ya kasa katabus! sai kawai yayi kwance a kanta ga joystick din nasa ta samu guri sosai a cikin ramin, inda ta bangaran Naja'atu notikan kwanta suka kwance babban burinta taji ya soma sosa mata gurin da yake mata kyaikyayi amma kawai yayi kwance a" kanta ya kasa aikata mata komai.. "Kuka tasa masa tana kiran sunanshi! ""Abbah Abbah'' yana jinta ya kasa cewa komai in banda nishi babu" abinda yake. "Kawai sai ta fara motsa jikinta tana d'an d'aga masa wai so take yayi, ko motsi ya kasayi Ta dinga" "motsa jikinta tanayi da kanta tana shashshafa bayansa, duk yana jinta kuma yana jin dadin abinda take amma ya kasa mayar mata da martani! Cikin wani irin mawuyacin hali ta samu satisfaction! tayi kokarin turesa daga jikinta ta tashi ta nufi toilet tana zumbura bakinta. Koda ta fito babu shi a dakin.tayi" "zukud'um! tana tunanin ina ya tafi! zuciyarta tace"" Ya tafi gurin Halisa ai dama sun saba raina miki" hankali...Kayanta ta mayar ta kwanta tana kukan takaici ai dole ne ma tabar musu gidansu.. "Halisa bugun kofa ta dinga ji tayi murmushin mugunta tare da gyara kwanciyarta, tana jinsa taki bude" "masa, Abba Abbas kamar zautace ya dinga buga kofar yana kiran sunanta, Halisa sai da tagama ja masa" "rai tukkuna taje ta bude masa kofa, ganin yanayin da yake ciki yasa ta rungumeshi suka nufi bed dama" "haka take so ya faru hakan ya tabbatar mata da cewar ya kasa ta'buka komai da yarinyar shiyasa ya dawo gurinta, sosai ta bashi kulawa ya hau ya dinga aiki tamkar ba zai bari ba, shi kansa mamakin al'amarin yake idan yana tare da Halisa har wani karfi yake ji, amma idan yana tare da Naja'atu gabadaya ya kan rasa karsashi gami da kuzari! babban abinda ke bashi mamaki shine yanda gabansa ke macewa" tamkar na mara lafiya. Wannan abin na bashi mamaki mutuka. *Littafin na kudi ne..!* Koda zaki ganshi a gruops to na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu toga yanda abun yake Vip group #600 Normal#300 Account: 0542382124...Binta Umar gtbank...Idan katin waya zaki turo sai kiyi min mgn ta whasap da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* Mdd *35* B'angaran Naja'atu kuwa Kasa bacci tayi a dakin bayan fitarsa ta dinga juye-juye abun duniya ya isheta "ita abin ma mamaki yake bata ai da farko ba haka hallitarsa take ba! amma yanzu ya akayi ya zama kamar wani lusari! takaicin al'amarin yasa ta bar dakin nasa ta gwammace ta kwanta cikin yaran yafi mata alkairi, dama ai ya riga ya tsufa a ganinta shekarunsa sun ja babu wani abin arziki da zai iya sai dai karfin sha'awar amma babu kuzari! Zuciyarta tace mata kin manta ranar da ya karbi budurcinki kenan? ke kanki kin san ba zaki kira Abbah Abbas rago ba. Shuru tayi tana tunani! gaskiya farko ta tsorata dashi sabida jarumtarsa amma tsakanin jiya da yau mugun haushi ya bata duk ya wani sakwarkwace ta'b!" yaushe zata iya kayan takaici! idan hakane to gaskiya Halisa na hakuri..Zuciyarta tace mata kin manta "ranar da Halisa takasa tafiya ranar da Yaya Ramlatu tazo, Abbah Abbas fa ba rago bane watakila bashi da" lafiya shiyasa ya kasa aikata komai. Gyara kwanciya tayi tana ta'be bakinta koma dai menene ita kam ba taga gurin zama ba tana ganin "dama kwad'ayi ne kawai irin nasa ina shi ina ita ai a kwai cutarwa a ciki a lokacin da take kan ganiyarta shi kuma ya tsufa to waye zai biya mata bukatarta shiyasa wasu matan ke bin mazan banza ko kuma su dinga neman junansu suna biyawa junansu bukata, ita ko tana ganin data fad'a halaka gwara ta nemawa" kanta mafita tun kafin tafiya tayi nisa. "Da safe Abbah Abbas nauyi da kunyar yarinyar ya hanashi hada ido da ita, koda ya shiga dakin bai bari" "sun hada ido da ita ba, ita kam sai kallonsa take tana girgiza kanta takaici kamar ya fasa mata zuciya dama ina da gami gashinan tun ba'aje ko ina ba ya gaza Allah ya sawwa'ke!" "Bayan sun gama break suka zauna a palo gabadayansu har yaran da yake basu da makaranta suna hutu," naja'atu idonta a kofar dakinsa so take ya fito ta tambayeshi zuwa gidan aunty Maryam Halisa ce ta fito daga dakin sai wani murmushi take kana kallonta kasan tana cikin farin taci uwar "kwalliya tamkar wata amarya ita kanta Naja'atun sai da tayi mata kyau a idonta, amma haushinta da take ji bai bari yasa ta kalleta ba sai ma ta mike ta nufi dakin Abbah Abbas din..Halisa kam zama tayi ta dora kafa daya kan daya tana sakin murmushi na samun nasara." "Yana kokarin fitowa daga dakin ita kuma tana kokarin shiga sukayi karo da juna, da sauri ya matsa gefe" "yana kallonta, ita kuwa tunda tayi masa kallo guda taji gwiwarta ta sage! wani iri kyau da kwarjini yayi mata a idonta, yayi gayu sosai yana sanye da filtex blu black d'inki tazarce sai yayi amfani da milk din hula (dara) irin ta larabawa a gogon fata ne daure a hannunsa yasa takalmi sau ciki Yayi kyau tamkar" matashin saurayi....Dabarbarcewa tayi ta manta abinda ya shigo da ita "Shi kuwa cikin kulawa yace.""Naja'atu ya akayi ne kina bukatar wani abu.''" "Ta dan ja hanci cikin kokarin saisaita nutsuwarta tace""Dama inaso na shiga gidan Aunty Maryam ne idan" anjima kadan. "Dan'bata fuska yayi yace""Me zakije kiyi."" Ta daga kai tana kallonsa da mamaki a fuskarta ganin yasa" "mata ido yana jiran amsarta yasa tace''Babu komai kawai inaso naje mu gaisa ne.""" "Yace.""Kin san bana son yawo ko? kada kice zakije kofar na'isa irin kwanakin baya." "Tace""Wallahi babu inda zanje to me akayi min a gidan da zanje kofar na'isa." "Yace.""Ai ba dole sai anyi miki laifi ba nasan ki da rawar kai ne idan kika je kofar na'isa kin san labari zai" "same ni sai na 'bata miki rai.""" "Tace""Insha Allahu ba zani ba." Juyawa tayi zata fita ya ri'ko hannunta ta juyo tana kallonsa. Gani tayi yana mata wani irin kallo. 'bata rai tayi ta dauke kanta ta gane kome yake nufi "Jin hucin numfashinsa dai-dai wuyanta yasa tayi saurin fizge hannunta ta bude dakin ta fita, lallai ina zata" "iya tsayawa ya tayar mata da hankali ya barta da wahala...Yaji takaicin abinda tayi masa dalilin da yasa da ya fito bai ko kalli inda suke zaune ba ya nufi kofar fita, Halisa da azama tabi bayansa, ita kuwa Naja'atu tana jin yaran nayi masa a dawo lafiya tayi shuru da bakinta." "Salim na zaune saman mota ya hangi fitowarsu, sai ya sakko daga motar yana wani sunkuyar da kansa" "kamar wani mutumin kirki! Yace.""Kawu barka da asuba.'' Abbah ya mika masa hannu suka gaisa Salim ya kalli Halisa yana murmushi yace.""Big anty an tashi lafiya."" Tace""Lafiya kalau Salim ina Yaya Ramaltu.'' Yace.""Tana nan kalau."" Tace ka gaisheta! Yana kokarin budewa Abbah Abbas mota yace""Insha Allah zan" fada mata...Halisa bata koma cikin gida ba sai da taga motarsu ta fita daga gidan tukkuna "Tana kokarin shiga sukayi karo da Naja'atu zata fita. Tace""A'a naja'atu ina zakije kuma.""? Ko kallonta ba" "tayi ba ta kama hanyar fita...Halisa tace""Naja'atu kina ji ina miki magana kin share ni." "Hannu ta daga mata a fusace! tace""Kinga Anty Halisa bana son gulma da munafurci dan Allah bake kike" aurena ba ballantana ki dameni da tuhumar ina zani aikin banza aikin hofi kawai wallahi kada ki dauka "duk abinda kike bana ganewa ina sane, kuma ke kika damu da wannan tsohon har kike satar kwana ki rubuta ki ajiye na kusa fita na bar miki gidanki dan banga gurin zama a cikinsa ba.""" Halisa ta bude bakinta tana kallonta cike da mamaki! Naja'atu buge zaninta tayi ta bar gurin Halisa ta juya tana wani irin murmushi ta nufi cikin gidan ranta wasai bukatarta ta kusa biya. Dakinta ta shiga ta dauki wayarta ta kira maigidan nasu. "Yace""Allah yasa dai lafiya. cikin alhini da yanayi na a tausaya mata tace""Yanzu yanzu na Naja'atu ta gama" zagina saboda kawai na tambayeta ina zata je shikkenan take zagina harda kiran ka tsoho da fadin cewar na fad'a maka wai a kurkusa zata bar maka gidanka domun kuwa ba taga gurin zama ba. "Cike da mamaki yace.""Naja'atu tace fada miki hakan."" Salim dake driving yasa kunne sosai jin an kira" sunan Naja'atu. "Halisa tace""Kwarai kuwa wallahi ni kaina banji dadi ba me yayi zafi! ni banga abin'ki a tattare da kai ba.""" "Jikinsa a sanyaye yace.""Koda ta dawo gidan kada ki sake shiga sabgarta ballantana ta sake zagin ki ki rabu da ita dani take zancen zan dawo na sameta. Halisa farin ciki ya wanke mata zuciya tace""To" "shikkenan Yallabai Allah ya dawo mana da kai lafiya."" Ya amsa da amin tare da kashe wayarsa." Naja'atu kam tana zama a gidan anty maryam kuka tasa. Anty maryam ta zauna kawai tana kallonta "dan babu yanda ba tayi da ita ba akan tayi shuru tayi mata bayanin abinda ke faruwa amma taki tayi shuru sai da taga dama tukkuna ta share hawayenta tana kallon aunty maryam din tace""Anty wallahi bashi da lafiya."" Anty maryam ta zuba mata ido tana kallonta da fadin""Waye bashi da lafiya."" ? Kai tsaye tace""Abbah Abbas mana Allah aunty yana da matsala babba ni bazan iya zama ba dan cutata kawai" yake. Anty maryam duk shekarunta kasa gane inda maganar ta dosa tayi. "Tace""Kinga ni kiyi min bayani yanda zan fuskanta wace irin rashin lafiya yake.""? Hanci taja tace""Baya iya" "biya mun bukatata kullum sai dai ya tayar min da hankali ya barni cikin sha'awa saboda haka tun kafin tafiyar nan tayi nisa ku san yanda zakuyi ku warware shi.""" "Anty maryam tayi 'kasa da kanta kunya kamar ta sa ta nutse a gurin, ashe naja'atu bata da kunya haka" har ta iya zuwa tazo tana yi mata wannan maganar gaba da gaba lallai 'yan matan zamani halinsu sai su! "Sai da ta aro jarumta tukkuna ta dago kanta tana kallon Naja'atun ta 'bata fuska sosai tace""Ke Naja'atu" bana son sharri wallahi! Ni tunda nake da Halimatu da Halisa babu wacce na ta'ba jin tayi wannan maganar! Sharri ne kawai irin naki! sannan har yaushe akayi auran naku da zaki tantance yanda al'amarin yake har kike cewa baya biya miki bukatarki wallahi kiji tsoran Allah. "Itama shan kunu tayi tace""Aunty Maryam ya zaki fad'i wannan maganar ? nifa macace kuma ina da" sha'awa sai kuma kice wani abu ni wallahi gaskiya na fad'a banyi masa sharri ba ki fadawa mijinki a san yanda za'ayi. "Anty Maryam ta rike bakinta tana kallonta cike da mamaki tace""Wai ke baki da hankali ne? wai kike" "tunanin zan fadawa wannan maganar? Humm! ba dani ba ke idan kina ganin kina cutuwa sai ki tsaya yayan naki ya dawo ki fada masa amma ni babu ruwana. Cikin takaici tace""To shikkenan ai kuwa wallahi" in tura ta kai bango sai na fad'a! ai sune suka cuce ni yama za'ayi su auran min tsoho mara kuzari ni kam ba zan iya wannan takaicin ba. Anty maryam shuru kawai tayi tana kallonta mamakin ta kawai take lallai *Zamani* Indai akace maka *Zamani* to magana ta 'kare ita kam tana jin koda mijinta baya iya gamsar da ita zata hakura ta zauna sabida tana jin kunyar taje gida ta fad'a to taya ma zata farayi wa iyayenta bayani *(Wannan ba dabara bace Aunty Maryam akwai 'kwaruwa ace namiji baya biya wa matarsa bukatarta "sai dai ya biya tashi, akwai matsala babba! matsalar da kan iya janyowa mace fad'awa ga halaka! mata da yawa suna nan sun fad'a harkar madigo duk sabida irin wannan matsalar akwai wanda kuma suke bin mazan waje da auransu da komai amma kuma mazajen nasu sun zama hoto a gurinsu. 'Yar uwa idan" kina fuskantar irin wannan matsalar kada ki zauna kiyi ta cutar kanki ko kuma ki jefa kanki ga sa'bon Allah! Akan ki sa'bi Allah gwara kin kashe auran kije kiyi wani shine yafi miki alkairi ko kuto kika kai al'kali ba zai ce miki don me ba sabida shima yasan matsalar gagarima ce. Allah kasa mu dace)* "Aunty Maryam ta mike da sanyayyan jiki ta kalli Naja'atun tace""Ni dai duk wannan surutun da kikeyi" "babu wanda na dauka a ciki dan sabida nasan karya kikewa bawan Allah nan wallahi ki sanja halinki Naja'atu.""" *(Eh gaskiya kam Naja'atu karya tayi wa Abbah Abbas lafiyarsa lau kawai Halisa ce tayi musu farraqu)* "Ganin anty maryam din na kokarin shiga kicin yasa tace""Dan Allah dan bani aron wayarki zan kira" "kawata."" Anty Maryam tace""Tana dakina ki shiga ki dauka." Da sauri ta mike ta nufi dakin nata...Kan mirror taga wayar ta dauka tare da zama bakin bed dinta...Numbar Munira tasa bugu daya tayi ta daga wayar. "Munira najin muryar Naja'atu tace""Kamar *Na'ja'atu Abbas qofa* Naja'atu tace""Eh nice kinyi mamaki" "ko."" Munira tace""Eh lallai nayi mamaki Naja'atu yau kin tuna dani kenan ai wallahi baki da kirki Naja'atu.""" "Murmushi tayi tace""Nasan dole dama ki fadi haka amma dan Allah kiyi hakuri kinji ko wayata ce ta lalace" "shiyasa kika ga na kiraki da wannan numbar wayar aunty na ce.""" "Munira tace""Babu komai ' k'awata ya kwana biyu! wallahi baki yanda nake ji ba a duk sanda na tuno" rayuwarmu ta makaranta. "Naja tayi murmushi tace""Wallahi nima haka munira ina kewarki sosai cikinmu duk ke kad'ai ce mai" "zumunci kinyi kokarin ziyartar inda nake nima a lokaci da nake shirye shiryen kawo miki ziyara wata kaddara ta gifta min.""" "Munira tace""Innalilihi Naja'atu me ya faru da rayuwarki Naja'atu ta goge hawayen dake zubo mata ta" "shiga bata labarin abinda ya faru bayan rabuwarsu. Munira tace""Yanzu dama Mamma Halimatu ba" "itace ta haifeki ba.""? Tace""Wallahi munira nima ban sani ba sai bayan mutuwarta. Munira tace""Ubangiji" "Allah ya jikanta halinta na gari ya bita, ammafa 'kawata Abbah Abbas yayi masifar bani mamaki lallai shi ko kunya baiji ba yazo ya wani aureki sabida son kai ai wallahi idan nice ba zan yarda ba gaskiya an cutar dake.""" "Naja'atu zuciyarta ta sake karyewa tana zirarar da hawaye tace""Munira na rasa wane mataki zan dauka" "wallahi mutumin nan ya nace min dik wani wulakanci da iskanci nayi masa kamar maye yaki yayi zuciya ya sakeni.""" "Munira tace""Kici kwalarsa kawai in ta kama ma ki zazzage shi!! nasan zai sake ki idan kikayi masa haka.""" "Naja'atu shuru tayi tana nazarin maganar! Anya kuwa zata iya cin kwalar Abbah Abbas! Tace""Munira ba zan iya yi masa hakaba yana da babban matsayi a zuciyata bazan tozarta shi irin wannan ba. Munira tace""To shikkenan wace shawara kika yanke ni dai idan zaki dauki shawara ta kiyi masa haka."" Tace""Idan na yanke shawara zanyi miki waya."" Tace""To shikkenan ni kuwa ina Salim kuma yaya yayi da yaji faruwar" "wannan al'amarin.""?" "Murmushin takaici tayi tace""Ya shiga tashin hankali da farko amma yanzu gani nayi kamar ma ya daina" "sona tunda har yake iya kirana da auntynsa."" Munira tace""Lallai Salim gaskiya baiyi hallaci ba amma babu komai koda bai aureki ba ai idan kin futo ba zaki rasa saurayi mai jini a jika ya aureki ba, alhamdullhi kina da kyau da duk suffofin da ake so a jikin mace, wallahi akwai wani abokin Muktar wanda zan aura kenan dan gayu ne sosai sunansa khamis yana da hankali da nutsuwa ga kuma kudi da" "duk abunda mace take bukuta, insha Allah zan hadaki dashi nasan ya ganki zai soki tunda kin cika mace.""" "Naja'atu tace""Ni yanzu babban burina na rabu da auran wannan tsohon saboda na tabbatar da cewar ba" "zanyi wani nauyi ba zan samu daidai dani na aura."" Munira tace""To shikkenan ina sauraranki idan kin yanke shawarar sai ki kirani ki fada min ni kuma zan taimaka miki saboda darajar k'awancen mu."" Tace""To nagode kawata sai kinji ni."" Sallama sukayi da juna, ta kashe wayar tare da 'kurawa kasan kafet" din dakin ido tana tunanin shawarar da zata yankewa kanta... *Littafin na kudi ne!* Koda zaki ganshi a gruops to na sata idan kina bukatar biyan kudin karatu toga yanda abun yake Vip gruop#600 Normal#300 Account: 0542382124..Binta Umar gtbank..Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* mddbhrbn36 "Aunty Maryam ce ta shigo dakin ta ganta ta zabga tagumi dan gabad'aya ma bata san ta shigo dakin ba," "aunty Maryam Jikinta ne yayi sanyi ta tsira mata ido cikin zuciyarta tace""Kodai yarinyar nan da gaske takeyi da maganar da tazo mata dashi to idan ba haka ba me zai sanya ta shiga damuwa irin haka, gaskiya to idan ya kasance gaskiya ne yarinyar zata shiga damuwa tunda ta lura bata da hakuri ta wannan bangaran kuma tana da karfin sha'awa tabbas kuwa tunda har ta iya zuwa tafad'a mata" maganar abin na damunta saboda haka zata yi dubarar fad'awa maigidanta taji abinda zaice. "Zama tayi a kusa da ita ta dafa kafadarta a sanyaye ta kira sunanta, ta juyo tana kallonta idonta na" kokarin kawo ruwa. "Anty maryam tace""Ki daina kuka kinji ko! jikina kuma yayi sanyi yanzu dana ganki cikin damuwa, tabbas" hakan tana iya kasancewa gaskiya ne insha Allah idan Abbah Magaji ya dawo zan fad'a masa abinda yake faruwa sai muji abinda zai ce a kan matsalar abokin nasa ke kuma dan Allah ki daina wannan kukan da kikeyi ita mace da kawaici da hakuri a kasanta. "Dan ta 'kara tunzura Anty maryam din tace""Ni wallahi anty bazan iya hakuri na jure ba ni bani da hakuri" "ta wannan bangaran kawai a san yanda za'ayi.""" "Aunty Maryam tace""Ni abinda yake bani mamaki anan kince bakya sonsa to ya akayi kike sakin jikinki" "dashi har wata mu'amula take shiga tsakaninku kike jin dadi wanda har kike ganin kamar yana cutarki.""" "Tace""Aunty shine kullum sai yazo yayi wasu abubuwa wanda suke sawa hankali na ya tashi ni wallahi da" "baya ta'ba min jikina bazan damu ba amma kullum sai yayi ta damuna ni kuma na kasa hakuri.""" "Aunty Maryam tace""Tom magana dai ta wuce kija bakinki kiyi shuru kada ki fadawa kowa kuma kada ki" "sake Halisa ta sani dan za tayi farin cikin hakan ki cigaba da bashi kulawa insha Allah idan bashi da lafiya to zai samu sauki ai kowace cuta nada maganinta.""" Shuru tayi kawai Aunty maryam ta cigaba dayi mata nasiha gami da koya mata dabarun zama da miji da kishiya Naja'atu jinta kawai takeyi domin ita ta riga ta gama yankewa kanta hukunci. "Sai bayan la'asar ta koma gidan, nan tarar da wata dattijuwa a zaune a palo ita dasu Saddiqa, ta zauna" "kan kujera tana fuskantar matar suka gaisa a nutse, matar tace""Sunana Larai daga gidan Hajiya nake tasa aka kawo ni nan gidan domin na dinga taimakawa matan gidan da aikace-akaice.""" "Sai da matar tayi mata bayani sannan ta gane cewar mai'aiki aka kawo musu, tace""To sannu da zuwa" "Allah ya bamu hakurin zama da juna."" Matar tace""Ameen ya Allah." "Tace""Ina kayanki suke."" Larai tace""Suna can wani daki a harabar gidan Hajiya tasa an kai mun can tace" "can ne masaukina.""" "Tace""To hakan yayi Allah ya taimaka.""" "Larai tace""Ameen"" Halisa ce ta fito daga dakinta ganin Naja'atu da larai suna hira sai ranta ya 'baci! Ta" "kalli Larai fuska a 'bace! dama can halisa akwai girman kai tace""Yana da kyau ki shiga kicin ki fara aikin ko.""" "Larai ta mike da sauri tana fadin ""To Hajiya a nuna min kicin din."" Tace""Muje na nuna miki yanda ake" "amfani da komai."" Larai tace""To."" kicin din suka nufa Naja'atu ta bisu da kallo tana girgiza kanta, Halisa" "ba 'yar gidan uban kowa ba amma dan kawai tana auran mai kudi sai shegen girman kan tsiya, tsaki taja" ta kalli Mussadiq dake mata magana "Tace""Ba gidan Alhaji naje ba gidan Aunty Maryam naje."" Yaron yace""Da kin sani kinje dani Yaya Naja'atu." "Tace''Wani weakend din sai ku tambayi Abbanku kuje ku yini a can.""" "Mufida tace""Aikuwa zamu tambaye shi."" Ta kalli Saddiqa da fadin""Saddiqa ya hannunki."" Yarinyar" "tace""Hannu ya warke kinga yanzu ina iya amfani dashi ba tare dana ji zafi ba."" Tana kokarin mikewa tace""Allah ya kara sauki."" dakin yaran ta nufa, ta shiga wanka ta fito daure da zanin atamfar jikinta jakar kayanta ta bude taga babu duk ta sanye su sai 'kananu irin na kanti sai dogwayen riguna ita kam ba zata sa doguwar riga ana zafi ba riga da sket ta dauka tasa a jikinta ta gyara gashinta tasa masa ribborn ta gaji da rashin kitso tana ganin dole ta tambaye shi zuwa kitso kanta kusan satin sa biyu a tsefe! gashi tubarkalla tana da gashi babu laifi....Dankwali abaya ta daura a kanta ta zauna tana hada kayanta dana yaran wanda da sukayi daud'a! ta fito palon tana kallon Mufida tace""Kije bakin gate kiga idan me muku" "wanki nan kice yazo ya dauka.""" "Yarinyar tace""To"" Da sauri ta mike zata fita..Halisa ta fito daga kicin tace""Ke ina zakije.''? Tace""Yaya" Naja'atu tace naje na kira Yunusa mai wanki.'' "Cikin tsawa tace""Koma ki zauna idan ita ba zata je ba to ta aiki wanda take da iko dasu." Yarinyar ta kalli Naja'atu dake tsaye tana kallonsu...Jikinta a sanyaye taje ta zauna saboda tana masifar jin tsoron mommyn nata tana kuma tsoron irin dukan da take mata....Saddiqa ta mike ta nufi dakinsu ta sako hijabinta ta nufi kofar fita. "Naja'atu kuwa murmushi tayi ta zauna kan kujera da fad'in ""Allah yasa nima na haifa kafin ki haifa" "ballantana kiyi min gori ina da masu share min hawaye ehe.""!! Halisa na jinta tayi mata banza so take kawai maigidan ya dawo taga irin hukuncin da zaiyi wa yarinyar na fita ba tare da saninsa ba kuma tasan ya tsani yawo komai shirin da kuke dashi kukan iya 'batawa dashi idan yaji maganar zuwa unguwa" shiyasa itama bata fiye zuwa sabgogin danginta ba saboda kullen da yake musu. Larai tuwo tayi musu na farar shinkafa yayi kyau sosai ga lafiyayyar miyar bushashshiyar kubewa da taji "nama da daddawa da kayan kamshi, cikin nutsuwa ta shirya musu gurin cin abincin tayi musu sallama ta nufi masaukinta." Halisa kuwa zuwa akayi ka cancad'o ado da wani uban material mai tsadar gaske sai dai anyi masa "banzan dinki riga da siket ne duk an tsaga shi hannun riga mai tsayi da gajere tasa turare mai kamshin gaske, palon ta fito tana shan k'amshi" "Naja'atu da yaran suka bita da kallo, Naja'atu Kallo guda tayi mata ta dauke kanta tana kunshe dariya!" Halisa ta lura da ita sai ta shareta ta zauna kan kujera hade da daukar romot tana dannawa! Yaran kuwa motsin kirki sun kasa yi wanda da kafin fitowar Halisa hayaniya suke akan film din da suke kallo amma zamanta a gurin duk yasa sun shiga taitayinsu Haka suna ji suna gani ta sanja musu tashar da suke "kallo ta mayar dashi Mbc1 tashar larabawa, gabadaya yaran basu ji dadi ba dan yanayin su sai da ya nuna. Naja'atu ta kalleta a da'kire! tace""Kallo fa suke zaki dauke musu dan Allah ki mayar musu su" 'karasa. Halisa ko kallonta ba tayi ba ta cigaba da kallon dramar da akeyi a tashar mbc1 din. Naja'atu ta mi'ka hannu zata dauki romot din ta wani fizge hannunta ta dauke romat din ta rike a hannunta. "Naja'atu tace""To ikon Allah! kina Iko da abinda ba naki ba? Kayan kallon nan fa ba daga gidanku kika zo" "dashi ba maigidan ne ya siya ya ajiye domun 'ya'yansa kawai kuma sai ki dinga 'kuntatawa yara kina son zuciyarki."" Halisa ba tare data kalleta ba tace""Ki cigaba da zagina kina min rashin kunya zaki gane baki da wayo wallahi.""" "Naja'atu tace""Babu wani zan gane bani da wayo ai gaskiya na fada miki dama ni tuntuni abinda yake" "had'ani dake son kai aikin banza kawai."" A fusace! Halisa ta juyo ta wanke mata fuskarta da mari ta mike tsaye tana wani irin huci! tace""Ke na gaji da rashin mutuncin da kike miki wai dan uwarki ni sa'arki ce.""! Naja'atu ta dafe fuskarta tana kallonta ta'b!!! Mikewa tsaye tayi a zafafe! kawai suka ji sallamarsa a palon...Naja'atu ta fashe da kuka tana sake rike fuskarta ta da fadin ""Kawai daga na fad'a miki gaskiya" "shine zaki mareni har da zagin uwata.""" "Ya k'araso gurin yana tambayar abinda ke faruwa, Halisa dai jikinta ne yayi sanyi dan ta kasa magana" data san zai dawo da wuri to da bata aikata abinda ta aikata ba shi kuwa ya dawo da wuri ne domin kawai yaga shin naja'atu ta dawo gidan ko kuma tana waje. Tana kuka ta kama hanya zata bar gurin. Hannunta ya rike ya dawo da ita yana tambayarta abunda ke "faruwa...Tana kuka tace""Kawai daga na aiki Mufida nace ta kira Mai musu wanki yazo ya dauka shine tace yarinyar ba zataje ba wai naje da kaina ko kuma na aiki wanda nake da iko dashi, sai kawai Saddiqa ta tafi ta kirawo shi yazo ya dauki wankin, to kuma yanzu yara suna kallon film dinsu kawai daga zuwanta tazo ta sanja musu tasha shine dan nace ta mayar musu su karasa gani sai kawai ta hau d'ura min ashar harda zagina."" Cikin gawurtaccen kuka ta 'karashe maganar. Halisa jikinta yayi sanyi lallai yarinyar nan" ta gawurta gurin iya sharri yanzu dame zata kare kanta ji tayi giwarta tayi sanyi Babu walwala a "fuskarsa ya kalli Halisa da fad'in ""Wai me yasa kema da girmanki kike mayar da kanki yarinya? Akwai Tv a dakinki me zai sanya ba zakije can kiyi kallonki ba sai kinzo ki takurawa yara kuma idan nayi magana kice ina fifita yara a kanki ke abinda kikeyi ya dace kenan.""?" "A sanyaye tace"" To ni dai bani da abinda zance anan gurin shuru shi yafi min alkairi amma duk abinda" yarinyar nan ta fada maka to karya take yi Tunda ta dawo daga yawonta take zagina dama kuma na fada maka tun kafin ta fita ta fara to ina tunanin inda taje an zugata! shiyasa ta shigo da neman fitina kuma ni "ban zauna dan na takurawa yaranka ba kayi hakuri.""" "Tana kare maganarta ta bar gurin, tana mamakin yanda al'amarin ya juye kanta tana so ya dawo gidan" taga irin cin mutuncin da zaiyi wa yarinyar sai gashi al'amarin na nema ya dawo kanta aikuwa dole ta lalla'ba kada ya kunyata a gaban yara shiyasa tayi gaggawar barin gurun. Halisa na barin gurin Ya shiga bin jikin Naja'atu da kallo drassing din da tayi yayi masa kyau! komai na jikinta ya futo kuma yau bata sanye da hijabi! Ganin yana kallonta ga yara a zazzaune sai tayi saurin zama kan kujera tana dauke kanta...Shima da sauri ya bar gurin gudun kada yaran su fahimci wani abun. "Mufida ce ta dauki romot din tayi saurin mayar musu da Mbc2 tashar da suke kallo, suka cigaba da" kallon film dinsu. Halisa da kyar ta iya binsa dakinsa ta taimaka masa yayi wanka ya shirya jikinsa suka zauna suna mayar "da maganar abinda ya faru ita dole sai ta wanke kanta ta d'ora laifin abinda ya faru a kan Naja'atu shi kuma ya kasa fahimtar ta shifa ba zai fahimci komai ba mutukar magana ta kasance a kan yaransa to yakan iya daukar mataki mai tsauri a kan koma waye (Lallai Abbah Abbas kana da son 'ya'ya da yawa) Halisa da taga ya kasa fahintarta sai ta kawai ta bar maganar ta shiga fada masa zuwan mai'aikin da hajiya ta turo...Yace.""To alhmdullhi naji dadin zuwanta kowa sai ya huta dama dake da Naja'atun" dukkaninku kuna ganin kyashin kulawa da yaran wannan kuwa kudi zan biya ta nasan zata kula min dasu. "Halisa ta rike bakinta tana kallonsa da mamaki a tare da ita tace""To me kuma yayi zafi da fadin wannan" "maganar."" ? Yace.""Duk maganar dana fada a kanku ai ba karya nayi ba, ke 'yar da kika haifa ma baki nuna kulawarki a kanta to akan wa zaki nuna."" Halisa ganin yana nema ya mayar da abin rigima sai ta shiga bashi hakuri wai ya bar maganar kada tayi tsayi ita dai tasan tana iyakacin bakin kokarinta a kan" "yaran, kuma tasan Allah yasan zuciyarta. Jinta kawai yake saboda halinta sai da ya fadawa wani" "Idanunta ne ya sauka kan ledojin kayan lefen Naja'atu da suke ajiye a gefe guda, tace""Wai wannan" "yarinyar ba zata dauki kayanta ta kai d'inki ba.""" "Yace.""Tace bata so ki kwashe ki bawa wanda ya dace! kafin mu tafi umara zamuje da ita ta duba duk" "abinda take so..Halisa zugum! tayi tana kallonsa cike da mamaki tace""Yanzu meye laifin kayan nan da" "zate ce bata so kai kuma zaka biye mata wallahi ka dinga amfani da kudinka a inda suka dace."" Cike da kishi ta fadi maganar" "Yace.""Duk da ban san kayan mata ba na duba naga kayan na gane basu da kyau da quality saboda haka" "tunda tace ba suyi mata dole a sanja mata wasu tunda hakkinta wannan kuma ni nace ki bayawa mabukata ko a cikin danginki ne.""" Halisa sai taji maganar tasa kamar da akwai cin fuska a cikinta Ikon Allah! Lallai yau ya shigo gidan da son yaci zarafinta dan haka sawunta a likkafa ta fita tabar masa dakin. *( To dama waye ya fad'a miki kullum ake kwana a gado Halin namiji ai yafi dubu yau zuma gobe mad'aci! haka suke Komai asirinki idan wani namijin ya burkice miki sai kin rasa yanda za kiyi gwara ma ki daina asirin shi zai fi miki alkairi*) Daure da alwala ya fito ya samesu a zaune a palon Naja'atu ta sake sai dariya take ita da yaran ya "kallesu yana jin dadi a ransa a duniya yana so ya gansu suna walwala yace.""Ku tashi kuje kuyi sallah! Da sauri suka kashe tv din shi kuma ya kama hanya ya fita da niyyar shiga massalaci" "Sai da ya sallaci isha'i ya shigo, kai tsaye gurin cin abincin ya nufa, Naja'atu da yaran suka bi bayansa," sukayi zaune suna jiran Halisa tana daki ta'ki fitowa sai haushi take ji...Ya kalli Mufida da fadin taje ta kira ta. "Yarinyar ta fito ta zauna tana kallonsa tace""Wai gata nan zuwa."" Suka cigaba da zaman jiran fitowarta" "bata fito ba, Ya kalli Naja'atu da fad'in ""Zubawa kowa abincinsa."" Ta kuwa mike da sauri ta shiga had'awa kowa nasa, dadi take ji itama yau ta samu galaba kan Halisa. Tun kafin ya fara cin towon ya bashi" "sha'awa kuma gabadaya girkin baiyi kama dana Halisa ba yace""Da alama wannan abincin na bakuwar da mukayi ne."" ? Tace""Eh nima bayan na dawo daga gidan aunty maryam na tarar da matar tace sunanta Larai daga gidan Hajiya."" Ba tare da yace komai ba yayi bisimillah a nutse ya fara cin abincin gaskiya yaji dadin abincin matar sosai ashe Halisa ba ta iya komai ba hakuri kawai yake amma yanzu tunda ya samu" mai aiki dattijuwa wacce ta iya girke-girken zamani dana gargajiya to yasan matsalarsa ta kare.... *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a gruops to na sata ne idan kina so ki biya kudin karatu ga yanda abin yake. Vip gruop#600 Normal #300 Account:0542382124...Binta Umar gtbank..Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* Mddbhrmbn37 "Har suka kammala cin abincinsu Halisa bata fito ba tana dakinta a kwance abun duniya ya isheta," "gabad'aya ba tayi tsammanin al'amarin zai kasance haka ba ita abinda taso shine yana dawowa yaci mutuncin yarinyar ko kuma yace ta koma inda ta fito kamar yanda ya saba yi mata a duk lokacin da ta fita ba tare da izininsa ba to tana dawowa ko zama baya bari tayi zai ce ta koma inda ta fito, sai tayi kuka ta bashi hakuri sosai tukkuna yake barinta ta shiga gidan Abunda kuma ya sake hassala mata" "zuciyarta shine ganin kwata-kwata daya shigo gidan baiyi maganar ba ballantana yayi wa yarinyar fad'an fitar da tayi ba tare da izininsa ba, bayan kuma d'azu data kirashi a waya ya nuna fushinsa harda cewa idan ya dawo sai ya hukunta yarinyar sai gashi ya kasa aikata komai a kanta ta tabbata idan itace ta futa ba tare daya sani ba sai yayi mata cin mutunci amma da yake Naja'atu ce ya kasa cewa komai, gaskiya alamarin yayi masifar bata mata rai! bayan haka kuma yana maganar zai dauki yarinyar suje siyayya ita kam ta rasa yanda zata kamo bakin zaren daga aiki ya fara kyau sai ya lalace! ta rasa wane irin sirri da asararai Baba malam yake dashi wanda da yakewa 'ya'yansa, lokacin Halimatu ma haka tasha wuya da jikinta da aljihunta, daga ta fara ganin daidai sai aiki ya wargaje! to yanzu ma ga Naja'atu tazo tana lalata mata aiki wai shin ya za tayi ne!? *(Hum Halisa kenan Baba malam babu wani abu da yakewa 'ya'yansa face addua itace maganin kowa ce irin masifa! kuma dama waye yace miki asiri na tabbata? asiri gaskiya ne tunda ya kama fiyayyan hallita annabi Muhammad slw! amma karfin addua bai sa yayi tasiri a jikinsa ba, karkarin asiri kwana bakwai zuwa ar'ba'in ya lalace shiyasa zaku ga masuyi kullum suna tafe kamar mahaukata! sannan kuma Wani lokacin asirin da Halisa keyiwa Abbah Abbas yana tasiri a kansa amma kuma akwai lokacin da asirin ba zaiyi tasiri ba a tare dashi ba tunda dai shi ya kasance mai yawan azkar da addua domin kare kansa da iyalinsa, idan hakane kuwa yana da kyau Halisa ta gane cewar aikin banza takeyi domin akuwa asiri ba zai ta'ba sanja mata Abbah Abbas ba ya koma lusarin namiji kamar yanda take b'ukata. Mata masu biye-biyen malam wallahi ku daina kuyi wa kanku fad'a!" babu wani abu da boka ko dan bori zai muku a duniyar nan face abinda Allah yayi muku suma bokayen Allah ne ya basu wannan ilimin domin sun kauce masa sunbi shaid'an to dama shi shaid'an kullum tunaninsa yaya za'ayi ya janyo wani jikinsa domin ya cutar dashi kamar yanda yayi wa Allah al'kawari! "Duk mutumin daya had'a Allah da waninsa to ya ta'be! Kuma Ubangiji ya lan'ance shi, Allah na yafe wa" bayinsa lafuka da yawa amma kuma baya yafewa bawansa idan ya had'ashi da abokin tarayya ba. Allah bashi da kishiya shi kad'ai ne tal sabida haka ka/ki nemi biyan bukata a gurinsa ba'a gurin wani ko wata ba.* "Naja'atu na kokarin barin daning din ya kalleta cikin kulawa yace."" ta koma ta zauna yana so za suyi" "magana."" a sanyaye ta koma ta zauna tana dan kallonsa. Yace."" Ina fatan baki mance cewar yau" "kwanaki bakwai din da musulunci ya tanadar miki suka 'kare ba."" Ta kalleshi tana dan nazari, ita ta manta dan ba lissafawa take ba. Yace.""Yau zan koma dakin Halisa insha Allah zaku cigaba dayin kwana" bibbiyu kamar yanda muka tsara ranar da kika zo gidan nan da sunan matata. "Shuru yayi wai ko za tayi magana, tayi shuru bata ce komai ba, sai ya cigaba da cewa''Sabida yawan" "sa'bani da kuke samu da Halisa yasa na yanke shawarar cewa zaki koma d'aya 'bangaran da zam...katse shi tayi tun kafin ya karasa tace""Umum! Abbah ni tsoro nake ji wallahi nafi so in cigaba da zamana anan."" Yace.""Ni kuma bana son tarayyarki da yara dan sabida watarana kada su gane wani abun ki" koma gurinki yafi alkairi. "Murya na rawa tace""Dan Allah ka barni anan d'in Abbah."" Yace."" ba zai yiwu ba Naja'atu a duk ranar girki" "zaki dinga yi min yawo da hankali a gaban yara na sabida haka na yanke wannan shawarar.""" Had'ashi da Allah ta shiga yi kan yayi hakuri ya barta anan din tayi al'kawarin zata zauna da Halisa lafiya. "Ganin tana kuka yasa jikinsa yayi sanyi yace""To shikkenan na kyaleki tunda kinfi kaunar ki takura kanki" "har yanzu kin kasa zama cikakkiyar mace a gidanta ke kenan ra'be-ra'be daga wannan d'akin zuwa wannan."" Shuru tayi ba tace masa komai ba." "Yace.""Insha Allahu sati mai kamawa zamuje umara nida Halisa da Hajiyarmu kafin mu tafi zamuje dake" sahad store ki had'o lefanki sannan kema tuntuni na siya miki mota inaso ne naga kin 'kara hankali da nutsuwa sai na baki key din. "A sanyaye tace""Abbah daka bar maganar lefan nan dan ni basu ne a gabana ba.""! Tsira mata ido yayi" "cikin sigar tuhuma yace.""Menene a gabanki.""!? Ganin yana mata kallon zargi yasa ta sunkuyar da kanta tace""babu komai."" Yace""Karya kike kina so kice abinda ke gabanki rabuwa da aurena ko.""? Da sauri ta shiga girgiza kanta gabanta na faduwa. Yace""Na fada miki ki cire wannan kudirin daga ranki ba zan" rabu dake ba har abada ina tunanin abu daya zakiyi min naji na tsaneki a rayuwata amma bana fatan ki aikata abun.'' Tayi kasa da kanta tana ji inama ya fad'i abinda baya so tayi masa wallahi da sai tayi komai munin abun dan kawai ta samu biyan bukatarta Ya kalleta yana lumshe mata kyawawan idanunsa "yace.""Tashi kije ki kwanta."" Yanayin yanda yayi mata magana a kasalance yasa jikinta yayi sanyi ta gaza" "kallon kwayar idonsa dan jin yanda wani irin feeling ke taso mata a hankali ta mike zata bar gurin, ya riko hannunta yana me tsirawa fuskarta ido...Gabanta ne ya dinga dukan uku-uku gefe guda kuma tana jin yanda d'umin hannunsa ke ratsa mata jiki....Kafin tayi aune taji ta a saman cinyarsa...Hannunta ya dora a saman wuyansa ya tsirawa bakinta ido shi kadai yake muradi! To itama da yake tasan dadin abin sai ta lumshe idonta tana dan sauke numfashi...Cikin nutsuwa ya tallafo fuskarta ya had'a bakinsa da nata ya shiga tsotsa babu kunya ta dinga yi mayar masa da martani al'amarin da yayi masifar gigitashi! ya shiga shasshafa jikinta yana cigaba da sucking din harshenta da le'bunanta tamkar zai shanye mata yawun bakinta haka yake kissing dinta. Jin yanayin jikinta ya soma sauya nipples d'inta sun soma tashi, sai tayi" gaggawa sauka daga jikinsa da sauri ta nufi daki ta rufe kofa tare da jingina jikin kofar tana wani irin mayar da numfashi. "Ya jima zaune a gurin kafin ya mike da mataccen jiki ya nufi dakin Halisa, tana kwance tayi shirin bacci" "tana jira ya shigo mata daki ta huce fushinta, aikam ganinsa cikin rashin kuxari yasa ta gane abinda yake da akwai sai tayi wata iriyar kwanciya cinyoyinta duk a waje...Bai saurareta ba sai da ya shiga toilet dinta yayi uzirinsa ya fito tukkuna ya nufi bed din Halisa a zuwan bacci takeyi da taji ya janyota jikinsa, sai ta mike zaune cikin fusata tace""Dan Allah Abbah Mufida ka rabu dani yau na huta kai kam kullum akin abu" "daya sam baka gajiya kamar ni kadai ce matarka, ni yau bacci zanyi ka kyaleni.""" Tana gama maganarta ta juya masa baya. Ya dinga kallon bayanta takaici kamar ya kashe shi gabadaya ma ji yayi baya sha'awarta Naja'atu yake sha'awa sanin da yayi ko yaje gurin Naja'atun ba wani abun arziki zai tsinana ba sai kawai ya cire abin a ransa yayi addua ya kwanta cikin ikon Allah kuwa bacci mai nauyi ya daukeshi Halisa tayi mamaki sosai tasan halinsa bashi da hakuri ko kadan amma duba yau ba "tare da ya nuna mata damuwarsa ba ya hakura, sai jikinta ya sake yin sanyi lallai dole ne ta sake tashi a" tsaye....... Sai wajejen shida da rabi na safe ya shigo gidan tun bayan fitarsa sallahr asubahi...Larai na palo ita kadai tana aikace akaice ta gaishi ya amsa yana kokarin kawar da damuwar dake fuskarsa.. Kai tsaye Dakin yaransa ya nufa...Suna ganin shugowarsa suka shiga gaisheshi kamar yanda suka saba. Naja'atu da dan murmushi a fuskarta ta dago domin gaishi sai taga fuskarsa a murtuke tamkar hadarin "dake daf da zubar da ruwa! Taji gabanta ya fad'i! Ta jima ba taga irin wannan yanayin daga gareshi ba, ya kalleta da idanunsa wanda suka zama jajaye duk da tsananin hasken su..""Ki same ni yanzu yanzu a dakina."" Abunda ya fada mata kenan ya fita daga dakin Jikinta a mace ta nemi hijabinta tasa tabi" "bayansa....Tsaye ta same shi hannuwansa goye a bayansa, Tana shiga yace""Rufe kofar.''Ta juya da sauri" tayi yanda yace. "Tsira mata idonsa yayi tana daga inda take yana daga inda yake bai motsa ba yace.""Zo nan ki maimaita" "min abinda kikaje kika fad'awa Maryam.""! Ta kalleshi cike da fargaba da tsoro! Cikin tsawa! mai razanarwa yace.""Ba dake nake magana ba.""?" "Bakinta na rawa tace""Babu abinda naje na gada mata wallahi.""!" "Sabida baki da kunya kuma kin raina Allah kike rantsewa dashi kin san girman wallahi kuwa.""? Shuru tayi" "hawaye na kokarin zubo mata, Yace.""Abokina Magaji ba zaiyi miki karya ba kana kuma Maryam ba sa'ar wasanki bace ballanta tayi miki karya! Shine saboda baki da mutunci kikaje kina kokarin tozartar dani a gurinsu ko? Ni ne bani da lafiya bana gamsar dake shin yanzu ke ba kiji kunyar zuwa ki fadi wannan maganar ba.""? Tana kuka tace""Wallahi Abbah har abada ba zan tozarta kaba kuma ni banji kunyar zuwa na fadi maganar ba dan sabida nasan ba karya nayi maka ba kai kanka kasan baka cika lafiya ba to ina ganin idan zamu cigaba da zama da juna akwai cutuwa shiyasa na fad'i maganar kuma ban fad'i maganar" "ba dan su fad'a maka ko kuma na tozartaka kamar yanda kake tunani.""" Zama yayi gefen bed tare da dafe kansa wani irin gumi yana tsatstsafo masa kamar ba safiya ba. Ya dago "kansa a burkice yace.""Naja'atu ban gaza miki ta wannan bangaran ba kiyi hakuri kinji ko! nima kwana biyu haka na tsinci kaina amma insha Allahu zanje ga likita domin na fada masa matsalata na tabbatar da cewar zaki sheda cewar ni din jarumi ne kuma gwaron namiji ne ta wannan bangaran tunda karon mu na farko dake kinga abinda faru so insha Allahu zaki same ni cikakken namiji mai biya miki dukkanin" bukatunki. "Cikin izgili daso dole sai ta tunzura shi Tace""A gaskiya Abbah ka daina wannan maganar da kakeyi, idan" za'a duba al'amarin nan a tsanake za agane kai ba tsaran aurana bane dan idan kace lallai xaka cigaba da "zama dani zaka cutar dani da rayuwata dan girman Allah kayi hakuri ka zauna zaman aure da daidai da kai ni kuma ka kyaleni na samu daidai dani na aura ina ganin shine yafi alkairi a tattare damu baki daya.""" Maganar ta sosa masa rai sosai da sosai wato har an kai matakin da yarinyar nan zata dinga yi masa kallon wanda ya tashi daga aiki mara mamora wai shin nawa ne ma shekarunsa a duniya da yarinyar keyi masa kallon tsoho wanda ya tashi daga aiki girgiza kansa yake cike da jin takaicin maganganun data "fada masa.Ita kuwa bude kofar dakin take kokarin yi domin ta fita ya dago kansa tare da fadin"" Kada ki futa zo nan."" Bata dauka wani abu zaiyi mata ba sai ta nufi inda yake, tana zuwa ya fuzgota ta fad'i a jikinsa, hijabin ya fizge ya kwantar da ita tare da kokarin cire mata kayanta. Tana kuka tana bashi hakuri" yaki saurara mata sai da ya tub'e mata kayanta tsaf! ya cire jallabiyarsa ya bar gajeran wando sabida hasken gari yasa yaja musu bargo ya rufe musu jikinsu. Hannunta ya kama ya tusa cikin gajeran "wandonsa jikinsa na wani irin kyarma yace""Ki r'ike da hannuki kiji yaya yanayinta yake ni ba ragon namiji bane kamar yanda kike tunani nafi karfin duk wani matashin saurayin da kike tunani! Naja'atu duk yanda kike tunani na wuce haka.""!! A tsorace ta ri'ke! Joystick d'in nashi taji ta wani iri a hannuta girmanta ya bata mamaki mutuka da sauri ta cire hannunta jikinta na rawa, tunani take to ya akayi haka kuma yau bata kwanta ba, addua ta shiga yi kan Allah yasa kada ta kwanta har sai bukatarta ta biya. Tana jinsa" yana ta wasa da sassan jikinta sha'awarta na 'kara tashi duk ta rikice gabanta sai zuba yake yana mata kaikayi gaskiya itama tasan tana da karfin sha'awa sosai!! a yanzu dai burinta kawai taji shi a jikinta. To shima nasa bangaran hakan ne dan jijiyarsa takai ta kawo kuma takai matakin da ya kamata a bata "abincinta, sabida haka sai ya cire bakinsa daga kirjinta ya gyara cinyoyinta yau ma bai manta da adduar" saduwa da iyali ba ya karanta sau uku ya saita cike da kwadayi yasa yana kokarin farawa jikinsa ya mutu kamar dai ranar farko yaji gabadaya giwarsa ta sage tayi sanyi kasala ta baibaye shi kawai sai yayi kwance a kanta yana futar da wani irin numfashi mai wahalar gaske. Takaici kamar ya kasheta tana ji kamar ta rufeshi da duka kota zazzage shi sabida bacin rai! Hawayen "bakin ciki ya soma zubo mata, haka nan ta daure ta dinga yi da kanta tana motsa jikinta a hankali a hankali tana kukan bakin ciki...Ta jima tanayi ta kasa samun gamsuwa gashi duk ta gaji sabida nauyinsa daya ke kanta kuka ta shiga yi mai gunji tana kiran sunansa hade tureshi daga jikinta. A yanda yake" kwance a jikinta shi kadai yasan kokawar da yake da jikinsa wai yana so ya yunkura ya tashi domin yayi yana ji tamkar an dauki (dala da gwaron dutse) an dora masa a kansa. (Bisimillahillazi layaduru "ma'asmihi shai'un fil'arabi wala fissamawati wahuwassamiulalim) adduar da yake ta nanatawa kenan a cikin zuciyarsa, cikin ikon Allah yaji kamar saukar wani abu daga jikinsa, ya yunkura ya mike tare da gyara giwowinsa sosai ya gyara mata kwanciya cikin wani irin kuzari da muzzakarinci ya soma bugunta yana" cigaba da nanata adduar a cikin zuciyarsa. *Wannan adduar tana kore duk wani shaidanin aljani da duk wani shaidanin mutum* *Littafin na kudi ne...!* Koda zaki ganshi a groups to na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu to ga yanda abin yake. Vip group #600 Normal gruop#300 Account: 0542382124..Binta Umar gtbank idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* Mddbhrbn38 Jin irin bugun da yake mata ne yasa jikinta ya shiga karkarwa ta wani rungume shi tana sake tura masa tare da shashafa jikinsa tsabar dadin da take ji ne ya sanya ta dinga shashshafa jikinsa tana kissing din fuskarsa ba tare data san tanayi ba sosai ta sakar masa jiki ta manta da duk wata 'kiyayya da take masa burinta kawai ta samu cikakkiyar gamsuwar da take bukata daga gurinsa.. Abbah Ya jima yana sarrafata a kwance kafin ya burkitar da ita ruf da ciki ya d'an tasar da ita gwiwarta ta dogare da kafitar gadon (goho) yana kaunar wannan stayel din sai dai bai ta'ba kwantatashi a kan kowa ba sai a kan Halisa dan ita kadai ce ke iya jurewa Halimatu kuwa da yake ba cikakkiyar lafiya ce da ita bai fiye takura mata da fitina ba..... *(maza da yawa nason goho yayin da su kuma matan ba kasafai suke yarda dashi ba saboda zafi da "rashin gane inda harkar ta dosa, amma dai yana da kyau kiyi hakuri idan mijinki ya bukaci yayi ta hakan sai ki bashi kwarin gwiwa kuma ki taimaka masa sai kiga kun zauna lafiya Kada fa kuga rashin kunyata gaskiya na fad'a muku wallahi 'kauyanci da gidadanci shine yake cutar da matan arewa babu abinda muka iya sai gasa da ri'ke manyan wayoyi da fafar shiga manyan motoci da 'karyar sanya sutturu masu tsada da gwalagwalai amma idan akazo wannan 'bangaran sai zance yasha bam-bam Dan Allah kuyi hakuri da yanda nake sakin layi a cikin wannan littafin al'amuran da suke ta faruwa kenan A rana na" "amsa kiran wayar mata sama da biyar masu kawo mun matsalarsu wai dan Allah ya zasu yi To Nakance kije ki gyara zamantakewar ki da mijinki da duk wanda kike mu'amula dashi sannan babu gardama da jayayya da miji idan ya umarce ki kiyi masa abu ta ko wanne fanni kiyi kokarin yi masa kada kuma ki raina samun mijinki kiga saboda bashi da kudi ko wata suttura ba zaki mutuntashi ba mutukar yana sauke dukkanin hakin ki da Allah ya d'ora masa to kiyi masa ladabi da biyayya! Amma kuma kada ki sake ki zama shashasha ki kama mutuncinki kada ki bari ya rainaki dan wasu mazan idan sunga matansu nayi musu biyayya sai kuma su dinga wulakansu saboda butulci, idan mijinki na kokarin ci miki mutunci bayan kuma kina sauke masa dukkanin bukatansu to idan kika zauna kika kyaleshi kece kika so! gwara" tun kafin tafiyar tayi nisa ki nuna masa ke mai daraja ce* Naja'atu jin yanda ya matseta jikin fuskar gadon ya rike mata wuya sosai yana bugunta yasa ta shiga taitayinta gabadaya ma ta daina jin dadin da take ji sai bakar azaba! gabanta sai wani irin zafi yake mata. Shi kuwa wani irin dadi ne yake ratsashi ya dinga sakin karamin ihu! abinda bai ta'bayi ba wai yana sex da mace ya dinga sambatun surutai Wannan dad'in naja'atu yasa ya manta a inda yake sai numfashi da huci mai zafi yake fesarwa. Halisa ta jima a tsaye a bakin kofar dakin tana murd'awa tayi tayi kofar ta bude taki...Cike da mamaki ta nufi dakin yaran nan ta tarar dasu sun Shirya tsaf cikin Uniform suna kokarin fitowa palon Gaisheta suka shigayi ta amsa tana neman Naja'atu a dakin Da bata ganta ba sai ta kalli Mussadiq da fadin ina Naja'atu take.'? "Yaron yace.""Tana dakin Abbanmu tun dazu da ya shigo yace ta same shi a can." Halisa taji gabanta ya fad'i! da sauri ta juya ta fita daga dakin...Larai na gaisheta ko sauraranta ba tayi ba ta nufi dakin a karo na biyu. Ba tare da tunanin komai ba ta shiga bubbuga kofar dakin tana kiran sunansa. Halisa ita take sha'aninta dan Abbah Abbas ba jinta yake ba ya riga ya samu sake ya samu kankanuwar yarinya mai tarin baiwa da ni'imar da ta kusa zautar dashi! Ya kasa barinta sai sanja mata kwanciya yake yana ha'karta tamkar wanda baya cikin hayyacinsa. Naja'atu kam wuya tasa tayi gum! da bakinta sai rintse idonta take dan tuntuni ta samu satisfaction har sau biyu yanzu babu wani abun da take fuskanta in banda wuya ga wata iriyar kunyarsa da take ji dalilin daya sa kenan take rufe idonta dan bata son ta dinga hada ido dashi yana cikin irin wannan yanayin. Halisa cike da tsabar bakin ciki da takaici ta bar gurin tamkar iskarta zata tashi a lokacin dan a jigace ta shiga dakinta ta kwanta kan gadonta tana kukan bakin ciki...Wato jiya data hanashi ashe ya shirya ci mata mutunci saboda rashin adalci ko tashinta baiyi ba ya bar mata dakinta kuma a cikin hakkinta ya kulle kofa da wata.(Kunji Halisa ko wato ta manta irin abinda ta dinga yiwa naja'atu cikin nata hakkin) *Nifa har yanzu na kasa tantancewa akan muhawarar mu daku ta kwanakin baya dan Allah a cigaba da "nemo mana fatawa daga gurin malamai shin ya hallata Namiji ya ke'be da matar da ba'a cikin dakinta yake ba, kamar dai yanda Abbah Abbas keyi a gidansa na tambayi malam biyu sunce bai hallata ba, sannan na tambayi wani malami shi kuma yace musulunci ya bawa namiji damar ya kusanci matar da ba'a dakinta yake ba, kamar dai yanda Hajiya Bhomis da Sistar Aisha Abdullahi suka fad'a! gabadaya" kaina ya kulle na rasa manene gaskiyar magana* Naja'atu taji jiki kafin Abbah Abbas ya saurara mata duk tayi muzu-muzu da ita lallai ta yarda da jarumtarsa dan gabanta har wani tsut-tsut! yake mata tana jin ma sai tayi ruwan dumi sannan zata ji sassauci...Bargo taja ta rufe jikinta kunyar idunya ta isheta. "Tana jin motsinsa a lokacin da yake kokarin shiga toilet sai ta mike da kyar tana neman kayanta tasa," "bayan tasa kayan da kyar ta mike tsaye ta dinga wata irin tafiya tana cije bakinta...Daf da zata fita ya fito daga toilet din..Dakatar da ita yayi da fadin""Kada ta fita a haka taje tayi wanka tukkuna." Babu yanda ta iya tazo ta wuce shi simi-simi ta shiga toilet din...Shi kuwa yana shirya jikinsa ya bar dakin..Yara tuntuni sunyi break fast dinsu sun wuce skull sai ya nufi dakin Halisa. Kwance ya tarar da ita ta tsurawa rufin dakin ido taci kuka ta koshi "Yana shiga ta mike zaune tana kallonsa bakinta na rawa tace""Kada ka kusanto inda nake idan ba hakaba" "sai nayi maka illah.""!! sai kawai ta tsaya yana kallonta dan gani yayi kamar ma ba ita bace!! Yace.""Ke me yake damunki? ni zaki illata.""." A fusace! ta diro daga bed din ta dauki kwalbar turare ta fasa tayo kansa tamkar mahaukaciya...Da sauri ya bude dakin ya fita yana mamakin al'amarin anya kuwa ba zai sa ayi wa Halisa ruk'iya ba. Koda ta fito daga dakin Kansa tayo da kwalbar a hannunta! Yayi saurin kaucewa yana kokarin murde hannunta!! Naja'atu ta fito daga dakin nasa duk ta zurma tayi wata 'yar rama ta lokaci guda. Halisa na ganinta cikin "wata irin hard'ad'diyar magana tace""Dama ke muke nema."" Sai ta nufe ta da abinda ke hannunta kafin naja'atu tayi wani yunkuri Halisa ta kai mata duka a fuska da kwalbar dake hannunta, aikuwa ta tsaga mata gefan kunne jini ya soma fita! Dafe fuskarta tayi jikinta na kyarma tana salati ta 'buya a bayansa" tsoro duk ya cika mata zuciya anya kuwa Halisa nada hankali. Murde hannunta yake kokarin yi domin ya kwace makamin tana sake fizgewa burinta kawai taga ta "samu Naja'atu! Wani wawan mari ya kwada mata a fuskarta, a take ta silale ta fad'i a gurin tana wata iriyar fuffuka da fitar da farar kumfa a bakinta..." *Halisa kin had'u da aiki kin gayyato ba'kaken aljanu jikinki za kuwa su hanaki kwanciyar hankali tunda dai Abbah Abbas da iyalinsa sunfi karfinsu a kanki zasu dinga hucewa.* Yau Pege din babu yawa kuyi manage sai mun hadu idan anjima da yardar Allah *Littafin na kudi ne..!* Koda zaki ganshi a gruops to na sata ne idan kina bukatar biyan kudin littafin ga yanda abin yake Vip Gruop#600. Normal gruop#300 Account: 0542382124..Binta Umar gtbank..Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* Mddbhrmbn39 A mutukar tsorace Naja'atu ta matsa gefe tana zare idonta tayi masifar tsorata da ganin abinda Halisa takeyi sai wasu surutai take wanda gabad'ayansu basa gane abinda take cewa. To shima Abbah Abbas din a nasa b'angaran ya dan tsorata da abinda Halisan takeyi sai dai da yake namijin gaske ne bai nuna ba tunda dama ba wannan ne karo na farko da halisan ta ta'ba tada iska a gabansa ba. Baba Larai mai'akinsu ce ta fito daga kicin taga abinda ke faruwa hankali a tashe ta 'karaso gurin tana "tambayar Naja'atu...A tsorace tace""Wallahi nima ban sani ba kawai naga ta fad'i a gurin ne....." "Baba Larai ta kalleshi jikinta a sanyaye tace""Alhaji anya Hajiya ba iskokai takeyi ba wannan birgimar da" "takeyi bata hankali bace.""" "Cikin alhini da damuwa yace.""Abinda ke damunta kenan insha Allahu kuma zanyi maganinsu. Ya kalli" "Naja'atu da fadin ta dauko masa ruwa...Kasa motsi tayi a gurin, Baba larai ita ta wuce da sauri taje ta dauko masa ruwa karamar roba ta kawo masa." Ya bude murfin ya tsuguna gaban Halisan ya shiga tofa addua a cikin ruwan kamar yanda yayi a kwanakin baya ya shiga yayyafa mata ruwan adduar a jikinta. Sai da duk ya Jike mata fuskarta da ruwan adduar sannan abinda takeyi ya lafa. Ya ajiye robar ruwan ya cigaba da tofa mata adduoi a fuskarta. Kamar anyi ruwa an dauke Halisa ta daina burgimar da takeyi jikinta ya shika bacci mai nauyi "ya dauketa..Mikewa yayi cikin yanayi na damuwa ya kallesu da fad'in ""Kada wanda ya tashe zata tashi da kanta.'' Baba larai tace"" Insha Allah babu wanda zai tunkari inda take Allah ya bata lafiya." "Ya amsa da ameen tare da kallon Naja'atu a nutse yace"" Kiyi hakuri da abinda tayi miki bata cikin" "hayyancinta. Naja'atu tsabar tsoro yasa ta manta da ciwon da Halisa taji mata a gefan fuskarta, tasa" hannu a gurin tana ta'bawa kawai sai taji danshi tana dubawa taga jini a hannunta amma ba sosai ba. "Hawaye ne suka zubo mata yanzu da badan yana gidan ba Halisa zata iya yi mata mummunan rauni kuma karshe babu wani mataki da zai dauka sai dai ace tayi hakuri Yace.""Ki sanjo hijab tunda wannan" "ya 'baci da jini sai muje asibiti a duba miki gurin, a sanyaye taje ta sake hijabi ta fito, Tarar dashi da Baba larai suna maganar Halisa inda yake cewa zai kira malaman rukiya suyi mata dan ya fahimci iskokin dake damunta masu cutarwa ne, Baba larai tace""To Allah yasa ayi cikin nasara."" Naja'atu ta d'aya gefan ta wuce tana waiwayen inda Halisan ke kwance gabadaya yanzu masifar tsoranta take ji........To Da yake tayi saurin kaucewa yasa Halisa bata samu nasarar illata mata fuskarta ba d'an gurin daya tsage aka wanke sannan aka bata magunguna masu kyau wanda zasu taimaka gurin dusashewar ciwon Bakin" "gate ya ajiye ta yace ta shiga gida zai wuce kasuwa, kuka tasa wai ita ba zata shiga gidan ba tsoron Halisa takeji sai dai ta shiga gidan aunty Maryam idan ya dawo da yamma ta dawo gidan.A take ya nuna mata rashin amincewarsa yace lallai sai ta shiga gidan Halisa bata isa tayi mata wani abun cutarwa ba, Tasa gaddama hade da fad'in ""Gashinan ta tsaga mata fuska da makami ai idan ta farfado ta ganta a gidan zata sake d'aukar makami a kanta! Suka dinga tababa ita dashi a motar Abbah bai ta'ba tsammanin yarinyar nada taurin kai irin hakaba, ita kuwa Naja'atu da biyu take masa haka dan kawai ta d'aga masa" hankali ne ya za'bi zama da Halisa ita ya rabu da ita "Ganin tana 'bata masa lokaci ne yasa yace""Ta fitar masa a mota tunda ita bata jin magana, aikuwa ta" "bude motar ta fita tana kuka kamar wacce aka aikowa da mutuwar iyayenta, yasa mata ido kawai yana kallon inda ta nufa, sai yaga ta dauki hanya tana tafiya tama wuce gidan aunty Maryam din da alama kofar na'isa zata nufa...Da sauri ya tari gabanta da mota taja ta tsaya tana kallonsa da idanunta da sukayi jawur! duk tana sane take wannan kukan iskancin...Gilashin motar ya sauke babu fara'a a tare dashi yace."" Ki shiga gidan aunty Maryam din amma kada ki sake kije kofar na'isa ki fada musu wata magana" akan al'amarin nan daya faru. "Ba tare da tace masa komai ba ta juya da niyyar zuwa gidan anty maryam, bai ja motar ba sai da ya" tabbatar da cewar ta shiga cikin gidan sannan yaja motar...Yana dab da fita daga layin Salim ya shigo da mota da niyar daukarsa bayan ya ajiye yara a skull Ganin kamar Kawun nasa na cikin damuwa yasa baiyi magana ba yayi saurin bin bayan motarsa data fice daga layin gidan. Aunty Maryam na ganin Naja'atu wujiga wujiga ga gefan fuskarta manne da plasta sai gabanta ya fadi tana rawar baki take tambayarta abinda ya sameta. "Cike da neman fitina gami da 'kara rura wutar al'amarin da ya faru tace""Halisa ce haka kawai ta dauki" "kwalabar turare tace sai ta burma mata ta kashe to da bata samu damar caka mata ba sai ta yanke ta a fuskarta, tana kuka ta cigaba da cewa kuma Abbah Abbas din bai dauki mataki ba karshe ma cewa yayi" wai tayi hakuri Halisan bata cikin hayyacinta. "Anty Maryam ranta ya 'baci mutuka tace""To a gaskiya wannan al'amarin ba zai yuwu ba tunda har Halisa" "takai ga matakin daukar makami a kanki to kuwa dole a dauki mataki a kan al'amarin! dan dama Abbah Abbas din ya saba goyawa Halisa baya ko lokacin da Halimatu take raye sau nawa Halisa za tayi mata abu baya daukar mataki sai dai kawai ya bata hakuri, dan kawai ya samu mace mai hakuri suka hadu suka" dinga cutar da ita bakin cikinsu ya kasheta to gaskiya a wannan karon dole manya su shigo cikin maganar. "Naja'atu tace""Shiyasa tun farko nake fada muku cewar wannan al'amarin da kuka k'ulla akwai cutarwa a" cikinsa ina zan iya zama da Halisa muguwar macace babu irin sharrin da ba tayi min a gidan kuma ya goyi da bayanta gashi yanzu ta kai har ta dauki abu zata kasheni wallahi idan baku raba auran nan ba to "zan gudu na bar muku garin kowa ya huta."" Cikin kuka na fitar hankali ta kare maganar" "Anty maryam jin maganar guduwa yasa hankalinta ya tashi tace""Daina kuka nima ban goyi da bayan ki" "cigaba da zama a gidan ba, bayan gagarimar matsalar da kike fuskanta ta rashin biyan bukata kuma a dinga barazana da rayuwarki, gwara tun kafin tafiya tayi nisa a san yanda za'ayi." Dakinta ta shiga ta dauko wayarta ta dawo ta zauna kusa da Naja'atun. "Numbar mijinta ta shiga kira, wanda a lokacin ma suna tare da Abbah Abbas din a kasuwa suna sake" "tattauna maganar jiya da naja'atu taje ta fadawa maryam din ta rashin gamsuwa...Abbah Magaji ya daga wayar da sallama a bakinsa, to da yake handsfree yasa babu abinda Abbah Abbas din baya ji Anty" "maryam muryarta na rawa tace""Abban Ilham abubuwa fa suna nema su lalace! ga Naja'atu nan muna tare da ita ta shigo min hankalinta a tashe tana kuka ga wani irin rauni a fuskarta wai Halisa ce ta dauki makami zata caka mata da bata samu damar caka mata ba sai ta yanke ta a fuskarta wallahi baka ga abun ba babu kyawun gani, a gaskiya yarinyar nan na cikin tashin hankali mai girma, Aure kwana takwas duk ta lalace kullum babu nutsuwa a tare da ita ga wannan babbar matsalar da na fad'a maka jiya a gaskiya yana da kyau ku zauna gabadayanku ku duba al'amarin nan kada garin son zuciyarku ku cutar da yarinyar nan Dan gaskiya xaman gidan Abokinka sai wanda ya shirya Halisa ba a zaune take ba."" Aunty" maryam ta karashe maganar ta tana sauke numfashi. Abbah Magaji ya dinga kallon abokin nasa ya rasa ma abunda zai cewa da matarsa dan duk ta daureshi "da jijiyoyin jikinsa...Tace""Abban Ilham kana jina kuwa.'' Yace.""Duk naji abinda kika fada idan na dawo gida zamuyi maganar insha Allahu kuma kada ki bari yarinyar taje ko ina sai na dawo.""" "Tace""To insha Allahu dama babu inda zan bari taje." Kashe wayarsa yayi ya cigaba da kallon abokin nasa dan yasan yaji komai kawai yana bukatar karin bayani daga bakinsa Abbah Abbas ya cire hular dake saman kansa yasa hankici ya goge zufar goshinsa ya kalli abokin nasa "cikin wani irin yanayi na tsantsar damuwa da tashin hankali yace.""Duk abunda Naja'atu taje ta fa'dawa Maryam hakane! Yau da safe kafin na fito al'amarin ya kasance tabbas Halisa ta dauki kwalbar turare da niyyar ta illatar dani kamar yanda tafad'a da bata samu nasara a kaina ba sai ta huce kan Naja'atu akan wani dalili nata na daban, amma Halisa bata dauki kwalbar turare da niyyar ta cakawa Naja'atu ta kasheta ba kamar yanda naji Maryam na fad'a maka yanzu..Sannan kuma inaso kasan da cewar abinda Halisan tayi bawai tayi shi bane a cikin hayyacinta ba ina kyautata zaton Halisa na tare da mugwayen aljanu wanda suke tunzura mata zuciyarta ta dinga kokarin aikata mummunan abu a kwanakin baya idan baka mance ba na fad'a maka cewar a ranar da Halisa ta samu labarin aurena da Naja'atu kwanana ne kawai a gaba dan wuka ta dauko zata kashe ni da ita da gaske caka min za tayi daba don nayi gaggawar murdeta na kwace wukar ba to da zata iya illatani kuma a ranar na tabbatar da cewar tana da aljanu" "dan a gurin suka bugeta.""" "Abbah Magaji ya jima kansa a kasa yana ta nazarin maganganun abokin nasa, to a gaskiya idan hakane" "zaman Halisa da Naja'atu a guri daya bai taso ba dole daya ta matsa ta bawa daya guri ma'ana ya zamana ko wacce na gidanta tare da sharadin 'kin ziyartar juna domin a samu daidaito da zaman lafiya, dan mutukar d'aya na zuwa gidan d'aya to kuwa matsala zata cigaba da afkuwa. Abbah Magaji ya dago" kansa a nutse yana kallon abokin nasa ya shiga fad'a masa shawarar da ya yanke a zuciyarsa wacce yake ganin kamar itace mafita a garesu "Abbah Abbas yace.""Tun farko haka naso ya kasance to a tsakaninsu Halisan da Naja'atu babu wacce na" isa nace ga yanda za'ayi tace to! Halisa ganin ido Naja'atu taurin kai! amma tunda al'amarin nan ya kasance da haka insha Allahu bayan munje umara mun dawo zan dauke Naja'atu daga gidan gabad'aya zan sanja mata gida idan ma bata so ta zauna a tsohon gidana dake d'anbare zan dai samar mata gurin zama wanda ya dace! Sannan ina k'ara baku hakuri a bisa abinda ya faru a yau insha Allah zan nemi "malamai domin su zauna kan Halisa a sama mata lafiyarta.""" "Abbah Magaji ganin yanda hankalin abokin nashi ya tashi yasa ya sassauta zuciyarsa yace.""Haba Alhaji" "Abbas meye abin bada hakuri ai ba wata matsala bace wannan insha Allahu Allah zai daidaita maka zamantakewar gidanka da iyalinka sannan kuma naji dadin kar'bar shawarata da kayi ina rokon Allah ya kawo zaman lafiya da daidato a tsakanin iyalinka."" Abbah Abbas ya mika masa hannu da fad'in Ameen ya" "Allah nagode sosai abokina.""" To 'bangaran Halisa kuwa sai kusan uku da rabi na rana ta farka da jan gindi ta shiga dakinta ta zabga "tagumi tana kallon guri guda, tunda taji kanta yayi mata nauyi da kuma kasala da ciwon jiki yasa ta gane cewar aljanunta ne suka tashi, hawaye ta dinga sharewa tana jin wani irin daci a bakinta, shin wai ita a haka zata kare rayuwarta ne a duniya bukatarta ba zata biya bane.? Sai da taci kukanta ta koshi sannan ta lalla'ba ta shiga wanka ta fito da wata iriyar masifaffiyar yunwa da kyar ta shirya jikinta ta zauna a zaune a kan dadduma tayi sallah saboda tsabar rashin tsoron Allah haka ta hada sallahr azuhur da la'asar" a zaune ba tare da tayi addua ba ta cire hijabin ta fita palo Larai tana zaune ita kadai tana kallon tv tana so hudu da rabi tayi ta shiga kicin...Tana ganin Halisa ta fito "tace""Hajiya sannu da jiki kin fito kenan.""" "Da kyar ta amsa tana kokarin zama kan kujera tace""Ki kawo min abinci yunwa nakeji."" Larai ta mike da" sauri ta nufi kicin domin kawo mata abincin. "Larai na ajiye mata abincin tace.""Ina Naja'atu take.""? Larai tace""Eh to tun dai da suka fita da maigidan" "bata dawo gidan ba."" Halisa tayi shuru tana tsakurar abincin mamaki take sosai akan ya akayi yarinyar ta iya samun galaba a kanta har ta iya janye hankalin mijinta ya rufe kofa da ita a cikin kwananta a gaskiya al'amarin yayi masifar girgizata wai yau ita yarinyar k'ankanuwa tayi wa satar kwana humm!! Da kyar" take cusa abincin tana tunanin irin mugun abun da za tayi wa yarinyar ta huce bakin cikinta. *Halisa in banda abinki meye abin damuwa bayan kinsan ko ya kulle kofa da yarinyar ba iya tsinana komai zaiyi ba to meye abin d'aga hankali kuma* Naja'atu na can tare da aunty maryam tana ta fad'a mata karya da gaskiya aunty maryam kuwa ta hau kai ta zauna dan saboda ta riga tasan halin halisa babu irin abinda ba zata iya aikatawa ba shiyasa taji gabadaya ba tayiwa yarinyar sha'awar zaman aure a gidan domin Halisa duk macen da zata zauna da ita sai ta shirya. "Sai bayan magariba suka dawo gidan shida Abbah Magaji sukayi sallama kowa ya nufi gidanshi, yayi" "mamaki da baiga Naja'atu a gidan ba...Tabbas yarinyar naso ta d'ora masa ciwo mai tsanani duk da cewar yana da tabbacin tana gidan abokinsa hakan bai masa dadi ba saboda shi a rayuwarsa ya tsani ya dawo gida ya tarar da babu daya daga cikin iyalinsa....Halisa ta daure ta kula dashi gurin cin abinci ya tambaye jikinta a sanyaye tace da sauki Yace.""Kin san abinda yake damunki kuwa."" Kamar wata shashasha tace""Ban sani ba wallahi."" Yace.""Kina tare da ba'ka'ken aljanu wanda ni tunda nake tsayin shekarun da nayi dake ban ta'ba sanin kina dasu ba sai da kikaji labarin aurena da yarinyar nan sannan kika fara tayar dasu shin kodai ke kika janyowa kanki su dan saboda ni nasan lafiya lau na aureki" "baki da wata matsala.""" "Murya na rawa tace""Kawai sai na janyowa kaina aljanu a ina zan gansu na janyosu dan Allah ka daina" "wannan maganar kada ka 'bata min rai. Shin kai baka tunanin iyayen matar taka zasu iya had'ani dasu ai wannan tsohon mai zama akan buzu kullum babu abinda ba zai iya ba, kullum yana nunawa duniya shi na Allah ne nan kuwa zuciyarsa tafi ta fir'auna.""" "Abbah Abbas 'bata rai yayi yace.""Bana son rashin kunya da zargi Baba malam bazai cutar dake ba malami" "ne shi ba boka ba kuma yana d'aya daga cikin malaman da zan kawo domin suzo suyi miki ru'kiya.""" "Jin maganar ru'kiya yasa ta fashe da kuka tace""Ashe har an kai wannan matakin da zaka dauko malamai" "su rufu a kaina suyi min ru'kiya ni kuwa wace iriyar iska ce dani da za kayi min haka.""" "Cike da mamaki yake kallonta yace""Okey wannan yana nuna min cewar kinfi so a rabu dake kiyi abinda" "kike so ko kuma suyi abinda suke so a kaina da iyalina kina dauko wuka da makami domin cutar dani da wanda ya shafe ni to idan kina sane kikeyi zanyi maganinki idan kuma su aljanun ne suke saki ki fad'a musu nafi karfinsu."" Halisa ta dinga kuka tana fad'in ""A ina zan gansu na fad'a musu sa'konka dan Allah ka bar maganar rukiyar nan."" Yace.""Baki da gaskiya tunda kike maganar a bar maganar rukiya hakan na nufin abubuwa da dama ana so a rabaki da wahala kina cewa a bari to bazan bari ba sai anyi idan kece" kika siye su da kudinki zasu fad'a kowa yaji Halisa gabanta ya dinga dukan uku uku shikkenan asirinta ya kusa tonowa Allah yasa aljanunta su rufa "mata asiri kada su tona mata asiri a idon duniya, adduar da takeyi kenan a cikin zuciyarta tana kuka." "Naja'atu kuwa tana can suna fafatawa da Abbah Magaji dan cewa tayi ba zata dawo gidan ba, Abbah" "magaji tun yana mata masifa har ya dawo rarrashi dan sabida yasan halinta da taurin kan tsiya da kyar ta hakura zata koma gidan, Abbah magaji yasa Aunty maryam ta rakota." Halisa da kyar ta iya amsawa aunty maryam gaisuwarta dama sun saba 'yar d'auke d'auken kai a "tsakaninsu, aunty maryam kasa had'a ido tayi da Abbah Abbas duk kuwa da cewar suna dan wasa a tsakaninsu, abinda yasa ta kasa hada ido dashi kuwa maigidanta ya fad'a mata cewar lokacin da ta kira wayarsa tana fada masa a binda ke faruwa Abbah Abbas din na kusa dashi kuma yaji komai, wannan dalilin yasa ta kasa zama a gidan tayi musu sallama da ta tafi...Naja'atu kuwa dama ko zama ba tayi a" palon ba ta shige dakinsu mussadiq tayi kwanciyarta. ******** A tsakanin kwanaki biyu zamantakewar gidan duk ta dawo wani iri Halisa tayi sanyi sosai tunda taji "maganar rukiya ta shiga nutsuwarta ta daina rawar kai sai ta yini a dakinta ma bata fito ba Naja'atu da Baba Larai ne kawai suke sha'aninsu. Yau ya kasance girkin Naja'atu ne, tana ta murna dare yayi su" "ke'be da maigidan dan gaskiya kwana biyu tayi missing din soyayyarsa ta shirya cikin 'kananun kaya wanda sukayi mata kyau sosai ta zauna a palo cikin yaran suna ta wasa da dariya, taji dadi sosai da taga halisa ta daina power a gidan Koda ya shigo gidan ya gansu a palon sai yaji farin ciki ya lullubeshi," "amma rashin ganin Halisa a cikinsu ya sosa masa rai! salo salo din da Halisa takeyi bayayi masa dadi ko kadan, dan haka bayan ya amsa gaisuwarsu kai tsaye dakin Halisa ya nufa. Naja'atu tabishi da kallo tana" "jan tsaki. ta tsani taga yana mu'amular arziki da Halisa( Ikon Allah wai Naja'atu meke damunki ne kullum kina cewa bakya son mutum amma kina kishi a kansa da alama kema kina bukatar ayi miki rukiyar). Samunta yayi a kwance tayi shuru, ya tsaya a kanta da fad'in ""Halisa wai me akayi miki ne" kika takura kanki kwana biyu bana jin dadin abinda kikeyi a gidan nan dan Allah ki saki jikinki kamar da ki cigaba da mu'amular ki da kowa. "Kuka tasa tace"" Ba dole na ke'be kaina ba tunda ni mai laifi ce a gidan nan yarinyar 'karama na zagina na" "bangazata nayi min dariya ai dole na takura idan kuma na dauki mataki a kanta a dauki laifi a dora min ai ni kam walwalata da farin cikina ya kare a gidan nan.""" "Yace.""Kiyi hakuri insha Allahu ta kusa ta bar miki gidanki ni nagaji da wannan tashin hankalin naku me" "yasa lokacin Halimatu kuke zauna lafiya da juna."" ? Tace""Halimatu daban take a cikin mata Naja'atu kuwa annoba ce a cikin mutane wallahi watarana yarinyar nan sai ta wargaza maka gidanka idan ba kayi da gaske ba." "Yace.""Magana dai ta wuce insha Allahu komai ya kusa zuwa karshe ki taso ki bani abinci."" Yafada yana" me juyawa da niyar fita..Halisa dama irin wannan damar take nema tunda tasan ba girkinta bane to tunda ya nema da kansa bari taje kodan ta cuzgunawa yarinyar Naja'atu na ganin sun fito daga daki a tare tayi saurin dauke kanta zuciyarta ta sosu amma dai ta share bata nuna komai ba gabadayansu suka zauna gurin cin abincin Tana kallon abubuwan da Halisan keyi "masa yayi shuru baice komai ba ga yara a zaune sai haushi ya isheta kawai ta mike tana kallon yaran tace""Kowa ya dauko plate dinsa muje palo muci a can."" Da sauri suka mike kowa ya dauki nasa, dama can haka suke daga tace musu ga yanda za suyi basa yi mata musu...Halisan dashi kansa suka bisu da" kallo domin kuwa sun rasa abin cewa.... To sai bayan goma na dare suka kashe tv kamar dai koda yaushe suka nufi daki domin shirin kwanciya...Naja'atu wanka akaje a kayi tayi bursh ta shirya cikin kayan bacci harda sa turare ta zauna tana jiran shigowar maigidan tasan dole idan ya shigo sai ya nemi data bishi dakinsa aikam zata bishi dan yini tayi cikin sha'awa da tashin tsigar jiki idan ta tuno soyayyarsa har wani lumshe idonta take. Har "karfe goma sha daya da rabi idonta biyu tana jiran shigowarsa shuru bai shigo ba, ranta ya baci sosai, a sanyaye ta shiga gyara shimfidarta dake kasan kafet taji ya turo kofar ya shigo da sallama ajiyar zuciya mai sanyi ta sauke ta amsa masa ya karaso cikin dakin sosai kai tsaye taga ya fara zagaya gadon yaransa yana musu addua kamar yanda ya saba! shuru tayi tana binsa da kallo har ya gama musu ya juya zai fita" ba tare da ya tanka mata ba Takaici kamar ya kasheta kamar wata shashasha tabi bayansa da kallo tana ji kamar taje ta rungumeshi...Kwanciya tayi tana kuka tare da takure jikinta tana jin danshi danshi a pant dinta tsabar sha'awar data yini dashi yasa ta zubar da ruwa sai kace kankana. Shi kuwa Abbah Abbas bacin ran da yake cike ne yasa yaji gabadaya ma baya sha'awar komai baban burinsa ya kwanta ya huta sannan kuma yayi tunanin yanda zai kawo zaman lafiya a gidansa dan ya lura ba k'aramin gagarimin aiki bane a cikin zaman Halisa da Naja'atu a gidansa. Washe gari gidan haka kowa ya tashi da rashin walwala dalili ruhikan gidan (Abbah Abbas da Naja'atu) basa cikin walwala sai ya kasance suma yaran basu da walwala Halisa kuwa a cikin yaran babu wanda yake ta tata. "Tsaf ya fito da shirin fita, Halisa da Baba Larai ne a zaune a palo suna hira...Ya duba yaga babu naja'atu a" "gurin kai tsaye sai ya nufi dakin yaran, nan ya sameta a kwance tashi tayi zaune tana kallonsa...Sai da ya kalli agogon dake daure a hannunsa sannan ya kalleta babu cikakkiyar walwala a tare dashi yace.""Ki shirya anjima kadan Salim zai zo ya kai ki kasuwa kamar yanda nayi miki al'kawari."" A dan sanyaye" "tace""To nagode."" Fita yayi ba tare da ya sake cewa komai ba." Shuru tayi bayan fitarsa tana tunanin sauyarsa kodai haushinta yake ji kan abunda ya faru jiya oho koma dai menene ai ba 'karya tayiwa matarsa ba ta tabbata idan da Halisa ta samu dama a kanta mugun rauni "za tayi mata, tasa hannunta a gefan fuskarta ta shafa inda ciwon yake cike da takaici tace""Allah yasa macuciya kawai.""" Salim yazo ya d'auketa kamar yanda ya fada mata...Kai tsaye sahad store dake zoorod suka "nufa...Naja'atu ta dinga kallon Salim a fakaice tana mamakin sauyawarsa Salim ya goge sosai yayi ki'ba ga wani uban haske da yayi idanunsa sun kara bud'ewa! sai taji duk jikinta yayi sanyi ganin kamar Salim din kamar yafi karfinta. Salim murmushi yayi ya kalleta yana kanne mata ido yace""Anty Naja'atu ya gida" "ina fatan kina nan lfy.""" "Ta 'bata rai murya na rawa tace""Salim bana son sunan nan da kake kirana dashi ni wallahi sai nake ganin" "kamar ka daina sona yanzu."" Salim ya shafa sajensa yana wani munafikin murmushi yace.""Ai naja'atu ina kyautata zaton da soyayyarki zan mutu hausawa na cewa fad'an da yafi karfinka sai ka mayar dashi wasa," "naga Kawu Abbas ya rike wuta a kanki shiyasa na cire rai da samunki.""" "Tace""Salim wallahi ina nan ina kokari kan al'amarin nan dan Allah ka daina wannan maganar indai zaka" aureni ni kuma nayi maka al'kawari insha Allahu zanyi duk yanda zanyi naga bukatarmu ta biya. "Yace.""Haba baby nifa jikina yayi sanyi wallahi bana tsammanin za'a samu budurci a tare dake nafi kowa" sanin waye Kawu Abbas a fagen son mata kullum a gabana shida abokansa na kasuwa suke siyan magungunan karfi domin saduwa da iyali na tabbatar da ba zai zuba miki ido yana kallonki ba. "Naja'atu gabanta na faduwa tace""Wallahi ka daina wannan maganar ni har yanzu budurwa ce to har" yaushe ma akayi auran da wata mu'alama zata faru a tsakanimu na fada maka fa kai zan mallakawa "komai nawa to me zai sanya ka dinga wannan maganar."" ...murmushi yayi yana sake sosa sajensa cikin shakiyanci yace. Amma dai nasan ko baiyi mai gabad'aya ba yana rungumeki ko.""? Da sauri ta sunkuyar" "da kanta tace""Dan Allah ka daina wannan maganar bana so."" Salim yace.""Shikkenan tunda bakya so na" "daina ina nan ina jira ki cika min al'kawarina ki fito ni kuma nayi miki al'kawarin auranki.""" Naja'atu siyayya tayi sosai kaya na manyan mata na kece raini manyan atampopi da lesuka da abaya "gami da mayafai masu tsada da takalma da kayan make up duk abinda take bukata sai da ta dauka akwatina hud'u ta cika da kayanta sukeje gurin biya Salim ya tura musu kudin kayansu ta banki, yaran dake aiki a gurin ne suka kwashe akwatin nan suka kai mota, daf da zasu fita daga get din Sahad din Abbah Abbas din ya kira wayar Salim din, cikin girmamawa Salim ya daga wayar da fad'in ""Kawu gamu nan zamu koma gida alhmdullhi na kaita ta za'bi duk wani abu da take bukata kamar yanda ka umarce ni."" Tana jin muryarsa yana cewa""To ya tabbatar da cewar ka shigar mata da kyan cikin gida."" Cike da ladabi yace.""Insha Allahu Kawu..Sunayin sallama Salim ya juyo yana kallonta yana d'an 'bata fuska yace.""Kinji mutuminki ko sai kace wani yaronsa wai yana cewa na shigar miki da kaya cikin gida nifa wallahi mugun haushinsa nakeji ina bala'in kishinsa. Dariya tasa tace""Kaji ka da wata magana to da" "meye kai idan ba yaron nasa ba, kawai kabi umarnin ubangidanka."" Yace.""Daga ranar da kika zama matata zan daina yi masa hidima yanzu inaso na cimma munufata ne a kansa shiyasa nake zama a karkashinsa."" Kallonsa ta shigayi tana mamakin wace irin munufa ce a zuciyarsa dangane da Abbah Abbas din, jikinta ne yayi sanyi cikin zuciyarta tana adduar Allah yasa munufar alkairi ce a zuciyar Salim din..Cike da hirar Abba Abbas din suka isa gidan..Salim ya shigar mata da akwatinan kayanta cikin gidan kamar yanda aka umarce shi, Halisa na ganin iyayen akwatina masu masifar tsada da daukar ido sai" hankalinta ya tashi 'kyashi da ba'kin ciki gami da kishi ya cika mata zuciyarta............ *Littafin na kudi ne!* Koda zaki ganshi a group na sata ne idan kina bukatar biyan kudin karatu ga yanda abin yake Vip Gruop#600 Normal#300 Account.. 0542382124....Binta Umar gtbank...Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *MANZIL ALWAFIR ABUJA * "_*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci, magungunansu babu almundahana a" ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu kowace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye akwai groups na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rigistar dasu kukanki ya kar'e idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_ Mddbhrmbn40 Naja'atu ganin yanda Halisa tayi kici kici da fuska yasa ta fasa shiga daki ta tsaya suna magana da Baba "Larai inda take cewa da ita tazo taga kayan data siyo..Baba Larai na washe baki taje kusa da naja'atun suka shiga kici kicin bude kayan, Halisa kasa barin gurin tayi tana ta satar kallon kayan ta gefan idonta...Ganin irin manya manyan lesukan da Naja'atu take ta fito dasu daga akwatin ne yasa hankalinta ya tashi cikin lesukan dik babu na kasa da dubu ashirin daga na talatin sai na hamsin sun kai guda biyar ga iyayen atampopi masu kyau da tsada! Naja'atu na dariya tace""Baba wai dani za'a rainawa hankali aje a had'o min wasu banzayen kaya ace sune lefena an dauka nima 'yar kauye ce."" Ta'karasa maganar tana" dariya kana ganinta kasan tana cikin nishadi. To kowa dai yayi zagi a kasuwa yasan da wanda yake..Halisa uffan ba tace ba ganin kayan lefen na'ja'atu yayi masifar daga mata hankali a 'kiyasin da tayi da akwatin nan da kayan dake ciki sun kusa tassama miliyan guda..lallai ba zata yarda da wannan rashin adalcin ba tana ganin idan ya dawo itama dole ya 'kara mata kudi akan abinda ya bata. "Baba Larai da bata san abinda ke faruwa ba tace""Aikuwa dai kaya sunyi kyau ubangiji Allah yasa ki kashe" "lafiya Allah kuma ya baku zaman lafiya dake da mijinki."" Domin ta sake cuzgunawa Halisa ta amsa da ""ameen Baba larai nagode."" Halisa ta kalli Larai fuskarta a murtuke tace""Ya kamata ki tashi haka ki shiga kicin yamma tanayi."" Baba Larai na 'yar dariya ta mike da fad'in ""Na tsaya kallon kaya ne Hajiya to bari" "na shiga kicin din.""" Halisa ta bita da kallon banza tana jan tsaki haushin matar take ji ganin kamar tasu tazo daya da naja'atu ita duk wanda zaiyi muamular arziki da yarinyar ba kaunarsa take ba. Naja'atu tana gyara kayanta cikin akwatin tana wa'kokinta tanayi tana satar kallon halisan dan duk "abinda takeyi a tsorace take tana jin tsoron kada aljanunta su tashi ta maketa a gurin amma saboda neman fitina bata fasa sakar mata da habaici ba. Halisa ta kalleta tana murmushin mugunta tace""Duk" wannan rawar kan da kikeyi zaki daina ne a tafin hannuna kike wallahi ni naso ki zauna a gidan nan da "banso zamanki a cikinsa ba da tuni kin dade a gidanku amma kinyi da 'yar halak wallahi sai na nuna miki ke 'karamar mara kunya ce.""" "A nutse ta kalleta kamar babu wani 'kulli a zuciyarta tace""Ikon Allah to me nayi miki da kike wannan" "maganar naga tunda na shigo ban ambaci sunanki ba ballantana nayi miki rashin kunyar da kike magana a kanta, kinga aunty Halisa bana son neman rigima dan Allah ki zauna a matsayinki na zauna a nawa.""" "Halisa tace""Sharrina yafi kala dubu kuma wallahi sai bukatata ta biya a kanki."" Wannan magana ta fad'e" "ta ne a lokacin da baba larai ta fito daga kicin kuma taji da kunanta...Tace""Subahanallahi duk me ya jawo wannan maganar Hajiya.""" "Naja'atu tayi saurin fadin ""Baba kin daiji da kunanki ko? gashinan da bakinta tana fad'in cewar sai ta" cutar dani to ni ban dogara da kowa ba sai da Allah na dogara kuma babu abinda mutum ya isa yayi min komai tsafinsa da asirinsa. "Baba Tace"" Haba naja'atu ki daina fad'ar wannan maganar kinji ko itama hajiyan bacin rai ne yasa ta fadi" "haka, Yau kwanana hudu a gidan nan amma na fahimci babu jituwa a tsakaninku dan Allah kuyi hakuri ku zauna lafiya da junanku ku daina ikirarin zaku cutar da junanku...Halisa ba tace komai ba ta bar gurin...Naja'atu ta kalli Baba Larai da fadin""Baba wannan matar bata da kirki ga hassadar tsiya wai fa ganin wad'an nan kayan ne yasa ta take wannan maganar kina dai kallo tunda na shigo gidan banyi mata" "magana ba.""" "Larai tace""Ina kallo wallahi itace babba amma kuma wani sa'in itace ke tada husuma a tsakaninku ke" kuma baki da hakuri ki dinga biye mata kuna tada hankalin maigidanku dan Allah ku daina abinda kukeyi ku zauna lafiya. "Tace""A'a baba nifa wannan maganar ba zan barta ba wallahi idan ya dawo sai na fada masa ga abinda" "tace a kaina.""" "Baba larai tace""Ikon Allah ke yarinyar nan baki da wayo waye ya fada miki komai ake fadawa miji yawan" kai 'kara ga miji yana sanyawa daga ya ganki gabansa ya fad'i! duk ranar da kuka samu sa'bani da kishiyarki ki daina gaggawar fad'awa miji idan kika saba da kai masa 'kara kullum zai dinga ganin kamar kece mai laifi. "Tace""To ai maganar ce gabad'aya ba tayi min ba wai sai bukatarta ta tabiya a kaina to me za tayi min?" burinta na bar mata gidanta bata san nama fita so na fita daga gidan ba. "Larai tace""Magana dai ta wuce naja'atu dan Allah ku zauna lafiya kuma ki daina yi mata rashin kunya da" "habaici abinda yake tunxura mata zuciya kenan."" Dariya tayi tace""Ni wallahi baba bada ita nake ba kawai dan ina wa'ka sai ta tsargi kanta dan rashin gaskiya." To koda maigidan ya dawo ta nuna masa kayan nata da ya duba shima sun bashi sha'awa sun burgeshi sosai yace ta dauki wanda take so sai suje da Halisa gurin da ake mata dinki dan yana sha'awar ire iren dinkunan da Halisa take masa ado dashi a gida shiyasa yake so ayi wa naja'atu irinsu. "Tace""Bata da ra'ayin haka tafi so a kaiwa telan da yake musu din'ki tsarin d'inkunansa yafi burgeta...Yace" tunda haka take so shikkenan sai ta shirya Gobe Salim zai zo ya kaita ta kai masa. Yau ma kamar jiya da ya shigo dakin gadajen yaransa yabi yayi musu addua ya fita daga dakin ba tare "daya kulata ba, hakika taji ciwo da takaicin abin ace kwana biyun girkinta sun tashi a banxa babu wani" dan romance da sauransu...Dan haka koda ya shigo da safe da kyar ta gaishe ta juya masa baya tana jinsa yana magana da yaransa bata tanka musu ba har ya fita daga dakin Sosai tasa ido taga abinda zai wakana a tsakaninsa da Halisa tunda yau ya kama girkinta ne...Halisa yau ingilish wear tasa ko kunya ba taji ga yara a gida koda yake Halisa ita abu takeyi kai tsaye a gidan sam bata jin kunyar yara Naja'atu dariya kawai take dannewa dan ganin yanda halisa aka ci gayu cikin wata iriyar riga mai gidan nono rigar bata da hannu gajere ne sai madaurai guda biyu a bayanta wani matsatstsan siket tasa halisa bata da gashi amma gwanar kitson 'karin gashi ce duk tsantseni da kula da addini irin na maigidan sai da ya saurara mata dan idan babu wannan kitson a kanta tana komawa tamkar namiji tunda gashin kanta bashi da yawa hakuri kawai yayi ya kyaleta take sa attecment a kanta amma kullum idan ya tashi fad'ansa zai ce mata ta san da sani sallahr da takeyi ta banza ce kuma idan danshi takesa gashin doki to "ba burgeshi take ba...Halisa tayi kunnan uwar shegu dashi, dole tasa ya hakura ya kyaleta ya sa mata ido." Kasancewarsa mai so yaga irin wannan dressing din a gidansa yasa da ya dawo yaga Halisa cikinsu "hankalinsa ya tashi fitinarsa ta kwana biyu ta motsa, dama tubarkallah ga Halisa da lafiyayyan jiki mai kyau sai yaji ya sake kwadaituwa da ita da irin salonta...Naja'atu duk tana hankalce dashi a gurin cin abinci ma da kyar yaci ya basu guri..a maimakon ya zauna a palo ya duba loptop kamar yanda ya saba sai taga kawai ya nufi dakinsa....Har kusan tara da wani abun na dare bai fito ba yana cikin dakin...Duk sai taji rashin dadi mussaman da taga Halisan tabi shi dakin..Cikin mutuwar jiki da jin wani irin zazzafan kishi" ta bar palon... a daran sai da taci kukanta ta koshi sannan bacci ya dauketa.. Koda ya shigo da safe barcin karya ta tsira har ya gama abinda yake ya fita daga dakin bata ido idonta ba. Haka zaman gidan ya cigaba da gudana duk ranar girkin Naja'atu sai yaji tamkar an dauke masa sha'awarta ranar girkin Halisa kuma kamar kara masa karfi da kuzari akeyi a jikinsa idan sun raba dare suna abu daya to da safe ma kafin suyi break fast sai sun maimaita wani( Ikon Allah Aljana *'Yar Zabira* ta sanja suddabaru kenan wato ranar girkin Naja'atu tana kashe masa jiki ranar girkin Halisa tana saka masa kuzari ashe ba rabu da bukar ba wai an haifi habu Allah ka karemu daga sharrin aljani ko wane iri ne) Naja'atu daina walwala tayi gidan dan saboda abubuwan da ake mata sun fara isarta kawai dai tana kokarin gaishe shi ne amma kwakkwarar magana bata yarda ta hadata dashi dan saboda mugun haushin sa da take ji. Yau ya kasance ranar girkinta kuma saura kwana biyu su tafi umara kamar yanda taji suna fada dan duk "wani shirye shiryensu sun gama har dakin yaran ya shiga ya sameta da daddare hannunsa rike da kwalin sabuwar waya iPhone! Gasheshi tayi ya amsa cike da kulawa bai zauna ba dan ji yayi tamkar ana axalzala zuciyarsa ya fita daga dakin...Ya mike mata wayar da fad'in ""Kar'bi kisa a charge sabuwar waya ce na siyo" "miki.""" "Kallon kwalin wayar tayi kafin ta mika hannu ta karba tace nagode."" Yasa hannu ya gaban rigarsa ya ciro" "dan karamin cover ya mika mata da fadin ga sim card din."" Karba tayi ba tare da tace komai ba..Kamar zaiyi magana sai kuma yaja bakinsa yayi shuru ya juya ya fita." Wayar ta bude tana dubawa murmushi tayi na farin ciki dan saboda wayar ta burgeta sosai kuma ko "babu komai tasan zata d'ebe mata kewa cajar wayar ta warware ta bude wayar tasa sim card din sannan tasa a chaji ta koma ta kwanta tana cigaba da tunanin yanayin rayuwar data tsinci kanta, yanzu ta samu waya bata da matsalar gurin neman kawarta Munira tana jira su tafi saudia ita kuma ta gudu garinsu" Munira su nemata su rasa tunda dai kowa ya kasa fahimtar abinda ke damunta. "Ranar da zasu tafi gabadayansu kofar na'isa suka nufa saboda harda Hajiya za'ayi tafiyar, Hajiya Abu" ganin Naja'atu kamar tana da damuwa yasa ta dinga rarrashinta da fad'in ta kwantar da hankalinta wata shida kamar yau ne insha Allahu ita aikin hajji za taje idan Allah ya nufa...To ganin yanda Hajiyar ta damu da ita yasa ta saki jikinta ta nuna ai babu komai ita bata kishi dan sunje umara da Halisa itama idan Allah ya nufa za taje...Hajiyan taji dadin hakan ta cigaba da kwantar mata da hankali ita kuma tana nuna komai ba komai bane. Gabad'ayansu ita da yaran da Yaya Ramlatu Alhaji da baba malam Abbah Magaji suka rakasu airport tare da fatan alkairi Abbah Abbas yabi yaransa daya bayan daya rungumesu yana musu addua. itama yanda yayi musu yayi mata tamkar yar cikinsa ba matarsa ba sam yanzu babu wata kyakykyawar mu'amula a tsakaninsu..Halisa kam sai wani Jiji da kai take tana hura haci ita gata matar da akeso...Ita kuwa Naja'atu mugun alwashi taci a kansa tana ganin ita ba 'yar wahala bace da zata zauna tana yi masa gadin yara ya tafi da matar so wallahi sai ta bar gidan koma me zai faru sai dai ya faru.... Satin su daya da tafiya Baba Larai ta rasa gane kan Naja'atu yau da lafiya gobe babu ga wani shegen "zazzabi me naci da takeyi kullum da daddare haka zai zo ya rufeta tayi ta makyarkyata, da safe kuwa da wani d'an iskan amai mai mugun da'ci take farawa ta dinga kakari kenan a toilet tana rike cikinta." Baba larai dai ba yarinya bace dan kallon farko da tayi wa yarinyar yasa ta gane cewar da akwai juna biyu "a jikinta, to dan saboda ta tabbatar yasa da Anty maryam da ta shigo dubasu ta sheda mata halin da ake" "ciki...Anty maryam tace""Nima sai da na zargi haka tunda Allah yasa gobe litinin sai muje asibiti a dubata. larai tace""Hakan shine ya dace." Naja'atu bata san wainar da suke toyawa ba kawai dai washe garin ranar aunty maryam ta shigo gidan da safe ta shiryata sun nufi asibiti....Gwajin farko da akayi mata a gano ciki dan kimanin sati uku. Wani irin kuka tasa jin abinda dr din tace Anty maryam tayi sauri sukayi sallama da dr sa'adatun suka fito daga asibitin dan saboda bata son dr din ta fahimci abunda ke faruwa. tun a mota Naja'atu ke kuka tana dukan cikinta had'e da fad'in ita wallahi bata da ciki idan ya kasance cikine da ita to kuwa sai ta zubar dashi dan bata shirya haiwuwa yanzu ba. Hankali a tashe suka iso gida aunty maryam ta wuce da ita gidanta domin ta rarrasheta akan tayi hakuri ta kar'bi kaddararta ta daina maganar zubar da ciki kada magauta suji irinsu Halisa kenan.......... *Littafin na kudi ne...* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar biyan kudin karatu ga yanda abin yake. Vip gruup #600 Normal#300 accont..0542382124..Binta Umar gtbank Idan katin waya zaki tura ki sameni ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *MANZIL _ALWAFIR ABUJA * _*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci magungunansu babu almundahana a ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu ko wace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye da akwai gruops na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rijistar dasu to kukanki ya 'kare idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_ Mddbhrmbn41 Aunty Maryam da 'kyar ta rarrashin naja'atu ta daina kukan da ta keyi ri'ke hannuwanta tayi ta tare da "tsira mata ido tana kallonta, hakika yarinyar na bata tausayi mutuka kuma sai yau ta sake gazgata irin 'kiyayyar da takewa mijin nata itakam tunda taji furucin da yarinyar keyi akan cikin da take dauke dashi, jikinta yayi sanyi da al'amarin.....Naja'atun kuwa wani irin ajiyar zuciya take saukewa gumi na tsatstsafo mata daga jikinta tsabar tashin hankalin da take ciki yasa taji jikinta yayi garau zazzabi dake damunta tuni yayi nasa guri! babu abinda ke d'aga mata hankali gami dasa ta a fargaba sai maganar cikin dake jikinta d'an kimanin satika uku. Aunty Maryam tace""Yawwa dama so nake ki dawo hayyacinki sai muyi" "magana dake irin ta masu hankali Naja'atu inaso kiyiwa maganata kyakykyawar fahimta shin kina so ki butulcewa Allah akan irin baiwa da ni'imar da yayi miki ko? shin kin san dubban mutane nawa ne suke neman haihuwa amma Allah be basu ba me yasa ke Allah ya azirtaki da samun karuwa kike cewa bakya so har kina i k'irarin zubarwa kinsan babban laifin da kike kokarin aikatawa kuwa.""? Aunty maryam" ta'kare maganarta cikin kwantar da kai gami da rarrashi. "Ido jawur! ta kalli anty maryam din tace""Aunty maryam ke yanzu kin yarda da abinda Dr sa'adatu ta" "fad'a! ni wallahi bani da wani ciki ki daina wannan maganar insha Allahu ba zan haihu da wannan mutumin ba dan ni bana sonsa.""" "Aunty Maryam ta ri'ke bakinta tana kallonta ranta a 'bace! tace""Wai ke har wata shahararriya ce ko" kuma wata mai muhimanci ce da kullum idan anyi magana sai kice bakya son Alhaji Abbas dame kike fishi? wallahi tallahi Naja'atu kiyiwa kanki fad'a ki kuma daina wasa da damar da Allah ya baki! Alhaji Abbas yafi karfin wannan iskancin naki! kinsan babu 'ya mace da zai nuna yana so a garin nan budurwa ko bazawara ba'a bashi ba amma saboda tsabar butulci ke kin same shi cikin sauki kina iskanci! dole na fad'a miki gaskiya koda zagi zage ni saboda ina gudun ranar da zaki zo kiyi nadama kiyi kuka da "idanuwanki a ranar da kika watsar da damar da Allah ya baki.""" "Hanci taja tace""Aunty maryam ni bazan ji haushinki ba dan kin fadi ra'ayinki a kan wannan auran kowa" "ya fad'i abinda yake so nima kuma na fad'i abinda yake raina bana munafurci shiyasa shima Abbah Abbas din kullum cikin fad'a masa gaskiya ta nake kancewar ko 'kwayar zarra bana jin sonsa a cikin zuciyata, in banda abinku a'ina kuka ta'ba ji anyi zaman aure ba soyayya! Kiyi hakuri idan maganata ta" baki haushi. "Aunty maryam tace""Oh!o ni ai yanzu kin daina bani mamaki da haushi al'amarinki sai dai addua ciki" kuwa tunda Dr ta duba ta ganshi to tabbas da akwai shi tunda gashinan kin kasa lafiya ni dai shawarata ta karshe dake shine kije ki zauna kiyi tunani a kan maganar dana fad'a miki idan kina ganin abinda kika "kudurta a zuciyarki shine dai-dai ni sai nace Allah ya jishshe mu alkairi.""" "Tana gama maganarta ta dauki jakarta ta shige dakinta, tana zama gefan bed ta ciro wayarta ta kira" mijinta ta sheda masa abinda Dr Sa'adatu tace dangane da rashin lafiyar naja'atun..Amma bata fad'a masa irin iskancin da yarinyar keyi ba. Abbah Magaji cike da tsantsar farin ciki ya nemi numbar abokin nasa ya shiga kiransa...Abbah Abbas "yana harami yana addua kiran wayar ya sameshi guri ya samu ya ke'be kana ya daga wayar, suka gaisa da abokin nasa yana tambayarsa iyali Abbah magaji yace kowa lafiya lau sai 'karuwar da muka samu ashe wai wannan zazza'bin da Naja'atu keyi na al'kairi ne yau da safe nace maryam ta kaita asibiti a" "dubuta nan Dr Sa'adatu ke tabbatar mata da cewar yarinyar na dauke da ciki na tsayin sati uku.""" Wani irin murmushi ne ya su'bce masa a take ya zube a gurin yayi sujjadar godiya ga Allah kafin ya mike "tsaye cike da tsantsar farin ciki yace."" Gaskiya naji dadin wannan albishir din naka na kuma 'kara tabbatar da cewa Allah sami'uddua'o ne ina gabansa ina rokonsa akan ya azurtani da 'ya'ya masu albarka ashe ya bani ban sani ba dole nagode wa Ubangiji a bisa wannan babbar kyautar da yayi min.'' Abbah Magaji yace na taya ka murna abokina hakika aure yayi albarka tunda gashi kafin aje ko'ina an samu" "karuwa Allah ne abin godiya muna kuma rokonsa da ya sauki yarinyar nan lafiya.""" "Abbah Abbas ya amsa da ""Allahumma ameen abokina nagode kwarai yanzu haka gabadaya hankalina" yayo gida wallahi. "Abbah Magaji yasa dariya da fad'in "" Haba Alhaji ka daure ka zauna ka cigaba da addua sati d'aya kamar" yau ne insha Allah. "Shima yana dariyar yace.""Kasan ni da son yara ina ganin kamar idan na dawo babyn kawai zan gani.""" Abbah magaji yayi tai masa dariya kafin suyi sallama cike da mutunta juna. Abbah Abbas cike da farin ciki ya koma masaukinsu Halisa na zaune ita kadai a palo ita kuwa Hajiya Abu na daki bayan ta idar da sallar walha sai ta shiga jan carbi dama haka takeyi ko tana gida sallar walha bata wuce ta. Halisa na ganinsa cikin walwala da farin ciki sai itama ta ara ta yafa ta dinga dariya tana "kallonsa...Rungumeta yayi tare da sumbatar gefan fuskarta yace."" Halisa Allah ya sake azurtani da samun 'karuwa."" Sai ta kasa gane maganarsa ta shiga kallonsa dariyar da takeyi ta ragu gabanta ya shiga bugawa da karfin gaske." "Yace""Yanzu nan Alhaji magaji yake sheda min da cewar Naja'atu nada juna biyu ashe zazzabin nan da" "takeyi bayan tawowarmu na alkairi ne.""" Wani irin rugugi! kirjinta yayi lokaci guda cikinta ya hautsine ta nemi yawu ta tarasa a bakinta gwiwowinta kuwa kamar an kwad'e mata su da ta'barya! kallonsa takeyi kamar sabuwar mahaukaciya "baki na rawa tace""Ya akayi hakan ta faru..""? Ya kalleta cikin wani irin yanayi yace.""Wannan wace iriyar banzar magana ce tambayata kike ya akayi haka ta faru.""?" "Sosa kanta tayi cikin wayancewa tace""To ai gani nayi auran naku ko wata d'aya ba'ayi ba ya za'ayi ace" "har kayiwa yarinyar ciki? anya kuwa ba 'karya bane ? idan ma da gaske ne to wallahi mybe dashi tazo."" Wani irin mari! ya kifa mata cikin fusata! yace.""Ashe baki da hankali Halisa jinina kike 'kokarin shegantawa! Wannan wane irin rashin mutuncin ne.""? Halisa tuni ta shiga hankalinta ta dawo hayyacinta ashe zancan zuccin da takeyi a fili ta fad'e shi..Hakuri ta shiga bashi da fadin"" Wallahi bata" "san ta fadi maganar ba kuma dai abin ne ya bata mamaki shiyasa take kwokwanto.""" "Tsaki yaja mai karfin gaske ya mike daga kusa da ita tare da fad'in ""Shashasha mara hankali kawai."" Kallo" tabi shi dashi lokacin da yake kokarin shiga dakin da hajiyarsa take ciki...Halisa zukud'um! tayi ta 'kurawa guri guda ido gabad'aya kanta ya kulle ta marasa wane irin tunani za tayi...Naja'atu nada ciki shin yaya akayi haka ta faru? me yasa naja'atu tayi ciki da sauri haka? Ita da Halimatu sai da sukayi shekaru masu tsayi a gidan basu dauki ciki ba me yasa ita Naja'atu ko wata daya ba tayi ba ta dauki ciki? shin wai ina Aljana *'Yar Zabira* take da har ta bari wannan al'amarin ya faru???? Wasu zafafan hawaye ne suka shigo gangarowa daga idanunta. "Hajiya Abu tayi farin cikin samun labarin cikin da 'Yar dakinta Naja'atu take dauke dashi, kafin ta bar" abun sallarta sai da ta daga hannunta sama ta roki Allah ya sauketa lafiya. Aunty maryam tsabar haushin abinda naja'atu takeyi yasa ta fita daga sabgarta ta cigaba da shige da "ficenta tsakanin kicin da dakinta, haushin hakan yasa ta mike tare da daukar ledojin magunanta ko sallama ba tayi mata ba ta bar gidan...Aunty maryam ta fito daga kicin bata ganta ba sai kawai ta girgiza kanta, tana nema mata sauki gurin Allah hakika tana jiyewa yarinyar ranar da zata zo tana nadamar" abinda ta aikata. "Baba larai ta ganta ta shigo fuskarta a daure ido jajawur! hankali a tashe tace""Naja'atu lafiya ina Hajiya" maryam din tun dazu ina nan a zaune ina jiran dawowarku Zama tayi kan kujera tana goge hawayen "daya tawo mata tace""Aunty maryam tana gidanta."" Baba larai jikinta a sanyaye tace""To Allah yasa dai lafiya? Fashewa tayi da kuka tace""Wai ciki ne dani.""? Baba larai tace""Alhamdullhi to shine kuma abin kuka da tashin hankali."" Naja'atu sakin bakinta tayi tana kallon matar. Baba larai ta cigaba da cewa ai" abin farin ciki ne ya sameki da duk wani masoyinki menene abin tashin hankali addua zakiyi Allah ya "rabaku lafiya.""" "Girgixa kanta ta shiga yi hawaye wani na bin wani tace""Baba har abada ba zaku gane abinda nake ji a" "cikin zuciyata ba, amma babu komai duk abinda ya faru da rayuwata kune sila."" Baba larai tayi shuru tana kallonta dan ita bata fahimci inda maganarta ta dosa ba...Mi'kewa tayi ta dauki ledar magungunanta da wayarta ta nufi daki...Larai ta bita da kallo cike daso ta fahimci menene yake a 'kasa" wanda ita bata san dashi ba "Ruwa ta dauko ta zauna gefan bed tana kuka tana had'iyar maganin kamar yanda Dr ta umarci tayi," "kwanciya tayi bayan tasha maganin ta tsirawa rufin dakin ido, wallahi sai ta zubar da cikin nan Da sauri" "ta mike zaune ta dauki wayarta tana kokarin neman numbar Munira Kiran wayarsa ya shigo, da sauri" "ta datse kiran nasa tana jan tsaki ta cigaba da laluben numbar munira..Allah sarki Abbah Abbas sake kiran wayar yayi! da sauri ta sake datsewa! sai kawai ya shiga bin wayar tasa da kallo, a duniya ya tsani ya kira waya a kashe masa, zuciyarsa ya bawa hakuri ya sake kiran wayar a karo na uku Sai suka ce" masa busy alamar ana amfani da wayar. Ajiyar zuciya yayi ya ajiye wayar a kusa dashi yana tunanin da wanda take waya """Lallai Naja'atu ciki fa kikace kina dashi har yaushe akayi auran da har zaki samu ciki kuma ma garin yaya" "kika bari haka ta faru.""? Munira ce take fadin wannan maganar." "Cikin dusashshiyar murya tace"" Munira ni dai dan Allah duk mubar maganar yanda akayi hakan ta faru ni" "yanzu burina naga babu cikin nan a jikina shine zan samu kwanciyar hankalin da nake bukata, Wallahi Munira ban shirya haihuwa yanxu ba ke ko na Shirya haihuwa to ba da wannan tsohon ba." "Munira tace""wallahi kina da gaskiya kawata ai yanzu an daina wannan ace kana zuwa ka wani haihu" baka mori kuruciyarka ba yara suzo su dameka duk ka zama tsoho shiyasa nida Muktar muka tsara rayuwarmu kafin auramu ba zamu haihu da wuri ba sai munyi kamar shekara biyar ko sama da haka lokacin mun mori kanmu. "Naja'atu tace""Wallahi Munira banga laifinki ba. Nima bani da ra'ayin haihuwa da yawa a duniya sabida" "gudun wulakancin namiji....wannan cikin da ace ina son ubansa zan iya bari na haife shi to gabadaya na tsani wanda yayi sanadiyarsa shiyasa kawai na yanke shawarar zuwa garinku inaso ki bani cikakken address insha Allahu gobe ko jibi zaki ganni a gidanku idan yaso idan nazo sai muyi sha'awar yanda za'ayi kinga cikin ma baiyi wani kwari ba ba zamu sha wahala ba. Munira tace""Eh gaskiya kinyi dubara" kada ki damu zan baki cikakken addrees din gidanmu idan kinzo zamuje Chamis akwai tablet din da zasu baki ki sha d'aya kisa d'aya a 'kasan harshenki sannan kisa d'aya a gabanki! insha Allah cikin sai yabi rariya.'' "Ajiyar zuciya ta sauke tace""Nagode sosai k'awata! ina jiran address din ta whasap."" Munira tace""To ki" kunna data zan turo miki.'' Da sauri tace to tare da kashe wayar. Abbah Abbas kuwa al'amarin ne ya daure masa kai sosai dan ya sake kiran wayar ya kai sau hudu sai suce masa line is busy mamaki yake to wace irin waya yarinyar take mai tsayi haka kuma da waye take wayar.? da yaga bashi da mai bashi amsa sai ya dauki wayar ya sake neman line! sanyi yaji a zuciyarsa jin wayar tana shiga sai dai har ta katse bata dauka ba! Takaici kamar ya kasheshi shin wai me yarinyar nan take nufi! mikewa yayi ya fita daga dakin Harabar gidan ya fita ya zauna kan wasu kujeru kasa hakuri yayi ya sake kiran wayar a karo mara adadi! Naja'atu ta bawa banza ajiyarsa dan kin dauka tayi ta kyale wayar nata ringing! wannan al'amarin yayi masifar dugunzuma masa zuciya sai yaji gabadaya zaman garin ya isheshi hankalinsa yayi gida wannan iskancin da yarinyar takeyi ba na lafiya bane! ya kira waya sama da sau goma saboda tsabar raini da wulakanci ta'ki dauka. Halisa ita kanta sai da ta fahimci baya cikin hayyacinsa to da yake itama ba'a cikin hayyacinta take ba sai aka rasa wanda zai rarrashi wani a tsakaninsu. "Washe gari da sassafe Aunty maryam tazo ta dubata, Naja'at gaisuwar arziki ba tayi mata ba, aunty" "maryam cikin zuciyarta take fad'in ""Albasa ba tayi halin ruwa ba..Aunt maryam na tafiya da kamar mintina ashirin saiga Alhaji Sama'ila da Hajiya Rabi Abbah Alhassan ya kawo su su dubata. Daurewa tayi" ta fito ta zauna tana sinne kanta kamar mutuniyar arziki suka gaisa da juna! suna tambayar yanayin jinta tace musu da sauki! Ta lura kowa da kowa na farin ciki da samuwar cikin jikinta ita kadai ce take cikin bakin ciki saboda son zuciya kowa ya kasa gane halin da take ciki Bayan tafiyarsu Alhaji Aunty Rakiya ce tazo matar Abbah Alhassan kenan itama wai tazo dubata! Naja'atu cikin zuciyarta tace duk zaku gama gulmarku ku daina. Tashi tayi ta bar musu palon aunty Rakiya ta zauna tare da Larai suna hira gefe guda kuma tana mamakin wulakacin da yarinyar tayi mata. "Abbah Abbas koda dare yayi bai sake yunkurin kiranta a waya ba, sai kawai ya kira wayar abokinsa ya" "tambaye shi yanayin jikin nata, Abbah magaji yace masa jiki yayi sauki sosai dan maryam ma bata jima da fitowa daga gidan ba." "Hankalinsa ne ya kwanta sukayi sallama da juna yana d'an jin sassauci a cikin ransa, amma idan ya tuno" wulakancin da yarinyar tayi masa yana ji tamkar yayi tsuntsuwa yaje yaci mata mutunci ko ya huce. Washe garin ranar Naja'atu da niyar guduwa ta tashi sai kuma su Baba malam suka dira a gidan! Ganinsu yasa duk jikinta ya mutu ta dinga share hawaye a fakaice tana nadamar abinda zata a kaita musu na bacin rai Nasihohin da malam yayi mata sunyi masifar kassara mata jiki taji kamar ta hakura kawai ta "cigaba da zama a gidan tunda haka Allah ya tsara mata rayuwarta, sai dai suna tafiya ko gida basu je" shed'aniyar 'kawarta Munira ta kirata a waya tana sake zugata kan abinda suka kudurta. Washe gari ta kuma tashi da yunkurin guduwa garin Jos garinsu Munira sai kuma Allah ya saukar mata da ciwon ciki. ta yini a kwance tana murkususu! duk da tasha maganin ciwon bai lafa mata ba sai dare lokaci guda ta rame saboda tsananin axabar da taci A daran ta sake kwanciya da kudurin garin Allah na waye wa zakara zai bata sa'a! aikuwa hakane ya "kasance yara na tafiya makaranta lokacin Larai na kicin tana aike aike ita kuma ta fito, cikin rashin kwarin jiki da karfin hali taja k'aramar akwatin kayanta ta fita daga cikin gidan..." *Littafin na kudi ne...!* Koda zaki ganshi a groups to na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake. Vip Group #600 Normal gruop#300 account.. 0542382124..Binta Umar gtbank...Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *MANZIR _ALWAFIR ABUJA * _*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci magungunansu babu almundahana a ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu ko wace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye da akwai gruops na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rijistar dasu to kukanki ya 'kare idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_ 42 Sai da ta ganta a cikin tasha tukkuna hankalinta ya kwanta ta samu wani ke'bantaccen guri ta zauna tana "mayar da numfashin wahala, gabadaya jikinta a rikice yake sam ba tajin dadinsa daurewa kawai takeyi, a hankali ta zuge zif din jakarta ta dauko wayarta ta bude numbar Salim ta nemo ta shiga kiransa." Salim na kasuwa a lokacin cike da zumudi ya daga wayar tare da ambatar sunanta Kuka tasa mai "shashsheka tace""Salim ina cikin tashin hankali mai girma dan Allah kayi hakuri da abinda zakaji daga bakina wallahi duk abinda ya faru tsautsayi da kaddara ne amma nayi al'kawarin sai na salwantar da cikin da yake kokarin ruguza mana farin cikinmu."" Cike da so yasan abinda ke faruwa yace.""Naja'atu wai meke faruwa ne? naji kina wata magana wacce na kasa fahintarta."" Hawaye tagoge tace""Salim ciki ne dani.""? Yaji gabansa ya fad'i! sai yayi d'if takaicin kamar ya kashe shi Ta cigaba da cewa""Dan Allah kayi" "hakuri salim kada kace na yaudareka ba laifina bane wallahi karfi ya gwada min har hakan ta faru gashi yayi min ciki ba tare dana fargaba wannan dalilin yasa na yanke shawarar zubar dashi dan wallahi ni bazan haihu dashi ba tunda bana sonsa."" Salim yayi murmushin mugunta da fadin""Yanzu kina ina.""? kai" "tsaye tace""Gani a cikin tasha zan bar garin gabad'aya dan nagaji da zama cikin wannan masifa." "Yace.""Kiyi hakuri kada ki tafi ki dawo gida sai mu san yanda za'ayi."" Tace""Salim nifa wallahi sai na zubar" "da cikin nan hankalina zai kwanta."" Yace.""To yanzu wane gari kika nufa haba Naja'atu kiyi hakuri ki kar'bi qaddara mana."" a fusace tace""au abinda zakace kenan Salim? ashe dama ni kadai nake wahalar da kaina a kanka ko."" Yace.""Ai dama na fada miki tuntuni kinfi karfina ni yanzu ke auntyna ce dan haka hakuri shi yafi alkairi a tsakaninmu."" Cike da bacin rai tace""Shikkenan salim nagode da butulci dama ai idan ba kayi min haka ba to baka cika namiji ba idan baka aureni ba akwai maza a duniya wanda suka fika komai da komai kuma ba zan fasa abinda na kudurta ba."" Tana gama maganarta ta kashe wayarta. Salim yayi sauri yayi serving din rocouding din da yasa ya sake kiran wayartata, kin dauka tayi" ta hada kanta da gwiwa sai kuka take. Salim ganin taki daga wayar sai yayi murmushi a fili "yace.""Alhmdullhi bukatata ta biya. numbar Kawun nasa ya shiga kira. Abbah Abbs ya daga wayar kafin" "ma yayi magana yaji muryar Salim din cikin tashin hankali yana fad'in ""Kawu gida babu lafiya Naja'atu ta gudu ka bude whasap na turo maka muryarta yanzu muka gama waya da ita tana sheda min hukuncin data yankewa kanta." "Abba Abbas kasa gane maganar yayi yace."" Kai ka nutsu kayi min bayani ina zata nufa bayan yanzu" "mukayi waya da abokina magaji yace tana gida lafiya lau...Salim yace.""Wallahi kawu babu wasa a cikin maganata idan kana so ka gazgata ka bude audion dana turo maka ta whasap..Abbah Abbs hannunsa na rawa ya kashe wayar ya shiga whasap kawai sai yaga yayi exipire tsaki yaja yayi saurin shiga playstore" domin dauko wani. "Can gida kuwa Baba Larai ta gama aikace-akaicen ta ta shiga dakin da naja'atun take domin ta dubata," "taga bata dakin sai tayi tunanin kota tana toilet sai ta zauna gefan gadon Mufida tana jiran fitowarta.....Zaman minti ashirin tayi a dakin ba taji motsinta ba, sai ta mike da sauri ta isa bakin bandakin tana kiran sunanta. shurun da taji ne yasa da sauri ta tura kofar bandakin, tana rarraba idonta a ciki babu naja'atu babu dalilinta...Cikin faduwar gaba ta fito palon tana dubata hade da kiran sunanta." "shuru taji babu alamunta a gidan, sai ta bude kofar palon ta fita da sauri ta nufi bakin gate." "Malam Ayuba maigadi na zaune shida Yunusa suna hira Larai ta karasa tace""Malam Ayuba kana zaune" "anan ko kaga fitowar Naja'atu."" Malam Ayuba yace.""Eh kwarai kuwa kimanin awa d'aya data wuce ta fito da akwati a hannunta nine ma na bude mata karamar kofa ta fita." "Baba Larai jin maganar akwati sai taji wani irin fargaba ya rufe ta, da sauri ta juya ta koma cikin gidan ta" dauko mayafinta kai tsaye gidan aunty maryam ta nufa tana adduar Allah yasa kada yarinyar nan tace zataje wani gurin "Aunty maryam ta shiga rud'ani mutuka jin maganar da Larai ke tafe da ita, Gaskiya naja'atu bata da" hankali kuma taurin kanta ne zai kaita ya baro. Waya ta dauka ta kira mijinta a sanyaye ta fada masa halin da ake ciki...Abbah magaji bai nuna alhini ba "dan shi a tunaninsa ina naja'atu ta sani da xata je? Yace.""Kada ku damu naja'atu babu inda za taje watakila tana can kofar na'isa gidan malam ko gidan alhaji dan haka dukkaninku ku kwantar da hankali.""" "Aunty maryam jiki a sanyaye tace to shikkenan Allah yasa tana can din."" Kashe wayar tayi tana wasiwasi" "a cikin ranta itafa ranta bai amince da cewar yarinyar na kofar na'isa ba, tafi zargin ta gudu ne kamar yanda kullum take cin alwashi sai ta bar gari gabadaya yanzu ta dawo daga rakiyar yarinyar," Abbah Magaji na kashe wayar kira ya sake shigowa yana dubawa yaga abokinsa ne da sauri ya daga "wayar da sallama a bakinsa Abbah Abbas cikin tashin hankali da damuwa yace.""Alhaji magaji ya akayi" "haka ta faru ? ya akayi kukayi sake irin haka har yarinyar nan ta samu nasarar fita daga gida da sunan guduwa inata nufa cikin halin lalura.""? Abbah magaji yace.""Subahanallahi! kada dai maganar da maryam" "take fada min gaskiya ne Alhaji.""?" "Abbah Abbas yace.""Gaskiya ne naja'atu ta had'a kayanta ta gudu! Yanzu na saurari recoding wayarsu da" "Salim ta kirashi ta sheda masa hukuncin da ta yanke akan cikina dake jikinta zata zubar dashi kuma komai rintse sai ta rabu da aurena shin me yayi zafi har yarinyar nan ta yanke mana wannan mummunan hukuncin."" Halisa dake gefansa a zaune wani murmushi ta saki ta sake gyara zamanta tana sake kasa" kunneta a kan wayar da yake. Abbah Magaji ya mike tsaye hankalinsa a tashe sai kiran kalmar innalilihi wa'ina ilaihi raji'un yake! "gabadaya kansa ya kulle ya rasa abinda zaice..Da kyar yace.""Wallahi Alhaji Abbas ban ta'ba tsammanin yarinyar nan zata aikata wannan mummunan aikin ba tabbas dana san haka zata faru zan dauko ta dawo gabana ta zauna har ka dawo! to rashin sani yafi dare duhu! babban tashin hankali anan shine ina ta" nufa cikin wannan halin da take ciki. "Abbah Abbas kamar yayi tsuntsuwa ya ganshi a Nejeria yace.""Nima shine babban damuwata amma babu" "komai dukkanin tsanani yana tare da sauki Allah zai tsareta ita da abinda ke cikinta idan Allah yasa dan dake cikinta zai taka duniya ina rokon Allah ya tsare min shi a duk inda zata shiga idan kuma bukatarta ta biya akansa sai na roki Allah ya maye min gurbi da wani.""Wannan kalaman na abokin nasa sunsa jikinsa yayi sanyi yace.""Alhaji kayi hakuri dan Allah insha Allah yarinyar nan ba tayi nisa ba tana kusa yanzu zan koma gida zansa aje a duba gidajen dangi ko can ta nufa dan Naja'atu bata san kowa a wani gari ba" "ballantana taje.""" "Murmushi takaici yayi yana jin wani irin d'aci a bakinsa yace.""Allah ya jishshemu alkairi."" kashe wayarsa" yayi yana jin wata masifaffiyar tsanar yarinyar a cikin zuciyarsa babu shakka ta salwantar masa da gudan jininsa sai ya nuna mata shi d'an halak ne.... Abbah magaji ya jima ri'ke da wayar a hannunsa ya shiga tunani da nazari akan abinda yarinyar ta aikata gaskiya bai ta'ba tsammanin faruwar haka daga gurinta ba sosai yarinyar tayi masa bazata. Kafin ya nufi gida sai da ya kar'bi wayar Salim ya saurari muryar Naja'atun nan ya sake gazgata maganar abokin nasa. kai tsaye motarsa ya shiga ya nufi kofar na'isa domin shedawa iyayensu halin da ake ciki. "Halisa ta matso kusa dashi tare da dafa bayansa cikin tausasawa tace""Kayi hakuri abban mufida ni dama" nasan da kamar wuya yarinyar nan ta bar cikin nan tunda da kunnena naji tafada cewar ita ba zata ta'ba haihuwa da kai ba tunda bata sonka kuma duk yanda za tayi sai tayi ka saketa ta auri wanda take so gashi kuwa ka gani kuma kaji da kunnanka wanda idan wani ne yazo ya fada maka cewa za kayi karya ne shiyasa kullum nake cewa dakai yarinyar annobace a cikin mu yana da kyau dai tun wuri ka nemawa "kanka mafita amma gabadaya zama da ita ba alkairi bane.""" Abbah shuru kawai yayi yana ta nazarin maganganun Halisan tabbas halisa tayi gaskiya yana da kyau tun "kafin yarinyar tayi masa wanwar! yayi gaggawar cire ta daga rayuwarsa dan bazai iya jure wannan al'amarin ba, wato shi ya gama shan wahalar dasa 'kwansa lokaci guda ayi masa asararsa gaskiya bai zai iya daukar wannan rashin mutuncin ba dole ne ya dauki mataki a kanta..Halisa ganin yanda ya fusata! sai taji dadi ta cigaba da zugashi kancewar kada ya yarda har in dai yarinyar tayi nasarar zubar masa da ciki" to ya dauki mataki mai tsauri a kanta. Jinta kawai yake yi yana ganin ita bata isa ta nuna masa ga irin hukuncin da zai dauka akan yarinyar ba ko wane irin hukunci ya dauka akanta ya barshi a zuciyarsa sai ya tabbatar da cewar ta samu nasara a kansa sannan zai zartar dashi. "Duk inda aka san za'a ga Naja'atu an dubata ba a ganta ba, hankalin iyayenta da duk wani wanda ya" "shafeta ya tashi, baba talatu kuka kawai takeyi dan takasa daurewa sai salati take tana kiran sunan Allah da fadin Allah ya bayyanta yarinyar a duk inda take Baba malam kuwa alwala ya daura ya hau kan" dadduma domin shedawa Ubangiji halin da ake ciki Abbah magaji da Abbah Alhassan kam gidajen redio suka nufa domin shigar da cigiya..to al'amarin ya fi karfinsu dole sai sun had'a da cigiya dan ganin duhun dare ya shigo babu wani labari. Yaya Ramlatu ta samu labari a bakin Salim bayan ya dawo daga kasuwa ya kunna mata roconding din ta saurara! aikuwa bata bari gari ya waye ba ta dauki mayafinta tare da wayar Salim din ta nufi kofar na'isa tana shiga gidan nasu kai tsaye sama ta nufa dakin Alhaji suka gaisa kamar abin arziki kawai sai ta kunna masa roconding din tace ya saurari abinda Naja'atu ta aikata. Alhaji Sama'ila da ba lafiya ya cika ba dalilin da yasa duk abinda akeyi be sani ba dan baba malam cewa yayi kada a fada masa saboda lalurarsa kada a tayar masa da hankali Jin audion Naja'atu yasa jikinsa ya rikice! sosai ya dinga salati yana kiran sunan Allah jikinsa na wani irin "rawa har sai da ta firgita da ganin halin da ya shiga...Abbah Alhassan ya shigo dakin ya ganta a zaune ga Alhajin na makyarkyata yana neman faduwa, da sauri yaje ya rikeshi yana salati! Yaya Ramlatu jikinta sanyi yayi ganin jikin mahaifin nata ya rikice sai ta shiga inda inda a lokacin da Abbah Alhassan ke tambayarta abinda yasa shi shiga damuwa tace""Itama tazo gaisheshi ta ganshi cikin wannan yanayi...Da sauri ya kira Salim a waya yace maza yazo zasu kai Alhaji asibiti Minti goma salim ya iso gidan suka" rirrike Alhajin suka sauka dashi kasa.....Hankali a tashe hajia Rabi amaryasa tabi bayansu ita kuwa Yaya "ramlatu a sanyaye ta fita daga gidan a maimakon ta nufi gidanta sai kawai ta shiga gidan Baba malam suna zaune cikin alhini da damuwa ta tsaya a kansu babu gaisuwa kawai ta kunna musu muryar 'yarsu! gurin yayi tsit! sai da suka gama saurara sannan ta kashe wayar ta kama hanya ta fita daga gidan ba tare da tace uffan ba, tana fita baba talatu ta cigaba da share hawaye tana girgiza kanta da fadin wannan" yarinya kin janyo mana abin kunya a idon duniya innalilihi wa'ina ilaihi raji'un. Naja'atu tana can tana gagaranba a garin jos dan tun bayan saukar ta a tashar garin tana fitowa daga mota wani matashi ya warce mata pose dinta da wayarta a ciki da kudadenta! abinka da tasha da turmutsutsu babu wanda ya ankara da abinda ya faru!! ta dinga kuka tana waige-waige a tashar ga duhun dare ya kawo kai yanzu ya za tayi ta kira Munira dan gabadaya ta manta sunan unguwar tasu "ballantana ta shiga motar da zata kaita unguwar ta nemi gidan...Hannunta ta kalla taga dari biyar da dari biyu ajiyar zuciya ta sauke wannan 'yan canjin sune kawai suka rage mata, dan haka da sauri taja akwati ta fita daga cikin tashar lokacin anata kokarin shiga massalaci domin sallar magariba. Tafiya me tsayi" "tayi ba tare data san inda ta dosa ba, gajiya da yunwa yasa ta nemi gefan titi ta zauna tana kalle-kalle!! ta jima a zaune a gurin tana kallon mutane nata shige da fice wasu matasan samari na nuna ta suna dariya sai ta tsorata ta mike da sauri ta bar gurin Sawun tafiya taji a bayanta tana juyawa ta ga wannan" "matasan suna binta sauri ta 'kara tana hard'ewa yayinda gefan cikinta ke wani irin murd'awa!!! Kafin ta ankara taga sun kewaye ta, a tsorace take kallonsu da fadin"" Ni bakuwa ce a cikin garin nan dan Allah ku" "taimaka min kada ku cutar dani.""" "Daya daga cikinsu yace.""Muma ki taimaka mana sai mu taimaka miki wane gida kike nema.""? murya na" "rawa tace""Wallahi na manta address din gashi wani 'barawo ya fizge min jakata da waya ta a ciki" "ballantana na duba."" Hahahaha! suka sa dariya suna nunanta dayan yace.""Kizo kawai muje dake masauki baki da matsala tunda kin hadu damu." "Tsorata tayi ta dan matsa gefe tana neman hanyar guduwa, wanda yake gefanta ya fizgo hijabinta yana" kokarin sha'ke mata wuya! da sauri ta fizge ta bangajeshi a guje ta kama hanya! aikuwa suka rufa mata baya...Takalmanta da akwatin kayan dake hannunta ta watsar ta dinga gudu tana kiran a taimaka mata! Jos dai ba daya yake da sauran gaguruwa ba! yawanci gidajensu babu doguwar katanga mafi akasari ma a waje suke rayuwa dan haka tana shigowa cikin mutane tana wannan gudun jama'a suka kewayeta suna tambayarta abinda ke faruwa...Su kuwa matasan samarin nan ganin ta tsere musu sai suka koma da baya suka dauke akwatin kayanta data jefar sukayi nasu guri Wata mata ce ta rike ta ta kaita gidanta ta zaunar da ita tana tambayarta daga wane gari take!? Naja'atu "kwanciya kawai tayi tana zirarar da hawaye wannan wace iriyar masifa ce? matar ganin bata kulata ba yasa ta tashi ta bata guri, dama abinci take siyarwa a kofar gidanta sai kawai ta koma ta cigaba da sallamar mutane. Wani irin kuka take tana rik'e cikinta wani matsiyacin ciwo yake mata! sai kyarma" jikinta keyi.....sai kusan sha d'aya na dare matar ta shigo gidan ita da 'yan yaranta biyu. Ganin Naja'atu "a kwance a inda take yasa ta tsaya a kanta tace""Baiwar Allah nifa tausayi kika bani shiyasa har nayi sha'awar taimaka miki amma dan wulakanci tun dazu sai magana nake miki kinyi min banza" "Naja'atu da kyar ta iya mikewa zaune tana share hawaye tace""Dan Allah kiyi hakuri bani da lafiya shiyasa" na kasa yi miki magana. "Tace""Me yake damunki.""? A hankali tace""Cikina ne yake ciwo.""? matar sam bata dauka ita din matar" "aurece bace tace""Yanzu dare yayi dana kaiki chamis amma bari na dauki miki ja da yallow kisha idan baiyi miki ba sai kisha kanwa zaki ji dadi." "Naja'atu tace""To nagode."" Daki matar ta shiga ta fito hannunta rike da plate a rufe da abinci a ciki tace" "ga abinci ki fara ci sai kisha maganin."" da sauri ta kar'ba dama yunwa na damunta...Lomar farko ta raina kanta dan jin yanda bakinta ya game da yaji!n attaruhu! miyar sai kace ta mayu saboda tsananin yaji!" "ruwa ta dauka da sauri tasha, ta dauka ta karayin loma guda...Tana zukar bakinta ga abincin da dadi" "amma sai uban yaji!!! Miyar ta ture ta shiga cin farar shinkafar amma duk da haka akwai yaji, wani irin amai ne ya shiga yunkuro mata ta dinga danneshi amma ina!! a guje ta nufi bakin rariya ta shiga kelayawa tana kakari da rike kirijinta da yake mata wani irin zafi matar ta tsaya a kanta tana yi mata" "sannu har ta gama ta riike ta suka dawo suka zauna tana mata sannu ta mika mata kwayoyin maganin ja da yallow da wannan maganin mai mugun dacin tsiya na tsayar da gudawa! ba tare da tunanin komai ba ta karbi maganin ta watsa a bakinta ta kora da ruwa!! (Shan magani barkatai ba tare da ka'ida ba yana janyowa mai ciki babbar matsala matar tace""Sannu bari na shiga na gyara miki guri ki kwanta gobe kafin na fita kasuwa zan kaiki asibiti a dubaki..Naja'atu daga mata kanta kawai tayi tana jin wani irin jiri" na d'ibarta. Misalin karfe daya rabi na dare ya tashi yaje ya dauro alwala ya fuskanci alk'ibula yana kaiwa Allah kukansa ni dai ban ta'ba ganin babban mutum na kuka ba sai akan Abbah Abbas gabadaya ya kasa daurewa ganinsa a gaban mai kowa da komai yasa zuciyarsa ta karye ya shiga zurarar da hawaye yana me kai masa kukansa. A daidai lokacin shima baba malam ya kadaice kansa da Ubangiji yana nemawa rayuwar yarsa sassauci gami da za'bin alkairi dan yanzu gabadaya al'amarin ya fice masa daga rai sai dai neman zabin Allah duk abinda kuwa ya zartar shine daidai. Karfe uku daidai Naja'atu ta mike zumbur! jin yanda wani irin mahaukacin ciwon ciki ya turnuketa kafin "kice me ta fita a hayyacinta...salati ta shiga yi tana murkususu a kan shimfidar da take kwance...Maman Sajida ta tashi da sauri ta kunna fitila tana kiran sunanta, Naja'atu hannunta ta rike tana hawaye tace"" Baiwar Allah ki taimaka min hakika ina azabtuwa a cikin wannan daran."" Maman Sajida tace""Sannu ni wallahi dana ga kinyi bacci na dauka kinji sauki ashe ke kadai kika san abinda yake damunki sannu bari gari ya karasa wayewa na kaiki asibiti.'' Naja'atu kanta kawai take dagawa tana ambaton Allah a cikin" zuciyarta... haka suka kasance har garin Allah ya waye maman sajida taje tayi alwala tayi sallah agurguje ta fita ta "kira makociyarta Maman Ladi suka fara kokarin kama Naja'atu domin su mikar da ita! Ita kuwa rintse idonta kawai takeyi cin yanda kwankwasonta ke amsawa sai kawai ta saki karamar kara ta koma ta zaune tana mike kafarta kawai suka ga jini na bin cinyoyinta...Sai suka shiga salati suka kamata da kyar suka kaita bandaki suka tsuganar da ita...Maman Ladi tace""Yariyar nan 'bari za tayi innalilhi! Maman Sajida tace ""bari naje na dauko babur . da dauri ta fita daga bandakin...Wai Naja'atu kwanciya tayi a bandakin duk kaxantarsa bai dameta ba taimakon Allah kawai take nema...Kafin maman Sajida ta dawo ma ai akin gama ya riga ya gama tuni cikin ya bi rariya tunda duk ga daddaginsa nan a kasan bandakin sai uban karni ne ke tashi a gurin Maman Ladi ta ri'ke bakinta cike da mamaki take kallon Naja'atun" "tace"" Ashe ma cikin baiyi kwari ba to Alhamdullhi tunda Allah ya rabaki da wahala haihuwar d'an shege a" "wannan zamanin ai masifa ce.'' Naja'atu a galabaice take kallon matar tace""Kina nufin cikin jikina ya" "fita.""? Maman Ladi tace""Ga zahiri nan kina gani a kasa yana bin rariya sai ki godewa Allah! ajiyar zuciya ta sauke tana godewa Allah a cikin zuciyarta." *Wayyo Allah Abbah Abbas * *Littafin na kudi ne...!* Koda zaki ganshi a group na sata ne idan kina bukatar biyan kudin littafin ga yanda abin yake. Vip gruop#600 Normal gruop#300 accont numbar 0542382124...Binta Umar gtbank...Idan katin waya zaki turo kiyi mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *MANZIR _ALWAFIR ABUJA * _*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci magungunansu babu almundahana a ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu ko wace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye da akwai gruops na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rijistar dasu to kukanki ya 'kare idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_ 43 "Maman Sajida ta shigo bandakin da sauri tana fad'in"" Maman Ladi kamata mu fito da ita ga babur can na" "samo a waje."" Maman Ladi tace""Wane na kamata ai tuni cikin ya zube kada ma kiyi asarar kudin motarki."" Sororo maman sajida tayi tana kallon Naja'atu dake durkushe kamar wacce take kan gwiwa!(mace mai naquda) A sanyaye tace""Ai shikkenan to Allah yasa haka shi yafi alkari ni wallahi ma ban dauka ciki ne da ita ba."" Maman Ladi tace""Ke dai maza kije ki sallami mai babur ya tafi sana'arsa kin barshi a waje."" Maman sajida tayi saurin juyawa ta fita daga bandakin...Maman Ladi ta kalli Naja'atu da" "fadin""Sannu yaya yanayin jikin naki.""?" "Murya na rawa tace""Jiri nake ji da ciwon mara."" Ta'be bakinta tayi tace""Ai dama dole kiji haka tunda kin" zubar da jini ciwon mara kuwa ai ya zama dole haka kawai da kuruciyarki da komai a maimakon kiyi aure ki raya sinna sai ki dinga bin maza duba dan Allah wani shegen gardi yayi miki ciki ya barki da wahala shi "yana can a kwance wallahi kuyiwa kanku fad'a.'""" "Wasu hawaye ne masu zafi suka shiga zubo mata, ashe kallon karuwa suke mata...Da kyar tace""Baiwar" "Allah ki daina yi min kallon karuwa wannan cikin na jikina yana da uba."" Maman ladi tace""Ai dama kun" saba dauko ciki idan ku kaga asirinku zai tuno kuce cikin ku yana da uba to dama wane d'ane bashi da uba! kowa ne d'a yana da ubansa sai dai wani ana samar dashi ta hanyar da bata dace ba. Naja'atu shuru kawai tayi tana jujjuya kanta gaskiya maganar da matar nan takeyi tayi bala'in 'bata mata rai Maman Sajida ce ta shigo bandakin suka taimaka mata ta mike tsaye ta jingina da bango(garu) "Maman sajida tayi saurin zuwa dakinta ta dauko mata daya daga cikin kayanta riga da zani na atamfa da sabon pant gami da audigar mata suka taimaka mata ta gyara jikinta, cikin kasala gami da jiri suka" kaita suka ajiye a tsakiyar ledar dakin. Maman Sajida ta dukufa aikin gyara bandakin yayin da ita kuma maman Ladi ta dage da surutai gami da "farfadar mugwayen kalmomi akan naja'atu tana zuga maman sajida akan ta koreta dan daka gani ba mutuniyar arziki bace.""" "Maman sajida tace""Nima shawarar dana yanke kenan anjima kadan idan ta samu nutsuwa zan zauna da" ita na tambayeta garinsu idan ta tsaya yi min inda inda to korarta zanyi dan ba zata janyo da mutuncina a gari azo anayi min kallon banza ba. "Maman Ladi tace""Wannan shine tunani mai kyau ni na tafi gidana dan zan shirya 'yan makaranta.""" "Maman Sajida tace""To nagode.""" "Naja'atu duk irin maganganun da sukeyi a bandakin tana jinsu, wasu zafafan hawaye ne kawai suke tsere" a kuncinta yanzu idan maman sajida ta koreta ina zata nufa na farko dai tayi al'kawarin ba zata koma "kano ba domun har yanzu bata karaya ba, tana nan a kan bakanta , na biyu kuma bata san gidansu" munira ba ballantana taje can tana ganin zata fadawa maman sajida labarinta watakila ita zata fahimceta. "Maman Sajida ruwan tea ta d'ora musu ta aiki yaronta ya siyo musu kayan shayi, sannan dama tana da" "ragowar miyar jiya me yajin tsiya ta du'mama da yake akwai nama a ciki sai ta samu dan madaidaicin abu ta zubawa naja'atu miyar ta hada mata tea din ta kai mata har inda take zaune, tace""Gashi nan babu yawa miyar jiya ce na d'umamaki sai ki dangwala da bread. ga tea nan kuma."" A sanyaye" "tace""Nagode abinda kikayi min Allah yayi miki.""" "Maman Sajida tana kokarin fita daga dakin tace""Ayya ai babu komai dan na taimake ki kina cikin halin" "taimako Naja'atu tea din kawai ta iya kur'ba tana jin yanda jini keta 'bul'bulowa daga jikinta, takure" jikinta tayi tana adduar Allah ya takaita mata wahala. Gabadaya miyar naman da maman sajida ta ajiye "mata ba tayi mata ba shiyasa ko kallonta ba tayi ba, tana gama shan tea ta mike da niyyar sanja guri! kawai taji jini ya tsinke mata! da sauri ta durkusa kasan dakin jikinta na rawa, zanin jikinta ta d'an janye nan taga jinin duk ya 'bata gurun..Maman sajida ta shigo ta ganta tana kuka gata a durkushe tace""Ke kuwa me yasa kike haka sai kace wata wacce zata haihu sai durkuso kikeyi."" Tace""Kiyi hakuri dan Allah" ina mikewa naga jini na bin jikina shine tsoro yasa na tsuguna. "Maman sajida tace""Ta'b! aikuwa gaskiya nayi miki na Allah da annabi ke zaki wanke kayan" jininki...Dakinta ta shiga ta dauko mata wasu kayan ta fita tana jan karamin tsaki! gaskiya tayi abinda zata iya haka kawai azo ana sata aikin jini. "Naja'atu tana kuka tana kimtsa jikinta, tasa zanin data cire ta goge inda ya baci ta fito da kayan a" "hannunta, bandaki ta nufa tasa su cikin bawo ta zuba ruwa da omo ta shiga wankewa...Maman sajida ta koma dakinta ta sake gyarawa sai mita take ta dauko turaran wuta tasa sannan ta fesa turaran kamshin daki ta nemi guri ta zauna tana jiran shigowarta." "Naja'atu tazo ta zauna jikinta duk yayi sanyi idan kuka ganta sai kun tausaya mata, sosai take bukatar" "kulawa sabida jinin data zubar. Maman Sajida ta kalleta a nutse tace""Meye sunanki. da sunan" "garinku""?" "Tace""sunana naja'atu kuma ni 'yar kano ce nazo jos ne gurin kawata munira ina sauka a tasha wani" 'barawo ya warce mun jakata da wayata da kudina duk a ciki..bayan na shigo cikin gari kuma wasu 'yan iska suka biyo ni da gudu suna so su cutar dani shine dalilin daya sa kuka ganni ina gudu. "Maman sajida tace""Ayya Allah y kiyaye gaba, sai dai abunda ya bani mamaki dake shine, dama kin san" "kina da ciki ko kuwa kema baki san kina dashi ba dan gaskiya ni kallo daya nayi miki naga kamar mutuniyar arziki ce ke.""" "Naja'atu tace""Nasan ina da ciki shine dalilin daya sa ma na bar garinmu nazo nan."" Maman sajida" "tace""Abun kunya kika gudarwa ashe.""? Da sauri ta girgiza kanta tace""Ko daya cikin nan da ubansa ba shege bane kamar yanda kuke tsammani...Auran dole akayi min da mijin yayata bayan rasuwarta........Tiryan tiryan Naja'atu ta sanar da mmn sajida labarinta...Maman sajida tace""Ni kam banji dadin abinda kika aikata ba na'jaatu da kinyi hakuri kin zauna da mijinki da yafi miki alkairi wallahi to da" "kikazo garin jos me kike tunanin zaki samu.""" "Tace""Nazo gidansu kawata ne amma bada niyyar na zauna ba idan an kwana biyu zan koma gida.""" "Maman Sajida tace""To ai kince kin mance kwatancen gidansu kawartaki."" Tace""Wallahi na mance Amma dai mahaifinta fitacce ne sunansa Alhaji Aminu d'an jarida! Maman Sajida tace""Ai nasan gidan can" "bayan layi ne.""" "Ajiyar zuciya ta sauke tana hamdala a cikin ranta...Maman sajida ta mike da fad'in ""Ni zani kasuwa yanzu" "idan na dawo da wuri sai na rakaki gidan idan kuma ban dawo ba sai dai gobe tunda kinga yanayin sana'ata ta dare ce."" Tace""To nagode maman sajida ai tunda na samu gidan zuwan ba zaiyi wahala ba sai kin dawo."" Tace""To su Walid da Sajida idan sun taso daga skull zasu shiga gidan maman ladi su zauna idan zaki shiga ki zauna kema sai ki shiga."" Girgiza kanta tayi tace""babu komai har kya dawo ina gida.""" Maman sajida tace to tare da kama hanyar fita daga gidan kafadarta rataye da jakarta. To can gida haka suka wayi gari cikin alhini gami da damuwar 'batan naja'atu! hauwasa sukace labarin duniya baya 'buya sai ga mutane suna doko sallama da sassafe suna shiga gidan malam da Alhaji wai sunzo jaje! wannan al'amarin ya sake d'agawa baba talatu hankali da yake bata iya tashin hankali ba tsakanin jiya da safiyar ranar duk ta rame kuka kuwa tayi har ta gaji! Jama'ar da suke ta tururuwar shigowa gidan yasa ta shige daki ta kwanta duk wanda yazo sai dai Baba Magajiya wacce ta kasance 'yar uwa a gareta ta sallameshi wasu dai gulma suke zuwa wasu kuwa suna zuwa ne domin su jajanta al'amarin to komai dai menene kaddara bata wuce kan kowa ba. 'Bangaran Abbah Abbas kuwa duk yana samun labarin abinda ke faruwa daga bakin Abokinsa da Salim dukkaninsu sun sheda masa cewar babu wani cigaba dan har yanzu babu wani wanda ya kawo musu labarin ya ganta a wani gurun Abbah Abbas kasa 'boyewa mahaifiyarsa al'amarin yayi duk ya sheda mata halin da ake ciki sosai hajia Abu ta shiga rudani da tashin hankali itama sai da ta zubar da "hawaye tana fad'in ""Ina yarinyar nan ta kai kanta da 'karamin ciki a jikinta me yayi zafi!? da har zata nemi salwantar da rayuwarta akan abinda babu dole a ciki, idan auran Abbas ne bata so to kam insha Allahu za'a warwareshi domun ta samu zaman lafiya in yaso daga baya sai ta auri wanda take so......Halisa kuwa sai nuna alhini da damuwarta take a kan lamarin gefe guda kuwa sai suyi waya sau uku da Yaya Ramlatu suna sake tattauna maganar da kuma 'karawa kansu kwarin giwa tare da sake gazgata maganar boka ai dama ya fada musu cewar yarinyar za'a nemeta a rasa yanzu abu daya ne ya" rage a cikin maganganun da bokan yayi. Naja'atu kasa zaman cikin gidan tayi sai ta lalla'ba tasa hijabinta ta fito wajen gidan ta samu rumfar kwanon da jama'ar maman sajida ke zama ta zauna tana kallon yanayin garin Tamkar bariki kowa sai abinda yake so yake yi mafi akasari ma 'yan matan garin basa yawo da mayafi a jikinsu gasu yawanci duk 'kananun kaya ne a jikinsu da wuya ka gane kafuri da musulmi Yanayin garin sam beyi mata ba sai dai kuma yanda suke gudanar da muamularsu ta babu ruwana da kai ya burgeta. "Babur ne ya ajiye maman sajida a kofar gida, ta mike a hankali ta iske gurin da take...Maman sajida ta" "shiga dauko ledojin kayan miyarta Naja'atu ta taimaka mata suka fito da kayan...Sallamar mai babur din tayi suka dauki kayan suka nufi cikin gidan......suna shiga mmn sajida ta shiga aikace akaice hura wuta tayi ta d'ora madaidaiciyar tukunya sannan tazo ta zauna tana gyara kayan miya, naja'atu kuwa suna hira" tana taimaka mata da yankan salak da kabeji! maman Ladi ce ta shigo gidan yara na biye da bayanta. "Mmn sajida tace""Wallahi yanzu nake zancan ku a raina."" Maman ladi ta zauna kusa da ita tana fad'in ""Ai" "nasan yau zakije kasuwa shiyasa naje na dauko su daga makarantar da kaina amma gaskiya yau kin dawo da wuri."" Maman sajida tace""Wallahi nima naga saurina yau ba cunkuso a kasuwar. Naja'atu tana jinsu" "suna ta hirarsu bata sa musu baki ba, haka kawai Maman ladi bata kwanta mata a ranta ba Taji maman" "ladi na cewa""Amma dai yarinyar nan ta fad'a miki daga wane gari take ko.""?." "Maman sajida tace""Eh daga kano take ashe gidan Alhaji Aminu dan jarida take nema tazo gurin Munira" "ne."" Mmn Ladi tace""To ikon Allah ai sai kiyi mata jagora zuwa gidan. Mmn sajida tace""Eh insha Allah gobe da wuri zan kaita gidan." Naja'atu takaicin maman ladi kamar ya kasheta ta lura matar 'yar bakin ciki ce sai kace a kanta take tabi ta damu! Bai dace mmn sajida na k'awan ce da ita ba tunda ita zuciyarta mai kyauce ta tabbata da mmn Ladi ce ba zata ta'ba yarda ta zauna mata a gida na yini guda ba. Kafin mmn Ladi ta tafi gidanta sai da tayi wa mmn sajida wayo ta kwasar mata kayan miya har yankakken salak din sai da mmn ladi ta d'iba sai dariyar ya'ke takeyi irin ta dubara. Ita kuwa mmn sajida sai girgixa kanta take tana mamakin rashin imani irin na makociyar tata ita da take da miji mai bata kudin cefane amma bata godewa Allah ba "tazo tana d'ebe mata kayan sana'arta bata duba irin wuyar da take sha da marayun 'yayanta kullum sai tazo ta dauke mata abu a gidan, ashana wannan mmn ladi bata siya sai dai duk sanda zata d'ora girki ta shigo ta dauki tata, idan taga maginta ta bude ta zazzaga gishiri ta zazzaga har manja da mankuli tsiyayar" mata takeyi...al'amarin dai na mmn Ladi babu mutunci da tausayi a cikinsa. *Ayi hkr ayi manège* *Vip Mdd ba haram bane naga comments dinku akan pegenmu na yau kuyi hakuri da duk wani pege da zaku karanta anan gaba a yanzu ne sa'kon labarin yake so ya isa shiyasa kuke jin rashin dadi! kuyi hakuri ku cigaba da karantawa daki daki insha Allahu zaku fahimci inda na dosa* *MANZIR _ALWAFIR ABUJA * _*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci magungunansu babu almundahana a ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu ko wace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye da akwai gruops na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rijistar dasu to kukanki ya 'kare idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_ Mdd 44 Naja'atu na zaune tana kallon yanda Mmn Sajida keta aikin abincin siyarwarta tana kallo ta kammala "komai ta shirya cikin kuloli gwanin sha'awa, Mmn Sajida nada tsabta da kula sosai a kan sana'arta shiyasa take da costomas sam ba tayin kwantan abinci komai yawan abinci idan ta fita dashi tas take siyarwa ta had'a kan kudinta..Mmn Sajida haifaffiyar jos ce iyayenta da kaninta duk suna garin tayi aure shekaru goma da suka wuce sun haifi yara biyu da mijinta kafin Allah yayi masa rasuwa, tun bayan mutuwar mijinta ta soma fuskantar matsala ta rayuwa 'yan uwanta dana mijin nata kowa kansa ya sani babu mai taimaka mata da sabulu ko omo yace tayiwa yara wanki idan taje neman taimako kafin ayi mata sai an gama wulakantata tukkuna to tunda ta fahimci rayuwar duniya haka take sai ta kama kanta ta shiga neman kudi duk domin ta rufawa kanta asiri da yayanta inda Allah ya rufa mata asiri ma gidan da take ciki na mijinta ne shiyasa wasu abubuwan sukayi mata sauki sai kawai ta yanke shawarar zamanta a ciki domin tasan babu wanda zata jewa da marayun 'ya'yanta ya ri'ke su tsakani da Allah ganin yanda duniya ta koma kowa kansa kad'ai ya sani kad'an ne masu tausayi da tsoron Allah Sai" kawai ta yanke shawarar siyar da Kayan d'akintata shiga sana'ar siyar da abinci cikin ikon Allah Ubangiji "yasa mata albarka a ciki Yanzu Mmn Sajida tafi karfin komai sai dai wani ma yazo yaci alfarmarta, Mmn" Sajida bata da rowa ko kadan sai dai abotarsu da Mmn Ladi yasa ta d'an koyi wasu munanan d'abi'u daga gurinta. Tare suka fita da Mmn Sajidan ta zauna kusa da ita tana d'an taimaka mata da wasu abubuwan. Mazan "da sukayi yawa ne a gurin yasa taji zaman gurin ya fita daga ranta, ta tsani kallon k'urrula ko kadan ta fahimci mazan garin su kuma dabi'arsu ce..Da har tayi niyyar shiga gidan kodan ta huta da kallon da ake mata sai kuma ta hakura ta daure ta zauna ta cigaba da taimakawa Mmn Sajida dan ta lura abin yayi mata yawa kowa idan yazo da kalar abinda yake so Naja'atu na kallon wani magidancin mutum" "wanda tunda ya tsaya a gurin yake kallonta yana mata murmushi, har sanda Mmn Sajida tazo kansa tana masa magana hankalinsa gabadaya na kan Naja'atu sai kace zai cinyeta. Mmn Sajida tace""Haba" "d'anTalle tun dazu nake magana kayi shuru yanzu idan wani na sallama kace na tsayar da kai.""" "Mutumin da ta kira da 'DanTalle ya shafa gemunsa a sanyaye yace""Mmn Sajida yaushe kika samu" "yarinyar nan lallai na kwana biyu banzo gurin nan ba."" Mmn Sajida sanin halin Dantalle yasa tasha kunnu sosai tace"" Bakuwa ce wannan kuma ba irin taku bace kai dai ka fad'i me kake so na zuba na had'a maka.""" "Yace.""Ki zuba min shinkafa da wake da miya."" Mmn Sajida na kokarin zuba masa tace"" 'Kashi ko nama" "wane zan sa maka."" ? Hankalinsa na kan Naja'atu yace""Ki samin 'kashi."" Mmn Sajida ta had'a masa komai ta mika masa ya dauki jarkar zu'bo guda d'aya a sanyaye ya nufi cikin 'yan uwansa dake cikin rumfar kwanon da Mmn Sajida ta tanadar musu." "Yana barin gurin Mmn Sajida taja tsaki tace""Narasa wane irin hali ne da Dantalle wallahi ko wace mace" "ya 'kyalla idonsa a kai yace yana so. Ta kalli Naja'atu da fad'in ""Nasan shi da mugun bin diddigin tsiya saboda haka kiyi taka tsantsan dashi koda wasa kada ki sakar masa fuska har Allah yasa ki bar garin nan.""" "Naja'atu a sanyaye tace""Nagode Mmn Sajida nima wlh mutumin gabadaya beyi min ba tunda ya tsaya a" "gurin nan yake kallona kamar maye."" Mmn Sajida tace""Kad'an kika gani ai haka yake mugun son mata ne dashi ga shegen aure auren tsiya hanzu haka matansa hud'u amma baya cin abinci a gidansa kullum" "yana nan yaci mai dadi ya barsu da garau garau shike nan yawon bariki da kashewa matan bariki kudi.""" "Naja'atu tace""Allah ya shiryeshi idan zai shiryu Koda DanTalle ya kammala cin abincinsa sai yazo ya" "tsaya yana gyara bakin aljihunsa domun fito da kudi Mmn Sajida taga ya dauko dubu hudu ya mika mata tace""A'a Ai dari shida ne kudin abincinka."" Yace.""Eh na sani nayi niyyar yi miki kyauta ne ki dauki dubu biyu sai ki bawa yarinyarki dubu biyu.'' Mmn Sajida tace""Anya za'ayi haka kuwa na fad'a maka komai" "kuma kasan ni bana cikin wannan shirman da kuke yi.""" "Yace.""Haba Me yasa kike wannan maganar Mmn Sajida ni bada wata manufa na baku kudi ba nayi niyya" ne kuma idan inason yarinyar nan da aure zan so ta bada wata manufa ba. "Mmn Sajida tace""To godiya mukeyi Allah ya 'kara budi."" Ya amsa da amin yana kallon Naja'atu da wani" "shegen murmushi a fuskarsa..Girgixa kanta kawai take tana mamakinsa lallai kam ya ci sunansa 'DanTalle ita wannan ko a 'kafa a daura mata shi a ta kwance da gudu, daka ganinsa idanunsa a bude suke kar!! dasu irin na mayaudara! Ya juya baya da niyyar barin gurin tabi shi da kallo! 'Tab! gabad'aya bashi da tsarin mazan da take so wani siriri dashi kamar zai karye sai dogon wuya kamar mari'kin lema a ganinta ma ina yaga kuzarin da zai tunkareta..ita duk wani siririn mutum raina shi takeyi tana ganin kamar basu da wani karfi da kuzari( Kaji wauta irin tana Naja'atu 'kananun maza ma sunfi jaraba kuma babu abinda za'a nuna musu)....Sai kusan sha daya da rabi na dare Mmn Sajida ta siyar da abincinta suka harhada" kayan suka shiga cikin gidan. Karfe takwas na safe sun shirya Naja'atu tayi wanka ta shirya tsaf Mmn Sajida ta bata sabuwar atampa da mayafi tasa a jikinta sannan kuma ta hada mata wasu atampopin kala uku tasa mata a leda viva Naja'atu ta dinga yi mata godiya tana mamakin karamcin matar gaskiya samun Mai hali irin nata sai an tona. "Suna kokarin karyawa Mmn Ladi ta shigo gidan, ganin naja'atu cikin sabuwar atampa sai tayi kici kici da" fuska ta wani dogare a bakin kofa tsabar bakin ciki da hassada yasa ta kasa shiga. "Mmn Sajida tace"" Ki shigo mana ki zauna dama yanzu nake cewa zan aika Walid ya fada miki ko zaki zo" "muje tare.""" "Mmn Ladi ta ta'be bakinta tana girgiza kanta da fad'in ""Babu inda zani aikin gidana ma ya isheni.""" "Mmn Sajida tace""To shikkenan ki shigo kisha tea gashi muna hadawa." "Babu kunya Mmn Ladi ta shigo tana ya'ke da fadin ""Kamar kuwa kin san ban karya ba har yanzu dan yau" mutsiyacin mutumin nan ko 'kwandala bai bani ba ya futa. "Mmn Sajida tace"" Ke Mmn Ladi kiji tsoron Allah ki daina tsinewa mijinki wallahi ki dinga hakuri da yau da" "gobe idan kina ganin ba zaki iya jurewa ba to ki nemi sana'ar yi amma zagin miji da tsine masa bashi da amfani.""" "Mmn Ladi na had'a tea tace""Ke rabu dani dan Allah wallahi jiya da kyar nayi bacci saboda tsabar takaicin" da mutumin nan ya 'kunsa min haba me za'ayi da talauci ace kullum a gidanka baka da sakakken abinci sai shinkafa da wake da mai da yaji haba jama'a wannan wace irin masifa ce ace kudin cefane dari biyu "mtsssw!"" takare maganar tare da jan dogon tsaki" "Mmn Sajida tace""To ina laifi da kika samu shinkafa da waken ni na samu mana! kina kallo fa ni nake ciyar" "da kaina da 'ya'yana ke kin samu kina rainawa wallahi ki dinga godewa kad'an sai kiga Allah ya wadataki.'' Mmn Ladi kur'bar tea take tana dangwalar bread da miya tace""Duk yanda zanso ki fahimta ba zaki fahimta ba mu bar maganar kawai.""" "Mmn Sajida tace""To ai dole na bari tunda bakya so a fada miki gaskiya."" Dariya kawai tayi ta cigaba da" cinye musu naman dake cikin miyar gabansu. Naja'atu tun abun na matar na bata mamaki har ya dawo bata dariya ikon Allah kenan wannan shi ake "kira Allah daya gari bambam! Mmn Ladi sai da ta cika cikinta tsaf sannan ta karkad'e zaninta mike tare da kad'a kan yaran ta tafi kaisu makaranta...Naja'atu sai so takeyi suyi gulmar Mmn Ladi ita kuma Mmn Sajidan ta'ki yarda, ta lura da Mmn Sajida tana da kyakkyawar zuciya akan matar." "Naja'atu tayi mamakin ganin gidansu Munira, ita kam bata dauka zata ganshi haka ba sabida irin karyar" da Munira take musu a aji cewar babanta mai kudi ne tsohon dan jarida ne da yake aiki a tashar bbc ta kasar waje! bayan nan kuma yana da company na siyar da motoci da sauransu 'karya iri iri Munira keyi musu su kuma suna yarda sabida ganin irin yanda ake zuwar mata ziyara cikin babbar mota hade da kayan abinci iri iri shiyasa suka amincewa. Munira bata gidan wai sun tafi shopping ita da "Muktar..Mmn Ladi bayan ta huta ta mike da niyyar tafiya, Naja'atu taji kwallah na kokarin zubo mata dan zaman da tayi da matar taji bata son rabuwa da ita. Mahaifiyar Munnira na hakkince a kan kujera" "Cikin nuna isa da nuna ita wata me kudi ce ta kalli Mmn Ladi da fadin""Ba zaki bari a kawo abinci kici ba" "sai kice zaki tafi.""" "Mmn Ladi tace""Alhamdullhi Hajiya kafin na fito daga gida sai da na karya tukkuna."" Mommyn Munira ta" "dan gyara zamanta cikin isa ta dauki pose dinta dake gefanta ta zuge zif din ta dauko dubu daya sabuwa kar da ita ta mika mata da fadin""Gashi ki shiga napep.""" "Murmushin takaici Mmn Ladi tayi tace""Nagode hajiya wallahi bazan karbi kudinki ba domun kuwa ina da" "kudin motar komawa gida ta kalli Naja'atu da fad'in"" To Naja'atu saduwar alkairi idan kin koma gida ki gaishe da mutan gidanku.'' Naja'atu tace""Nagode sosai insha Allah zan fada musu."" Mmn Ladi sa kai tayi ta fita daga palon tana mamakin izgili da wulakanci irin na matar gidan koda yake dama tun kafin ta tako kafarta cikin gidan take da labarinta sai 'karyar arziki alhalin kowa yasan aikin da babban d'ansu yake yi a gari 'Ri'ka'kken d'an 419 ne (damfara) Laya ta mussaman ce dashi wace yake ma'kalawa a 'kugunsa" "yana shiga ko ina yayi satarsa ya fito ba tare da an ganshi ba, shiyasa komai na rayuwa baya yanke musu" a gidan kuma iyayensa sun sani basu hanashi ba sai ma 'kara masa kwarin gwiwa da suke!. Duk kuwa d'an kasuwar da ya sake yayi mu'amula da *Bash* to ya zama sorry dan sai yayi masa tas! kuma yasa malamansa sun d'aure masa baki *Bash* mugun hatsabibin mutum ne. Jama'ar garin kuwa tamkar masu jin tsoro an rasa wanda zai fito yayi magana kowa yaja bakinsa yayi shuru sai dai idan surutu ya tashi ayi a bayan fage. Naja'atu har duhun dare ya shigo tana zaune a guri guda a rakube dan dama Mommyn Munira bata da sakin fuska tunda suka gaisa wata magana bata sake shiga tsakaninsu ba. Sai bayan magariba ne da taga zaman palon ya isheta ta mike salo salo ta nufi wani daki dake cikin palon taje ta zabga tagumi tana tunanin wannan wane irin shopping ne Munira ta tafi tun safe bata dawo ba gashi dare yayi Gaskiya sai dai tana tunanin bayan shopping din sunje wani gurin ita da saurayin nata. Abinda naja'atu bata sani ba shine Munira ma kwata kwata bata kwana a gidan ba tana can gidan Muktar din kwananta biyu kawai dai Mommyn tata ce ta tsara cewar sun tafi shopping ne. Kwanciya tayi tana share hawaye abin duniya ya isheta gabadaya kuma hankalinta yayi gida tana tunanin yanzu wane hali iyayenta suke ciki sai Musaddiq da yake yawan fad'o mata a rai! Abbah Abbas kuwa dama tuni ta cireshi daga cikin ranta tana ganin ta ku'buta daga hannunsa har abada. "Mai Aikinsu ce ta shigo da sallama a bakinta tace""Wai ki fito kici abinci inji Hajiya."" ta mike da sauri tare" "da fadin""To gani nan.""" Mai aikin ta juya ta fita daga dakin minti biyu ta mike tabi bayanta..Tana fita taga Mommy a zaune a "gurin cin abinci da waya a hannunta tana fad'in ""Munira kina da hankali kuwa yau kwananki biyu a waje ko kiran waya bakya yi ashe kina so jama'ar gari su fargaba da lalacewar da kukeyi keda muktar din tun kafin auranku ace kungama sanin junanku wannan wace irin rayuwa ce? to komai dare ki dawo gida" domun tun safe kike da ba'kuwa kawarki ce tazo daga kano. "sama sama taji muryar Munirar na fad'in "" Ayya Mommy dama yau zan dawo wallahi Muktar din ne" "bashi da lafiya shine na tsaya na kula dashi."" Mommyn tace""Bashi da iyayene da lallai sai kece zaki kula dashi ai koma meye zai faru sai ku bari a shafa fatiha tukkuna."" Tace""mommy ba lallai ne ya samu kulawar da yake bukata ba daga gurin mamansa ni kuma shiyasa na tsaya na kula dashi har ya warware kuma mommy meye yayi saura a tsakanina dashi tunda iyayenmu sun mallaka mana junanmu muktar ya" "bada sadakina ni banga laifi ba dan na kwana a gidansa ba.""" "Tace""Ni ba cewa nayi kiyi min tsari ba duk rayuwar da kike so ita za kiyi ni dai nace ki dawo gida yau" "kinji na fada miki."" Tace""Insha Allahu ko dan saboda Naja'atu zan dawo yau.""" Naja'atu jikinta ne yayi bala'in sanyi jin irin abunda ke faruwa da rayuwar Munira! dama sai da tayi zargin "wani abu ashe Munira bata da kamun kai tana bin saurayi har gidansa tana kwana dashi ba tare da aure ba, gaskiya al'amarin ya bata mamaki mutuka. Mommyn ta kalleta bbu fara'a a fuskarta tace""Kixo ki" "zauna kici abinci munyi waya da ita tace""Gata nan a hanya."" Naja'atu kawar da mamakin fuskarta tayi ta" "nuna kamar ba taji wayarsu ba taje ta zauna gurin cin abincin tace""To bbu komai Allah ya dawo da ita lafiya.""" "Tana kokarin mikewa daga gurin ta amsa da ""amin'' *Bash* ne ya shigo palon yana sanye da k'ananun" kaya wanda sukayi masa kyau sosai *Bash* irin mazan nan ne masu tsayi da murd'ad'adan jiki shiyasa k'ananun kaya suke masa kyau fari ne tas gashi kyakkyawan gaske! kyawunsa da kudinsa da kuma yanayin tsarin hallitarsa yasa 'yan mata suke haukacewa a kansa! shi kuma yana cin karansa babu babbaka a kansu duk wacce ya bukaci yayi sex da ita babu gardama zata amince masa *Bash* mugun manemin mata ne kuma dan shaye-shaye na bugawa a jarida ga neman nemanta ga *Luwad'i* duk yana yi...sana'arsa tafi kala goma domin *Luwadin* ma da manyan mutane yake suna bashi mahaukatan kudi Shiyasa gabad'aya bashi da ra'ayin aure yana ganin aure kamar damuwa ne tunda babu abunda ya nema ya rasa to zai iya kare rayuwarsa ba tare da ya auri wata mace ba. Naja'atu kallo guda tayi masa taji gabanta ya wani irin faduwa! a take taji wani irin sonsa ya sauka a "zuciyarta, duk da ta kasance mace mai kyau amma kyawun *Bash* yayi masifar tafiya da imaninta Wow! irin maxan da take bala'in so wannan hand some din waye zai had'ashi da Salim bare kuma wani tsoho irin Abbah Abbas!sum she idonta tayi tana jin yanda gabanta ke faduwa kaunar *Bash* na sake ruruwa" a cikin zuciyarta. To shima nasa 'bangaran kallo guda yayi mata yaji yana sha'awarta dan yana bala'in son mace duguwa "saboda tana da zurfi duk irin mi'kewar da joystick dinshi tayi idan yana sex da doguwar mace tana samu guri..Ya lura yarinyar za'a je da ita ga tsayi ga nonuwa tubarkallah...Yana shafa tarin sumar kansa yaja kujera ya zauna da murmushi mai kyau a fuskarsa...Mommy tace""Ashe baka fita ba dama.""? Yace."" Tun misalin shida na safe na fita ban jima da dawowa bane."" Tace""Okey to bari na had'a maka abinci ko.'' Yana kallon Naja'atu yace""Mommyn wannan babyn fa duk cikin famliy naki dana Daddy ban san da ita ba."" Tace""Sunanta Naja'atu friend din Munira ce ta kawo mata ziyara tun daga kano."" Yace.""Wow! beb sannu kinji ko ya kano me yasa ban ta'ba saninki ba dik da cewar duk wasu friends din Munira na sansu" amma ke nayi mamakin da ban ta'ba saninki ba. "A sanyaye tace""Tare mukayi *Andal skull* da Munira sunana Naja'atu Abbas 'kofar na'isa."" Yace.""Okey" "sai yanzu na gane me yasa duk sanda muka je visiting bana haduwa dake.? tace""mybe bana kusa ne."" Girgixa kansa ya shiga yi yana sakar mata kayataccen murmushi kafin yace.""Amma kin san kina da kyau ko""? Murmushi tayi ta sinne kanta wani irin dadi na ziyartar zuciyarta da alama ta fahimci cewar guy ya fad'a tarkonta kamar yanda ta fad'a nasa. Mommy kuwa barin gurin tayi tana jin dadin ganin yaron" nata ya tanka Naja'atu addua take Allah yasa su daidaita kansu dan tana bala'in so taga yayi aure..... "Cikin sigar Yaudara da sigar janye hankali ya kwantar da murya yace.""Naja'atu kallon farko nayi miki naji" "ina sha'awarki ina fatan zaki mallaka min kanki koda na rana daya ne."" Taji gabanta ya yanke ya fad'i! Ashe Sha'awarta yake ba sonta yake da aure ba?" "Ta dan bata fuska tare da fad'in ""Gaskiya bana cikin jerin irin wannan matan."" murmushi yayi yace.""Nima" na fahimta ke me hankali ce okey idan kin shirya aure nima na shirya zan aureki ina tunanin zan karya al'kawarin dana daukarwa kaina a kanki Jin wannan magana tasa yasa wani irin farin ciki ya lullu'beta babu shakka tazo garin Jos a sa'a tunda tayi nasarar samun wannan guy da yake da wahalar samu...... *Waye yake maganar Salim da Abbah Abbas idan su Bash na guri * *Ammafa kada ku dauka ina team din Bash No! Har yanzu ina tare da Abbah ina kuma taya shi alhini da jimamin faruwar wannan al'amari* *Tofa gwanar taku ta tsinci dami a kala duk ta rud'e ta samu saurayi mai jini a jika wanda zai iya da jarabarta anata ganin Bash ne zai iya dauke mata dukkanin laluranta akwai dramar * *Littafin na kudi ne..!* Koda zaki ganshi a gruops to na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake Vip gruop #600 Normal gruop#300 accont: 0542382124..Binta Umar gtbank..Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *MANZIR _ALWAFIR ABUJA * _*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci magungunansu babu almundahana a ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu ko wace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye da akwai gruops na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rijistar dasu to kukanki ya 'kare idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_ Mddbhrmbn45 "*Bash* ya sake tausasa muryarsa kamar wani mutumin kirki yace.""Idan kin amince min da wuri nake so" "ayi komai a gama dan akwai tafiyar da take tunkaro ni aiki zai kaini kasar Ghana inaso in tafi dake can sai muyi amarcinmu hankali kwance.""" Lumshe idonta tayi tana jin wani irin feelings na taso mata jin maganar amarci yasa ta sake kwadaituwa da auran *Bash* domin tana ganin a yanzu za tayi irin auran da take muradi Cikin wani irin yanayi "Tace""Zaka iya auran bazawara.""? *Bash* yayi sak yana kallonta, da wani irin yanayi na alhini gami da damuwa tace""Ina da aure yanzu haka dalilin auran dolen da akayi min da mijin 'yar uwata data mutu yasa nazo nan garin.....Tiryan tiryan ta bashi labarin rayuwarta..." "*Bash* ya shiga murza fatar goshinsa cikin damuwa yace.""Amma banji dadin wannan labarin naki ba" "wallahi wannan dattijon yayi min shigar sauri amma babu damuwa tunda ina sonki zan iya auranki a haka yanzu babban burina ya sake ki dan yanda kika bani labarinsa na fahimci mai taurin kai ne watakila dik wannan abun da kikayi masa sai iya 'kin rabuwa dake amma idan yasa gardama da taurin kai sai kawai muyi maganinsa."" Tace""Kada ka damu a jikina ina jin zamana dashi yazo karshe zai iya sakina idan yaji na zubar masa da ciki domin yana da bala'in son yara bana tsammanin zai iya hakura ya kyaleni.....Kuma zan tura masa text domin na tabbatar masa da cewar cikinsa ya lalace nasan hakan sai" sake tunzurashi... "*Bash* yace.""Okey ina ganin yanzu ma zaki iya tura masa text din ayi ta ta 'kare dan wani irin kishinsa" "nake ji a cikin zuciyata."" Murmushi tayi tare da mika hannunta domin kar'bar tsadaddiyar wayar tasa. Daidai lokacin Munira ta shigo palon hannunta rike da wasu ledoji sha'ke da kyan ciye" "ciye..Ganinsu zaune guri guda yasa tace"" Kai gaskiya kunyi bala'in dacewa da juna kada dai har soyayya ta shiga tsakaninku gaskiya idan haka ta kasance zanfi kowa jin dadi wallahi *Bash* na shegen" "murmushinsa yace.""Munira kina da wannan Friend din baki ta'ba nuna min hotonta ba ai da tuni nine zan aureta amma kika bari wani tsoho yayi min shigar sauri."" Munira ta 'karaso gurin tana wata irin dariya ta farin ciki ta bawa Naja'atu hannu suka tafa suna dariya..Munira ta zauna kan kujera tana fad'in""Wallahi Broth Allah ne kawai yayi ba kai zaka fara auran Naja'atu ba amma tuntuni na dade dayi maka sha'awar auranta kawai sabida nasan baka so ayi maka maganar aure yasa banta'ba nuna maka" "hotonta ba amma yanzu naji dadi sosai daka ganta da idonka kace kana so.""" "Cike da sha'awa yace.""Munira Friend dinki tayi sosai dan lokaci guda ta tafi da zuciyata matsalata guda" "auran da yake kanta shin wace shawara kuka yanke akansa.""" "Munira tace""Haba broth kada ka damu wannan auran ai dashi da babu duk daya suke insha Allahu sai" "ya saketa komai nacin sa.""" *Bash* ya mi'ke tsaye idanunsa kan Naja'atu yana mata wani irin kallo wanda kana ganinsa kasan na "sha'awa ne yace""Ki rike wayar a hannuki zuwa gobe da safe zan 'karba amma ki tabbatar da cewa kinyi masa text din da kika fad'a.""" "Tace""Insha Allah zan masa kada ka damu."" Hannunsa ya zura a aljihun jins din dake jikinta ya wani tsira" "mata shu'uman idonsa gabad'aya jikinsa ya mutu ai dole ne ya fita ya nemi biyan bukatarsa...Munira ta dinga dariya tana fad'in ""Lallai yau ina kallon soyyaya mai zafi! Had'uwar farko Naja'atu kin rikita min dan uwa gaskiya naji dadin wannan al'amarin."" *Bash* Yayi saki murmushi had'e da sosa kanshi ya kama" hanyar fita yana wata shegiyar tafiya irin ta marasa kunya. Naja'atu murmushi kawai take dadi na ziyartar zuciyarta salon kallon soyayyar da *Bash* ke mata shine yake sake rikita ta tana jin sonsa na sake karuwa a cikin zuciyarta.. Tare suka shiga dakin ita da Munira ta zauna gefan gado tana ta duba wayar Bash din Hotonansa ne kala "kala yawancin pictures din bana Najeria bane yayi su a kasashe daban daban! ganinshi rungume da turawa black americas bai dameta ba tana ganin ai wayersa da kudinsa ya cancanta yayi mu'amula da kowane irin jinsin mutum..Munira ta fito daga wanka tana kintsa jikinta tace""Gaskiya Naja'atu kinsha wuya na tausaya miki kuma wannan matar data taimake ki yana da kyau naje nayi mata godiya."" Tace""Gaskiya kam yana da kyau idan an kwana biyu muje na rakaki gidanta...Munira ta zauna kusa da ita tare da fad'in ""To alhamdullhi Yanzu mun samu ciki ya zube ba tare da munsha doguwar wahala ba" yanzu babban abunda yake gabanmu shine rabuwa da wannan tsohon. Hankalinta nakan wani had'ad'dan hoton *Bash* wanda ya dauke shi yana sanye da kayan wanka a bakin swimming hoton yayi masifar dauke mata hankali ganin zahirin *Bash din* ya sake firgitata sai ta sake kwadaituwa da auransa hakika ta samu nasarar auransa to ta kere sa'a kuma zata iya shiga koina dashi ta nuna shi da sunan mijinta ba kamar Abbah Abbas ba da take jin kunya a dangatata dashi a matsayin miji... Munira ganin Naja'atu bata fuskantar maganar da take yasa ta le'ka cikin wayar tana dubawa! Dariya "tayi tace"" Naja'atu kenan naga alama kema kin mutu akan Brother d'ina Humm! na taya ki farin cikin samun zuciyar *Bash* 'Yan mata da yawa suna sonsa baya ta'ba sauraransu amma ke gani daya yayi miki ya haukace harda maganar aure duk da kasancewarki bazawara yana da kyau kiyi gaggawar nemawa" "kanki mafita tun kafin damar da kika samu ta kufce miki.""" "Ajiyar zuciya ta sauke tace""Yanzu wace shawara kike ganin ta dace? Ni da cewa nayi zan tura masa da" "text na fada masa cikinsa ya zube kuma ina nan ina jiran takardarta."" Munira tace""Wannan shawarar tayi.....Kawo wayar na rubuta masa text din...Naja'atu tasa numbarsa da yake amfani da ita a saudia, Munira babu sallama ta shiga rubuta text din kamar haka." _Ni ce Naja'atu ina so in tabbatar maka da cewar wannan cikin daka yi min yabi rariya dama tun kafin haka ta faru sai da na fad'a maka bani da ra'ayin zama da kai ballantana har na haihu dakai komai ya faru son zuciyarka ne ya janyo maka. Abbah banso muyi irin wannan rabuwar da kai ba amma ina ganin hakan shine daidai Ni ce dai Naja'atu ina nan cikin koshin lafiya bayan samun nasarar rabuwa da masifar daka 'kunsa mun a cikina ina nan ina jiran saki daga gareka idan baka sakeni ba to kuwa zanyi ta zama a inda nake har'karshen rayuwata_ Kafin a tura text din Naja'atu sai da ta karanta kusan sau biyar tana ganin kamar maganganun sunyi "tsauri da yawa! amma kamar wacce aka sawa lemon tsami a baki ta kasa cewa komai tana kallo Munira ta tura text din ya tafi gabanta sai ya tsananta fad'uwa cikin zuciyarta tana ji kamar bata kyauta ba...Munira tace""Yana da kyau ma a tura masa ta whasap dan naga kamar yanayi ko.""? A sanyaye tace""Duba ki gani."" Munira ta shiga dubawa taga numbarsa tana whasap amma kuma kwanansa biyu bai hau ba, dan tun ranar daya bude ya saurari audion da Salim ya turo masa bai sake kunna data ba dan dama ba kasafai yake shiga whasap din ba. Tace"" Ya kwana biyu baya kai amma Bari a tura masa" "domin ya dauki abin da muhimanci.""" Naja'atu dai shuru tayi Munira sai zartar da hukunci takeyi ita kuma gabanta sai faduwa yake tana adduar Allah yasa ya mayo da martanin saki. Munira kayan ciye ciyen data shigo dashi ta baje musu suka dinga ci suna hira Naja'atu dai daurewa kawai take bini bini sai ta duba wayar dake hannunta wai ko ya turo amsa. Jiki a sanyaye ta ajiye wayar ta nufi toilet din dake cikin dakin tayi wanka ta kimtsa jikinta tare da sanja pad ta fito Munira ta bata sababbin kayan bacci tasa tasa turare ta zauna tare da daukar wayar tana sake dubawa. Ita kuwa Munira tana kwance a bad daga ita sai 'karamar vest da gajeran wando wanda ya matseta sosai pictures take dauka kala kala tana turawa Muktar ta whasap..... *Allah ya shiryaki Munira* 'Bangaran Abbah Abbas kuwa bai samu damar duba wayarsa ba sai lokacin da yazo kwanciya dan basu dade da shiga masaukin nasu ba sun fita duk gabadayansu sun dan shiga kasuwa dalilin barin 'kasar da za suyi jibi idan Allah ya nufa dama kwana goma sukeyi ko sati biyu suke dawowa. Halisa na kokarin kwanciya a kusa dashi taga ya mi'ke zumbur! Gabanta ne ya fad'i! tayi saurin matsawa dan ta dauka marinta zai yi! sai dai kuma ganin ya tsirawa fuskar wayarsa ido yasa da sauri ta 'leka kanta tana dubawa! Text din ta karanta tsaf! kuma ta fahimci daga Naja'atu yake. Wani matsiyacin dad'i ya rufeta wayyo yau da ita kadaice a gurin sai ta taka rawa ciki ya zube burinta ya cika. Kukan munafurci ta fashe dashi ta "shiga tafa hannu tana fad'in""Innalilihi wa'ina ilahi raji'una! yanzu yarinyar nan sai da ta zubar da cikin nan? anya naja'atu tayi maka adalci kuwa? me kayi mata take maka irin wannan 'kiyayyar Allah ya baka zuria tayi maka asararsa kuma sabida bata da kunya cikin izigila take fad'a maka ga abunda ta aikata" "maka kai jama'a amma wannan yarinyar bata kyauta ba wallahi.""" Shuru yayi domun bakinsa mutuwa yayi murus! ya dinga kallon fuskar wayar yana ta karanta text din kamar me koyon karatu!! ya jima cikin wannan yanayin kafin ya samu damar furta kalmar innalilihi wa'ina ilaihi raji'un!!! Ya kashe wayar ya ajiyeta kana ya mike ya nufi toilet domun dauro alwala...Halisa murmushin jin dadi tayi ta juya bayanta tare da jan bargo ta rufe jikinta cike sa nishadi da farin ciki bacci mai dadi ya dauketa. Dadduma ya tsaya ya fuskanci al'kibula ya tayar da sallah...Raka'a biyu yayi ya jima a sujjadar karshe yana rokon Ubangiji sassauci ya d'ago tare da sallame sallahr nan ma ya jima hannunsa a sama yana addua kafin ya shafa a fuskarsa ya mike yana jin wani kuzari a jikinsa zuciyarsa tayi wasai babu wani bacin rai tabbas tunda har Allah ya zartar da irin wannan hukunci to hakan shine alkairi a rayuwarsa. 'Yar jakarshi da yake tafiya da ita ya dauko ya zauna kasan kafet ya bud'eta a nutse ya dauko wani memo ya ya bud'e ya yagi pepar d'aya ya dauki biro a nutse ya soma rubutu a jiki.... *Jikina na karkarwa na le'ka domun naga mai yake rubutawa. ziraro min shikkenan Naja'atu ta cuci kanta* yanke jiki nayi na fad'i hawaye na _NI ABBAS SAMA'ILA NA SAKI MATA TA NAJA'ATU MALAM SANI SAKI DAYA INA RO'KON ALLAH YASA HAKA SHINE YAFI ALKAIRI A TSAKANINMU._ *Kuyi hakuri dan Allah Nima ba'a son raina ba Labari ne yazo a haka* *Littafin na kudi ne..!* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abun yake. Vip group #600 Normal gruop#300 accont 0542382124...Binta umar gtbank..Idan katin waya zaki turo kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *MANZIR _ALWAFIR ABUJA * _*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci magungunansu babu almundahana a ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu ko wace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye da akwai gruops na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rijistar dasu to kukanki ya 'kare idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_ Mddbhrmbn46 A nutse ya linke takardar da yayi rubutun ya bud'e tsakiyar memo d'in yasa ya mayar da jakar ya rufe "tare da mikewa da ita a hannunsa zuwa yayi a dana ta a inda take kana ya nufi bed din ya kwanta yana jin nutsuwa da kwanciyar hankali na saukar masa a zuciyarsa tabbas rabuwa da auran Naja'atu shine alkairi a tare dashi, dan idan ya tilasta kansa zama da ita to kuwa zai ta had'uwa da takaici da 'bacin rai watakila ma sanadiyar hakan ciwo ya kamashi dan a yanda yake da kaunar 'ya'ya gami da adduar Allah ya bashi zuria da yawa baya tsammanin zai iya zama da kowacce irin macece mutukar zaiyi wahalar dasa 'kwai ta zubar masa babu shakka ko wacece zai iya rabuwa da ita rabuwa ta har abada...Cikin kwanciyar" hankali yayi bacci da asubah ya tashi zuciyarsa wasai baya ta'ba nadamar abinda ya aikata ga yarinyar. 'Bangaran Naja'atu kuwa kwana tayi tana munanan mafarkai wanda taga Halimatu tazo mata da wasu fararan kaya masu kyalkyali sai dai yanayin yanda taga 'Yar uwartata ya bata tsoro fuskar Halimatun babu walwala ta tsira mata ido kawai tana kallonta ita kuma sai magana take mata tana kokarin rike hannunta sai ta fizge ta bar gurin da sauri ta dinga waige waige tana kiran sunanta amma bata ganta ba......Sannan kuma duk a cikin mafarkin taga mahaifiyar ta na kuka ita da Mussadiq suna kiranta. a tsananin firgice ta tashi tana had'a gumi! ta dinga kallon dakin gabanta na fad'uwa gaskiya mafarkin nan ya bata tsoro tunda Halimatu ta rasu bata ta'ba yin mafarki da ita ba sai yau shiyasa jikinta yayi sanyi Wayar *Bash* ta dauka ta kunna ta haske dakin a maimakon ta tashi taje ta dauro alwala sai kawai ta shiga dube dube a wayar wai ko bayan kwanciyarta Abbah Abbas ya turo replay ta gama dube duben ta ba taga komai ba a sanyaye ta ajiye wayar ta mike ta nufi bandaki domin yin alwala. Kafin ta tayar da sallah sai da ta tashi Munira tukkuna ta hau dadduma. Munira kuwa zuwa tai tayi fitsari ta dawo ta sake kwanciya dama can Munira bata sallah sai gari ya waye. Naja'atu bayan ta idar da sallah "zama tayi kan daddumar abin duniya ya dameta mafarkin da tayi yayi masifar bata tsoro mussaman ganin mahaifiyarta na hawaye tasan duk inda suke suna can cikin tashin hankali da damuwa, ta dinga share hawaye tana fad'in Ba laifina bane tun farko na fada muku bana so bana sonsa kuka kasa fahimtata."" Munira tayi firgigt ta mike zaune tana kallonta tace""Naja'atu lafiya kike kuka.""? Hawaye ta share tace""Munira wani mummunan mafarki nayi wallahi tabbas iyayena na cikin damuwa da rashin ganina."" Munira tace""To ai dama dole su shiga damuwa da rashin ganinki ai tun farko laifinsu ne yanzu" "dan sun neme ki sun rasa ai kansu zasu tuhuma sai su gane auran dole ba abune mai alfanu ba.""" "Girgiza kanta kawai tayi tace""Munira naga Yaya Halimatu a mafarki tana cikin 'bacin rai ga Mussadiq na" "kuka yana kiran sunana jikina ya soma sanyi da wannan al'amarin wallahi."" Munira taja tsaki tace""Ai shikkenan sai kije kiyi tayi waye ya fada miki mafarki gaskiya ne? dan Allah ki daina wannan maganar idan zaki saki jikinki ki saki jikinki kawai ki watsar dasu koma meye ya faru ai sune suka janyo me yasa" "suka aura miki wanda bakya so.""" Girgixa kanta ta cigaba dayi hawaye na sake zubo mata...Ita kuwa Munira ta mike ta nufi bandaki tana surutai kan damuwar da taga Naja'atun ta shiga.... Abbah Magaji na zaune yana karya kummalo Halisa ta fito daga dakinta hannunta rike da wayarta ta "zauna kusa dashi, tace""Kaga ina ta kiran numbar ba dauka ba kuma wannan numbar itace nake tsammanin ta 'Kawarta, dan bana mance ranar da tazo tace na bata aron waya zata kira 'kawarta a jos.""" "Yana goge bakinsa yace.""Bani numbar na gwada kira."" Wayar ta mika masa yasa numbar a wayarsa" "cikin ikon Allah tana fara ringing aka dauka....Hands free yasa yayi sallama...Munira ta amsa da fad'in "" Da waye nake magana.""? Yace.""Kina magana da wani bawan Allah ne daga kano shin ko kinsan wata" "yarinya Naja'atu.""?" Naja'atu sai da ta kusa sakin fitsari a wando jin muryar Abbah Magaji radau a kunnanta!!! Munira tayi "saurin kallonta idanunta duk sunyi gwale gwale. Abbah Magaji yayi gyaran murya had'e da fad'in ""Hello kina jina kuwa.""? Munira ta shiga inda inda da fad'in "" A'a ban santa ba wallahi."" Yanayin yanda take maganar cikin rashin gaskiya yasa ya fahimci cewar yarinyar da hadin bakinta dangane da faruwar al'amari...Yana kokarin yayi magana Munira ta kashe wayar suka 'kurawa juna ido ita da Naja'atu, ya akayi tun ba'aje ko ina ba asirinsu zai tuno..Naja""atu kuwa ai tuni hawaye sun 'balle mata fargaba da" tsoro duk sun cika mata zuciya. Abbah Magaji yabi wayar da kallo yana mamakin kashe masa da yarinyar tayi girgiza kansa yayi tabbas "biri yayi kama da mutu, wayar ya sake kira. Munira ta zabura tana kallon wayar ta'ki dauka har ta katse" "Abbah magaji ya sake kiran wayar nan ma Munira taki dauk'a..Sai kawai ya ajiye wayar yana murmushi hade da kallon anty Maryam yace.""Duk yanda akayi yarinyar nan tasan inda Naja'atu take kuma da alama da akwai hadin bakinta dangane da faruwar al'amarin."" Anty maryam tace""Nima tunda naji yanda take amsa maka a tsorace yasa na fahimci tana da masaniya akan abinda yake faruwa yanzu koda anje jos din ai ba'asan a ina za'a same inda yarinyar take ba ballantana a tambayeta inda Naja'atun take."" Yace.""Kada ki damu mutukar layin yana aiki zansa ayi min bunkicen inda suke gobe zan shirya na nufi jos" din. "Tace""To Allah yasa a dace ai gobe ma abokin naka zasu dawo ko.""? Yace.""Eh insha Allah bana tsammanin" "ma zai sameni dan da wuri zan tafi."" ajiyar zuciya ta sauke tana sake tausayawa Naja'atu halin data jefa kanta." "Munira tace""Dallah ki daina kuka mtwwss wai sai me idan sunzo sunga inda kike ke ba zaki iya kaisu kuto" "bane alkali ya kwatar miki 'yancin ki ko dole ne akace sai kin zauna da wanda suke so ni wallahi banta'ba ganin inda akayi hakaba."" Naja'atu na kokarin yin magana Bash ya shigo dakin yana sanye da t_shat fari tas da 3qutar wuyansa sanye da siririyar sarqa tamkar wani arne sai wani irin kamshin turare yake mai dadi! Yana ganin Naja'atu na kuka yaji hankalinsa ya tashi ba tare da tunanin komai ba ya zauna kusa da ita had'e da rungumo kafadarta yana tambayar abinda yasa ta kuka! Naja'atu tsorata tayi ta matsa gefe tana share fuskarta...Munira ce ta shiga fad'a masa abinda yake faruwa...Tsaki yaja ya dauko wayarsa dake cikin aljihun wandon jikinsa ya mikawa Munira wayar da fad'in ""Ki samin numbar mutumin da ya" "kira yanzu ni zan fada masa Naja'atu tana jos sai me.""?" "Da sauri Naja'atu ta kalleshi yace""Baby maganar rufe rufe bata kamata ba gwara ayi komai a bayyane ni" "zan tsaya miki a duk inda za'aje ba zaki koma gidan wannan tsohon ba tunda bakya sonsa zan shigar miki da 'kara kuto.""" "Munira tace""Nima haka nace mata ta daina kuka tana tayar da hankalinta ai akwai sharia!" "Naja'atu girgiza kanta tayi tana hawaye tace""Bash ina ganin kima da darajar iyayena bana so na 'bata" "musu rai ko kuma na tozartasu dan Allah kada wata mummunar kalma ta shiga tsakaninka da yayana kaji ko.""" "Yace.""Baby ke kina daukar al'amarin da sauki ko? okey na fahimci kaunar da kikewa mahaifanki bai kai" wanda kike min ba ina ganin zan cireki daga rayuwata kawai shi yafi alkairi. "Da sauri ta ri'ke hannunsa tana girgiza kai tace""Wallahi ba haka bane ban hanaka ka kira yayana kuyi" "magana ba amma kada ka zageshi ko ka fada masa mummunar kalma."" Yace.""Okey na fahimce ki insha Allah zan kiyaye.""" "Abbah Magaji na kokarin shiga motarsa kira ya shigo wayarsa koda ya duba sai yaga sabuwar numbar," "zama yayi cikin motar tare da kara wayar a kunnasa. Bash yace.""Sunana *Bashir Aminu dan jarida Jos!*" "Abbah magaji jin an kira sunan Jos yasa yayi saurin amsawa da fad'in ""Malam Bashir ni kuma sunana Magaji Sani ina garin kano ina fatan naji kyakkyawan labari daga bakinka." "Bash yace."" Inaso na sheda maka cewar 'Yar uwarka mai suna Naja'atu tana hannuna yanzu hakama" "tana kusa dani."" Abbah Magaji cikin farin ciki yace.""Alhamdullhi Allah mungode maka daka bayyana mana wannan yarinyar dan Allah inaso ka bata wayar zamuyi magana." "Bash yace.""Wannan lokacin baizo ba tukkuna Alhaji Magaji shin mai yasa kuka d'aurawa yarinyar nan" "aure da wanda bata so? kun san illar dake tartare da irin wannan auran kuwa.'""? Abbah Magaji yayi" "kasa'ke! jin irin maganganun da Bash din ke masa."" Katse shi yayi ta hanyar fad'in ""Kaga mu bar" "wannan maganar tukkuna domin yanzu mu ba itace a gabanmu ba ganin yarinyar nan da sanin halin da take ciki shine a gabanmu maganar aure dole bata taso ba.""" "Bash yace.""Naja'atu na nan kalau kamar yanda kuke fata sai dai kuma cikin da take dauke dashi ya" zube!!! "Abbah Magaji yace.""Subahanallahi garin ya akayi haka ta faru.""? Bash yace.""To muma bamu san ya" "akayi hakan ta faru ba dan kafin tazo garemu al'amarin ya kasance."" Cikin jimami da damuwa Abbah Magaji yace.""Allah ya mayar da alkairi ku kuma Allah ya saka muku da alkairi insha Allahu gobe da wuri" zan dauko hanya inaso ka bani cikakken address d'in inda zan same ku.'' "Bash yace.""Babu damuwa zan baka address din inda muke a garin jos zuwa anjima zan tura maka text sai" "ka duba.""Abbah Magaji yace"" To nagode sosai Allah ya saka da alkairi."" Sallama sukayi da juna kowa ya kashe wayarsa." Abbah Magaji jikinsa a sanyaye ya nemi numbar abokinsa domin ya sheda masa cewar anga matarsa "amma kuma baya tsammanin zai iya fad'a masa cewar yarinyar ta samu nasarar zubar masa da jiki, shi yanzu gabad'aya kunyar abokin nasa ma yake wallahi hakika da yasan Naja'atu zata basu kunya da baiyi ruwa da tsaki ba gurin ganin tabbatuwar auran! yanzu dai bashi da wani abinda zaice da abokin nasa dangane da abubuwan da suke faruwa sai dai kawai ya cigaba da bashi hakuri duk hukuncin kuwa da ya yanke a kan yarinyar hakan ba zaiyi masa ciwo ba saboda yasan itace ta janyowa kanta babu shakka ba kowane mutum ne zai yarda a zubar masa da ciki ba bai dauki mataki ba. A nutse suka gaisa da juna" kafin Abbah Magajin ya sheda masa cewar an samu labarin ganin Naja'atu a garin jos. Abbah Abbas ya nuna bai san komai ba sannan kuma ya nuna farin cikinsa sosai kana kuma yace kafin dawowarsu gobe lallai Abbah Magajin yayi kokarin zuwa domin daukota.Sallama sukayi da juna kowa na danne abinda ke cikin zuciyarsa. Mutanan kofar na'isa sunyi farin ciki sosai da labarin da Abbah Magaji yaje musu dashi na bayyanuwar "Naja'atu dake garin Jos ya kuma sheda musu da cewar su sake kwantar da hankalinsu yana tsammanin tana hannu nagari, amma kuma koda wasa bai sheda musu lalacewar cikin jikin da take dauke dashi ba." Alhaji Sama'ila dashi Baba malam sunyi farin ciki sosai kuma sun godewa Allah tabbas adduarsu bata fad'i a kasa ba. Jama'a mutanan unguwa sai shigowa baba Talatu suke a cewarsu wai sunzo taya ta "murnar bayyanuwar 'yarta, to ita dai sai ta rasa ma a'ina mutane ke samun labari tunda dai duk" abubuwan dake faruwa a tsakaninsu sukeyi amma abin mamaki kafin kice me jama'a har sunji suna shigowa gulma da munafurci! haka nan ta daure ta dinga kar'bar mutane wanda da yawa daga cikinsu gulma da munafurci ne ke kawo su ba wani abunba. To har duhun dare ya shigo Abbah Magaji bai ga text din da Bash yace zai turo masa. Sai bayan yaci "abinci ya nutsu tukkuna ya sake neman numbar Bash din kawai sai akace masa layin baya aiki yayi ta trying wayar na katsewa anty maryam dake kusa dashi a zaune tace"" Jikina baya bani cewar mutumin da ya kira ka mutumin kirki ne idan da gaske taimakon yarinyar zaiyi me yasa tun dazu da kukayi waya dashi ba turo maka cikakken bayanin idan zaka same shi ba, duba fa tun dazu kake kiran wayarsa na" katsewa. "A sanyaye Abbah Magaji yace""Naga alama yana so yayi mana wasa da hankalinmu ne kuma nima na" "soma zargin rashin gaskiya a tare dashi idan ba rashin gaskiya mai zai sa ya cire layinsa daga jikin wayarsa bayan yasan ga yanda mukayi dashi."" aunty maryam tace""Gaskiya da akwai alamun rashin gaskiya Allah dai ya kare yarinyar nan daga fad'awa hannun 'bata gari."" Cikin rashin jin dadi da tunanin" "neman mafita ya amsa da ""ameen"" shuru sukayi kowanne na tunani a cikin zuciyarsa" Da Asuba Abba magaji na dawowa daga massalaci ya kunna wayarsa ko minti biyu baiyi da kunnawa ba text din Bash ya shigo da sauri ya shiga yana dubawa! hamdala yayi a fili kana ya shiga kiran numbar Bash din...'Kin shiga wayar tayi kamar jiya yayi ta traying ta'ki shiga cike da mamaki yake kallon wayar tashi to anya kuwa guy nan bashi da wata 'boyayyar manufa? me yasa baya bari a sameshi a waya............Bash Layin kansa sunfi hamsin wayoyinsa kuwa sun kai koma saboda yanayin sana'arsa yasa baya barin layi ya kwana a wayarsa shikenan sanja layi yana basaja Bash ya iya taku shiyasa jami'an tsaro suka kasa kamashi. Koda aunty maryam ta shigo dakin sai ya sheda mata cewar ya samu text din da suke tsammani yanzu ta kar'bi wayar ta duba tana godewa Allah Abbah Magaji a gurguje ya shirya dan ko break ba tsaya yi ba ya fito aunty maryam ta rakashi har bakin motarsa tana masa fatan dawowa lafiya. Abbah Magaji kafin ya isa garin jos sai da ya kira Abbah Abbas ya fad'a masa ga halin da ake ciki A Lokacin suma jirginsu "na dab da sauka, cike da nuna komai ya wuce yayi masa fatan dawowa lafiya da kuma samun nasarar dawowa da yarinyar cikin koshin lafiya." Naja'atu tun kafin Abbah Magaji ya sauka a gidan take cikin wani irin yanayi na damuwa tana tunanin ko "da wane ido zata kalleshi, yanzu ne kunyar abunda tayi yake damunta hakika tasan ta aikata musu abunda zai zubar da kima da mutuncinsu a gari, to amma anata ganin ai sune suka janyo hakan ta faru" tunda sun kasa fahimtar daidai sunbi son zuciyarsu. Abbah Magaji daidai inda Bash yace ya tsaya anan yayi parking din motarsa ya fito da wayarsa tare da "neman numbar Bash din yana adduar Allah yasa ta shiga kada ya barshi a cikin mota ba tare da yasan inda zai nufa ba......Abin mamaki kiran farko Bash ya daga suka gaisa yace masa gashinan zuwa."" Abbah magaji ya kashe wayarsa yana jiransa gabadaya jikinsa yayi sanyi da yanayin halin munafurci da guy yake" nuna masa. Bash ya iso guri cikin wata lafiyayyar mota mai muguwar tsada.! Abbah Magaji kallo daya yayi masa ya tsinke da al'amarin guy sai kace wani kafuri yayi wata iriyar shiga "irin ta 'yan iska hatta da gashin kansa ya sanja masa hallita ya dawo browan ga wani irin aski dake kansa irin na gararrun turawan america. Cikin wata 'yar iskar tafiya ya nufi motar Abbah Magajin, sai yayi" saurin bude mota ya fito ya tsaya yana kallonsa har ya karaso! Cikin wani irin tantiranci ya bashi bayan hannu wai su gaisa! Abba Magaji ya girgiza masa kai had'e da "bashi tafin hannunsa da fad'in""Salamu alaikum."" Bash yayi 'yar dariya yasa hannunsa cikin nasa ya amsa da ""Amin wa'alaikasalam."" Abbah Magaji yace.""Ashe kasan da haka me yasa za kayi min gaisuwa irin ta" "kafurai.""?" "Dariya bash yayi yace.""Afuwa na riga na saba ne wallahi ya gida ya hanya ya ka baro iyalinka.""?" "Abbah Magaji yace.""Kowa lafiya kalau abokina amma banta'ba tsammanin ganin ka haka ba."" Bash ya" "sosa tarin sumar dake kansa yace.""Saboda me kace haka.""? Abbah yayi murmushi a nutse yace.""Yanda kake hausa yasa na fahimci cewar kai bahaushe ne kuma musulmi to amma ganin da nayi maka a yanzu yasa na d'ora ayar tambaya a kanka."" Bash yasa dariya yana kallon Abbah magaji kafin ya d'aga kafad'arsa sama yace.""Kamar yanda kake tsammani eh hakane ni musulmi ne gaba da baya cikin famliy na babu tubabbe dukkaninmu a cikin musulunci muka taso yanayin dressing d'ina da yawanci wasu abubuwa nawa ra'ayina ne hakan so ina ganin hakan bazai shafi addinina ba."" Abbah Magaji ya shiga girgiza kansa yana nazarin maganar. Bash yace.""Muje gida na sadaka da kanwarka amma zaka bar" "motarka anan zamuje cikin motata."" Abbah magaji yayi saurin juyawa domin kulle motarsa yana fad'in" """Babu damuwa hakan yayi.""" Abbah Magaji yana ta mamakin yanda Bash ke amsa wayoyin jama'a shi dai tunda ya zauna a cikin motar "ba zai iya irga iya adadin mutanan da Bash ya amsa wayarsu ba, Nazarin motar kawai yake yana mamakin irin kwalaben giyar dake ciki ga tarin takardun wiwi nan da sauran kayan maye duk da motar na kamshin freshnar hakan bai hana shi jin warin kayan mayen dake ciki ba, haka dai ya daurewa" zuciyarsa har suka isa gidan...... *MANZIR _ALWAFIR ABUJA * _*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci magungunansu babu almundahana a ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu ko wace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye da akwai gruops na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rijistar dasu to kukanki ya 'kare idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_ Mddbhrmbn47 *Bash* bai sauki Abbah Magaji a ko'ina sai a dakinsa Abbah Magaji ya samu guri ya zauna a nutse yana "bin dakin da kallo..Bash ya bude fridge ya dauko masa ruwa da lemo masu sanyi a ajiye a gabansa Abbah magaji yace.""Nagode."" murmushi kawai yayi ya juya ya fita daga dakin ba tare da yace wani abuba. Abbah Magaji bai dauki lemon yasha ba dakin kawai yake kallo sa'ko da lo'ko gabadaya ya tsargu da yaron dan daka gani ba mutumin arziki bane! a hankali ya dauki ruwa ya bude ya d'an sha ya" "mayar ya ajiye, jin kira ya shigo wayarsa yasa yayi saurin dubawa abokinsa ne Ya kara wayar a kunnansa had'e da yi masa sallama, Abbah Abbas ya amsa a nutse yake sheda masa cewar sun sauka yanzu." "Abbah magaji Yace masa shima yanzu haka yana inda yake tsammanin samun Naja'atun. Abbah Abbas yace.""To Allah yasa adace.""Sallama sukayi da juna Abba magaji na kashe wayarsa Bash da Naja'atu da Munira suka shigo dakin, Naja'atu sai 'buya take a bayan Bash tana sinne kanta kunyar hada ido take da dan uwan nata...Shi kuwa Abbah magaji tunda suka shigo yake binta da kallo yana mamakin irin kwalliyar da tayi wato su suna can hankalinsu a tashe ita tana nan tana ado da kwalliya..Kafin ya ankara yaga Bash ya rike hannunta ya zaunar da ita a kusa dashi. ya bisu da wani irin kallon mamaki! kujera ce 1sitar amma sun nani'ka da junansu. Kunyar hakan yasa ta sunkuyar da kanta 'kasa murya na rawa take gaishe shi shima a sanyaye ya amsa ganin abinda yafi karfinsa to hakan me yake nufi? ina kuma Naja'atu ta baro auranta? bashi da mai bashi amsa sai kawai ya zuba mata ido ya kasa cewa uffan! ganin irin kallon da yake mata ne yasa jikinta yayi sanyi sai ta fashe da wani irin kuka hade da had'a hannuwanta guri daya tace""Abbah magaji dan Allah kada kuga laifina dangane da faruwan wannan al'amarin wallahi ba laifina bane laifinku ne tunda tun farko na fada muku cewar bana sonsa bana sonsa kuka kasa ganewa har sai da kuka daura min aure dashi sabida haka yanzu duk wani mummunan abu daya biyo" "baya kune kuka janyo ni bani da laifi.""" Abbah Magaji maganganun da Naja'atu takeyi sunyi masa tsauri sosai har hazar yanzu ya kasa "magantuwa sai dai ido kawai yake binta dashi mamakinta na kashe masa jiki...Bash ya dan rungume kafadarta yana rarrashinta wai tayi shuru ta daina kuka komai yazo karshe insha Allah, Abbah Magaji yana zaune yana kallon ikon Allan Bash sai matse masa 'kanwa yake yi a gaban idonsa. Ransa a 'bace ya" "buga musu tsawa da fad'in ""Kai ka kiyaye fa wannan yarinyar matar aure ce musulunci bai baka damar" "ta'ba matar da bata kaba."" Bash ya wani sha kunu yana kallon Abbah Magaji da fad'in ""A shirye nake dana d'aukaka 'kara akan auran rashin adalcin da kukayiwa wannan yarinyar wannan ai son zuciya ne me" yasa wai mafi akasari mutumin kano baida wayewar kai ne? meye amfanin auran dole da kukewa "'ya'yanku tunda wannan yarinyar tace bata son mutumin nan to ya saketa mana dole ne.""? Abbah magaji yaji wani irin gumi na yanko masa bakinsa na rawa yace."" Waye yace maka auran dole akayi mata kuma kai meye ya shafeka da shiga cikin al'amarin da har kake maganar d'aukaka 'kara shin kasan waye Alhaji Abbas kuwa.""? Bash ya zakud'a kafadarsa yace""Sanin waye Alhaji Abbas bashi ne a gabana ba abinda yake gabana anan shine ya saki Naja'atu na aureta shine abinda yake a gabana idan kuna ganin zaku yafe Yarinyar nan saboda ta bujirewa umarninku to ni Bashir zan ri'keta har 'karshen rayuwarta ta duniya."" Abbah Magaji yace.""Inaso ka fad'a min meye manufarka akan yarinyar nan.""? Kai tsaye yace.""Munufa ta ta alkairi ce inaso in aureta bayan kun warware wannan auran da kuka 'kulla."" Abbah Magaji yayi shuru yana ta nazarin maganar Bash din *Aure! Aure! Aure!* wane Uba ne zai dauki 'yarsa ya bawa wannan lalataccen auranta duk wanda zai ga Bash mutukar mai hankali ne zaiyi kokarin nesanta kansa dashi saboda sam bai cancanta ma ka hada hanya dashi ba ballantana gaisuwa ta haka" dashi! Ya dago kanshi yana kallon Bash din gabadaya yanayinsa ya nuna yana cikin tashin hankali da damuwa "yace.""Wannan maganganun da ka fada min suna nuna cewar da sanya hannuka gurin zubewar cikinta kun hada baki da ita kun zubarwa da abokina ciki domin ku cimma wata manufa taku ko.""?" "Bash yayi murmushi hade da sosa kanshi yace.""Bana munufarci Alhaji idan da sa hannuna gurun" "zubewar cikin nan da tuni na fad'a maka sabida nasan da kai da abokin naka babu wani abu da kuka isa kuyi dan haka ka ma daina wannan maganar kafin Naja'atu tazo gurinmu cikinta ya zube a wani guri."" Abbh magaji ya shiga goge gumi yana kallon Naja'atu yace.""Yanzu meye ribarki ta zubar da cikin halak Naja'atu kin manta waye Alhaji Abbas a tare dake ko? Abokina Abbas bai cancanci wannan sakayyar" daga gurinki ba. "Tana kuka tace""Wallahi ni ban zubar da cikin nan ba da kansa ya zube amma ni ban zubar ba."" a zabure!" "kafin kowa ya ankara ya kai mata wani bahagon mari! tasa kuka tana sake 'boyewa a bayan Bash! Abbah magaji ya mike jikinsa na kyarma! yace.""Yaushe kika zama 'yar iska Naja'atu irin tarbiyar da akayi miki kenan? ashe kina so ki zubar mana da mutunci a duniya da auranki kike rungume wani namiji! zaki fito" "daga nan ko sai na sumar dake a gurin nan."" Yakarasa maganar cikin hargagi!!!" "Bash ya mike tsaye da sauri ya janye shi daga gurin ya zaunar dashi kan kujera yace.""Alhaji duk wannan" "hargagin da kake ba zai taimake ka akan komai ba kawai kabi komai a sannu a hankali sai a samu maslaha na fada maka wallahi sai inda karfina ya kare akan wannan al'amarin dan ina son naja'atu itama tana sona babu wanda ya isa ya hanamu mallakar junanmu shi wannan tsohon mai zuciyar yara shi nake so ya yankewa kansa hukunci tun kafin a'lkali ya 'kira shi.""" Abbah Magaji yaji wani irin kuttun bakin ciki da takaici ya tokare masa a makoshi tabbas zai zare hannunsa daga cikin al'amarin yarinyar kodan ya tsira da mutuncinsa gurin abokinsa... ya kalli Bash din "da idanunsa wanda sukayi jajawur yace.""Yanzu zaka bani yarinyar nan ko kuwa ba zaka bani ita ba.""?" "Bash yace."" Sai abinda tace idan tana da ra'ayin bin ka gatanan a zaune ta fada maka.""" Abbah magaji ya tsirawa Naja'atu ido yana so yayi mata magana amma tsabar bacin rai ya hanashi cewa komai... "Kallonta kawai ya gaza furta kowace kalma ita kuma ganin haka yasa tace"" Ni bazan koma ba har sai na" tabbatar da cewar babu auran kowa a kaina sannan zan bika idan na koma zaku iya tursasani na koma gidan Wanda bana so Abbah magaji ya dauki wayarsa ranshi a bace ya shiga neman numbar abokinsa lokacin yana kofar na'isa tare da mahaifinsa suna tattauna maganar yana kuma sanar masa da irin hukuncin da ya yanke lokacin shi kuma Mahaifin nasa yake nuna masa ya janye hukuncin da yanke hakan bai dace ba. Wayar abokin nasa ya dauka yaji muryarsa cikin bacin rai yana sheda masa abinda "ke faruwa... Kai tsaye yace ya bashi Naja'atun zasuyi magana da ita, da yake hands free ne Bash yana jin muryar Abbah Abbas din yana magana, Abbah magaji ya mikawa Naja'atu wayar da fadin ""Gashi yana so yayi magana dake......'Kin kar'bar wayar tayi Bash ya kar'ba ya kara mata a kunnanta. jin muryar Abbah" "Abbas din yana magana yasa gabanta ya tsananta fad'uwa kiran sunanta yake ta gagara amsawa sai sheshshekar kukanta yake ji a kunnansa. A nutse yace."" Kince ba zaki dawo gida ba sai anyi miki abinda" "kike so ko? shuru tayi ba tace komai ba. Ya dan sauke ajiyar zuciya yana sake jin wani irin tsanarta na d'arsuwa a zuciyarsa yace.""Kada ki damu tun ranar da kika tura min text na datse igiyar aurena guda daya dake kanki ina fatan Allah yasa hakan shi yafi alkairi kiyi hakuri ki dawo gida saboda samun kwanciyar hankalin iyayenki."" Jin abinda yace yasa taji wani sanyi na saukar mata a zuciya shima bash dake kusa da ita murmushi yayi kawai ya cire wayar daga kunnanta ya kashe ya mikawa me ita. Abbah" "magaji rasa bakin magana yayi ya dinga binsu da kallon takaici Bash ya mike da fadin ""Bari nayi wanka" "ina tsammanin tare zamu tafi inaso naje na nuna kaina a matsayin wanda zai auri Naja'atu."" Abbah magaji uffan bai ce masa ba har ya shiga toilet dinsa. Naja'atu ita da Munira suka fita daga dakin cike" "da farin ciki bukatarsu ta biya, shi kuwa bayan fitarsu daga dakin guri guda ya tsirawa ido kawai yana kallo babu shakka hukuncin da abokin nasa ya yanke baiyi masa dadi ba ko kadan! to amma yana adduar Allah yasa haka shine yafi alkairi Naja'atu kuwa ya tabbata da cewar sai ta girbi abinda ta shuka da hannunta yanzu shi dai zaiyi kokarin sadata da iyayenta shikkenan sai ya zare hannunsa daga kanta idan Allah ya kaddara auranta da Bash to shi kam dan kallo ne babu abinda ya shafe shi duk tsuntsun" daya ja ruwa shi ruwa kan doka. Abbah magaji yana zaune Bash ya kintsa jikinsa cikin sabuwar shadda galila mai kalar sararin samaniya "(sky blue) dinki tazarce da dogon hannu mai link yasa hula irin ta kanawa sai kace wani mutumin arziki yayi wani irin kwarjini da kamala, Abbah magaji na zaune yana ta mamakinsa babu shakka yaron ya shirya tsaf domin zuwa ya yaudari su baba malam to idan ba hakaba meye nasa manyan kaya harda hula, Bash na daura agogo ya kalli Abbah Da murmushi a fuskarsa yace.""Nasan duk wanda ya gan ni cikin famliy naku zai yaba dani da cancanta ta a matsayin wanda zai auri Naja'atu ina fatan kai ma a" "matsayinka na makusancinta ka sanya mana albarka a cikin al'amarin.""" Abbah Magaji na kallon rashin kunya da tsabar jahilci shikkenan daga anyi saki kuma sai a shiga neman "aure ai ya bari yarinyar tayi iddah tukkuna. Yace.""Bashir da alama baka da ilimin addini waye yace maka" ana neman aure cikin iddah ai ka bari yarinyar tayi iddah tukkuna in yaso sai kayi wata magana. Bash "yace""A'a da zafi zafi akan bugi karfe alhaji gwara naje na gabatar da kaina in yaso koma meye sai ya biyo baya."" Abba magaji ya bishi da ido cike da tsantsar mamakin maganarsa gaskiya jahilci bai yi ba." Abbah Magaji motarsa ya shiga a maimakon Naja'atu tayi masa kara ta shiga motarsa sai ta nuna jin tsoransa yana kallo ta zauna gaban motar Bash ko kallonsa ta'kiyi takaicin haka yasa yaja motarsa da karfi... ya bar gurin.. Bash na murmushin samun nasara yaja tasa motar suka dauki hanya. sai da "sukayi nisa sosai ya kalleta yace.""Baby wannan dan uwan naki fa na fahimci baya k'aunar alaqa ta dake ko kad'an!."" murmushin takaici tayi tace.""Bash bana tsammanin Abbah magaji zai kaunace ka dan shine babban abokin Abbah Abbas to kaga kuwa dole ya tsaneka."" Cike da rashin damuwa yace.""Hakan bai dame ni ba mutukar kina sona iyayenki sun amince dani ai bukata ta biya."" Jin abinda yace yasa gabanta ya fadi addua ta shigayi kan Allah yasa su baba malam su amince mata da auran Bash dan yanxu" gabadaya shine babban burinta. Alhaji Sama'ila da Baba Malam dashi uban gayyar ne a zaune a guri daya suna tattaunawa kan al'amarin da yake faruwa. Alhaji Sama'ila yana ta nuna rashin jin dadinsa dangane da hukuncin da d'ansa ya yanke a kan naja'atu shi kuma Baba malam yana nuna masa hakan ba laifi bane dan Abbas ya saki naja'atu domin samun maslaha ga junansu ya kuma nuna masa shi bai ji takaicin faruwar hakan ba dan dama ya riga ya barwa Allah al'amarin yana ganin tunda hakan ya kasance to shine alkairin Dukaninsu suna zaune suna jiran tsammanin dawowar Abbah magaji tare da Naja'atun To Sai daf da magariba suka "iso, Abbah magaji bai saurare su ba ya gyara parking na motarsa ya fito ya nufi massalacin dake jikin gidan Alhaji Naja'atu da kyar ta iya fitowa tana ta 'boye kanta a cikin mayafi gabanta kuwa sai faduwa" "yake...Bash ganin Abbah magaji na alwala a cikin massalaci sai shima kamar gaske ya nufi inda yake Naja'atu kuwa tsayuwa tayi ta rasa ina zata shiga gidan Alhaji ko idan baba malam Munira tace""Wai" tsayuwar me mukeyi ne? haba duk kinbi kin damu kanki dan Allah ki daina jin tsoron abinda zai faru "babu fa wanda ya isa yayi miki abinda Allah be miki ba ki saki jikinki dan Allah.""" "Hawaye ta d'an goge tace""Mu shiga gidan Alhaji munira ba zan iya shiga gidanmu ba ina jin tsoron Baba" "Talatu da Abbah Magaji kada ya shigo ya doke ni."" Munira tace""To muje gidan Alhajin tunda kinfi amincewa da nan."" Kai tsaye suka nufi gate gidan tana tafiya tana hard'ewa saboda matsatstsen siket d'in Munira dake jikinta gashi ba hijab bane mayafi ne a jikinta shiyasa duk ta tsargi kanta! Abbah Abbas da Alhaji sune suke kokarin fitowa daga gidan Naja'atu jin 'kamshin turaransa yasa ta zabura! da sauri ta matsa gefe tana kauda kanta! Abbah Abbas karaf! idanunsa ya sauka a kanta duk da ta 'boye fuskarta" hakan bai hanashi ganeta ba kallon zatin jikinta kawai ya fahimtar dashi itace! cike da mamaki yake kallonta kwana uku kacal a jos ya mayar da ita watsatstsiya wane irin suttura ne wannan a jikinta sun fito mata da jikinta! da sauri ya kauda kansa ya wuce domin shiga massalaci Tana ganin wucewarsa ta "zube 'kasan gurin tana gaishe da Alhaji dake kokarin wucewa dan shi sam be ganeta ba, Jin muryarta yasa yayi saurin juyuwa yana amsawa da fad'in ""Naja'atu kece.""? murya na rawa tace"" Eh."" yace.""To masha Allah ku shiga cikin gidan mu zamu shiga massalaci domun gabatar da sallah."" A sanyaye tace ""To"" tana kokarin mikewa Alhaji kasa barin gurin yayi har sai da yaga sun shiga gidan tukkuna ya nufi" massalaci zuciyarsa sam babu dadi dangane da faruwar al'amarin. *Littafin na kudi ne..!* Koda zaki ganshi a gruops to na sata ne idan kina bukatar biyan kudin karatu toga yanda abin yake Vip group #600 normal group #300 account 0542382124...Binta umar gtbank..idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *MANZIR _ALWAFIR ABUJA * _*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci magungunansu babu almundahana a ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu ko wace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye da akwai gruops na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rijistar dasu to kukanki ya 'kare idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_ Mddbhrmbn49 Halisa da Yaya Ramlatu ne a zaune a palon Hajiya sai hira suke cikin nishadi sunayi suna ciye ciye kana "kallonsu zaka fahimci cewar suna cikin walwala da farin ciki...Hajia Abu lokacin ta hau sama domin daura alwala su kuma bayan barinta gurin ne suka tsiri gulmar abinda ya faru inda Yaya Ramlatu ke fad'in""Ai wallahi Halisa na sake gazgata al'amarin mutumin nan da 'yar shagamu ta kai mu gurinsa kinga ni dai duk abinda ya fad'a zai faru gashi ya kasance gaskiya kiyi kokarin siyawa 'Yar shagamu turaman atampopi muje tare dake gidanta mu kai mata domin mu sake nuna mata jin dadi da farin cikinmu sabida kin san hausawa nacewa dan towon gobe ake wanke tukunya nan gaba zamu iya zuwa mu sake" "neman wata alfarmar gurinta shiyasa nake so ki kyautata mata sosai dan itama taji dadi.""" Halisa na shirin yin magana su Naja'atu suka shigo palon..Naja'atu ganin Halisa da Yaya Ramlatu a zaune "yasa jikinta yayi sanyi da kyar suka shiga palon suka zauna cikin kokarin aro jarumta tace""Anty Halisa sannunku Yaya Ramlatu Ina wuni.""? babu wanda ya amsa mata a cikinsu Halisa sai binta da ido take tana ta'be bakinta, ita kuwa Munira ganin Naja'atu tayi musu magana basu amsa ba yasa ta kama kanta 'kafarta ta d'ora kan d'aya tana taunar cingum had'e da duba tamfatsetsiyar wayarta. Yaya Ramlatu ta" "ri'ke bakinta tace""Oh! ikon Allah ke kuma Naja'atu garin yawon karuwancin naki kika samo wannan mara kunyar yarinyar daka ganinta 'yar isaka ce da wasu idanunta a tsaye irin na marasa kunya.""!Munira ta zubawa Yaya Ramltu idonta ranta a 'bace da jin irin mugwayen kalaman da take jifanta dasu. Za tayi magana Naja'atu ta rufe mata bakinta tace""Dan Allah kada ki kulata ki kyaleta duk wanda ya wulakanta wani kansa ya wulakanta."" Halisa tace""Ke Naja'atu Yaya Ramlatu kike kokarin gayawa magana? ai gaskiya ta fad'a a kanki dake da kawarki idan ba yawon karuwanci kika tafi ba to me ya had'a ki da wannan me wankakken idon."" Munira ta nuna Halisa da hannu tace""Wallahi kika sake kirana da wannan kalmar sai na wanke ki da mari zan nuna miki tsageranci na yanzu."" Halisa ta ri'ke bakinta tana kallonta tace""Sai ki mareni mara kunya kawai. Naja'atu tace""Kinga Halisa mu ba tashin hankali ne ya shigo damu gidan nan ba saboda haka dan Allah ki fita daga sabga ta kada ki sakeyi min magana tunda dai yanzu bani da al'aka dake."" Da sauri Ramlatu tace""To dan ubanki tashi ku fice mana daga gida tunda da bakin ki kin fad'a baki da al'aka damu ubanki kika shigo kiyi mana a gida."" Naja'atu jin zagin yayi yawa yasa ta fashe da kuka da fad'in ""Ki daina zagina dan banga abin zagi ba anan."" Ai kamar 'kara tunzura ta take ta dinga zabga mata zagi tana ambato sunanan Baba Malam tana cusa masa ashar! Munira tace""Amma ke kam anyi tsuhowar banza."" Yaya Ramlatu ta fusata ta fitar da hannu ta tsinka mata mari wanda yayi dai-dai da sakkowar hajia daga sama kuma duk akan idonta komai ya faru Cike da bacin rai ta zauna tana" "kallon Ramlatu tace""Yanzu meye amfanin abinda kikayi da girmanki da komai kina shiga sabgar yara.""" "Sai kawai ta fashe da kuka da fad'in"" Wallahi hajia raina ne ya 'baci! shiyasa na kasa daurewa wai" yarinyar nan itace take fad'a mana cewar dasa hannunta gurin zubewar cikin Naja'atu ko kunyar idona ba taji ba take fadin haka ita kuma Naja'atun na sake tabbatar mana da gaskiyar magana harda cewa wai yanzu bata da wata al'aka damu tunda ta rabu da auran jaraba ciki kuma ta zubar duk abinda zamu yi sai "dai muyi.""" Naja'atu da Munira kasa magana sukayi suna mamakin iya sharri na matar sai kuka take tana fyatar hanci kamar gaske. Halisa kan dariya kawai take cikin zuciyarta itama mamakin iya sharri na ramlatun take. "Hajia Abu ta kalli Naja'atu tana so tayi magana sai ta riga tana kuka tace""Wallahi hajia ba haka bane" "sharri ne ni ban sha wani abu domin na zubar da ciki ba da kansa ya zube amma wallahi duk cikin magabar da Yaya ta fad'a babu gaskiya a ciki."" Ya Ramltu tace""Ubanki ne yake miki karya kaji ni da mara kunyar yarinya wa zaki yaudara? ashe har kin manta irin maganganun da kika fad'awa Salim to idan ke" "kin manta mu bamu manta ba munufuka kawai kin bar zuriarmu har abada.""" "Hajia tace""Ya isa dan Allah duk zancan tashin tashina bai taso ba abinda ya faru ya riga ya faru kuma" zamu ajiye shi a matsayin kaddara haka Allah ya hukunta sabida haka kada na sake jin kin zagi naja'atu ko kin fadi mummunar kalma a kanta Naja'atu bata isa ta tsarawa kanta abunda take so ba komai ya faru da rayuwarta kaddara ce ciki kuma da ya zube dama can Allah ya hukunta ba zai taka kasar duniya ba "munafatan Allah yasa haka shi yafi alkairi.""" Yaya Ramlatu 'kus! tayi dan ba tayi tsammanin hajiyan zata goyi da bayan yarinyar ba ganin yanda ta "nuna 'bacin ranta lokacin da taji labarin zubewar cikin..Halisa da yake neman gindin zama take a gurin hajiyan sai ta 'kaskantar da kanta kamar mutuniyar kirki tace""Wallahi kuwa hajia ai nima haka nace duk abubuwan da suke faruwa kaddara ce Allah yasa Auran Abbah Mufida da yarinyar ba zaiyi tsayi ba shiyasa duk haka ta faru amman mu munso Auran yayi albarka ya zama mutuwa ce zata rabasu kamar" "yanda ta ratsa tsakaninsa da Halimatu.""" "Hajia tace""Ke da yake mai hankali ce kin gane yanda lamarin ubangiji yake amma ita waccan da" "girmanta da shekarunta tana abubuwa irin na yara.""" Yaya Ramlatu sunkuyar da kanta tayi kunyar duniya ta isheta hajia ta kunyatata gaban yara kananu ita kuma halisa da yake ta fita dubara ta wanke kanta kasa d'ago kanta tayi dan tana jin kunyar had'a ido da yaran Munira kuwa sai dariya take 'boyewa taji dadi sosai da hajiyan tayi wa matar wankin babban bargo. Sai bayan sun fito daga sallahr isha'i ne suka samu zama gabadayansu a kofar gidan baba malam da yake "dogon dakali ne mai fadi da tsayi kuma yana sawa kullum a share a shimfida katuwar tabarma saboda masu daukar darasu! Suka zazzauna harda Bash da yake ta wani sunkuyar da kansa, cikin nutsuwa yabi kowansu yana mik'a masa hannu har yazo kan wanda yake tunanin shine abokin adawarsa Abbah Abbas ya rike hannunsa suka gaisa cikin kulawa da mutunta juna sabida shi bai san abinda ke tsakaninsa" da tsohuwar matar tasa ba to koma dai ya sani bashi da abinda zaice tunda ba huruminsa bane. A nutse "Bash yayi musu bayanin yanda akayi Naja'atu tazo garesu ya kankantar da kansa sosai ya nema mata afuwa a gurinsu gami da cewar su dauki dukkanin abubuwan da suka faru a matsayin qaddara sannan kuma kodan gaba su guji yiwa 'ya'yansu auran da basa so ko dan gujewa faruwar matsala makamciyar wannan."" Baba malam da Alhaji sai godiya suke masa dan gabadayansu sun yaba da hankalin yaron kuma abinda yayi musu ba zasu ta'ba mantawa dashi ba shiyasa suke tayi masa godiya tare da yiwa iyayansa addua. Cike da jin dadi Bash yake amsawa yana shafa wuyansa hade da sunkuyar da kansa irin" na munafukai Abbah Magaji da Abbah Abbas kallonsa kawai suke baran Abbah Magaji da yasan waye "Bash d'in shiyasa bakinsa ya mutu yakasa cewa komai yana jin yanda Bash yake ta basu labarin waye mahaifinsa, ba'aje da nisa ba suka gane mutumin tunda gabadayansu masu sauraran redio ne shi kuma Aminu dan Jarida yayi suna sosai akan aikinsa kuma yayi aiki a gidajen redio da dama shiyasa su ganeshi" nan take. "Alhaji yace.""Duk da bamu ta'ba ganin mahaifinka ido da ido ba amma muna sauraran muryarsa hakika" "mahaifinka ba 'boyayye bane kuma munji dadi da yarinyar ta kasance a gurunku idan ka koma gida kayi wa mahaifinka godiya a bisa karamcin da akayi mana."" Bash yace."" Ya kwana biyu baya gida aiki ya kaishi amuruka amma idan ya dawo zan fad'a masa sa'kon gaisuwarku."" Baba malam yace to babu damuwa Allah ya dawo dashi lafiya."" Gurin ne yayi shuru na minti biyu kowa na sa'ke-sa'ke a cikin ranshi, Bash ya gyara zamansa kansa a 'kasa yace""Malam ina neman alfarma a gurunku idan zan samu."" Da sauri Baba malam yace.""Wace irin alfarma kake nema yaro."" ? Bash yace.""Inaso idan Naja'atu ta 'kare iddah na aureta idan babu damuwa."" Baba malam yayi murmushi yana kallon Alhaji yace.""Kaga mahaifinta nan dashi za kayi magana."" Bash ya kalli Alhaji yana dan murmushi Abbah magaji mikewa yayi had'e da" "zura takalminsa ya mikawa abokinsa hannu da fad'in ""Zan nufi gida Sai ka shigo kenan."" Abbah Abbas yace.""Ka zauna a 'kare maganar da kai mana."" Girgiza kansa yayi yace.""Tunda duk kuna gurin ai babu matsala ina fatan Alheri a cikin al'amarin."" Baba malam da Alhaji suka amsa da ameen.'' Shi kuwa Abbah Abbas ido kawai ya zubawa Bash yana kuma sauraran amsar da Alhajin zai bashi Alhaji Yace.""Babu" "komai Bashir shi aure rabo ne idan Allah yasa wannan yarinya matarka ce sai kaga ka aureta idan kuma baka da rabo sai kaga wani ya aureta amma dai musulunci bai baka damar tunkararta a yanzu ba ka bari tukkuna ta kare iddah sai ka shiga layin zawarawan ta."" Bash yace.""To nagode sosai Alhaji nagode da karamci ina kuma addua Allah yasa Naja'atu rabona ce."" Suka amsa da ameen banda Abbah Abbas da yake jin takaici na neman dagargaza! masa zuciyarsa mtwsss! mi'kewa yayi dan ganin zaman ma da yake a gurin bashi da wani amfani ya daure ya bawa iyayan nasa hannu da fad'in ""Shima zai wuce gida domin yaje ya huta, Bash ya bashi hannu da fad'in "" To Alhaji a huta gajiya nagode sosai da kulawarku a kaina."" Abbah Abbas ya daure ya amsa da babu damuwa kai ma ina maka fatan alkairi tare da adduar sauka" "lafiya.""" Kai tsaye cikin gidan Alhaji ya nufa yana tafiya tamkar zai tsaga 'kasa sabida yanda yake taka ta da karfi! wai! kishi ne ko me? Koda ya shiga palon samun Naja'atu yayi da Munira sai ciye ciye suke na irin tsabar da sukayi ta saudia sun sake suna hira harda shewa ga Halisa a zaune a gefe kamar wata mujiya!!! dan tuni Yaya Ramlatu ta tafi.......Saboda ba kunyar da hajia ta bata shi yasa ta kasa zama sai ta tattara tsarabarta ta 'kara gaba cike da takaicin abinda hajiyar tayi mata..... Halisa ta tsurawa tv ido kamar mai kallo amma ita kadai tasan takaicin dake cikin zuciyarta gefe guda kuma tana mugun mamakin d'aurin gindin da yarinyar take dashi a gurin hajia.........Naja'atu tunda ya shigo palon bakinta ya mutu sunkuyar kanta 'kasa tayi Munira nata magana amma bata tanka mata ba..To itama Munirar kamshin lafiyayyan turaran da taji ne yasa ta kalli bakin 'kofa....Ta tsira masa ido tana tunanin inda tasan shi...Abbah Abbas ne mai zuwa musu visiting makaranta sai taga kamar ya dawo matashi gabad'aya mutumin ya'ki tsufa! wallahi bata ta'ba tsammanin zata ganshi hakaba ta dauka za taganshi furfura ta baibaye masa fuskarsa sai taga akasin haka ya sake zanzarewa yayi wani fresh dashi...Gaskiya ya burgeta tana son namijin da yake kula da kanshi kuma dan gayu. Muryarsa ce ta katse musu tunaninsu inda yake magana da Halisa "yana tambayarta ina Hajia? Halisa na fari da ido tace""Bata jima da hawa sama ba."" Ba tare da yace komai ba ya nufi saman...Gabad'ayansu har ita Naja'atun suka bishi da kallo Halisa ta juyo tana kallonsu tare" "da ta'be bakinta tace""Sai dai kallo daga nesa dan wutsiyar raqumi ta riga tayi nesa da 'kasa komai na babba yafi na yaro! wannan dai mijin mace d'aya itace Halisa.""! Munira ta d'age! girarta tana murmushi had'e da girgixa kanta tace""Wallahi kiyi mana shuru da bakinki idan ba hakaba ki raina kanki ko yanzu mukayi ra'ayin komawa zamu koma har kike wani cika baki Ji wata magana dan Allah ""Wai komai na" "babba yafi na yaro hahahaha to me zaki nuna mana.""? tafada tana she'ka mata dariya hade da nunata da hannu."" Halisa tace"" Eh ai dole nayi magana naga kun bishi da kallo sai kace zaku cinye shi."" Naja'atu ta tab'e bakinta tana girgiza kai tace""Dan Allah Munira kiyi mata shuru ni bana son damuwa wallahi so nake ma su tafi su bamu guri mtwws! Halisa tace ""Aikin banza kawai ki daina dena za'kewa a gidan da baki da gado dashi sai kace gidanku sai wata fuffuka kikewa mutune."" Naja'atu shuru tayi bata tanka mata ba, Munira kuwa ta mayar da Halisa kamar mahaukaciya sai dariya take mata, Halisa ta cika tayi fam fam! takaicin ya isheta, aikuwa yana saukowa wai zata kai mai 'kara! ya kuwa buga mata razannaniyar tsawar da tasa ta dauki jakarta babu shiri tayi waje! bayanta yabi ba tare da ya kalli iskar" da ta d'ebo su ba. *Littafin na kudi ne...!* Koda zaki ganshi a gruops na tasa ne idan kina bukatar ki biya kudin littafin ga yanda abin yake Vip group #600 normal gruop #300...account 0542382124...Binta umar gtbank...Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *MANZIR _ALWAFIR ABUJA * _*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci magungunansu babu almundahana a ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu ko wace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye da akwai gruops na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rijistar dasu to kukanki ya 'kare idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_ 50 "Bayan fitarsa daga palon Munira tace"" Ammafa k'awata banyi tsammanin ganin Abbah Abbas haka ba" "wallahi na d'auka zanga ya 'kara tsufa gami da furfura sai naga kamar ma 'kuruciya aka 'kara masa yanzu dan Allah waye zai dauka waccan matar matarsa ce sam basu dace da juna ba."" Naja'atu ta kalleta da mamaki a tare da ita tace""Ban gane inda maganar ki ta dosa ba Munira kina kallon mutum da girmansa da shekarunsa amma kike wata maganar 'kuruciya kawai dan dai ma'abocin ado da kwalliya ne shiyasa tsufansa baya fitowa.'' Munira tace""Nima ai abinda nake nufi kenan ba wani abuba. *(Kunji Munira ta" waske taga Abbah Abbas ta qyasa shine ta kasa yin shuru hum!)* Shuru sukayi na minti biyu kafin kira ya shigo wayar Munira koda ta duba sai taga Bash ne da sauri ta "dauka tana tambayarsa inda yake, yace yanzu haka yana masaukinsa yaje ya kama daki a hotel saboda haka gobe da wuri ta shirya su zasu tafi a 'karshe yace ta bawa Naja'atu wayar zasuyi magana. Cike da" "zumudi ta kar'bi wayar ta kara a kunnanta murya 'kasa-'kasa tayi masa sallama Bash jin muryarta a narke ya sake tayar masa da feelings ya rungume pillow hade da matse shi a kirjinsa yana ji tamkar ita ya rungume a jikinsa, ya shiga yi mata bayanin yanda sukayi dasu baba malam Naja'atu ta nuna farin" cikinta sosai da sosai dan bata ta'ba tsammanin iyayen nata zasu amince mata da auran Bash din ba. Sosai ta saki jikinta dashi a waya suka dinga hira tana kyalkyala dariya hade da sake jin tsantsar "kaunarsa na ratsa jikinta, Hakika Bash ya isa soyayya kuma yasan matakan sace zuciyar mace shiyasa lokaci guda ya sace raunanniyar zuciyar Naja'atu da salon soyayyarsa. Nan Hajiya ta sauko ta samesu" ta tana waya tana jin muryar hajian suna magana da Munira amma tsabar shau'kin hirar soyayyar da suke da Bash yasa ta gagara juyowa ballantana ta fahimci maganar da hajian take. Munira mikewa tayi ta nufi wani daki dake cikin palon nan hajia tace su shiga su kwanta Naja'atu motsi kasa yi domin bata so ko kadan tayi missing din kalma guda dangane da kalaman da Bash ke mata. Munira har tayi wanka ta shirya jikinta naja'atu bata shigo ba to itama duk dare sun saba waya da "Muktar dinta tasan yana can yana neman wayarta zaiyi tunanin koda wani take hira sai ta fita palon tace"" sarkin soyayya yana da kyau nima ki bani wayar naji muryar masoyina."" Cike da shagwaba tace""Sweetie kaji Munira tana min gori akan waya ko. Bash yayi wata birgima akan bed din da yake" "kwance yasa hannu kan katuwar jijiyarsa data mike cikin sar'kewar murya yace.""Darling bata wayarta" "insha Allah gobe kafin mu tafi zan baki daya daga cikin wayoyina sai mu dinga gaisawa da juna kafin Allah ya mallaka mana junanmu."" Tace""To godiya nake sweetie Allah ya kara mana kaunar junanmu."" a sar'ke yace.""ameen babyna ammafa yau da kyar zan iya bacci dan gabadaya kin tayar min da sha'awa gabana ya mike sosai ke kadai nake bukata beb."" Wani irin yanayi ta shiga jin abinda yace sai itama taji tana sha'awar kadaicewa dashi lumshe idonta tayi a sanyaye tace"" Nima ina cikin kewarka Bash sai dai muyi hakuri da juna har sai sanda Allah ya mallaka mana junanmu."" Bash ya sauke ajiyar zuciya yana sake danne joystick dinsa dake ta faman motsi tana kara hawa yace.""Yanzu ba zaki taimaka min da wani abuba ki dauki hoton nononki yanzu ki turo min dashi ta whasap din Munira nasan kallon breast dinki zai" "sanya na samu sassauci.""" "Gabanta ya tsananta faduwa jin abinda yace murya na rawa tace""Kayi hakuri Bash ba zan iya ba ka bari" "na zama mallakina zakiyi duk abinda kake so dani."" Sai ta kashe wayar tana kallon munira wacce ke tsaye tana jin muryar bash din sama sama da abinda yake bukata a gurin kawarta...Tace""Haba Naja'atu meye dan kin tura masa brest dinki kece fa kika tayar masa da hankali ba sai kiyi kokarin kawo masa nutsuwa ba wallahi tun yanzu ki kama zuciyarsa a hannuki dan na fada miki tarin 'yan matansa idan kika sake kika" zauna gardama to zaki sha mamaki.'' Naja'atu shuru tayi tana tunanin maganganun Munira anya kuwa zata iya daukar hoton nononta ta tura "masa, gaskiya ba zata iya ba, Mikewa tayi hade da mikawa Munira wayarta ta nufi daki, munira tabi bayanta da kallo tana ta'be bakinta ita a ganinta ba laifi bane dan budurwa ta nunawa saurayi wani sashe na jikinta ai duk a cikin so ne( 'kalubale gareku 'yan matan da zawarawan da suke da irin wannan d'abi'a wallahi duk saurayi ko bazawarin da zaice miki yana so yaga wani bangare na jikinki to ba sonki yake ba dan iska ne yana so ku watse ne a waje koda ya aureki auran ba zaiyi qarko ba dan zargi ne zai shiga a tsakaninku ayi ta samu matsala ba'a namiji dan iska sai mace mutukar kika bada 'kofa to shi kuma namiji dama haka yake so zai shigo miki da iskanci iri-iri duk iskanci namiji idan bai ga kofa ba" dole ya kyaleki) Washe gari tsaf suka shirya Naja'atu da Munira suna fitowa palo tayi tozali da 'Ya'yanta a zaune Baba larai ta kawo su....Sai dai yanayin yanda taga fuskokinsu cikin rashin walwala yasa jikinta yayi sanyi Ta zauna a hankali tana rike hannun Mussadiq da fadin yaushe kuka zo.? Yaron babu walwala a fuskarsa ya gaisheta..Saddiqa da mufida suma suka gaisheta babu walwala a tare dasu ta amsa cikin damuwa da yanayin data gansu a ciki. "Baba larai cikin ya'ke da kokarin danne damuwarta tace""Naja'atu banji dadin abinda kikayi ba wallahi" "ashe duk abinda nake fada miki a gida ba kya dauka shuru kawai kike min ashe ke kin san abinda kika shiryawa kanki da 'kuruciyarki da komai zaki 'bata rayuwarki.""" "Zum'bura baki tayi tace""Dan Allah baba larai mu bar maganar nan ta riga ta wuce hajiya ma tace a daina" "tayar da ita duk abinda ya faru Allah ne ya hukunta amma ku daina dora laifi a kaina."" Baba larai tace""To Allah ya huci zuciyarki naga kamar bakiji dadin maganata ba, dama Alhaji ne yace a kawo miki kayanki" "gasu can a gefe guda.""" Kallon inda kayan nata tayi taga akwatin nan lefanta da sauran kayanta na gidan dauke kanta tayi ba tare da tace komai ba. Hajiya ce ta sauko daga sama ganin Larai da yaran a zazzaune yasa ta saki fuskarta ta zauna kan kujera suna gaisawa da larai hade da tambayarta hidima da yara. Larai tace alhmdullhi sannan ta fada mata abinda ya kawota gidan "Hajia tace""Hakan yayi dama nayi tunanin wanda zan tura ya kwaso mata kayanta to Allah yasa haka shi" "yafi alkairi."" Larai ta amsa da amin Saddiqa ce ta mike fuskar nan ta a had'e ta kalli su Mussadiq da" "fad'in ''Ku taso mu shiga gidan Baba malam."" Yaran suka mike da sauri Hajia tace""A'a kishiyata" "kumbure kumburen me kikeyi ko gaisuwa babu."" Saddiqa ba tare da ta kula ta ba tasa takalmanta ta fice daga palon tana kokarin mayar da kwallar dake so ta zubo mata. Gani take kamar hajian ce ke daurewa" Naja'atu gindi tana abinda take so! hajia a maimakon ta nuna damuwarta dangane da faruwar al'amarin sai taga kamar ma murna take tana nunawa duniya kamar ba itace ta haifi Abbansu ba. Baki a sake suka bi yaran da kallo har suka fice daga palon. Baba Talatu na zaune a tsakar gida bayan sun gama karya kummalo ita da baba malam suna tattauna "al'amuran da ya shafesu baba malam yana yi mata bayanin manufar Bash akan Naja'atu, Baba Talatu ita dai kwata kwata al'amarin be kwanta mata a rai ba saboda kallo guda tayi wa yaron taji ba tayi na'am dashi ba dalili ganin yanda le'bunansa sukayi ba'ki'kirin hakan ya nuna mata cewar yaron na shaye shaye dan duk wanda yake shaye shaye to yakan fita daban da sauran mutane bayan haka kuma yanda yake sinne kansa sam yaki yarda su hada ido hakan yasa ta fahimci kamar akwai alamun rashin gaskiya tare dashi, to ganin yanda maigidan nata yayi na'am da yaron ne yasa tayi shuru ba tace komai ba amma gabadaya al'amarin be kwanta mata ba. Su saddiqa suka shiga da sallama a bakinsu suka samu guri" suka zazzauna ko wanne fuskarsa babu dadi Baba malam ya dinga tsokanarsu kamar yanda ya saba "amma babu wanda ya tanka masa karshe ma Saddiqa fashewa tayi da kuka ta nufi daki ta kwanta a gado tana kuka. Baba Talatu ta shiga goge hawaye tana fad'in ""Ai yarinyar nan Naja'atu tasa zuciyoyin yaran" "nan a cikin masifa da damuwa Allah ba zai barta ba sai ya saka musu abinda tayi musu sabida taga suna kaunarta shiyasa take musu abinda ta gadama to babu komai Allah ya kawo musu wacce zata tallafesu."" tana kuka sosai take maganar. Baba malam yace.""Kada ki sake yin wannan furucin akan yarinyar nan ki" barwa Allah ikonsa domin babu wanda ya isa yaja da abinda ya zartar muna so naja'atu ta zauna da uban yaran nan Allah bai kaddara hakan ba dabadayanmu bamu san abinda yake lullu'be ba saboda haka dukkanimu sai mu taru muyi hakuri mu dauki kaddara da ce cewar haka Allah ya nufa amma kada ki sake "kiyi wa yarinyar nan baki.""" Baba talatu ta mike tana goge hawaye da gefan zaninta ta shiga kicin ta dauko kunu cikin kofin silba ta "ajiyewa mussadiq a gabansa tace""Dauki kunu kasa kaji ko ko zaku ci awara."" Mufida ta d'aga kanta tana share fuska, kicin din ta koma ta dauko awara me yawa a cikin silba ta ajiye musu a gabansu ta nufi dakinta ta rarraso saddiqar suka fito tare. Baba malam na kokarin fita su Naja'atu suka shigo gidan sai" ya koma ya zauna..Baba talatu kauda kanta tayi daga inda suke Baba malam ya nuna musu gefan tabarmar da yake zaune. Naja'atu kamar ba'kuwa taje ta zauna munira ta zauna a kusa da ita suka shiga gaishe dashi Cikin kulawa ya amsa musu suka juya suna gaishe da baba talatu ciki ciki ta amsa hankalinta na kan mussadiq tana gyara masa awarar dake gabansa Shuru gurin yayi naja'atu sai kokawa take da zuciyarta dan kuka ne yake kokarin kwace mata ganin yanda iyayenta nata keyin baya baya da ita sai kace basu santa ba. Abbah magaji ne ya shigo gidan da shirin tafiya kasuwa. Naja'atu tunda ya shigo gabanta ke faduwa ta kasa hada ido dashi saboda tsabar "tsoro murya na rawa take gaishe shi ba tare daya kalleta ba ya amsa kana ya shiga gaishe da iyayensa. Baba malam yace""Dama inaso mu tattauna maganar yaron nan bashir da kai."" Kai tsaye" "yace.""Malam bana cikin wannan al'amarin sabida bana so nan gaba wani abu ya faru sunana ya fito idan Naja'atu ta za'bi Bashir ya zama abokin yaruwarta to ina mata fatan alkairi."" Baba malam ya 'bata rai yace.""Wannan wace irin magana ce ka keyi meye aibun yaron? kai tsaye yace""Bashi da hali mai kyau ni na gani da idona kuma na sheda shiyasa nace babu ruwana."" Malam yace.""Komai munin halinsa muna masa fatan shiriya akwai matasa da yawa wad'anda suka zama wani abu a duniya bayan a can baya sunyi gagara Allah ya shiryesu sun koma salihai masu tsoron Allah saboda wannan dalilin naka ba zai hanamu mu dauki naja'atu mu bawa yaron nan ba domin ita shiriya ta Allah ce muna addua Allah yasa sanadiyar auran nan ya gyara kusakuransa."" Abbah magaji ya sauke ajiyar zuciya had'e da mikawa da niyyar tafiya yace""To Allah yasa haka shine yafi alkairi ni zan wuce kasuwa."" Baba talatu tayi masa fatan dawowa lafiya baba malam ya mike suka fita suna sake tattauna maganar. To Bash bai zo gidan ba sai bayan" sallahr azuhur tukkuna sai da ya gama yawace yawacen sa tukkuna ya shiga unguwar lokacin Munira ta shirya tsaf shi take jira ita kuwa naja'atu cike take da alhini da damuwa dan har kusan rungume juna sukayi ita da Bash din sabida tsabar shau'ki da sha'awar junansu da suke. Bash ya dauki daya daga cikin manya manyan wayoyinsa ya bata tare da sa mata sabon sim card tayi ta masa godiya kana ta rakashi har cikin gidan alhaji yayi musu sallama suka fito suka shiga gidan malam Bash gurin malam kawai ya samu cikakkiyar kulawa baba talatu kam kin fitowa tayi tana daki ta amsa gaisuwarsa har suka fita daga gidan bata fito ba. Naja'atu yini tayi a kwance dan bayan tafiyarsu Bash din kasa zama tayi gidan malam sabida babu fuska "gurin matar gidan sai ta tattara ta bar gidan ta nufi gidan alhaji dama duk wani kayanta na gidan, ta shiga" daki ta kwanta cike da damuwa gabad'aya halin ko in kula da baba talatu take nuna mata shine ya tsaya mata a rai. Sai yamma can ta fito palo ta zauna kusa da hajia suna d'an ta'ba hira hajia Abu macace mai mai da d'an wani nata kwata kwata bata 'kullaci naja'atu ba wai dan ta'ki zama da d'anta gabad'aya ta dauki a'lamarin a matsayin qaddara. Kamar koda yaushe hakane ya kasance bayan sun taso daga kasuwa kofar na'isa suka nufa shida Salim "dake driving dinsa, kasancewar lokacin sallar magariba yayi yasa basu shiga gidan ba sai bayan da suka gabatar da sallar tukkuna suka nufi gidan harda Alhaji wanda suka hadu a massalacin Naja'atu ce kad'ai" a palon hajia ta shiga sallah! Alhji gaba yayi Abbah Abbas da Salim suka tsaya a gurin Hajia Rabi suna gaisawa. Naja'atu na ganin shigowar Alhaji cike da ladabi ta gaishe shi ya amsa cikin kulawa had'e da kokarin hawa samansa. gyara zamanta tayi ta cigaba da latse latse a wayarta ita da Bash suke hira sai "zantukan soyayya yake mata tana jin dadi Hancinta ne ya shaqo mata kamshin turaransa, tayi saurin" "dago kanta, wayar ce ta kusa faduwa tayi saurin ri'kewa gabanta ya wani fad'i! shaf ta manta yana zuwa gidan da irin wannan lokacin da tuntuni ta bar palon dan bata kaunar abinda zai had'a fuskarta da tasa...Kallo d'aya yayi mata ya kauda kansa yana bin palon da kallo babu hajia a gurin Ya juya bayansa" "yana kallon Salim daya shigo yace.""Haura sama kacewa hajia gani nazo zamu gaisa ba zama zanyi ba.""" "Salim da sauri yace""To Kawu."" Saman ya nufa yana dan satar kallon inda naja'atu take zaune." "Kujera ya samu ya zauna ba tare da ya kalleta ba, ita kuwa gabadaya ji tayi ta muzanta simi-simi ta mike" "da wayar ta ta nufi dakin da take jikinta duk ya mutu ta rasa me yasa Abbah Abbas keda kwarjini mutukar yana guri takan rasa karsashi da nutsuwar zuciya...Daf da zata shiga dakin taji gyaran muryarsa hade da kiran sunanta, Gabanta na faduwa ta juyo amma bata yarda ta hada ido dashi ba, Yace.""Baba Larai ta kawo miki kayanki ko."" Kanta ta d'aga masa, Yace.""Okey ki duba da kyau abinda baki gani ba naki sai kiyi magana a kawo miki."" A sanyaye murya na rawa tace""To."" ta juya da sauri ta shiga dakin, zama" "tayi gefan gado tare da tsirawa fuskar wayar hannunta ido! shin wai shi Abbah Abbas din nan wane iri ne? tayi masa laifi amma sai tausasa mata yake kamar ma yana nuna abunda tayi bai dameshi ba, tausayinsa taji ya kamata sai ta kwanta tana hawaye tasan dai daurewa kawai yake a yanda yake da son 'ya'ya dole yaji ciwon lalacewar cikinsa aikuwa tunda taga bai dauki abin da zafi ba zata yi masa text ta bashi hakuri ta kuma tabbatar masa da cewar ita bata sha komai ba dan ta zubar masa da cikinsa cikin ya zube ne sakamakon irin 'bakar wahalar data sha lokacin zuwanta jos. Da yake tana da numbarsa a kanta sai" kawai tasa a sabuwar wayar tata tayi serving ba tare da tunanin komai ba ta shiga rubuta masa text kamar haka. _Assalamu alaikum Abbah Kayi hakuri da abubuwan da suka faru tsakanina da kai wallahi nima ba'a son raina ba hakan ya faru kayi hakuri ka yafe min. sannan inaso in tabbatar maka da cewar wallahi ban sha komai ba domin na zubar maka da ciki ba Allah ne ya aiko da tsautsayi a kansa kayi hakuri da abunda "Allah ya qaddara a tsakaninmu ina mana fatan alkairi tare da fatan Allah yasa haka shine yafi alkairi.""_" Tura text din tayi ta ajiye wayar a gefanta tana adduar Allah yasa idan ya karanta yayi mata kyakykyawar fahimta kuma yace ya yafe mata *Cai!! Caii!Ca!! VIP MADADI BA HARAM! BANE COMMENTS 'DINKU HAR SAI DA YA KUSA SANI CIWON KAI TO NI DAI NA MA RASA ME ZANCE MUKU SHIYASA NAYI GUM! DA BAKINA DA YAWA DAGA CIKINKU SUN CE DAMA HAKA NAKE SUNA FAD'IN SAI LABARI YA DAUKO DADI SAI NA RIKIRKITA SHI TO IDAN KUKA GA HAKA NA FARUWA MARUBUCI NASO YA ISAR DA S'AKONSA NE! EH HAKANE SUNAN LITTAFIN MADADI!! MADADI ZAI TABBATA DA YARDA ALLAH AMMA KAFIN HAKAN YA FARU SAI ANJI RASHIN DAD'I DANI DAKU DA ABBAH ABBAS NA'JA'ATU DA DUK WANI MAKUSANCINSU SAI SUN SHIGA JIMAMI DA ALHINI KAFIN SUYI DARIYA AYI HAKURI DA HALINA MY FANS INSHA ALLAH ZAN FARANTA MUKU RAI A GABA. NAGODE KWARAI DA GASKE * Vip group 600 Normal gruop#300 accont...0542382124...Binta umar gtbank...Idan katin waya zaki turo kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *MANZIR _ALWAFIR ABUJA * _*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci magungunansu babu almundahana a ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu ko wace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye da akwai gruops na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rijistar dasu to kukanki ya 'kare idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_ 51 Naja'atu Kasa fitowa palon tayi har sai da ta tabbatar da cewar ya tafi sannan ta fito da sanyayyan jiki ta "zauna kan kujera tana sake duba text din data tura masa. Hajia ta kalleta a tsanake tace"" Naja'atu ki" "kwantar da hankalinki kinji ko kada ki damu da yanayin rayuwar da Allah ya shirya miki mu bamu dauki al'amarin da zafi ba ki saki jikinki a nan gidan komai kike bukata ki fad'a min insha Allah zan share miki hawaye da nan gidan da gidan Malam Sani duk d'aya ne zaki zauna a hannuna har sanda Allah yasa kika 'kare iddarki sai kiyi aure ga dukkanin mijin da Allah ya za'ba miki gabad'ayanmu muna yi miki fatan alkairi da adduar za'bi nagari."" Kasa daurewa tayi ta kalli Hajian tana share hawaye tace""Hajia nagode sosai da karamcin da kukayi min nima ina neman afuwarku a bisa abinda da ya faru kuma inaso in tabbatar miki da cewar wallahi ban zubar da ciki da kaina ba tsautsayi ne ya ritsa dashi koda can da nake ikirarin zubarwa bazan iya ba kawai dai ina fad'a ne amma wallahi bani na zubar ba wahala ce tasa ya zube."" Hajia Abu tayi murmushi tana girgiza kanta tace""Kada ki damu Naja'atu kinji na amince da maganarki kan cewa baki zubda ciki ba, idan Allah ya qaddara zamansa a jikin ki komai abu sai kin haifeshi sannan kuma zaki iya haifarsa ya d'auke abinsa sabida haka ki kwantar da hankalinki dama can Allah bai nufa abinda ke cikin naki zai taka kasar duniya ba muna rokon Allah ya mayar muku da alkairi gabadayanku. Cikin shehshekar kuka ta amsa da ameeen..Hajiya tace""Ga abinci can yanzu Magajiya mai aiki tazo ta ajiye yana da kyau kije kici ki kwanta ki samu nutsuwar zuciya."" A sanyaye ta mike ta nufi" inda kololin abincin suke a ajiye. "To har tayi shirin bacci ta kwanta ba taga amsar sa ba, sai taji rashin dadin abin tana tunanin ko bai yarda" da maganar ba koda yake dama tasan da kyar idan zai yarda da cewar ba ita ta zubar da cikin ba ita dai Allah yaga zuciyarta bata zubar da ciki ba duk wanda ma zai zargeta ya zalince ta( Magana zarar bunu naja'atu ke kika furta sai kin zubda ciki dan haka da yawa mutane zasu karyata maganarki ta cewa bake kika zubda shi ba) Video call d'in da Bash yayi mata ne yasa ta manta da damuwar dake damunta suka shiga soyewa ita da "masoyinta, Tana kallon Bash daga shi sai gajeran wando faffadan kirjinsa mai dauke da gashi ba'kikikirin na kara d'imautata sha'awa da sonsa na 'kara ninkuwa a zuciyarta, to shima Bash din nasa 'bangaran hakane dan shi al'amarin nasa ya fi nata tsanani jijiyarsa wacce ta mi'ke a cikin gajeran wandonsa ya shiga nuna mata yana lumshe mata ido wai ta taimaka masa ta tu'be kayanta ya dinga kallonta a haka ko zai samu satisfaction! a tsorace! ta kashe wayar gabanta na fad'uwa! Gaskiya Bash yana da katuwar jijiya ta tsorata mutuka da ganin girmanta jikinta ya shiga kyarma tana tunanin ranar da zai burma mata ita a jikinta...Bash kuwa ganin ta kashe data ne yasa a gigice ya shiga kiran wayarta kin d'agawa tayi sabida tsoro anya kuwa ba zata taka masa burki ba kuwa kamar abinda yake yi yayi yawa bashi da kunya ko kadan...Maganar Munira ta tuna inda take ce mata sai tayi da gaske a kan bash din saboda idan ta tsaya wasa to 'yan matansa dake rububinsa zasu kwace mata shi, tana son Bash mutuka amma kuma bata so ya dinga nuna mata zulamarsa a fili sai taga kamar sha'awarta yake ba sonta yake ba, amma kuma a duk sanda ta tuna da kalaman soyayyar sa da al'kawarikan da yake mata sai taga tamkar tafi kowace mace dace da samun masoyi mai sonta da kaunarta dan Allah Pillow ta rungume tana sauke numfashi a" hankali a hankali bacci ya dauketa mai cike da mafarkin Bash da soyayyarsa. Kamar dai yanda ya saba zama a palo duk daran duniya ya duba loptop to yauma hakane yana zaune a "palon shi kadai da loptop a cinyarsa yana dubawa akwai sa'konni da yawa sabida ya kwana biyu bai duba ba shiyasa hankalinsa ya dauke sosai ko tunanin Halisa bayayi wacce take can tana jiran shigowarsa dan a matse take da sha'awa dalili koda suka je saudia tsayin sati biyu da sukayi sau biyu kacal ya kusanceta al'amura suka rikice shikkenan ta rasa gane kansa idan ta ganshi a kwance taje ta nema shi baya bata had'in kai sai yace ta rabu dashi da abinda ya dameshi idan ta tsananta sai yace shifa yazo garin ne domin ya kad'aice da Ubangijinsa ba jima'i ne ya kawo shi ba. Hakuri takeyi ta kyaleshi amma gaskiya tana cutuwa, to ganin sun dawo gida ne yasa ta bankad'i magungununta na mata ta tsumu sosai da sosai tana adduar Allah yasa ya bata had'in kai ta fito daga dakinta cikin 'yar mitsitsitar riga cinyoyinta duk a waje ta fesa turaran da yake saurin dauke masa a hankali...Kusa dashi tazo ta zauna tana shafa gadan bayansa had'e da sumbatar gefan fuskarsa. Ko gezau beyi ba hankalinsa na kan loptp dinsa..Sai" "kawai ta shiga kokarin dauke masa loptop din daga cinyarsa, tsawa! yayi mata da fad'in ta matsa daga kusa dashi ta kyaleshi aiki mai muhimanci yake."" Halisa ta shiga mamakin abunda yayi mata! A fusace! tace""Wai dan Allah me kake nufi dani ne? Na lura ka tsiro da wasu halaye wanda ban sanka dasu ba shin ni me ya shafeni kuma da kake kokarin huce fushinka a kaina? tunda yarinyar nan Naja'atu ta aikata" maka abu kake jin haushina sai kace nice nayi maka kana kokarin danne min hakkina haka akeyi ? kafi "kwana goma baka neme ni ba ko na nema ka baka kulani ya kake so nayi."" Murya na rawa ta karasa" maganar. Shuru yayi mata ya cigaba da dube dubensa...Halisa ta sha'ka sosai da sosai ta dinga sakin maganganun "da ranta yake so tana kuka amma d'an tahalikin nan ko kallonta baiyi ba cike da tsantsar tashin hankali ta bar gurin, ta shiga dakinta ta zabga uban tagumi tana tunanin masifar data rikito mata, to wai shin me hakan yake nufi ne?? Zuciyarta tace Asirin da ki kai masa ne ya karye sai kin sake wani!!! Idan haka ne kuwa tabbas ba taga ta zama ba! za tayi iya hakura da duk wani hukunci da zaiyi mata amma banda horon hana ta hakkinta gaskiya ba zata iya da wannan ba a halin da take ciki tana ji tamkar taje ta janyo shi dole yazo yayi mata dan yanda take tsiyaya Allah ne kawai zai mata magaji...Kwanciya tayi tana kuka takaici kamar ya kasheta, da dai ta kasa hakura sai ta mike kamar bugaggiya ta koma polon nan ta tarar babu shi a gurun ya kashe fitila yayi shigewarsa dakinsa yasa key...bugu ta dinga yi yana jinta ya shareta dan mugun haushinta yake ji yana ganin kamar itace tayi masa laifi ba Naja'atu ba!( Humm! Halisa ashe tsugune bata kare miki ba koda yake hausawa nacewa idan zaka gina ramin mugunta ka gina daidai misali dan watarana kaine zaka fada ciki)..... Tsaf yayi shirin baccinsa ya kwanta kan bed da wayarsa a hannunsa yana kokarin kashewa ya lura da text din Naja'atu, a nutse ya shiga yana dubawa, Ya jima yana nanata karanta text din yana mamakin hakurin da take bashi, to meye ma'anar hakurin da take bashi ?" Ciki dai yasan ita ta zubar masa saboda ita da kanta ta tabbatar masa da hakan lokacin yana saudia sai yanzu kuma da bukatarta ta biya tazo tana bashi hakuri! Baya tunanin zai iya zama da kowace irin mace mutukar zata salwantar masa da albarka da Allah ya bashi komai son da yake wa mace zai iya rabuwa da ita har abadah...Najaatu tayi nasara a kansa sai dai kawai yace Allah yasa ka masa. Numbar yabi ya rubuta mata amsa kamar haka. "_""Babu komai kada ki damu magana ta wuce a gurina.""_" Yana tura text din ya kashe wayar tare da gyara kwanciyarsa ya rufe kafafunsa da bargo yana addua a cikin zuciyarsa. Halisa da kyar ta iya samun bacci a daran koda asubah ma da ya shigo dakin so tayi ta ri'keshi ta karya "masa alola yayi gaggawar yaki ce ta daga jikinsa ya fita daga dakin, shifa gabad'aya sha'awar sex din a ka cire masa daga cikin ranshi tunda abun nan ya faru ya daina jin sha'awar komai na rayuwa abinci ma dan ya zama dole ne yake tsayawa yaci Halisa ba tare da tayi yunkurin tashi taje tayi alwala ba ta" dauki wayarta ta shiga kiran Aminiyartata Ramlatu. Yaya Ramlatu na kokarin tada sallah taji ringing din "wayarta sai da gabanta ya fadi kafin ta dauki wayar tana dubawa cikin zuciyarta tana fadin""Allah yasa ba" mutuwa akayi ba kiran waya da asubah Ganin numbar Halisa yasa gabanta ya sake faduwa da sauri ta kara wayar a kunnanta tare da zama a bakin gadonta. "Halisa sai da taci kukanta ta koshi tukkuna ta warwarewa Ramlatu abinda ke faruwa!!! Ramlatu tace""Ni" "wallahi na dauka wani gagarimun abune duk kin sa gwiwata ta sage."" Halisa tace""Ni kam gagarimun abune a gurina Yaya Ramlatu ke naga dama ai wannan al'amarin kamar be dame ki ba kina kallonmu muna fad'i tashi gurin shaye shayen magani sai da kiyi ta ingiza mu kina zaune a guri daya ni yanzu na kira ki a waya ne muyi shawarar yanda za muyi dan wallahi gabakid'aya d'an uwanki ya rikice min na rasa gane kansa da gindinsa tunda al'amarin nan ya faru shikkenan ya sanja hali sai kace ni nayi masa laifi.....Ramlatu tace""Ni kam wannan masifa ta Abbas ta isheni wallahi haba jama'a ayi tayi masa magani ana jifansa da asiri kamar ba'a jikinsa ba daga zarar aiki yayi kyau sai warware shin yanzu ya kike so ayi" "dan wallahi gabadaya tunani na ya kare kan al'amarin nan.""" "Halisa tace""Nifa babban abinda yake da'ga min hankali kin had'a shimfida dani da yake idan babu" "wannan harkar ina tunanin zan iya bin maza."" Yaya Ramlatu tace""Subahanallahi!( Duk macan dake yawace yawace na bin bokaye da malaman tsubbu watarana sai tayi tunanin aikata zina koda kuwa mijinta na dauke mata dukkanin lalurarta akwai sanda wani bokon zai bukaci kasantuwa da ita domin biyan bukatarta Allah ya tsare mu ya kare mu daga sharrin duniya) Yaya Ramlatu ta cigaba da cewa"" Haba Halisa kada laifukan naki suyi yawa mana ki daina maganar aikata zina zaki zubar mana da mutunci abinda za'ayi yanzu idan ya fita kasuwa ki fito da wuri muje gidan 'Yar Sa'adu ko za'a dace ta baki maganin da zaki dinga sa masa a abinci yana ci wanda zai dinga tayar masa da sha'awa kinga dole idan" "sha'awa ta dameshi ya kusanci inda kike.""" "Halisa ta share hawayenta tace""To wannan shawarar taki tayi ma'ana aikuwa yana tafiya kasuwa zaki" gan ni a gidanki. Sallama sukayi da juna Halisa ta d'an ji sassauci a zuciyarta ta mike ta nufi toilet domun daura alwala lokacin garin hr yayi haske. 'Bangaran Naja'atu kuwa bayan ta idar sallahr asubahi kamar yanda ta saba sai ta kunna wayarta tana "kunnawa kuwa text ya shigo hannu na rawa ta shiga tana dubawa, wani irin farin ciki ne ya lullubeta ganin amsar da ya bata, sai taji hankalinta ya kwanta sosai dan dama bata so kwata kwata ya 'kullace" ta ko kuma ya dinga kallonta a matsayin wacce ta aikata masa mummunan ta'addanci. To kamar yanda Halisa ta fad'awa Yaya Ramlatu hakane ya kasance maigidan da yara na fita itama ta "kintsa jikinta a gurguje ta fito ta samu baba Larai na goge a palo tace mata za taje unguwa, Baba larai tayi mata fatan dawowa lafiya ta juya ta cigaba da aikinta." Ba suja wani dogon lokaci ba suka nufi gidan 'Yar sa'adu yau ma kamar koda yaushe 'Yar sa'adu na zaune "a gurin zamanta mata sunkewayeta suka shiga gurin da sallama a bakinsu suka nemi guri suka zazzauna ana gaisawa. 'Yar sa'adu na murmushi tace""Lallai yau tunda na ganki nasan akwai bayani da kwana biyu" "kinyi min yaji kin daina zuwa ina fatan dai ba wata matsala kika kawo min ba.""" "Halisa tace""Matsala babba na kawo miki wallahi kuma inaso ki share min hawaye na."" Yar sa'adu tasa" "dariya tare da bawa ta gefanta hannu suka tafa tace""Lallai to ina sauraranki nasan dai zance gizo baya wuce na ko'ki hummm! maza kenan maza mutanan mu idan babu ku babu mu hahahaha.""! d'akin ya d'auki dariya jin irin kirarin da 'Yar sa'adu tayi wa maza!" "Halisa ta shiga zayyanewa 'Yar sa'adu abinda yake tafe da ita, 'Yar sa'adu murmushi tayi tace""Rabu dashi" "zanyi miki maganinsa dama wani sa'in ai haka suke idan iskancinsu ya motsa! humm! babu komai Allah ya taimake ki kinzo akan ga'ba! akwai wani *'Dan anace* dana samo shi daga Garin *Jega* wannan maganin ba kowa nake siyarwa dashi ba kema dan mun saba dake ne tsohuwar costomar ce ke shiyasa zan siyar miki dashi amfani d'aya zakiyi dashi ki gigita masa tunani wallahi sai ya zama tamkar mahaukaci ke zaki sha mamakin aikin da maganin nan zaiyi miki mutukar kin fara amfani dashi a kan tsari."" Halisa da sauri tace""Na amince da maganarki 'Yar sa'adu dan duk maganin dana ke siya a gurinki" "babu na banza ki fada min kudin maganin ko nawa ne zan biya.""" "Yar sa'adu tace""zaki bani dubu dari da hamsin hakan ma sauki nayi miki wallahi."" Halisa babu neman ragi" "tace""Bani accont numbar naki sai na sa miki kudin dan yanzu kudin jakata basu kai haka ba." 'Yar sa'adu ta bata accont numbar dinta a take a gurin tasa mata kudinta ita kuma taje ta dauko mata maganin cikin wata 'yar mitsitsiyar kwalbar fiyafiya maganin ba'kikkirin dashi. Yar sa'adu tayi mata bayanin yanda za tayi amfani da maganin sannan sukayi mata sallama suka tafi. A daran ranar Halisa ta dinga binsa a jiki a jiki tana marairaice masa tana kuka da bashi hakuri wai idan "laifi tayi masa ya gafarce ta bai kamata ya dauki fushi a kanta ba tunda ba ita tayi masa laifi ba, to shima ganin ta damu yasa ya ji tausayinta ya kuma yi tunanin abinda yake mata bai kamata ba tunda ba ita tayi masa ba to yana da kyau ya daina shiga hakkinta....biye mata yayi suka nufi dakinta anan ta baje kolin" iskancinta dama already ta tusa *'Dan anace* wannan bakin maganin na gurin 'Yar sa'adu a can cikin matuncinta ta turmutsa maganin Abbah Abbas ya afka suka dunga suburbudar juna Halisa taji masifar dadin maganin dan har matseta yayi kuma ta lura shima mijin nata yana nishadantu wa kwarai da gaske sai bayan sun samu gamsuwa ne ya zare jikinsa domin zuwa ya tsarkake kansa anan ne ita kuma "Halisa taji tamkar an barbad'a mata barkono a gabanta, hannu tasa a gurin cikin wani irin jin radad'i ta sanya 'yar 'kara tana kokarin yunkurawa ta mike zaune nan ma taji tamkar an caccaka mata allurai cikin gabanta da wani irin sauri ta koma ta kwanta tana zazzare ido gabanta sai wani irin fad'uwa" yake.................. * WAI!!! NI FAD'IMATU !!! YAU HAR SAI DA NA RASA VOICE D'IN WANDA ZAN SAURARA AMMA DAI NAFI SAURARAN VOICE DIN 'KAWATA MC ALLAH YASA NA FADI SUNAN DAIDAI SISTAR AISHA ABDULLAHI NA SAURARI VOICE DINKI HAR YANZU BAMU SAUKA DAGA MAUDI'IN DA MUKE KAI BA MUNA CIKIN MAUD'UIN LITTAFIN MADADI GASKIYA NAYI DARIYA SOSAI DA SOSAI JIN COMMMENTS DIN KI NA KUMA KARA TABBATAR DA CEWAR ABBAH ABBAS NA DA MASOYA MUTUKA MOMMYNA TA NIJAR ITAMA TUN SHEKARAN JIYA MUKE FAFATAWA DA ITA KAN AL' AMURAN DA SUKE FARUWA TSAKANIN NAJA'ATU DA ABBAH TO YAU MOMMYNA DA DUK WANI MA'KIYIN HALISA PEGE NAKU NE KUYI RAWA KU JUYA DOMIN KUWA HALISA ZATA SOMA GIRBAR ABINDA TA DADE TANA SHUKAWA * *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a gruops to na sata ne idan kina so ki biya kudin karatu ga yanda abin yake Vip gruop#609 normal gruop#300 account...0542382124...Binta umar gtbabk..idan katin wata zaki tura ki min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *A lokacin da kake had'a mutum da Allah kan ya daina abu to shi kuma a lokacin shed'an yake 'kara ingiza shi! Masu fitar min da book na had'a ku da Allah ku bari masu sharing a gruops ina kallon ku a groups d'in da muka had'a daku kuna shearing hankalin ku kwance ba zance muku komai ba saboda nasan da baku ganshi ba ba zakuyi sharing ba amma dai yana da kyau kuyiwa kanku hisabi abinda kasan idan anyi maka ba zakaji dadi ba to kaima kada kayi wa wani! Masu karanta book din Madadi baku biya ba kuma duk ina kallonku 'Kauna ce ta janyo haka amma dai dan Allah a rage son kai da son banza azo a biya kudin karatu mutum sai ya karanta hankalinsa a kwance Gabad'ayanku masoyana ina 'kaunarku * 52 Jin irin yanda headquarter d'in nata ke mata wani irin 'kai'kayi da rad'ad'i ya sanya da sauri ta turmutsa "yatsunta a can ciki inda tafi jin kaikyayin ta dinga kwakula tana lumshe idonta sosai take jin dadin yanda take sosa gurin da k'aikyayin ya dameta duk ta wage kafafunta kamar zararriya sai zura yatsunta take a gabanta tana kwakula. Cikin wannan yanayin ya fito daga wanka ya sameta, gabadaya ma hankalinta" "baya kansa tana can duniyar susa tana lumshe ido, razananniyar tsawa! ya buga mata da fad'in ""Halisa meye haka kikeyi.""? A firgice ta cire hannunta daga gurin ta mike zaune tana kallonsa! kafin tayi magana taji tsinkewar wani ruwa daga gabanta yana bin cinyoyinta. Murya na rawa tace"" Wallahi bayan" rabuwar mu naji gurin yana min wani irin kaiky Kafin ta 'karasa maganar tayi saurin sake sa hannunta "a gurin tana sosawa sakamakon jin yanda gurin yayi mata wani irin caccaka ta dinga sosawa tana masa bayanin halin da take ciki Yace.""Sau nawa ina hanaki cushe cushen magungunan banzan da kikeyi!" "aikin banza kawai kinje garin shashancin ki na banza da wofi kinsa abinda zai cutar dake sai ki tashi kije ki wanke gurin da ruwan d'umi."" Halisa wasu zafafan hawaye ne suka shiga zubo mata wai shin me yake shirin faruwa da ita ne? wane irin magani ne wannan wanda Ya sa'adu ta siyar mata wanda yake kokarin janyo mata gagarimar matsala? jikinta a mace ta mi'ke da kyar ta nufi toilet Shi kuwa jallabiyarsa ya" dauka yasa ya fice daga dakin ya nufi nasa. Halisa tsugunawa tayi a toilet din tana sake zura yatsunta tana sosawa nan taji wani katon nama ya fito daga gabanta ya cika gurin yayi fam!! yunkuri tayi ta sake d'ora hannunta a gurin taji wannan tsokar naman ta sake girma! Ihu!! ta kurma ta mi'ke tsaye gabanta na dukan uku uku? shin me yake yunkurin fitowa daga jikinta sai kace wacce zata haihu! cikin fad'uwar gaba ta sake tsugunawa a tsorace ta sake sa hannunta still wannan tsokar naman na nan a inda take! jikinta ya dinga kyarma! ta dinga tsiyayar da wani irin gumi na tsantsar tashin hankali da rud'ani!!! Halisa ta kai awa guda a toilet tana aikin abu daya da ta yunkurin mayar da abunda yake kokarin fitowa daga gabanta sai ya sake dawowa haka ta dinga yi tana kuka da kiran sunan Allah dan gabadaya ta tsorata da al'amarin! wannan karon maganin gurin 'Yar Sa'adu na nema ya janyo mata matsala babbah! Da kyar tayi wanka ta shiga ruwan zafi ta dade wai ko abun zai koma sai dai har ta gama "zamanta a ruwan d'umin ta fito abun bai motsa daga inda yake ba, cikin wata iriyar tafiya ta fito daga" toilet din ta kwanta bed dinta cike da alhini da damuwar bala'in da yake shirin rikito mata. "Har yara suka tafi skull Halisa na cikin daki bata fito ba, baba larai na ganin maigidan ya fito ta gaishe shi" "a nutse ta bar palon, Abbah Abbas ya zauna gurin cin abinci da wayarsa a hannunsa, Salim ya kira yace maza yazo ya daukeshi da wuri yake so ya fita....Bayan sun gama waya da Salim a nutse ya karya ya" "mike ya nufi dakin Halisa, nan ya tarar da ita tana kuka ta takure jikinta a guri guda." Cike da mamaki yake tambayarta abinda yake faruwa take kuka da safe dan shi gabad'aya ma ya manta "da abunda ya faru da ita a jiya. Kasa fada masa tayi saboda tana jin tsoro kada yayi mata fad'a! Yace""Ba" zaki fad'a min abinda ke da akwai ba kin zauna kina kuka meye amfanin hakan da kikeyi ke ba yarinyar kankanuwa ba ki zauna kina aikata abu irin na yara. "Da kyar tace""Wallahi tun jiya wani abu yayi tsiro daga gabana na rasa kome ye nayi nayi ya koma ya'ki" "komawa."" Cike da mamaki yace.""Wane abu ne zaiyi tsiro ya fito daga matuncinki sai kace wanda akayi shuka gurin Kinga kiyi min bayani yanda zan fahimta.'' Hawaye ta share tace""Wallahi Abban Mufida ba" karya nake ba nima na tsorata mutuka wata 'Yar tsokace ta bullutso daga gurin ! "'Yar dariya yayi domin shi abun ma dariya ya bashi Kai tsaye yace""Bud'e min naga tsokar naman data" "bullutso."" Yafad'a yana nufar inda take. Halisa a tsorace take kallonsa dan gabadaya bata so yaga abin" tana jin tsoron abinda ka iya zuwa ya dawo "Zama yayi kusa da ita yana jan kafafunta had'e da so ya yaye zanin dake jikinta, jikinta ne ya dinga rawa" "cike da fargaba da tsoro tace""Abban mufida ka bari dan Allah ba sai ka gani ba." "Yace.""Aikuwa dole sai naga wannan tsokar data bullutso komai 'boye 'boyen ki sai na duba nagaji."" Cike" da zolaya yake maganar dan gabadaya ma ya mayar da abun wasa da dariya! Halisa hakura kawai tayi ta kyaleshi ya bude mata jikinta yana duba headquarter dinta yana laluben abun da idonsa Lokacin da idonsa yayi masa tozali da abinda halisa ke fada masa sai da gabansa ya fadi! da sauri ya "kalleta cikin wani irin yanayi na tashin hankali yace.""Wannan wane irin abune ya fito miki a matunci gashinan har yana kokarin rufe miki kofa shin tun yaushe ne hakan ya kasance dake.""?" "Halisa data muzanta! mirya na rawa tace""Jiya ne bayan abunda ya faru tsakaninmu sai kawai naji kamar" ana caccaka min allurai a ciki ga kaikyayin da gurin ya dinga yi bayan na gama sosawa ina shiga bandaki naga abun ya fito. "Kici kici da fuska yayi yana mata wani irin kallo yace.""Ki dauko min maganin da kika sa wanda ya janyo" "miki wannan masifar.""! Rantse rantse ta shaga yi ita wallahi bata sa komai ba...Yace.""Halisa kome ki keyi fa na sani nasan irin shaye shayen magunan da kikeyi akaina kuma watarana ina ganinsu da idona na tabbata akwai abinda kikasa a gabanki wanda ya janyo miki wannan abu saboda haka tun kafin ranki ya 'baci ki tashi ki dauko min maganin."" ! Halisa ganin yanda yasha kunu ne yasa ta mike a sanyaye ta bude wardrobe inda take ajiye ajiyen magungunanta ta laluba ta dauko kwalbar maganin saboda haukanta sai" da ta kusa sanya maganin gabadayansa kadan ta rage bayan kuma ba haka 'Yar sa'adu tace mata ba! Mika masa tayi ya kar'ba yana dubawa! Bude kwalbar yayi ya shanshana maganin yaji yana wani irin kamshi tabbas idan bai manta ba jiya yaji kamshin maganin a jikinsa dangwalar maganin yayi a hannunsa yaji wani irin danqo tamkar cingum!! yatsun hannunsa suka had'u da maganin suka manne guri guda! "Yace.""A ina kika samo shi.""? Shuru tayi gabanta na faduwa! Tambayar ya sake maimaitawa babu rahama" ko kadan a tare dashi!. Halisa dake neman mafita tana kuka ta shiga fad'a masa cewa a gurin wata "matane da Yaya Ramlatu take kaita gurinta. Jin ta kira sunan Ramaltu sai abin ya bashi mamaki yace.""" "Me yasa ko Yaya Ramlatu a cikin shirmen ki? ko dama ita take saki kina shaye shayen maganin mata bana son kiyi mata sharri dan ganin matsala na kokarin afkuwa dake.""" "Tace""Wallahi tunda nake ban san hanyar gidan boka da malami ba sai ta hanyar 'Yar uwarka Ramaltu" "kome nakeyi itace take d'ora ni a hanya."" Abbah Abbas bude bakinsa yayi kawai yana kallonta yace.""Halisa da bakinki kike fad'a min kina zuwa gidajen bokaye.""? Wani irin kuka ya kwace mata tace""Abbah Mufida ka gafarce ni wallahi ba laifina ne ni kad'ai ba Yaya Ramaltu itace take sani a gaba" muyi komai tare ni yanzu babbar matsalata wannan matsalar data tunkaro ni! Girgixa kansa kawai yake yana mamakin al'amarin! ikon Allah 'Yar uwarsa uwa daya uba d'aya itace ke cutar dashi da iyalinsa yanzu meye amfanin d'ora Halisa a turba mara kyau da Ramlatu keyi! menene amfanin cutar dashi da takeyi? me yayi mata a rayuwa da har zata bada goyan baya a cutar dashi idan halisa tayi masa asiri matarsa ce zata iya aikatawa amma ita saboda k'arfin zumunci da 'yan uwantaka bai kamata tayi masa haka ba Ya jima yana kallonta gabadaya kansa ya kulle ya rasa wane irin tunani zaiyi dangane da wannan mummunar maganar da yaji daga bakinta wai Ramlatu 'Yar uwarsa uwa daya uba daya itace take jagorantar matarsa domin xuwa gurin bokaye a asirce shi Halisa ganin yanda ya zuba mata ido yana mata wani irin kallo yasa takasa tsayar da hawayen dake zubo mata sai yanzu ta fahimci wautar da ta tafka gabadaya bata cikin hayyacinta shiyasa tayi su'butar baki ta fad'a masa abinda suke shukawa shin yanzu idan yayi bunkice ya tabbatar da gaskiyar maganarta da wane ido zata kalleshi na farko dai ita da kanta ta fad'a masa tana zuwa gurin malamai da bokaye babu wanda yayi mata sharri ballantana ta kare kanta...Sunkuyar da kanta tayi ta cigaba da kuka tana murza yatsun hannuwanta!.... "Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke ya Mi'ke tare da duba agogon dake daure hannusa yace."" Idan kina" iyawa ki tashi muje asibiti domin a duba a ga abinda keda akwai amma ki sani bani kika cuta ba kanki kika cuta wallahi idan kina zuwa gurin boka domin ki mallake ni 'Karyar ki tasha 'karya ni ba irin mazajen da mata ke kaiwa gurin bokaye bane wai ko kunyata baki ji ba da bakin ki kika fada min cewar kina zuwa gurin malamai! shin me na rage ki dashi? meye bana miki a rayuwa zaki dinga biye biyen bokaye me kike nema a duniyar nan wanda bana miki? Halisa tayi shuru sai kuka take. Ya girgiza kansa yana jin wani irin "takaici da mugun haushinta yace.""Kada kiga na rabu da Naja'atu ki dauka zan zauna dake ke kadai 'Karya kike koda baki kaini gurin malamanki ba sai na sake aure kuma budurwa zan aura in yaso sai ki sake d'aura d'amarar kai sunana gurin bokayenki. Sannan kuma maganin banza da kike sha a kaina kada ki daina kanki kike cuta bani ba."" Halisa kuka kawai take tana bashi hakuri wai wallahi tsautsayi ne ita bata" kaishi gurin malami dan a cutar dashi ba! Cikin tsawa mai tafe da hantara yace tayi masa shuru domin kwata kwata shi ba zai saurari maganarta ba "da bakinta ta fada ba wani shege ne yayi mata qazafi ba. Shuru tayi kamar ruwa ya cinyeta hawaye sai tsiyaya yake a kuncinta tana jinsa yana ta zabga mata cin mutunci tayi 'kus! da bakinta addua ma take ka da yace ya saketa!! Da zai fita daga dakin a fusace! yace.""Idan kinga dama kina iya fitowa na kaiki" "asibiti ba dan halinki ba."" Yana gama maganarsa ya fita daga dakin rai a 'bace!" Sosai Dr Sa'adatu ta shiga tsananin tashin hankali ganin abinda ya zazzago daga cikin matuncin Halisa dake kwance a wani hado kafafunta a bud'e! Dr Sa'adatu kasa aikin tayi ita kadai sai da ta kira 'Yar uwarta suka zo suna ta wagewa Halisa kafarta suna haska headquarter d'inta da wata 'yar 'karamar fitila "irin tasu! Dr Na'ima ta sauke ajiyar zuciya ta kalli Halisa da cinyoyinta suke rawa tsabar tension hawayen ma sun daina zuba sai zazzare ido kawai take Dr Na'ima tace""Gaskiya Hajia Halisa kin bani mamaki" wallahi! yanzu da girmanki da shekarunki kike aikata aiki irin na matasan yara kefa uwace ke zakiga yara na aikata abu mara kyau ki hanasu Fisabillilahi yanzu abinda kikayi ya kamata? ina amfanin cushe cushen maganin mata da kukeyi? kullum maganar da mukeyi kenan a kafafan sadarwa kancewar mata su daina irin wannan kwamacalar saboda muhimancin virginal d'insu ya wuce ace su had'a shi da komai! Guri ne mai muhimanci a jikinki mace da ya kamata ta mutuntuna shi amma saboda cutar kai kawai sai kuje ku dinga siyan maganin da baku san da wace tsiyar aka had'ashi ba kuzo ku cusa a matuncinku wai duk dan ku mallaki namiji humm! wannan zalintar kaine dan a yayin da wata matsala ta afku dake shi wanda kikeyi dominsa bazai saurareki ba karshe ma kina zaune ya dallo miki amarya sabuwa dal kuma baki isa ki hanashi ya aikata abinda yake so da ita ba. Yanzu dan Allah wa gari ya waya? Hajia Halisa kin dade kina sake saken maganin mata a gabanki ba tare da kina tunanin wata matsalar ba sai gashi kuma lokaci guda matsalar ta afko miki a sanda bakiyi tsammani ba. Dole na sanar miki da abinda ke faruwa dake hajia cikin tsokokin naman dake gabanki wani bangare ya samu nakasu sakamakon cushe cushen maganin da kike yasa naman gurin ya zazzago ya fito wanda idan ba'ayi da gaske ba to ruwan dake a fita a gurin zai iya janyo miki shiga matsala babba dan gurin zai iya fitar da tsutsa ba tare da kinyi tsammani ba! amma yanzu munyi kokarin mayar da tsokar data fito insha Allah akwai magungunan da zamu rubuta miki mutukar an siya kuma kina amfani dasu a kan 'ka'ida wannan ruwan dake fita a jikinki zai tsaya kuma wannan abun daya fito zai koma mazauninsa amma akwai sharad'i kan cewar maigida zai daina kusantarki har sai mun tabbatar da cewar gurin ya daidaita sannan sai ku koma mu'amular aure kamar koda yaushe! Sai kuma shawarata karshe da zamu baki dake da masu aikata hakan dan Allah ku daina ba lallai sai ta wannan hanyar bane zaku mallaki mazajenku kuma ku daina yarda da rantse rantse da dik wata mai magani za tayi muku akan ko wane irin maganin da zata baku tace kusa a gabanku. duk macen da tayi sabo da cushe cushen magani a gabanta to babu shakka tana tattare da dana sani anan gaba. Halisa kunyar duniya ce ta isheta Yara 'kananu sun gane mata sirrinta suna farfada mata maganar da "suka ga dama! kai gaskiya bata ta'ba nadamar rayuwa ba irin ta yau! tayi data sani yafi sau dari a cikin zuciyarta kuma sai yanzu tagane wautarta ta kuma gane mugunta Yaya Ramlatu take mata ai itama macace me yasa koda wasa bata ta'ba yarda ta siyi magani tayi amfani dashi ba, sai dai ita tayi ta ingixata tana siya da kudi mai tsada gashi yanzu matsala mai muni ta afkar mata ita tana gefe guda babu abunda ya dameta. Cike da kunya ta mike zaune tana gyara daurin zaninta gabadaya ta kasa had'a ido" dasu sabida kunya su kuwa da yake akan aikinsu suke sai bayani suke mata suna gargadinta akan ta daina abinda take aikatawa domin cutar da kanta take.. *Littafin na kudi ne..!* Koda zaki ganshi a gruop to na sata ne idan kina bukatar karanta book din ga yanda abin yake...Vip gruop#600 normal gruop#300 account 0542382124...Binta umar gtbank...Idan kati zaki turo kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *MANZIR _ALWAFIR ABUJA * _*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci magungunansu babu almundahana a ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu ko wace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye da akwai gruops na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rijistar dasu to kukanki ya 'kare idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_ 53 "To koda Halisa ta kira Yaya Ramlatu a waya ta sanar mata da halin da take ciki, Ya Ramlatu sosai ta shiga" tashin hankali mutuka domin a yanda Halisan take kuka tana fad'a mata abinda ya sameta ko waye dole ya tsorata sannan kuma hankalinsa ya tashi...Da yake mijinta ya dawo kuma itace da girki yasa ba taje gidan a ranar ba sai dai kullum tana kiranta a waya tana tambayar ta yanayin jikin nata. To da sauki dai za'ace dan Halisa ta shiga taitayinta sosai da sosai kuma bata wasa da shan magani da wanda akace ta dinga sawa a cikin headquarter din nata kullum sai tasa sau uku a rana shiyasa al'amarin yayi sauki dan ruwan dake fitowa ya ragu sannan kuma abinda yayi tsiro fito ya koma amma dai duk da haka idan tasa hannunta tana ta'boshi sai dai ba kamar kwanaki uku da suka wuce ba.... Gabad'aya Halisa tayi sanyi a gidan kullum tana daki a kwance tana tunane tunane tana zubda hawaye! Baba larai da yaran sai da suka fahimci cewar matar gidan na cikin damuwa dan duk irin iko da isar da takeyi a gidan ta rage ko magana za tayi musu cikin sanyin murya take...Shi kuwa Maigidan sabgar gabansa kawai yake yi dan a cikin kwanakin al'amuran sa suka sake bunkusa Ya samu wasu manya manyan kwangila daga gomnati shiyasa gabadaya baya samun lokacin kansa ballanatana na wani amma dai duk da haka yana kokarin shiga dakin halisan ya dubata kafin ya fice harkokinsa. Kofar na'isa ma tun ranar da yaje bai samu damar sake zuwa ba sai dai idan ya dawo gida yakan kira iyayen nasa a waya su gaisa da juna. Yaya Ramlatu bata samu damar zuwa duba Halisa ba sai da mijinta ya tafi tukkuna dan Kishiyarta Sakina "zaunar da mijin nasu tayi ta sheda masa duk irin abunda Ramlatun takeyi idan baya gari! Aikuwa ya fusata sosai dan sabida yasan halin sakina ba zata ta'ba fada masa karya ba, ya bud'ewa Ramlatu wuta sosai sukayi ta babu kyau babu dad'i! wanda har sai da Salim d'ansu ya shiga tsakani jin mahaifin nasa na yunkurin sakin mahaifiyar tasa hankalinsa ya tashi ya dinga bawa mahaifin nasa hakuri da kyar ya hakura ya kyaleta amma yayi mata tas tas! kuma jikinta yayi sanyi mutuka dan tunda taji furucinsa a kanta ta shiga hankalinta idan ya saketa ai ya cuceta da girmanta da komai yasa ta zawarci! sai ta hakura ta kyaleshi har ya gama hutunsa na sati uku ya tafi , a ranar kuwa da ya tafi ta dauki mayafi ta yafa ta fice" daga gidan tana yar da habaici! Sakina girgiza kanta tayi tana mamakin taurin kai irin na kishiyar tata Halisa ta warware samul! sai dai rashin walwalar maigidan a tare da ita ya sanya duk wani kuzari da "karsashinta ya dakushe a gidan, al'amarin da ya dameta mutuka gaisuwa kawai ke had'ata dashi da safe......idan kuwa ya dawo daga kasuwa da daddare ya zauna a palo yana dube dubensa a loptop to ta sake ta tunkari inda yake sai tayi nadama dan sai ya farfad'a mata munanan maganganun da zasu sanya zuciyarta bugawa. Dalilin da yasa kenan take kaffa-kaffa dashi amma dai duk wata kyautatawa tana yi" masa domin ta wanke kanta a gurinsa. Ga'badaya Halisa 'kin kar'bar uzirin Yaya Ramlatu tayi ta nuna mata fushinta sosai akan abinda tayi mata ace tayi ciwo irin wannan amma ba zata zo ta dubata akan lokaci ba sai da ta samu sauki sannan zata zo gaskiya ba taji dadin wannan abunba. Ramlatu ta fad'a mata cewar maigidanta ne ya dawo shiyasa bata samu damar zuwa ba kuma ina laifi tunda kullum tana kiranta a waya suna gaisawa! Jin haka yasa Halisa ta sake karatun ta nutsu ashe itace mara kishin kanta wacce take wulakanta auranta tana daukar mayafi ba tare da mijinta ya sani ba tana fita! gaskiya bata ta'ba tsammanin haka halin Ramaltu yake ba sai yanzu dole ne kuwa tayi taka tsantsan da ita dan ba zata sake yarda da ita ba tana ingizata inda zata ta kaita inda zata cutu ita kuma tana gefe guda babu abinda ya dameta......... To haka al'amura suka cigaba da tafiya tsakanin 'bangarori guda kowanne 'bangare yana yin abinda yake ganin shine daidai da rayuwarsa' Bangaran Naja'atu sai abinda yayi gaba dangane da soyayyarta da Bash kullum suna ma'kale a waya suna soyayya sunyi wani irin sabo na ban mamaki! Naja'atu ba tajin kunyar yin ko wace irin magana da Bash mutukar ta shafi soyayyarsu! Ta daina jin kunyarsa yanzu ko wace magana ya fad'a mata da wacce ta dace da wacce bata dace ba sai ta mayar masa da martaninta sosai ta zama mara kunya saboda alqarta da Bash wanda take ganin shine dadai da rayuwarta. A tsakanin wattani uku da tayi a gidan Alhaji tayi wani irin qiba da kyau na ban mamaki komai nata ya ciko ta bunkusa ta kai ta kawo babu abinda take bukata sai namiji ita kanta tasan tana da sha'awa a kusa shiyasa take Allah Allah ta 'karasa iddarta a daura musu aure dan ita dashi duk a matse suke da junansu Bash yace tana kammala idda da sati biyu za'a daura auransu dan ba za'a ja dogon lokaci ba. 'Bangaran Abbah Abbas kuwa tuni ya cire wata Naja'atu cikin zuciyarsa a da da farko ne al'amarin yake "damunsa daga baya kuma da yaga yanda rabuwarsu ya janyo masa kwanciyar hankali a gidansa dashi kankin kansa da kuma cigaba ta fannin harkokinsa sai kawai ya cireta a ransa ya godewa Allah gami da adduar Allah yasa hakan shine alkairi! Yanzu babban burinsa ya samu nutsuwa ayyukan dake gabansa suyi sauqi ya shiga duba wacce zai maye gurbin Naja'atu da ita dan tunda ya saba zama da mata biyu yana ganin ba zai iya bari ba, mussaman yanzu da Halisa ta zama hoto a gurinsa dan tsoron tunkararta yake da bukatarsa saboda gudun abinda ka iya zuwa ya dawo an samu da kyar ta samu lafiya yana jin tsoron yaje ya zunguro mata ciwon ya dawo shiyasa tsayin wattani uku da faruwar al'amarin bai tunkareta da wata maganaba, ba wai dan baya jin sha'awa ba kawai yana daurewa ne domin a zauna" lafiya. Misalin karfe hud'u da da kwata na yamma Salim yayi parking din dalleliyar sabuwar motarsa da Kawun nasa ya siya masa ya fito daga motar cikin shigar 'kananun kaya kamar koda yaushe yasha gayu kana ganinsa kaga dan burni....Daya bangaran ya nufa ya bude mata ta fito Wata matashiyar budurwa ce ta "fito daga motar mai matsakaicin tsayi! babu laifi tana da kyau daidai gargwado sai dai kuma bleecing din da takeyi ya soma lalata mata fatar jikinta kana kallonta zaka gane idanunta a bude suke! Tana sanye da atampa super dinkin doguwar riga mai falmaran da madauri a baya, tayi wani katon a cuci da yayi tsayi a kanta tayi rolling da karamin gyale kafafunta na sanye da takalmi mai tsayin dunduniya da madaurai! lebenta kuwa yaji jan jan baki tana da fara'a sosai dan data fito daga motar ma sai dariya take tana haske shi da hakoran makkan dake bakinta Salim sai murmushi yake yana jin dadin samun Salimat a matsayin matar da zai aure Salimat ta ture hamshakan maza masu kudi da muqami tace shi take so! shiyasa yau ya dauko ta ya kawo ta ta gaisa da kakaninsa Hajiya da Alhaji! Gefe guda kuma yana so ya cizgunawa zuciyar Naja'atu dan ba karamin jin haushinta yake ba dangane da nuna halin ko in kula da take masa gabadaya ta watsar dashi tana nuna masa dashi da babu duk daya tunda ta samu wanda ya" fishi! shine shima yau ya dauko Salimat ya kawo musu ita su ganta.. Hajiya da Naja'atu suna zaune a palo su Salim suka shigo! Hajia na ganin Salimat jikinta yayi sanyi ikon "Allah a ina Salim yaje ya samo wannan tsohuwar ai ta girmeshi! Daurewa tayi ta kawar da abinda ke zuciyarta ta karbi Salimat hannu biyu suka gaisa a mutunce.""" "Naja'atu na dan mirmushi tace""Salim wannan itace antyn nawa."" Yace.""Eh ya kika ganta."" Yar dariya tayi" "tace""Wallahi tayi kuma kun dace Allah ya nuna mana lokacin yasa zaayi damu.""" Salim baiyi tsammanin haka da gurinta ya dauka za taji haushi sai yaga akasin haka sai ma jan Salimat din "take da hira. Da zasu tafi hajia tayi wa Salimat kyauta sabulai da turaruka masu kamshi, Naja'atu har" bakin mota ta raka Salimat din tana daga mata hannu Wannan al'amarin da ya faru ya sanya salim jikinsa yayi sanyi ashe dai da gaske Naja'atu ta daina sonsa. Koda yake shima yasan Bash yafi shi komai da komai na rayuwa amma dai duk da haka yasan shine yake da nasara a kanta tinda har ya samu damar ruguza zamantakewar auranta da Kawunsa.dama babban burinsa kenan. Bayan Sati hud'u Naja'atu ta 'kare iddarta alhamdullhi Mahaifin Bash tare da 'yan uwansa guda biyu sunzo da sadakinsu an tattauna maganar daurin aure. cikin wad'anda suka kar'bi sadakin sun had'a da Alhaji Sama'ila Abbas Abbas 'Kanin Baba Malam mai suna Ya sayyadi Nazifi! Abbah Magaji kam koda ya samu labarin zuwan iyayan Bash din cewa yayi yana da uziri a kasuwa ba zai samu zama ba babu wanda ya tursasa shi akan dole ya zauna a karbi sadakin dashi ya kama hanya yayi tafiyarsa kasuwa. Abbah Abbas kuwa sai bayan sun kar'bi sadakin sun tsayar da ranar daurin aure sati biyu masu zuwa ya sami sukunin tafiya harkokinsa. Naja'atu a ranar yini tayi cikin farin ciki da annushuwa burinta zai cika na auran muradin zuciyarta idan ta tuna da cewar harda Abbah Abbas a cikin wa'yanda suka kar'bi sadakinta sai taji wani farin ciki ya lullu'beta tasan komai ya wuce a gurinsa kamar yanda ya fad'a mata a text dinsa tunda har ya tsaya a cikin al'amuranta to tasan da cewar tuntuni ya yafe mata shiyasa ta saki jikinta take harkokinta cikin kwanciyar hankali. *Massalacin Juma'a na b.u.k* Kamar yanda muka sani cewar mafi akasari malaman addini gami da limamai na da wani irin tsari da "a'kida a kan 'ya'ya yansu na aurar dasu ga wanda suke ganin yana da yanayin aqidar su da d'abi'arsu to hakane ya kasance da *Malam Sharif Bala* wanda ya kasance fitaccen malamin da yayi fice a jahar kano, wanda kuma ya kasance limamin babban massalacin juma'a dake b.u.k. mutumi ga Abbah Abbas" wanda suke da kyakkyawar alaqa mai kyau a tsakaninsu to yau bayan an idar da sallahr juma'a ya tsayar da Abbah Abbas din domun ya sheda masa irin kyautar da yayi masa saboda ganin cancantarsa da kuma yanda yake tsaye a kan addininsa da kuma hidimtawa addinin musulunci yaga dacewar ya bashi 'Yar sa Mai suna Zaibab yar kimanin shekara goma sha biyar To lokacin da Abbah ya gama sauraran uzirin Limamin sai yayi wani murmushi mai ma'ana yana "godewa da Allah a zuciyarsa, a lokacin da yake yunkurin dubawa kansa macen da zai aura sai gashi lokaci guda anyi masa kyautarta babu shakka ba zai watsawa mutumin qasa a ido ba, dik da cewar bai san yarinyar ba bai kuma ta'ba ganinta ba hakan ba zai hanashi kar'barta ba a matsayin matar auransa" "ba, yana adduar Allah yasa auranta ya zama alkairi a rayuwarsa." Malam Sharif yaji dadi sosai da Amincewar da ya samu daga gurin Abbah Abbas d'in inda a nan take yace Juma'a mai zuwa za'a a daura aure a ka kawo masa yarinyar gidanshi....Anan shi kuma Abbah "Abbas din ya kawo masa uzirinsa kan cewar yayi hakuri ya d'an bashi lokaci kadan zai yi wasu shirye shirye, malam sharif ya amince da uzirinsa amma bai yarda a ja dogon lokaci ba." **** Bayan sati daya da zuwan iyayen Bash ranar Alhamis Sai gasu Munira ita da ka'wayen mommynta da 'Yan uwanta sunyi mota biyu suna tafe da setin akwatina mai shida shida goma sha biyu kenan! Ko wacce akwati sha'ke da kaya tamkar za'a bude dan karamin kanti! akwai wani dan kit dake dauke da gwala gwala manya manya masu masifar nauyi da tsada! Al'amarin da yayi masifar firgita Baba talatu ita da 'Yan uwanta irin wannnan uban kaya da uban gold sai kace ana hauka!!! kafin 'yan kawo kaya su tafi zance ya soma tashi a unguwa cewa ashe Naja'atu mai kudi ta gani shiyasa ta fujirewa auran Mijin 'Yar uwarta kai kowa dai d irin abunda zai fad'a akan al'amarin da yawa daga cikin mutanan unguwa sai suka dawo ganin laifin Baba Malam a ganinsu ai shine bai tursasa yarinyar ta zauna da Auran madadin da akayi mata ba suna ganin shima kamar kwadayin abin duniya ne ya sanya ya amince da rabuwar auran to idan ba hakaba mutanan da sukayi maka hallaci ai bai kamata ya watsa musu qasa a ido ba. Haka dai rukuni rukunin mata suka dinga shigowa wai sunzo ganin lefa!Baba talatu ita da ido kawai take binsu dashi tana mamakin sanya ido da bindiddigi irin na mutane. Ya Ramlatu data samu labarin abinda ke faruwa bata zauna ba sai da taje ta kashe kwarkwartar idonta aikuwa ta dinga addua Allah yasa d'an yankan kai yarinyar ta daukowa kanta. Ita kam Naja'atu ko a jikinta al'amarin bai firgitata ba saboda tasan a irin kaunar da bash yake mata zai iya narkar da gabadaya kud'ad'ansa akanta. Ana ya gobe daurin auran da yamma Naja'atu ita da Salimat budurwar Salim dan yanzu sun zama qawaye tun salim na jin haushi har ya hakura ya kyalesu...Salimat ita ta kai Naja'atu gurin gyaran jiki aka gyara mata jikinta sosai sannan akayi mata kitso da lalle wanda yayi masifar yin kyau! Naja'atu ta fito amarya sai wani murmushi take tana jin nishadi Bayan sun dawo ita da Salimat din gidan Baba malam "suka shiga, nan suka tarar da Aunty maryam da Baba talatu a zaune suna tattauna al'amuran da suka shafesu...Naja'atu koda taga aunty maryam kunya ce ta rufeta sai ta sunkuyar da kanta kasa tana yar" dariya gami da gaisheta "Aunty maryam tace""Ai dole kiji kunyata naja'atu abubuwan da kikayi baki kyauta ba koda yake dawo da" "abinda ya wuce bacin rai ne saboda haka ina miki fatan alkairi da adduar Allah yasa gidan zamanki ne Allah ya baki zaman lafiya da nutsuwa zaman aure da mijinki."" Baba Talatu ta daure fuskarta sosai da" "sosai tace""Dama inaso na aika a kira ki domin akwai maganganun da nake so nayi dake!" "Naja'atu tayi shuru gabanta na faduwa Baba talatu tace""Babu abinda zance a cikin wannan auran naki" sai dai nayi shuru da bakina amma bana yi miki fatan nadama a rayuwarki ammafa ki sani duk wanda kika zalinta a cikinmu idan bai yafe miki ba sai hakki ya kama ki! Gobe za'a daura miko aure da wanda kike so kuma goben dai zaizo ya daukeki ku tafi can inda yake...Ina so na fada miki cewar ki zauna a dakinki duk rintsi duk wuya kada wata wahala tasa kiji sha'awar dawowa gida domin ki 'karasa zubar mana da sauran mutuncin da muke dashi a cikin unguwa! Babu maganar kawo kara ko kuma yaji ki zauna komai wahala tinda ke kikaji kika gani zaki iya! Daga karshe nake miki fatan alkairi da samun "nutsuwar da kike bukata.""" Kuka kawai takeyi ta kasa cewa komai! shin me wad'annan maganganun na mahaifiyarta suke nufi a kanta? Idan ta fahimta kenan Baba talatu na nuna mata cewar tunda suka dauketa suka bawa Bash sun yafeta daga zuriarsu kome.? Aunty maryam ce kawai ta rarrasheta amma baba talatu sabgar gabanta kawai takeyi....Jiki a sanyaye suka mike suka nufi gidan Alhaji Suna shiga gate din gidan Abba Abbas na kokarin fitowa daga mota Salim yayi saurin rufe motar bayan fitowar tasa. Salimat kasancewar tasan "matsayin sa a gurin Salim yasa da sauri cikin ladabin karya ta tsuguna har kasa tana gaisheshi! ya amsa cikin kulawa gami da kokarin ratse su ya wuce!! Naja'atu ta bisa da wani irin kallo gabanta na fad'uwa, gwiwa a sage suka shiga palon Nan suka sameshi shida mahaifiyarsa suna maganar data shafesu," "hajia Abu ganin sun shigo yasa ta saki fuskarta da fad'in"" Naja'atu kun dawo ai ina nan inata fad'a kan cewar wannan irin gyaran jiki ne ace tin safe ku fita babu ci babu sha ai dole ku galaibata! A sanyaye ta zauna kan kujera da fadin."" Wallahi hajia guraran La'asar muka dawo mun shiga gidan baba malam ne" "kuma munci abinci a can."" Hajia tace""To alhamdullhi dama tunani na inda zaku samu abinci kuci." "Naja'atu a hankali ta d'an saci kallon inda yake zaune tace""Abbah ina wuni inasu Mussadiq.""? Ya dan" "kalleta babu yabo babu fallasa yace.""Lafiya lau Naja'atu Mussadiq na gida lafiya."" Shuru tayi na second biyu kafin tace""Abbah Dan Allah gobe a kawo min su inaso na gansu."" Wani irin kallo ya watsa mata wanda yake nuna alamun baki isa ba, ya dauke kansa ba tare da yace komai ba ya mi'ke tsaye yana duba" agogon hannunsa ya kalli mahaifiyarsa tare da fad'in shi zai wuce gida sai da safe idan ya shigo daurin "aure."" Hajia tace""To Allah ya kaimu amma kada ka manta ka tawo mana da yaran domin nima ina" "kewarsu koda yake ai kai dama ka saba rowar 'ya'yanka ko gaisuwar juma'a baka kawo su."" Murmushi kawai yayi ya kama hanyar fita tare da fad'in ""Insha Allahu idan be manta ba zai zo dasu.Hajia tunda taji ya fadi haka tasan ba kawo su zaiyi ba sai kawai ta shiga girgiza kanta tana mamakin hallayar d'an nata" kamar shi kad'ai ne mai 'ya'ya a duniya baya so ko kad'an 'ya'yansa su matsa daga kusa dashi.. *Littafin na kudi ne...* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake. Vip gruop#600 normal gruop#300 account... 0542382124...Binta umar gtbank. Idan kati zaki turo kiyi min mgn ta whasap da wannnan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* Cikin rashin walwala gami rashin nutsuwar zuciya Abbah Abbas ya shiga gidansa . duk a sakamakon "tozali da yayi da yarinyar da ya riga ya cire ta gabad'aya daga cikin rayuwarsa to sai gashi a yau ganin da yayi mata ya tayar masa da tsumin sonta da jin wani irin kishinta gami da jin kishin yaron da take shirin aura, tunda ake maganar auran bai ta'ba shiga yanayi na damuwa da tashin hankali irin yau ba, wannan yana nufin cewar yau yayi mata ganin karshe kenan tun gobe zasu daura mata aure da wanda suka kar'bi sadakinta dashi wannan al'amarin shine ya janyo masa ji wasu kibiyoyin kishi wanda suka zo suka tokare masa a maqoshinsa! da kyar yake iya bude baki yayi magana tsabar yanda yake jin wani irin tu'ku'ki! bakin ciki a cikin zuciyarsa, koda ya fito daga motar bai tsaya duguwar magana da Salim ba sai kawai ya daga masa hannu ba tare da yayi wata magana ba ya nufi cikin gidan nasa. Salim kuwa cike da farin ciki ya juya kan motar domin fita daga gidan Halisa ta d'an ji dama dama" "gabadayansu suna zaune a palo ita da yaran ya shigo, suka shiga yi masa barka da zuwa harda Baba larai dake ta kokarin kintsa musu gurin cin abinci Ya daure sosai ba tare da ya nuna musu damuwar da" yake ciki ba ya amsa ya d'an tsaya yana magana da yaran kafin ya nufi dakinshi Halisa cikin faduwar "gaba da tararrabi tabi bayansa, samunsa tayi zaune a gefan gado yana kwance a gogon hannunsa, ta zauna a hankali tana sake yi masa barka da dawowa, bai kyareta ba kuma be hantareta ba kamar yanda yake mata a kwanakin baya ya amsa tare da umartata data hada masa ruwan wanka! Halisa cike da murna da farin ciki ta nufi toilet din tana adduar Allah yasa ya gama fushin da yake da ita dan ba karamin galabaita tayi da tsatstsauran hukuncin da yanke mata ba. To a takaice dai a daran ranar Halisa sai" da tayi yanda tayi ya kusanceta ita dashi suka kasance cikin wani irin yanayi na tsantsar tashin hankali da "damuwa, dan gabadaya Halisa tayi wata iriyar bud'ewa koda Abbah yasa joystick dinshi zuruf ta shige ya" dinga kokarin ganin ya samu satisfaction abun ya fassakara dan gabad'aya joystick d'in yawo ta dinga yi a headquarter din halisa ko'ina ya motsa sai yaji kwararo-kwararo babu inda ya ri'keshi! Gashi a lokacin yayi masifar kwadaituwa da al'amarin burinsa kawai ya samu gamsuwar da yake bukata amma babu dama! Cikin wani irin yanayi na tsantsar damuwa ya zare jikinsa a nata kawai ya zura kafafunsa kasan gado tare da dafe kansa takaici da bakin ciki kamar su kasheshi Halisa ta janyowa kanta babbar illah a rayuwarta ta cutar da kanta da abinda yake da mutukar daraja da martaba a tare da ita a yanzu da ita da babu duk daya suke a gurinsa tunda ta kasa dauke masa bukatarsa dama wannan dalilin ne yasa yayi ta fargabar tunkararta da wata magana saboda yana gudun 'bacin rai Halisa na zubda hawaye ta dafa "bayansa tana bashi hakuri duk tayi wani irin sanyi ta zama abar tausayi ita kanta tayi masifar tsorata da jin yanayin yanda gabanta ya bud'e! dan duk wani budiri da yake yi a gurin taji kuma ta gani Jijiyarsa ta kasa tsayawa guri daya sai yawo takeyi a gurin ita a karan kanta tayi tayi duburar da za tayi ta ri'keshi abin ya fassakara gurin ya riga ya sakwarkwace! ya saki tamkar bakin tsohuwar rijiyar data zaizaye ta tana kokarin ruftawa! kokarin kama jijiyar tasa takeyi wai tayi masa dabura irin wanda take masa idan tana al'ada! aikuwa a fusace! ya tureta ya mike yana jan tsaki! bandaki ya nufa domin ya gyara jikinsa, Halisa ta dora hannunta aka tana kuka mai tsanani da fad'in ""Na cuci kaina nayi wa rayuwata illah yanzu menene mafita a gareni? na lalata martabata da mutuncinta nasan yanzu zanyi ta fuskantar kalubalan rayuwa. ('Kalubale gareku mata masu sake saken maganin matsi a gabansu wallahi ku kiyayi kanku" akwai manya manyan cutuka da zaku janyowa kanku) Koda ya fito ya tarar da ita tana kuka babu walwala ko ta kwabo a tare dashi yace ta bashi guri baya son "damuwa yana so ya kwanta ya huta! Jikinta a sanyaye ta dauki rigar baccinta tasa ta kama hanya ta fita daga dakin cikin wata iriyar tafiya tamkar wacce ta rasa laka a jikinta, saboda tsananin bacin ran da yake ciki ko binta da kallo beyi ba ya sanya jallabiyarsa ya hau kan dadduma domin gabatar da sallar nafila" kamar yanda ya saba yi a dik daran duniya. *KADDARA TA RIGA FATA!!!!!* To jama'a da yawa sun sheda da daurin auran Naja'atu malam Sani da Bashir Aminu dan jarida akan sadaki naira dubu hamsin wanda bayan an watse daga gurin daurin auran kowa ya kama gabanshi Alhaji Sama'ila ya samu Naja'atun da kudin sadakinta ya damka mata a hannunta kana kuma cikin tattausan lafazi ya shiga yi mata nasiha mai ratsa jiki! daga karshe yayi mata fatan alkairi gami da zaman lafiya da mijinta. Naja'atu na kuka tana sauraran nasihar da Hajia Abu ke mata itama dai kwatancin irin ta mijinta tayi mata sannan itama tayi mata fatan alkairi tare da zaman lafiya a gidan auranta. Sannan da kanta ta dauketa ta kaita gaban iyayenta tace lallai su sa mata albarka kuma suyi mata adduar zaman lafiya a gidan auranta....Baba malam addua sosai yayi mata Baba Talatu itama tayi kokarin kawar da abinda ke cikin zuciyarta ta sanyawa auran albarka kamar yanda hajian ta bukata. Alhaji Sama'ila ne ya yanke shawara kan cewar dole a wakilta mata guda biyu ko uku domin suje suga inda za'a ajiye naja'atun Baba malam yaji dad'in shawarar da alhajin ya kawo babu shakka shawararsa a bar dubawa ce. Hajia Rabi amaryar Alhaji da wasu mutum uku daga bangaran Baba Talatu suka shirya tsaf domin rakiyar amarya garin jos. Naja'atu jin shawarar da aka yanke yasa ta k'ebe a guri "guda ta kira wayar Bash din ta sanar masa halin da ake ciki wanda shi da a tsarinsa kawai yana so ya dauketa ita kadai su tafi, to amma uzirin data kawo masa bai girgiza shi ba yace mata babu damuwa insha Allahu su jiraye shi da misalin karfe biyu na rana yana wani uziri daga ya gama zaizo ya daukesu, dama shi da abokansa guda biyu ne kawai suka rage dan ana gama daurin aure mahaifinsa da sauran jama'ar da suka rufo musu baya suka tafi...Shi da abokansa suka rage domin daukar amarya kamar" yanda suka tsara. Baba Magajiya da Hajia Rabi har suka wayi gari a garin jos a kuma gidansu Bash wato gidan alhaji Aminu "dan jarida basu ji ance su shirya a nuna musu gidan amarya ba, tun bayan saukar su garin aka saukesu a wani daki ba'a kara bi takansu ba sai dai daga zarar lokacin cin abinci yayi za'a kai musu mai rai da lafiya, Naja'atu kuwa dama suna sauka a garin ko awa daya basu yi ba Bash ya kirata a waya ta sameshi a dakinsa, Munira ce tayi mata jagora har dakin nasa, lokacin abokansa kowa ya kama gabansa sai shi kadai daga shi sai garamin wando yayi wata iriyar kwanciya yana shafa kirjinsa da hannunsa Naja'atu Ganinsa a haka ya tayar mata da wani irin feeling mai zafin gaske! a take tsigar jikinta ta dinga tashi ta dinga tunano irin zazzafar soyayyar da yayi mata al'kwarin zai gwada mata duk randa sukayi aure! Cikin kasala ta karasa shiga dakin, Bash a d'imauce ya mike zaune ya janyo hannunta ta fada saman kirjinsa ya matseta sosai yana kokarin sa hannunsa a cikin rigarta! ajiyar zuciya mai zafi ta dinga saukewa tana langwabewa a jikinsa yana cigaba da lugwigwitata tana jin dadi! bargo guda suka shiga ita dashi suka dinga tsotse tsotse suna rungume rungume! har dai suka kasa hakura suka fara kokarin aikata mai gabadaya! dan saboda yanda suka fita daga cikin hayyacinsu! Na'jaatu kanwa takar tsami kwarnafi ya" kwanta dan duk tarin sha'awar data tara tsayin wattanin da suka gabata sai da bash ya kawar mata dashi! Suka yini suna abu daya ko nan da can bash yaki bari ta fita a haka tana ji tana gani ta kwana a dakinsa sai da safe tukkuna ya bari ta koma cikin gidan Lokacin ne ta tarar da su Hajia Rabi sun shirya tsaf domun tafiya gida! cikin kunya gami da jin nauyi ta samu guri ta zauna tana gaishesu! suka amsa mata babu wata cikakkiyar walwala a tare dasu dan saboda gabad'ayansu sun sha jinin jikinsu dangane yanayin zamantakewar mutanan gidan! haka dai sukayi sallama da juna kowanne da damuwa a cikin zuciyarsa. Naja'at ta d'an ji damuwa da tafiyarsu amma dare yanayi da ta kasance da Bash ya mantar da ita kowa da komai ya shiga wanke mata zuciyarta da kalolin soyayarsa mai wahalar samu. To koda su hajia Rabi suka koma gida babu wacce ta fadi wata magana da zata tayar da hankalin jama'a! "Hajia ta shiga har dakin Amaryata bayan tayi mata barka da dawowa sai take tambayarta yanayin gidan da aka kai Naja'atun....Hajia Rabi tace""Guri ne mai kyau da tsari sannan kuma kamar yanda Bash din yayi al'kawarin cewar zai sawa matarsa kayan daki da duk wasu abun bukata ya cika alkawari dan haka gida sai dai a godewa Allah. Hajia Abu tayi farin cikin jin wannan labarin da amaryarta ta fad'a mata dan haka gabad'ayansu har gidan baba malam din sai kowa ya kwantar da hankalinsa suka yiwa amarya" fatan zaman lafiya tare da mijinta. A cikin kwanaki bakwai da auran Bash da Naja'atu sun 'barje soyayya sosai dan gabadaya Bash daina fita yayi kullum yana gida suna aikin abu daya Naja'atu tayi sabo da sex sosai dan wani sa'in ma kafin bash din ya nemata da wata bukata ta nemeshi! haka suke wannan rayuwa tamkar tumakai duk ibadah irin na Naja'atu tarayyarta da Bash sai da tayi rauni yanzu Naja'atu ta daina sallahr asubahi a kan lokaci kullum sai gari ya waye takeyi saboda raba dare suke suna aikin abu daya idan suka gama babu maganar su tsarkake jikinsu Bash zai rungumeta da najasa a jikinsu suyi ta bacci shi kuwa shed'an dama haka yake so kullum cikin kara ingizasu yake suna ya dinga qissima musu a zuciyarsu cewar dan basu yi sallar asubah a kan lokaci ba ai ba wani abu bane.... *Littafin na kudi ne...!* Koda zaki ganshi a gruopa na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake Vip group #600 normal gruop#300 accont ...0542382124...Binta umar gtbank...Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* ***** Rayuwar Bash da Naja'atu haka ta cigaba da tafiya cikin rashin tsari! Sun mayar da kansu tamkar tumakai basu da aiki sai abu d'aya su kwana su yini a makale da juna Naja'atu ta zama wata fitinanniya ta gaske inda shi kuma Bash ke kara d'ora ta a kan hanya ta hanyar kawo mata magungunan turawa wanda suke sanya ta tayi ta zubar da ruwan dadi yana hawa kanta yana shanyewa. Watansu "daya da aure Bash ya koma harkokinsa, sosai ta shiga damuwa saboda ta daina samun abunda take so a kai a kai dalili idan ya fita tun a subah baya dawowa sai cikin dare mafi a kasari a buge yake dawowa shiyasa ko taje kusa dashi baya iya yi mata komai haka zata hakura ta kwanta kusa dashi tana hawaye ta riga ta saba da sabon da yayi mata shiyasa duk dare kafin tayi bacci sai taci kukanta ta koshi Tsayin sati" "biyu haka al'amuran suka cigaba da tafiya a tsakaninsu Bash idan ya fita tun asuba baya dawowa sai tsakar dare kai wani lokacin ma kwana yake, a'lamarin ya dinga damunta yana ci mata rai Akwai ranar" "da suna zaune da munira tace""Munira dama Bash yana shaye shaye? kusan kullum sai naga kamar ba'a cikin hayyacinsa yake dawowa gida ba sannan dan Allah inaso ki fad'a min sana'ar da yake kinga fa idan ya fita tun farar safiya baya dawowa sai dare ya raba ke wani lokacin ma kwana yake a waje Munira" "tace"" To ke ina ruwanki da sana'ar da yake yi? ke dai ba'a kawo miki abinda zaki ci kisha ba me ya dameki da sanin dole sai kin san sana'arsa? Maganar shaye-shaye da kikayi Eh yanayi a wannan zamanin d'ai-d'ai na matasan samari ne wanda basa shaye shaye meye laifi a ciki tunda ba da kudin wani yake" siyan kayan shaye shayen ba. "Tace""Munira daga tambaya sai magana mai zafi ina laifi dan na tambayeki sana'ar da mijina yake yi ina" "da hakki na sani ai.""! Munira tace""Dan Allah Naja'atu mu bar maganar nan haka kada rayukanmu suzo suna 'baci na fada miki cewar ki bari duk ranar da kika rasa abinda zaki ci sai kiyi wannan tambayar amma yanzu baki da hurumin yinta tunda bamu gaza miki da komai ba, tsayin wata daya da kikayi a tare" "damu ki duba kiga yanda kika dawo jawur dake kinyi ki'bi kin murmure to me zai dame ki.""" Naja'atu na kokarin yin magana Mommy ta fito daga dakinta ganin fuskokinsu babu walwala yasa ta tsaya tana tambayar ba'asi! Munira cikin fusata! ta shiga fada mata abinda ke faruwa. "Mommyn ta yiwa Naja'atu wani irin kallo rai a 'bace! tace""Ke! bana son bindiddigi da sanin sai kin san" komai na sirrin gidan nan ki tsaya a matsayinki na matar Bashir meye na cewa dole sai kin san sana'arsa ko yankan kai yake ina ruwanki? kedai a kula dake a sauke miki hakkin ki shine bukatarki saboda haka kada na sake jin kinyi wannan maganar Bashir sana'a yake mai kyau da inganci a matsayinki na matarsa "kiyi masa fatan alkairi kawai ba sai dole kinbi diddigi a kansa ba.""" "Kanta a 'kasa tana kokarin mayar da 'kwallar dake kokarin sauko mata tace""Mommy kiyi hakuri ba nufi" "na mummunan abu ba amma tunda kince babu ruwana insha Allah bazan kara magana ba.""" "Mommy taja tsaki tare da kallon Munira tace""Ni zanje gidan bikin Hajia Lailah sai na dawo."" Munira" "tace""Mommy tsaya ni muje tare ni kaina zaman gidan ya isheni.""" Mikewa tayi da sauri taje ta dauki gyalenta suka fita ba tare da sun kula Naja'atu dake zaune a gurin ba. Suna fita hawayen da take ta kokarin mayarwa suka shararo a kumatunta wannan wace irin rayuwa mutanan nan sukeyi! kawai saboda ta tambayi meye sana'ar mijinta sai su rufeta da masifa! gaskiya idan hakane to akwai wani abu da suke 'boyewa wanda basa so ta sani! "Ta jima zaune a palon tana tunane tunane kafin ta miki jiki a sanyaye ta koma gurinsu, zama tayi kan" "kujera da wayarta a hannunta tana neman wayar Bash din, wayar na fara ringing sai taji an kashe ta kira sau biyar yana kashewa abinda bai ta'ba faruwa ba tunda sukayi aure! hankalinta ya sake tashi ga tsoron gidan ya baibayeta bargo taja ta rufe jikinta tana hawaye hade da cigaba da kiran wayar tasa...Bash dake tare da abokan harkarsa suna shirya yanda zasu shiga wani bank suyi sata a kufule! ya tashi daga cikinsu a sakamon kiran wayar da Naja'atun, a fusace! Yace.""Wai dallah malama meye kika damu" "mutane da kiran waya ne.""? Gabanta ya yanke ya fadi jin irin tsawar daya buga mata." "Murya na rawa cikin tsoro tace""Bash ni kadaice a gidan ina jin tsoro mommy da munira sun tafi gidan" "biki dan Allah ka dawo da wuri kaji ko.""" "Tsaki! yaja mai karfi yace""Zan koma cikin mutane kada ki sake ki kara kirana a waya wallahi kika sake" "kirana sai na wulakantaki idan na dawo gida haba! kin dameni da kiran waya sai kace ni kadai ne mai aure mtwww!!! Sai kawai ya kashe wayarsa ba tare da ya saurari ta bakinta ba.""" Naja'atu kasa'ke tayi da waya a hannunta gabad'aya hawayen da takeyi ma k'afewa yayi makogwaronta ya bushe qamas! tana mamakin abinda yake shirin faruwa da ita. Mommy da Munira kuwa ashe ba gidan biki suka nufa ba dama sun shirya fita tare domin zuwa suje su mayar da kayan lefen Naja'atu da suka hayo a wani katafaran kanti gabadaya da akwati nan da abinda suke ciki dama tun ranar da aka kawo Naja'atun washe garin ranar bayan su Hajia rabi sun tafi Mommy ta kira wayar d'aya daga cikin yaran kantin da sukayi hayar kayan yazo da mota ya kwashe kayansu a lokacin Naja'atu nacan gurin Bash suna biyan bukatar junansu wannan al'amarin ya faru turmin "atampa biyu da les daya kawai naja'atu ta tsira dasu a cikin kayan amma daidai da pant da breziya vest duk na lefan Abbah Abbas ne take amfani dasu, dan gabadaya kayanta hajia Abu ta had'a mata kaf aka kaita jos din dasu Kayan lefen Abbah da kayanta na gida su kawai take amfani dasu dik a tunaninta" akwatinnan kayanta na dakin mommy ta adana mata su kafin su tare a gidansu. Sai bayan sallar isha'i mommy da munira suka dawo gidan koda suka dawo babu wanda ya nemi inda "take, itace ma da ta gaji da kadaici ta kira wayar Munira tana tambayarta ko sun dawo...A wulakance tace mata E....Allah sarki naja'atu cikin murna ta nufi sashen...To sai dai rashin ganin walwala da sakin" "fuskarsu yasa jikinta yayi sanyi ta zauna a d'arare! tare da fadin""Mommy kun dawo lafiya."" ?" "Ba tare da ta kalleta ba tace""Lafiya lou."" Sai kawai ta juya suka cigaba da hiran 'Yan uwansu ita da" Munira...Har ta gaji da zamanta a gurin ta mike da niyyar tafiya Munira bata kulata ba jikinta babu kwari tayi musu sallama ta fita daga palon. "Koda ta koma gurinsu zama tayi ta zabga tagumi! ko ina babu dadi kenan gurin Bash da mutan gidan," dan kawai tayi tambaya sai su dauke mata wuta! ita a ganinta ba laifi bane dan ta tambayi sana'ar da mijinta yake. Da kyar ta iya cin abinci tayi wanka tayi sallar sannan ta shirya jikinta cikin kayan bacci ta kwanta tana tunane tunane gami da jiran dawowar mijin nata tayi al'kawarin zata cire tsoro da fargaba ta tambayeshi wace irin sana'a yake. har karfe daya na dare Bash bai shigo gidan ba lokacin bacci yaci karfinta nan ta b'ingire bacci mai nauyi ya dauketa. "A buge ya shigo gidan, ya watsar da abubuwan dake hannunsa a kan kujerar dakin, kai tsaye bed din ya" "durfafa! ya tsaya a kanta yana rangaji! Blet din 'kugunsa ya kwance ya sa'bule Jins din shima a gajeran da yake ciki ya cire shi, katuwar Sandarsa mai uban kauri da tsayi tayi tsalle ta fito hannu yasa ya shiga jijjigata yana wani irin nishi!! ya wani fizge bargon dake jikinta! a zabure! ta mike zaune tana kiran" sunansa had'e da kokarin kunna light din dakin. Ganinsa tayi zigidir a tsaye a kanta ga sandarsa a tsaye kamar zata tsone mata ido! bata ta'ba karewa jijiyar bash kallo ba sai yau! a tsorace ta matsa gefe tana zazzare idonta! gaskiya ta firgita da ganinta yanzu duk girmanta haka take ratsa jikinta? Kafin ta dawo hayyacinta ya janyo kafafunta da karfin gaske! rigar jikinta ya fizge ya had'a da wuyanta ya matse da rigar ya makure mata wuya sosai ya kwantar da ita kan bed din ruf da ciki ya hau kanta! ya kwanta Duburarta ya shiga bud'ewa da hannunsa yana kokarin zura yatsansa a gurin! Wani bala'in zafi taji ya ratsa mata jikinta! a tsorace! ta dinga kiran sunansa tana tureshi! shin me yake shirin faruwa ne! Ji tayi yana kokarin tusa mata sandar tasa a gurin! Wani irin kukan kura tayi ta bangajeshi da karfi ta mike zaune jikinta sai karkarwa yake! Bash me yake nufi za'ayi da ita *Luwad'i!!* Innalilihi wa'ina ilahi raji'un!. Wani gigitacan mari ya taska mata! a gigice! ya janyota da karfi ya sake mayar da ita ruf da ciki ya cigaba da yunkurin zurkud'a mata katuwar sandarsa a duburarta! Ihu! ta dinga kurmawa tana kiran sunan Allah! tare da magajiyar ya d'agata kada ya sake yabi wannan "hanyar da yake shirin yabi domin ba ita Allah ya hallata masa yabi ba.""" Wanda yayi nisa baya jin kira Bash! kokarin tura Sandarsa yake a gurin yana wani irin nishi tare da dukan "mazaunanta da hannuwansa!....Naja'atu jin da gaske dai bash yake yasa ta haukan karya ta dinga buge buge tana wani irin abu kamar zata tada iska sai wani irin fuffuka takeyi tana shasshekar kuka kamar ranta zai fita.....Bash wanda yake a tsananin bukace dayin harkar ya d'agata a fusace! ya kai hannu zai kwasheta da mari! ta riga shi! dan wani gigitaccen mari ta kwad'a masa jikinta na tsiyayyar da wani irin gumi!! Ta dira daga bed din tana kallonsa hawaye na karakaina a kuncinta tace""Turr!! da kai da halinka! Turr da wannan mummunar d'abi'a take Yanzu Bash ina a matsayin matarka ta aure kake kokarin yin luwad'i dani? Dama ashe haka kake dama harkar da kakeyi kenan shiyasa mahaifiyarka da Yar uwarka suke jin haushina dan na tambayesu hakika nayi nadamar za'ben ka a matsayin mijina kuma kaci amanar soyayyar da nake maka. Bash ya jima hannunsa dafe da kuncinsa yana mamaki marin da yarinyar tayi" masa! kamar shi *Bash* wata 'yar iskar yarinya zata sa hannunsa a fuskarsa ta mareshi babu shakka sai ya nunawa yarinyar nan ita karamar mara mutunci ce! A fusace! Ya sauko daga bed din ya d'auki blet dinsa daya cire ya durfafeta! da mugun karfi ya shiga lafta mata a jiki yana 'kunduma mata manya manyan zagi irin na marasa tarbiya. Naja'atu ihu! take tana "kuka hade da kare jikinta da hannuwanta Bash yana sake shimfida mata blet din a jikinta ta ko'ina! Wani wawan duka ya kai mata a kan nonota na dama! a take ta silale a gurin tana wata iriyar makyarkyata tare da fad'in ""Wayyo Allah nonona.""!! Bash ya jefar da belt din yana wani irin huci! nan kasan ties din ya danneta! yasa yatsansa cikin HQ d'inta ya dinga kwa'kula yana wani irin gurnani! tura yatsansa yake cikin gurin kamar me neman wani abu! sai da yaji ruwa ya shiga bulbulowa sannan ya d'aga kafafunta ya d'ora saman kafadarsa ya saita katuwar sandarsa ya zurkuda mata! wani irin bugu da jajjage ya shigayi ji tamkar mahaukaci haka ya dinga jajjaga jikinsa a jikinta yana ihu! had'e da murza nonowanta da suke" tsalle saboda tsabar yanda yake wujijjigata! Tsananin azabah! yasa Naja'atu fita daga cikin hayyancinta dan yanda Bash ke jajjagarta zaka gane ba dan taji dadi yake ba kawai dan ya azabtar da ita ne aikuwa ta azabtu mutuka dan tunda ya d'ora kafafunta saman kafadarsa ya rike bai saurara ba sai da yayi release sau uku tukkuna ya jefar da ita a gurin ya tashi yaje ya kwanta! Naja'atu wani irin nishin wahala take saki tana zirarar da hawayen azabah! yau Bash ya nuna mata rashin imani 'karara! gabanta wani irin motsi yake yana mata mugun zafi! ga cinyoyinta sunyi wani irin tsami! saboda yanda bash ya tale mata su tamkar wacce za'ayi wa kaciya!! motsin kirki ta kasa yi sai wani irin nishi takeyi kamar wacce ranta zai bar gangar jikinta.... *Littafin na kudi ne...!* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake Vip group #600 normal grupp#300 accont numbar...0542382124..Binta umar gtbank...Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar. *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* ***** Yanda Bash ya barta a wulakance a kasan ties a haka Wani wahalallan bacci ya d'auketa baccin mara dadi mai cike da firgici gami da mafarkai marasa kyau da ban tsoro!. Shida da wani abu Ya farka garau! ya mike zaune yana sakin wata shegiyar hamma! hannuwansa ya d'aga sama yana wata iriyar miqa!!! karaf idanunsa suka sauka a kanta tana yashe a inda take sai kace mushe sai baccin wahala takeyi Bash miyau ya had'iya yana lasar le'bansa na qasa tare da tsirawa tsayayyun nonowanta ido! wata gawurtacciyar sha'awa ce ta taso masa! tunda yake mu'amula da matan bariki bai ta'ba cin karo da wacce takai dad'in Naja'atu ba shiyasa idan ya hau kanta baya gajiya ko kadan ita Ido a rufe ya nufi "inda take..Daukarta yayi ya nufi bed din da ita yana kokarin sa'bule karamin wandon jikinsa ta bud'e idonta a tsorace ta matsa gefe guda dan har tana bugewa da katakon gadon! hawaye ne suka fara tsere a kumatunta murya na rawa tace""Bash dan Allah kayi hakuri kada ka kasheni! al'kawari da amana bece haka ba me yasa zaka dinga azabtar dani? dama ashe duk al'qawarrikan da kayi min na kar'ya ne? Jiya ka bani wuya ka zalince ni gashi kana so ka aikata sa'bon Allah dani! wallahi Bash ban ta'ba tsammanin haka" "halinka yake ba."" Tana wani irin kuka da makyarkyata take maganar." "Fuska a murtuke yace.""Ke ki shiga taitayinki wallahi duk sanda kika sake jifana da mummunar kalma sai" "naci kutumar ubanki! inace ke d'in matata ce sai da na bada sadaki naira dubu hamsin aka daura min aure dake to kan me zaki ce ba zanyi abinda nake so dake ba! ki sani duk ta hanyar da nayi niyyar saduwa dake tanan zan sadu dake banga uban da ya isa ya hanani ba tunda na biya sadaki.""" """Innalilihi wa'ina ilaihi raji'un! Bash kasan kuwa abinda kake fad'a? kasan irin bala'i da masifar da kake" kokarin jefa kanka a ciki? Wallahi Bash Ubangiji ya tanadarwa masu aikata Luwad'i azabah mai tsananin gaske a ranar lahira dan Allah ka tuba ka daina wannan mummunar dabi'a. "Wani bahagon mari ya kwada mata yana huci yace."" Dan Ubanki idan na daina ke zaki bani sana'ar yi ko" kece zaki dauki nauyina da duk abinda nake bukata da har zaki zo kinawa mutane wa'azi? to bari kiji ni ba kafurci nake aikatawa ba wannan harka na dauketa a matsayin sana'a kuma da ita na aureki dan haka ki iya bakinki a ko'ina idan naji maganar a bakin wani naki wallahi sai na baki mamaki sai na wulakantaki! "Bedshirt taja ta rufe jikinta tana wani irin kyarma! tace""To wallahi tunda haka ta kasance kai mushiriki ne" kuma fasiqi mara jin magana da rashin tsoron Allahn daya halliceshi! inaso ka sauwake min tun tafiya ba tayi nisa ba a tsakanimmu kuma ba zan gaji da fad'a maka cewar nayi nadamar auranka ba. Wani murmushi mugunta yayi ya tusa hannunsa a cikin tarin sumar dake kansa yana yamutsawa "yace""Haba beb ai banga uban daya isa ya sani na sake ki ba hahahahaha! qarya ma kenan! na sake ki? ashe bani da hankali ai kin shigo hannuna kenan yarinya ni ba gaulan namiji bane da zan sake ki wannan shashashan tsohon ya mayar dake gidansa! Ko yanzu idan na tuna bani na fara fasa tantanin" budurcin ki ba to nakan ji haushi da bakin cikin wani tsohon banza ya rig ! Kafin ya karasa maganar ta "katse shi ta hanyar d'aga masa hannu hawayen tausayin Abbah Abbas gami da nadamar abinda tayi masa na sakkowa a kuncinta tace""Bash kada ka sake zagin wannan mutumin a gabana domin ni yafi min kai sau dubu ka bani mamaki wallahi! nayi maka rana kai kayi min dare! meye banyi maka ba? wace irin sadaukarwa ce banyi maka ba amma abinda zakayi min kenan.""!!! Bash ya ta'be bakinsa yana mata kallon banza yace.""Wannan maganar da kikayi a yanzu ta nuna min cewar har yanzu da sauran kaunar tsohon mijinki a zuciyarki ko!? Da sauri tace""Kwarai kuwa Ba zan ta'ba daina kaunar Abbah Abbas ba domin yayi min hallacin da kai ka kasa yi mi......""Gigitaccan mari ya taska mata! ta zabura da sauri ta" dafe kuncinta tana kallonsa bakinta sai kyarma yake. "Ya tsira mata jajayen idonsa yana huci! Yace.""Zaki janyo nayi aika aika Naja'atu zan iya kashe shi wallahi!" "ke! baki san waye Bash ba ko.""!!? Ya'kare maganar yana zazzare mata idonsa jijiyar kansa tayi wani rud'u rud'u!. A tsorace take kallonsa tana mamakin furucinsa kisa! wannan kalma ta tsaya mata a cikin ranta!" Qus! tayi da bakinta jikinta sai rawa yake tana binsa da kallo taga ya nufi wasu drowars guda uku da suke kusurwar dakin Wani guri taga yana ta'bawa a jikin drowars ta bud'e sai kawai taga ya dauko bundiga ya nufo inda take. Ta mike tsaye a tsorace tana rufe jikinta da bedshirt tana karkarwa had'e da maqure jikinta a jikin bango(garu) zama yayi gefan bed taga ya budeta yana gyarawa tunda take bata ta'ba ganin bundiga da harshashi (bullet) ba sai yau! duk sanyin da ake a gari gumi takeyi sai kallonsa take le'banta na rawa "Ashe d'an ta addah ta auran bata sani ba, waye ya bawa Bash lasisin ri'ke bindiga a garin jos?" "Cikin gangarewa da nuna shi isheshshene taji yana cewa .""Wallahi duk ranar da kika sake ambato sunan" "wannan banzan tsohon mijin naki a ranar sai ya kwana a lahira da kaina zanje na sheqe!! shi da wannan bindigar ta hannuna! Zakiji mummunan labari wallahi zan kasheshi na kashe banxa babu abinda wani ko gwamnati ta isa tayi min.""!" "Murya na rawa tace""Kayi hakuri dan Allah ba zan sake ba insha Allahu.""! Ya mike da bundigar a" "hannunsa da fad'in"" Na fada miki bana magana biyu idan na sake jin sunan Abbas a bakinki to zakiji mummunan labari."" Shuru tayi tana kallonsa ya mayar da bindigar ya dawo inda take kusantota yayi" ya matseta jikin bangon yana shanshana wuyanta hade da so ya kwace bedshirt din data rufe jikinta dashi Kauda kanta ta shiga yi tana jin yanda zuciyarta ke tashi sakamakon jin wani irin wari mara misali da bakinsa keyi gabad'aya hucin numfashinsa da yake fesa mata nema yake ya bugar da ita dan wani irin jiri ne yake d'ibarta kanta ya dinga juyawa yana sarawa. Kafin tayi wani yunkuri ya dauketa cak! ta kaita bed ya kwantar da ita ruf da jiki ya haye kanta bayan ya sa'bule wandonsa! kuka takeyi tana tureshi da ragowar karfin da ya rage mata. ''Bash kaji tsoron Allah kada kayi Luwad'i dani kada ka janyo mana azabar Allah Bash!! kada ka cutar dani "ni ban cuceka ba ka nufi zuciyar da take kauna da alkairi kada ka nufe ni sharri! dan Allah kada kayi wannan harkar dani ni musulma ce.""!! Sambatun surutan da takeyi kenan tana tureshi had'e da kokarin kwace jikinta" A lokacin ne shi kuma shed'an yake 'kara tunzura shi ya dinga dukan mazaunanta yana bud'esu da kokarin tusa tsayansa a cikin duburarta sai wani irin nishi yakeyi yana goga mata jijiyarsa a jikinta!!! Sai da ya bud'e duburar sosai kana ya d'agota ya matse mata wuya tare da had'eta da jikin katon gado ya fara kokarin tusa sandar tasa a inda yayi masifar kwaid'utuwa dashi! """Wayyo Abbana! Wayyo rayuwata Abbah Abbas ka taimaka min! Ya Allah kada ka bari bukatarsa ta biya" "a kaina nayi nadamar wannan rayuwar da nake cikinta Allah ka dauki raina na huta da ganin wannan ranar.""! Surutan da takeyi kenan tana kuka had'e da kokarin kwace kanta! Bash bai saurareta ba sai ma sake matseta da yakeyi yana sake bud'e kafafunta yana kokarin shigar da sandarsa a inda yake so ""Innalilhi wa'ina ilahi raji'un! Na shiga ukuna Bash kada ka kasheni wallahi bazan iyaba! Dan" "Allah ka sawwake min wallahi na yafe maka! nima na gane rayuwa yanzu kuma nayi nadamar abinda na aikatawa Tsohon mijina Nasan hakkinsa ne yake bina Abbah Abbas ka gafarce kaga dai rayuwar dana jefa kaina a cikinta."" Kamar zautacciya haka ta koma sai sambatu take tana fizge fizge! duk ta galabatar dashi ta hanashi ya ciki muradinsa! A kid'ime! a kuma fusace! ya shiga kwakkwad'a mata mari! ta koina yana furzar da wani irin huci yace""Nace ki daina kiran mutsiyacin mutumin nan kin'ki ko lallai babu" "shakka sai ya ba'kunci lahira.""" "Tana kuka wurjajan! duk ta furgice ta fita daga hayyacinta tace""Bash dan darajar Allah da manzonsa kayi" "hakuri kada ka kashe shi wallahi Abbah bashi da laifi ni na zalince shi ka huce fushinka a kaina idan zaka zane ni da blet irin jiya bazan damu ba amma dan Allah kada ka sake yunkurin yin luwadi dani ka duba girman Allah kada ka sake zaka iya kwana a kaina kana biyan bukatarka bazan gaji ba zan jure har sai sanda kayi gamsuwar da kake bukata."" Tana maganar tana tsiyayar da hawaye tare da had'e tafikan" hannayenta guri guda sai wani irin mazari da numfarfashi take tamkar wacce tayi 'yar tsere. "Tsaki mai karfin gaske yaja ya wani janyo kafafunta ta fad'o saman jikinsa, rugumeta yayi qam!qam! a" jikinsa yana sansanta had'e da sumbutar sassan jikinta! Gabanta faduwa kawai yake tana adduar Allah yasa dai yaji magiyar da tayi masa wallahi zata iya yarda ya yini akanta mutukar bai zaiyi luwadi da itaba. Bash jagwalgwala ta ya cigaba dayi yana ta marmatsa mata brest sai so yake su hada baki ta'ki bashi "damar haka kyankyamim hada baki take dashi saboda yanda take jin yanda bakinsa ke fitar da wani irin wari mara misali To duk irin wassanni da bash ke mata hakan besa taji sha'awarsa a jikinta ba," gabadaya ma ruwan jikinta kafewa yayi HQ dinta ya bushe qamas! Tana ji tana gani Bash ya danna mata sandarsa a jikinta ta dinga rintse idonta tana jin yanda yake wani irin sukuwa a kanta yana bugunta da karfin gaske! Rashin wadatacciyr ni'ima ya sanyata tayi muguwar galabaita kafin Bash ya samu satisfaction tasha bakar wahala mutuka haka ya sauka daga kanta ta kasa motsa ko da yatsanta guda saboda tsananin halin azabar da take ciki. Tana sallar tana kuka gami da rokon Allah ya fitar da ita daga wannan babbar masifar data jefa kanta a "ciki! Eh gaskiya ne ita da kanta tasan rashin jin maganar na gaba da ita ne ya janyo mata shiga wannan masifar! sai yanzu take ganin irin babban kuskuran data tafka a rayuwarta! Wai shin ma meye laifin Abbah Abbas data 'kishi! meye aibunsa? zuciyarta tace mata ""Tsufa ne babban abinda yasa kika tsaneshi."" Wasu hawaye suka shararo mata! E gaskiya ne a wancan lokacin taqi Abbah Abbas saboda tsufansa tana ganin Kamar akwai matsala idan ta zauna dashi tunda ba tsaran auranta bane, shiyasa ta dinga yunkurin rabuwa dashi domin ta auri daidai da rayuwarta wanda take tunanin shine zai iya bata dukkanin soyayyar da take bukata!! Sai gashi kuma tun ba'aje ko'ina ba taga bambamcin auran tsoho da yaro! Wane irin kulawa da soyayya ne bata samu ba a gurin Abbah Abbas? wane irin rarrashi da kyautatawa ne mutum nan beyi mata ba? Tun kafin tasan wacece ita yake hidima da ita shine cinta shanta suturarta iliminta da duk wata dawainiya tata! komai na rayuwa ta samu a hannun bawan Allah nan, amma sabida tsabar son kai da rashin adalci ta watsa masa qasa a ido ta fujire masa ta dinga nuna masa qiyayya qarara har sai da ta samu nasara a kansa ya saketa, burinta ya cika na auran muradin zuciyarta sai gashi kwalliya bata biya kudin sabulu ba tun kafin aje ko'ina Bash ya yanke mata mummunan hukuncin da bata ta'ba tsammani ba, Hakika da ta zauna zaman aure da d'an ta'adda! kuma dan Luwad'i irin Bash to gwara ta zauna zaman aure da tsoho dan shekara saba'in ko tamanin dan tasan a gurinsa zata samu nutsuwa da kwanciyar hankalin da take bukata! Hakika sai yanzu tayi karatun ta nutsu kuma ta fahimci alherin da iyayenta suke nemanta dashi tana fujirewa shin yanzu da wane ido zata kalli Iyeyenta ? da wane kuma zata kalli Abbah Abbas din? me za taje ta fad'a musu yana faruwa a tsakaninta da Bash, shin zasu kar'bi maganar ta da muhimanci ko kuwa? Duniya dasu gabad'ayansu sun san da cewar ita da kanta ta za'bi Bash tace musu shi take so ya zama abokin rayuwarta... kuma har hanzu bata manta gargadin da Baba talatu tayi mata ba yana nan a kwakwalwarta bata manta ba! A" yanda rayuwar nan ta juya mata baya wa zata tunkara a cikinsu ta fad'a masa matsalarta ya yarda..... *Ayi hakuri da error * *Litttafin na kudi ne...!* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin book din ga yanda abin yake. Vip Gruop#600 normal group #300 account.. 0542382124....Binta umar gtban Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *MANZIR _ALWAFIR ABUJA * _*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci magungunansu babu almundahana a ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu ko wace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye da akwai gruops na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rijistar dasu to kukanki ya 'kare idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_ *******Humm! Rayuwa kenan Naja'atu 'yar gata kuma 'yar gaban goshin Abbah Abbas ita ce kasance "a wulakance a lalace a hannun Bash! shi yaci mutuncinta mahaifiyarsa da 'Yar uwarsa suci mutuncinta su wulakanta su takata yanda ransu yake so, gabadaya munira ta sanja mata tsakaninsu kallon banxa ne" "da baqar magana, sosai take cikin mawuyacin hali da takura wayarta kuwa dama tuntuni ya 'kwace dan" ranar da zai kwace wayar tana jin mahaifiyarsa na zugashi a kan ya kwace wayar domin wai barin wayar a hannunta a kwai matsala kada taje ta tona masa asiri a gari Aikuwa a ranar ya kar'be wayarsa ya "barta cikin halin bakin ciki da damuwa kasancewar wayar na d'ebe mata kewa sosai haka dai cigaba da ta kasance cikin damuwa gami da nemawa kanta mafita domin tana ganin Bash da mahaifiyarsa da 'Yar uwarsa rayuwarta kawai suke nema to idan ba hakaba me tayi musu da zafi da zasu dinga a zabtar da ita! abinci sun daina bata mai kyau wani sa'in ma yini take da yunwa a gidan sai taji tana shirin mutuwa tukkuna za taje ta tsaga billeta tace tana bukatar abinci to nan ma sai anja mata rai za'a sa mai aiki ta kawo mata shima ba wanda zai gamsar da ita ba, hakanan take hakuri ta kar'ba taje taci ta kwanta, sannan komai dare Bash ya dawo daga yawonsa haka zai afka mata yayi ta sasakarta tana ihun wahala saboda gabadaya rashin gamshashshen abinci mai gina jiki yasa ni'imar ta ta dauke kullum a bushe take qamas! haka bash yake gwada mata rashin imani yayi ta jajjagarta yana kokarin kaita lahira Aikuwa" kafin kice kwabo ta lalace ta zama tamkar zautacciya kusan kullum cikin firgici take daga ta kwanta bacci za tayi ta muguwayen mafarkai marasa dadi! rashin abinci da rashin kwanciyar hankali da kulawa ya mayar da Naja'atu shuru shuru kullum tana dakinta a zaune ko a kwance yanzu ta daina wasa da ibadah lokacin sallah nayi za tayi ta d'aga hannunta sama tana rokon Allah ya kawo mata mafita. Ranar Lahadi Mommy da Munira tun safe suka fita gidan sai ya kasance shuru kadaici da damuwa ya isheta sai ta shirya tsaf ta fito cikin hijabi ta fito harbar gidan tana kalle kalle so take ta samu ta fita daga gidan taje ta nemi gidan mmn sajida ko zata taimaketa da shawarwari tunda dai mmn sajida tasan labarin rayuwarta to watakila akwai irin taimakon da za tayi mata. Maigadin gidan ne taga ya bude gate mota ta shigo gabanta ya yanke ya fad'i dan a tunaninta ko Bash ne "har tana mamakin abinda ya dawo dashi kuma! sai taga bashi bane mahaifinsa ne ya fito daga motar yana sanye da 'kananun kaya shart da jins da farin gilashi a idonsa, dama bata ta'ba ganinsa ba sai a hoto kallo daya tayi masa ta sunkuyar da kanta tana jin faduwar gaba! wani irin kallo Alhaji Aminu yake" "mata, da sauri ta tsuguna har kasa tana gaisheshi." Yana wani murmushi irin na shegun 'yan duniya ya amsa yana shafa gemunsa ta mike tana kokarin "komawa gurinsu....Yace.""Doghtar zo muje akwai muhimiyar maganar da nake so nayi dake."" A sanyaye ta kalleshi tana mamakin maganarsa wace irin magana zaiyi da ita, cikin zuciyarta tace ko dai ya samu labarin bakar wahalar da muta nan gidan suke baki zai rarrasheki! A jiyar zuciya ta sauke tabi bayansa" cikin gidan tana jin faduwar gaba kad'an. Kasa nutsuwa tayi a palon sanin da tayi cewar babu kowa hatta da mai aiki bata zauna ba itama ta tafi sabgoginta tunda tasan da cewar masu gidan basa nan tayi tafiyar ta sai da yamma zata dawo tayi aikace aikacenta. Tana zaune a inda take taji muryarsa yana kiranta daga cikin dakinsa...Ta amsa da sauri ta mike ta nufi dakin Gabanta ne yayi wani irin faduwa ganinsa daga shi sai gajeran wando a tsaye a bakin kofar dakin Da sauri ta juya zata fita kawai taji ya ri'ki hannunta ya janyota ta fad'o jikinsa! taji yana kici kicin "kulle kofar. ""Innalillahi wa'ina ilahi raji'un! Abinda ta ambata kenan tayi kukan kura ta bangaje shi da" mugun gudu ta fita daga dakin tana gyaran hijabinta daya tattare! A sukwane ta fito a harabar gidan tana rarrabawa idonta sai haki! take tana waige waige! can ta nufi bakin gate gabanta na dukan uku uku! tana kokarin bude karamar kofa maigadi ya fito daga dakinsa ai kafin ma ya karaso ta bude ta fice daga gidan maigadi daya fuskanci cewa itace sai ya mayar da kofar ya rufe ya koma ya zauna hankalinsa kwance dan baiyi tunanin guduwa tayi ba... Hanya ta kama ta dingi tafiya tanayi tana goge hawaye gami da nanata kalmar innalilihi wa'ina ilaihi raji'un! jama'a wane irin gida Allah ya kaita Ashe shima maigidan d'an busuru ne? wai shin to da yake kokarin kulleta a dakinsa me yake shirin yi mata. "Tsayin wata uku da tayi a gidan bata ta'ba ganinsa ba saboda washe garin daurin su yayi tafiya, a" tunaninta dawowarsa kenan! amma saboda tsabar shi mara mutunci ne zai haike mata a matsayinta na matar d'ansa! Babu shakka rayuwarta na cikin gagarimin had'ari! dole ne ta nemawa kanta mafita tun kafin wata mummunar qaddara ta afka mata. "Taci bakar wuya kafin ta kai kanta gidan mmn sajida, lokacin ma da taje bata nan ta tafi kasuwa cefena," sai ta samu rumfar kwanon da jama'a ke zama ta zauna tana wani irin nishi mai wahalar gaske Duk "wanda zai wuce sai ya kalleta kai wasu ma har tsayawa suke suyi mata magana, ganin haka yasa tayi shahadar shiga gidan mmn ladi! tana shiga soron gidan ta soma jin muryar mmn ladi sai zage zage takeyi! kafin tayi wani yunkuri taga mutum ya fito yana gyara kwalar rigarsa sai zabga tsaki yake, da yake Saleh ba a cikin hayyacinsa yake ba bai ma ganta ba yasa kai ya fita daga gidan Naja'atu tayi kasaqe tana jiyo" "mmn ladi na fad'in ""Shege tsinanne wallahi na daina yarda kana yi min hawan qawara kullum sai kazo kana cikani da dad'in baki da daddare ka haye kaina kayi ta suburbudata amma washe gari idan na tambayi kudin cefane kace baka dashi to wallahi na daina yarda da kai tunda abun ya zama rashin mutunci to kwanan auran ma siyarwa zanyi idan kana bukata sai ka biya kudin zan barka kayi aikin" "banza kawai.""!!" Naja'atu gabanta ya tsananta fad'uwa shin wane irin zaman aure mmn ladi takeyi da mijinta? idan akwai matsala su rabu ai babu dole mai zai sanya kullum su dinga tsinewa junansu. Gidan ta shiga da sallama "a bakinta, mmn ladi na huci! tace"" Ke kuma daga ina? dama baki tafi garinku ba.""? a sanyaye tace""Na" "tafi qaddara ta sake dawo dani.""" "Mmn ladi taja tsaki mai qarfi tace""Ke! kowa da kika gani yana da matsala dan Allah kada kice zaki fad'a" min matsalarki ki rabu dani naji da matsalar da ta dameni. "Zama tayi kan tabarma tace""Mmn ladi dan Allah zauna mu fuskanci juna."" Mmmn ladi tayi mata wani" "irin kallo kafin ta zauna tana kallonta tace me kike shirin fad'a min ne.""?" "Murya na rawa tace""Mmn ladi dan Allah ki dinga sawa zuciyarki ruwan sanyi kafin na shigo gidan nan" duk naji irin xage zagen kikeyi dan Allah ki daina babu kyau zagin miji da tsiyatashi ko banza kun haihu da juna idan ya lalace zaki fi kowa jin ciwo saboda yayan da kuka haifa tare. "Mmn ladi ta sauke gwaron numfashi kafin tace""Wallahi naja'atu mutumin nan bashi da mutunci tunda" "ya aureni yake bani wuya, gabadaya baya sauke hakkina da yake kansa kin dai zauna kwana biyu kinga irin rayuwar da nakeyi abinci ma da kyar yake bani! da farko na dauka babu ce sai da nayi bunkice na gane cewar yana samun kudi kawai yana bakin cikin ya kawo gida sai dai yaje ya lalatar a waje da daddare kuma ya isheni da jaraba shiyasa na yanke shawara kan cewa duk ranar da ya nemi yayi wani abu dani sai ya biya ni dan ni ba shashar mace bace.'' Naja'atu shuru tayi tana nazarin maganar matar tace""Mmn ladi ki daina wannan maganar dan Allah musulunci bai hallata hakan ba, ki amince da mijinki a duk lokacin daya bukace ki mutukar ba a cikin tsarki kike ba, sannan dan Allah ki daina kama mijinki da kokawa kuna dambe a gaban yara kinga karfin ku ba daya bane kuma kina da 'ya mace watarana abinda kika aikatawa akan babanta itama shi zata aikatawa mijinta, kuma idan ban manta ba kwanaki naji mmn sajida na yi miki nasiha kan cewar ki dinga hakuri da kad'an! idan ba zaki iya ba to ki kama sa'ana shi kuma ki kyaleshi da halinsa mutukar yana zalintarki sai ubangiji ya saka miki wannan tashin hankalin da" kikeyi da masifa ba shine zai kawo miki kwanciyar hankali ba. "Mmn ladi jikinta yayi sanyi jin nasihar da naja'atu tayi mata tace""Shikkenan na'ajatu zanyi kokarin ganin" "na dauki shawararki amma wallahi abin ne da ciwo ace dari biyu shine kudin cefanan gida ki duba kiga yanda rayuwar nan ta koma komai yayi tsanani!! kuma yanzu da kike maganar na kama sana'a ina naga jarin da zanyi sana'ar dashi."" ? Ajiyar zuciya ta sauke tace""Insha Allahu ni idan na samu yanda nake so zan baki jari ki dinga sana'a domin ki rufawa kanki asiri amma dan Allah ki daina wannan mummunar d'abiar da kikeyi a gidan auranki."" Allah sarki Naja'atu rayuwa ta koya mata hankali wai yau itace takeyi wa wata nasiha...Mmn Ladi tace""To nagode sosai Naja'atu Allah ya saka da alkairi."" Naja'atu na kokarin yin magana mmn Sajida ta shigo gidan ganin naja'atu yasa ta tsaya tana mamaki! murmushi mai ciwo naja'atu tayi tace""kinyi mamakin ganina ko.""? Mmn sajida tace""Wallahi kuwa ai na dauka kin tafi.""" "Naja'atu a sanyaye tace""Na tafi mummunar qaddara ce ta sake dawo dani.'' Mmn sajida ta rike bakinta" "had'e da fadin wace irin mummar qaddara kuma.""? Mmn Ladi tace""Nima mamakin maganar nake dama" "yanzu nake shirin tambayarta sai gashi kin shigo.""" "Mmn sajida ta zauna kusa da ita tace""Ni wallahi jikina yayi sanyi da jin wannan maganar naja'atu wace" "irin qaddara ce ta dawo dake garin jos.""?" Zafafan hawaye ne suka shigo zubowa daga idonta tana kuka mai tsuma zuciya ta shiga basu labarin "abinda yake faruwa, tun daga farkon al'amarin harkarshe bata 'boye musu komai ba sai da ta fad'a musu." "Maman Ladi ta rike baki cikin mamaki gami da al'ajabi tace Ikon Allah ""Yanzu Naja'atu dama ashe kece" matar da Bash ya aura? mu dai mun samu labarin cewar yayi aure ya auri yar kano kuma bazawara har a gari a kan dinga surutu da yawa mutane na cewa dama sai da yaje inda ba'asan halinsa ba ya nemi aure dan gabad'aya mu nan mun sanshi kuma mun san mummunar sana'arsa ta 419 (damfara) gami da sace sace a manya gurare uwa uba Harkar luwadi da yake yi Gaskiya duk wanda yake da hankali ya kuma "san waye bash to ba zai dauki 'yarsa ya aura masa ba dan a zahirin gaskiya bash ba mutumin arziki bane kuma ba mutumin da zakayi fatan ka had'a zuria dashi bane! sai kuma maganar mahaifinsa da kikace ya kulleki a daki yana neman lalata dake gaskiya nayi mamaki sosai dan a sanin da jamaar gari sukayi masa mutumin kirki ne! to amma babu mamaki Ubangiji ne yayi nufin tona masa asiri watakila ya dad'e yana lalata da 'ya'yan mutane sai yanxu asirinsa ya tuno gaskiya duniyar nan a bar tsoroce wallahi naja'atu na tausaya miki da tun farko kinzo ki fad'a min halin da ake ciki wallahi da bazan barki ki auri Bash ba(Allah sarki mmn sajida a lokacin da idanun naja'atu suka rufe kome zaki fada mata a kan auranta da bash ba zata dauka ba) Mmn Ladi tace""Ni wallahi abin ne ma yake bani mamaki na rasa abinda zance Allah dai" yasa baki da ciki dan shine babbar matsalar a yanzu. "Naja'atu na goge hawaye tace""Bana tsammanin inada ciki mmn ladi ni tunani na yanda zanyi na ku'buta" "daga hannun wad'annan mugwayen mutanan.""" "Mmn Sajida tace""Gaskiya zamanki a tare dasu bai taso ba yana da kyau ki nemawa kanki mafita kije gida" "ki shedawa iyayenki halin da ake ciki.""" """Mmn sajida ina jin kunyar tunkarar iyayena da wata magana wallahi mahaifiyata tayi min gargadi" "kancewar kada na sake nazo gida da wata matsala tunda dai ni naji na gani da auran bash to naje na zauna nayi hakuri Mmn Sajida tace"" To ai wannan matsalar babbace dole su san da ita idan baso suke" "ki shiga cikin masifa ba."" Shuru tayi tana kuka gami da tunanin yanda za tayi." Naja'atu haka ta wuni a gidan mmn sajida suna ta bata sharwarin yanda za tayi da zata tafi mmn sajida "ta bata dari biyar hade da soyayyan nama mai uban yawa, har bakin titi suka rakota ta shiga napep su kuma suka juya suna sake tattauna maganar..." Cikin fargaba ta shiga gidan tayi sauri ya shiga gurinsu ta rufe da key sabida har yanzu tsoro takeji kada 'katon kwarton gidan yasan ta dawo yazo ya afka mata Da yake taci abinci ta koshi a gidan mmn sajida bata damu ba sai tayi kwanciyarta tana ta istigifari a cikin zuciyarta. *ANGO* 'bangaran Abbah Abbas kuma al'amura suna ta tafiya cikin tsari da kwanciyar hankali maganar auransa "da Zainab ta kammala iyayensa da duk wani makusancinsa yasan da maganar, Halisa ta shiga cikin tsantsar tashin hankali da damuwa jin cewa mijin nata zai auri yarinya mafi karancin shekarun Naja'atu sai duk ta raina kanta kullum tana kwance a daki tana nadamar rayuwa. Duk abinda ake bukata ango" yayi Abbah Abbas yayi wa yarinyar sannan itama halisan yayi mata dadai gwargwado duk domin ya kwantar mata da hankalinta. Gidanshi dake 'Danbare yasa aka sake qawata shi da abubuwan morewa rayuwa da jin dadi! dama bangare uku ne nashi guda na amarya daya na uwargida daya. Kafin "zuwan ranar daurin auren da kansa yaje har gidan Limamin yaga yarinyar masha Allah ya yaba sosai da ita Zainab mai matsaikacin tsayi da 'yar qiba amma ba mai muni ba, kuma masha Allah tana da kyau daidai gwargwado dan ba za'a sata a layin munana ba, sai dai yanda yarinyar ta kar'be shi tana nuna masa iyayi da rashin ta ido abin ya bashi mamaki mutuka ya lura da yarinyar na sonsa sosai mussaman yanda take yawan kiran wayarsa a kai a kai da sassafe zata kirashi ta gaisheshi idan rana tayi zata kirashi ta tambayeshi yanayin kasuwa, idan dare yayi kafin ya kwanta sai ta kirasa tayi masa sai da safe! Sai al'amarin ya dinga bashi mamaki mutuka yana mamakin wayo da dubarar yarinyar babu shakka ko cikin mata uku ya ajiyeta zata iya zama dasu saboda tana da wayo da kuma iya mu'amula ba irin Naja'atunsa sarkin rigima da koke koke ba. Yanzu dai komai ya kammala an kuma tsayar da ranar da za'a daura aure" juma'a mai zuwa bayan an gabatar da sallar juma'a. ****** Naja'atu daina shiga sashen su mommy tayi har sai da ta tabbatar da cewar maigidan ya gama hutunsa ya tafi sannan ta cigaba da shiga nan ma idan ta shiga da sun gaisa bata dadewa take fitowa! Munira "kuwa dama dawowar mahaifin nasu ne yasa ta tsahirta da abinda take, yana tafiya kuwa ta cigaba da" yawace yawacenta sai taje gidan Muktar tayi sati daya ko biyu acan ba tare da damuwar mahaifiyarta ba.......... bash da abokanan sana'arsa sunyi nasarar shiga wani babban bank sunyi gagarimar sata ta maqudan "kudade, dama duk sanda suka bushi iska haka suke shirya irin wannan ta'addacin saboda sun tanadi matakan kare karansu kome zasuje suyi a guri babu wanda zai gansu sai bayan sunyi sun gama ma'aikatan gurin zasu fahimci akwai matsala haka zasuyi ta binkice daga inda matsalar ta afku idan sun kasa ganowa sai su hakura. To yau dai Allah ya nuna musu ikonsa idan sunayin abu suna ganin babu" "wanda yake ganinsu to shi yana ganinsu kuma yau yayi nufin tona musu asiri bayan sun fito daga bank din sun shiga motocinsu lokacin CCTVCAMERA ta tona musu asiri dan wani irin qara ta dinga yi tana nuna akwai babbar matsalar dake faruwa, kafin kace kwabo ma'aikata da jamian tsaro kowa ya ankara sun fito hankali a tashe nan suka hangi motacin su Bash na kokarin fita daga bank din, a guje! jama'an tsaro suka shiga mota suka bi bayansu da harbi! abunka da dare gari yayi shuru sai karar harbi ne ke tashi Su bash sun tsorata mutuka dan rana bata ta'ba kwace musu irin yau ba, sai kawai kowa ya shiga" kokarin tserar da kansa. Bash tunda ya samu ya sunkuci wata jaka wacce take sha'ke! da kudi yayo fit ya fito daga motar ya nausa cikin daji ya dingi gudu shima yana sakin harbi da bundigarsa. Sauran su ganin "matakin da bash ya dauka dama shine garkuwarsu tunda shine kadai yake da bindaga, sai kawai suka bude mota suka fito da gudu suna kokarin arcewa! Cikin ikon Allah Allah ya bawa jami'an tsaro sa'a suka" "rufar musu, da harbi a take suka fad'i a gurin suna wani irin ihu! da rirrike kafafunsu." Bash kuwa yana samun nasarar shiga gida sai ya sauke ajiyar zuciya ya sake rike jakar kudin dake "hannunsa da kyau, yana wata iriyar tafiya ya nufi bangaransa, maigadi dai binsa da kallo yake dan yanda ya shigo gidan a guje kuma a gigice ya nuna masa cewar akwai babbar matsalar dake faruwa." Naja'atu na tsaka da bacci ta dinga jin motsi da buge buge a firgice ta mike zaune tana kokarin kunna "hasken dakin, Shi ta gani yana ta aikin zazzage kudi yana shiryawa cikin wata akwati mai fadi! A tsorace tace""Bash wannan kudin fa.""? ""Shiiiii.""! Yayi mata hade da dora yatsansa a saman le'bansa! Naja'atu" tayi shuru tana kallonsa gabanta sai buguwa yake babu shakka Bash sata yaje yayo a wani gurin Tana zaune tana kallonsa ya gama shirya kudin tsaf-tsaf taga ya mike ya bude gurin kayansa ya dauko wasu bakake yasa a jikinsa ya sunkufe kansa da bakar hula ya saka face mark a fuskarsa hankalinta ya tashi miyau ya qafe a bakinta lokacin da taga yazo ya tsaya a kusa da ita sai da ta kusa sakin fitsari! jajayan "idanunsa kawai take kallo, taji yace.""Naja'atu yau karshen zama dake yazo na sakeki saki uku! inaso ki" "cireni daga rayuwarki ki manta kinsan Bashir a rayuwarki, burina ya cika na samu kudaden da zasu isheni" "na qetara qasar waje naje naci karena babu babbaka saboda haka wannan itace magana ta dake ta karshe.""! Yana gama maganarsa ya sunkuci! akwatin kudinsa ya kama hanyar fita. Cikin wani irin" "masifaffan yanayi na tashin hankali da razani ta d'aga hannunta hade da kiran sunansa *""BASH!!""*" Juyowa yayi ya kalleta yayi wani irin murmushi kafin ya daga mata yatsun hannunsa biyu ya bude kofar dakin ya fita da gaggawa! """Innalilihi wa"" ina ilaihi raji'un."" Kalmar da ta iya furtawa kenan ta kwanta a gurin tana wani irin kuka na" tsantsar tashin hankali gami da nadamar rayuwar da Bash ya jefa kansa a ciki Haka ta kasance har asubah! lokacin da take yunkurin mikewa domin daura alwala a lokacin ne kuma ta dinga jin kukan motar jama'an tsoro a cikin gidan A furgice ta mike tsaye ta nemi zaninta ta daura kan rigar baccinta ta "zura hijabinta ta fara kokarin fita, tana fitowa palo suka shigo su kusan bakwai ko wanne hannunsa da bindiga suka shiga rarraba idanunsu a palon!! Hannu tasa ta rufe bakinta jikinta na wani irin karkarwa! Babban cikinsu yace.""Ina Bash yake shi kadai muke nema kada ki firgita."" Saboda tsananin firgicin da take ciki kasa magana tayi ta zube a gurin tana sake qumshe bakinta ji takeyi tamkar ana ragargaza mata gwiwowinta. Tsawa! mai qarfi ya buga mata ya d'ora mata tsinin bindiga a goshinta yace.""Zaki fada" "mana inda mijinki yake ko sai na sakar miki bullet.""! Allah sarki Naja'atu fitsari ne ya kwace mata a gurin, cikin wata iriyar magana tace""Ya had'a kayansa ya fice daga gidan tun misalin biyu da rabi ya shigo naga yana hada kudi a kwati da nayi magana yace nayi shuru bayan ya gama ya tsaya a kaina tare da fad'a min" "hukuncin da ya yanke a kaina ya sake ni saki uku.""" "Bakin bindigar ya cire daga kanta yace.""Tashi muje kiyi mana jagora cikin gidan inda iyayensa suke. Ta" mike da sauri suka tasa ta a gaba har dakin Mommy wacce take ta sharar baccinta. Jin tsinin bindiga a "saman goshinta yasa ta tashi a firgice tana zazzare ido! ganin jamian tsaro yasa gabanta ya yanke ya fadi! ta kalli naja'atu a tsorace tace""Me yake faruwa ne? naja'atu yanzu sai dai kika tonawa mijinki asiri.""?" "Jin wannan magana da tayi yasa babban cikinsu yace.""Ina Bash.""? Ta kalleshi cike da fargaba tace me" "yayi muku kuke nemansa wallahi matarsa sharri tayi masa.""" Lafiyayyan mari ya kwada mata ya kalli na gefansa hade da umartarsa daya daura mata ankwa! Mommy "ta dinga kuka tana musu magiyar su kyaleta da fadin duk zargin da suke akan yaronta ba gaskiya bane. Yace.""Tunda mun samu labari daga bakin maigadi cewa uban yaron baya gari to ke zamu kama" mu daure a madadinsa duk inda yake idan yaji labarin kina hannunmu zai bayyana kansa dama mun "dade muna bunkice a kansa alhamdullhi yau Allah ya bayyana mana shi."" Mommy kuka kawai takeyi tana basu hakuri sunki kulata suka angiza keyarta" Naja'atu kasa motsi tayi jikinta sai rawa yake tana kallo suka sata a cikin motarsu tana kuka tana kiran "sunanta tare da fadin ta taimaka mata, hakika ranar taji tausayin matar sosai da sosai! babu shakka son zuciyarsu shine ya janyo musu shiga wannan masifar su haifi d'a a cikinsu amma su dinga turashi yana" "sata ai dama hausawa nacewa duk tsuntsun daya ja ruwa shi ruwan kan doka, tabbas da haihuwar d'a" irin Bash to gwara Allah ya barka babu haihuwa domin hakan shi zai fi maka alkairi a rayuwarka. A sanyaye ta juya domin zuwa taje ta had'a kayanta. * Yau akwai Celaberation Vip madadi ga pege din da kuke ta jira ya iso Sai dai kuma akwai sauran qalubale anya kuwa mutumin naku zai mayar da Naja'atu dakinta kuwa? duba da cewar Allah yayi masa sauyi na Alkairi ina ganin da qyar idan zai waiwayi naja'atu da maganar kome amma dai bari mu gani * *Littafin na kudi ne. * Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina da bukatar biyan kudin karatu ga yanda abin yake Vip group #600 normal #300 accont numbar...0542382124...Binta umar gtbank...Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 57 "Wata qaramar akwati mai tayoyi ta samu a dakin, ta kwashe masa tarkacen kayansa da suke ciki a" guruguje ta shirya 'yan kayanta da basu kala biyar ba ta rufe da sauri ta gyara hijabinta ta dauki akwatin ta kama hanyar fita daga dakin Tana fitowa harabar gidan taga dandazon jama'a harda 'Yan jarida sun "cika gidan suna tayi wa maigadi tambayoyi, tsorata tayi dan gabadaya bata so a watsa hotonta a duniya jama'a su ganta su sheda ta a matsayin matar d'an ta'addah! Tana kokarin ratsesu ta fita daga gidan wani dan jarida yasha gabanta yana yi mata magana tare da kara mata wayarsa a daidai bakinta, rufe fuskarta tayi da hijabinta muryarta na rawa tace""Dan Allah ka matsa ka bani guri na fita ni ban san a binda ke faruwa ba. Dan jaridar yace.""Hajiya a matsayinki na matar Bash wanda ake zarginsa da aikata" munanan ayyuka wanda suka sa'ba dokar qasa da kuma dokokin musulunci muna bukatar jin ta bakin ki "dangane da wannan al'amarin da ya faru."" Jin muryar d'an uwansu yana tambayar Naja'atun yasa da sauri sukayi mata caaaa! a kanta kowa na miqa abin daukar rahotonsa a bakinta. Tana kakkare" "fuskarta da hijabin ta tace""Na fad'a maka nima ban san komai ba akan wannan al'amarin kuma ka daina" "dangantani da Bash domin yanzu ba mijina bane.""! Tana maganar suna daukar hotonta had'e da daukar muryarta. "" Duk da haka hajia ba zaki rasa ta cewa ba a kan wannan abun tunda dai a kan idonki" "komai ya faru."" Da sauri ta dauki akwatinta ta fice daga gidan, kamar mayu suka bi bayanta har wajen gidan suna daukar hotonta. sai da ta qule tukkuna suka koma cikin gidan tare da titsiye maigadi da" tambayoyinsu kamar yanda suka saba. Dari biyar din da Mmn sajida ta bata kwanakin baya da ita tayi kudin mota mai Napep ya ajiye ta har "kofar gidan, ta bashi kudinsa da sauri ta shiga gidan tana jan akwatin hannunta." Mmn Sajida na yanka salak kawai ta ganta ta shigo a firgice!! Mmn Sajida ta ajiye wukar hannunta da sauri ta miqe ta rike ta tana dudduba jikinta had'e da godewa Allah! Naja'atu rungume ta tayi ta dinga wani irin kuka na tsantsar tausayin kanta...mmn sajida kasa daurewa "tayi sai ta shiga tayata kukan tana rarrashinta da kalamai masu sanyi, har sai da ta samu tayi shuru hankalinta ya dawo jikinta tukkuna tace"" Naja'atu naji dadin ganinki wallahi dama tun dazu nida mmn ladi muke zancen ki dukkaninmu mun shiga damuwa sakamakon jin abinda ya faru da mijinki mun samu labari cewar jami'an tsaro sun kama mahaifiyarsa saboda basu samu nasarar kama shi ba sai muke ta fargaba ko sun hada dake sun daure, mun dade da mmn ladi muna tattauna maganar kafin ta shiga" gidanta. "Naja'atu na goge hawayen da suka kasa tsayawa tace""Mmn Sajida tunda nake banta'ba shiga masifa irin" "ta jiya da yau ba! Allah ne kawai ya nufa ina da sauran kwana a gaba da tuni sai dai kuji mummunan labari 'Yan sanda sun harbeni."" Mmn Sajida ta rike ha'ba! cike da tu'ajibin al'amarin tace""Haka kawai baki ji ba baki gani ba su harbe ki sai kace kece kika turashi yaje yayi sata ai naji dadi da suka kama uwar tasa tunda dama sune suke daure masa gindi nasan yanzu ai duk inda labari yake yajewa Alhaji Aminun" "shima nasan sai sun daureshi kuma insha Allahu asirinsu sai ya tuno.""" "Ajiyar zuciya ta sauke tana girgiza kanta tace""Mmn Sajida na tabbata jami'an tsaron nan da basu tarar da" "mahaifiyarsa a gidan ba to ni zasu kama a madadinsa kinga kuwa dole na shiga tashin hankali wallahi har yanzu ban dawo daidai ba.""Mmn sajida na kokarin yin magana Mmn Ladi ta shigo gidan, ganin Naja'atu a zaune yasa ta sauke ajiyar zuciya tana godewa Allah ta zauna suna sake jajanta al'amarin a nan ne" Naja'atu ta tabbatar musu da saki ukun da Bash yayi mata. "Mmn Ladi ta dinga tsine masa tana fad'in "" Allah ya rabaki da masifa Naja'atu fatan mu anan shine Allah" "yasa baki da ciki shikkenan kin rabu da alaqaqai gabad'aya."" Naja'atu tace""Ni sai maganar ciki kike kina fad'ar min da gaba na fad'a miki tun zuwan da nayi kwanakin baya bani da ciki dan Allah ki daina wannan maganar."" Mmn ladi tace""To shikkenan na daina tunda bakya so Allah ya kiyaye gaba."" gabadayansu" "suka amsa da ""ameeen Ya Allah.""" "To labarin al'amarin dake faruwa a garin Jos ya zagaya sauran jahohi ta hanyar kafafan sadarwa, kowa" sai fad'ar albarkacin bakinsa yake...To Abbah Abbas ma dai a labaran karfe hudu na tashar freedom redio ya saurara lokacin ma yana kasuwa. Al'amarin ya firgitashi jin mai gabatar da labaran na fadin sunan Alhaji Aminu dan jarida yana sake jajjadawa cewar a cikin masu laifin harda d'ansa mai suna Bashir wanda dubunsa ta cika a ranar dama kuma tsohon mai laifine wanda ake nemansa ruwa a jallo......Yana tsaka da mamakin al'amarin yaji sun sako muryarta lokacin da takewa d'an jaridar nan bayani kan ya kyaleta da tambaya ita bata san komai ba. Wani irin gumi ne ya shiga tsatstsafo masa a saman goshinsa Yasa hankici ya goge yana cigaba da sauraran muryar mai labaran Sai da a ka gama "labaran tsaf! ya samu damar ajiye wayar ya shiga mamakin al'amarin ya jima sosai cikin alhini da tunanin wace irin rayuwa yarinyar take ciki kafin ya sauke ajiyar zuciya daga bisani yayi furucin alkairi akan abunda ya faru tare dayiwa wad'anda ake tuhuma da laifin adduar shiriya, da fatan Allah yasa 'karshen masifar kenan Ammafa jin muryar Naja'atu cikin tashin hankali ya tsaya masa a zuciya yana so" "yayiwa abokinsa magana idan sun tashi daga kasuwa yana tunanin wani abu, zai dai saurara ya gani ko" shi abokin nasa zai fara tuntun'barsa da maganar yasan tabbas ya samu labarin abinda ke faruwa da 'Yar uwar tasa.... Bayan kwana uku al'amura sunyi sauqi Naja'atu ta samu nutsuwa gidan Mmn Sajida sosai take kulawa da "ita gami da bata ingantaccen abinci mai kyau tana ci ta koshi, sannan idan sun ke'be tayi ta rarrashinta gami da nuna mata ta kwantar da hankalinta ta dauka abunda ya faru da ita qaddara ce bayan nan kuma ta shirya fuskantar iyayenta da maganar domin su san halin da ake ciki...Duk sanda Mmn Sajida tayi mata wannan maganar takan shiga damuwa sosai da sosai, itafa yanzu gabad'aya kunyar had'a ido take da kowa dan idan ta koma gida bata san da wane ido zata kalli mutane dashi ba, auran data qallafa ranta a kansa gashi anyi mata amma wata uku da kwanaki ya wargaje anyi mata saki mafi muni irin wanda Allah baya so, to ta yaya ma zata iya yi musu bayanin yanda al'amuran suka kasance, kullum da wannan" tunanin take kwana da kuma shi take tashi. "Yau dai Mmn Sajida kafin ta fita gurin sana'arta tace""Lallai dole sai ta kira wayar wani mafi kusa da ita ta" fad'a masa ga halin da take ciki dan zaman da takeyi bashi da amfani iyayenta basu san halin da take ciki ba. "Gudun 'bacin ran Mmn Sajidan yasa ta kar'bi wayar tata ta sanya numbar aunty maryam a kai, gabanta" na dukan uku uku ta shiga kiran number Aunty maryam na gidan Alhaji suna ta shirye shiryen daurin aure kasancewar washe garin ranar daurin auren Abokin mijinta shiyasa ta yini gidan Alhaji suna ta aikace aikacen walimar da angwaye zasuyi bayan daurin aure. Duk da bata sheda numbar ba hakan bai hanata dagawa ba tayi sallama a nutse "tare da fad'in ""Da wa nake magana.""" "Naja'atu tayi wani qwal-qwal! hawaye na kokarin sauko mata sai dai ta daure murya na rawa tace""Anty" "maryam kina magana da Naja'atu.""" "Cike da farin ciki Aunty maryam tace""Naja'atu idonki kenan? ashe kina nan kin ya damu kwana biyu me" "ya samu wayarki ne sai ayi ta kira bata shiga.""" "Murya na rawa tace""Lalacewa tayi."" Tace""Ayya! shiyasa mana to ina fatan dai kina lafiya ya maigidanki.""?" "Tace""Lafiya anty ya nake jin hayaniya a kusa dake.""" "aunty maryam tace""Ina gidan Alhaji wallahi muna aiki Gobe bayan sakkowa daga sallar juma'a Abbah" "Abbas zai daura aure."" Aunty Maryam bata fad'i maganar da wata manufa ba tsakaninta da Allah ta fadi" maganar ba dan ta cuzgunawa naja'atu ba tunda ita a ganinta ai babu wata alaqa a tsakaninsu da zai sanya taji zafi dan zaiyi aure. Ita kuwa Naja'atu ji tayi tamkar Naja'atu maryam din ta fad'a mata ranar mutuwarta wani irin zazzafan "gumi ya shiga yanko mata. Zazzafan kishi! ya turnuqeta! murya na rawa tace""Aunty maryam wace" "magana naji kina yi waye zaiyi aure ban fahimce ki ba.""?" "Aunty maryam ta fuskanci sauyin yanayi a tattare da Naja'atun sai ta sassauta murya tace""Abbah Abbas" "nake nufi nace dake gobe zai daura aure insha Allahu.""" "Kuka ta fashe dashi murya na rawa tace.""Aunty maryam da bakinki kike fad'a min wannan maganar shin" "kin san halin masifar da nake ciki kuwa.""? Aunty maryam tayi kasaqe da waya a kunnanta jikinta yayi sanyi jin irin kukan da Naja'atun takeyi, tace""Kiyi shuru dan Allah kiyi min bayanin abinda ke faruwa.""" "Kai tsaye tace""Aunty Maryam Bash! Yayi min saki uku yau kwana uku da suka wuce."". ""Innalilihi wa'ina" ilahi raji'un! kalmar da aunty maryam ta furta kanan wacce tayi dadai da zuwan hajia gurin tana tambayar ta abinda yake faruwa take furta wannan kalmar......... *Littafin na kudi ne...!* Koda zaki ganshi a gruopa na sata ne idan kina bukatar biyar kudinn karatu ga yanda abin yake... Vip gruop#600 normal group#300 account.. 0542382124...Binta umar gtbank...Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan number. *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* Barkamu da Juma'a My Fans Ina rokon Allah ya sadamu da alkairan dake cikinta 58 Hajia Abu ta qaraso inda aunty Maryam take hankali a tashe take tambayarta abinda ke faruwa. "Aunty Maryam jiki a sanyaye tace""Naja'atu bari zan kira ki anjima.""Sai kawai ta kashe wayar tana kallon hajian bakinta sai rawa yake yi tsabar fargaba da tashin hankali ya hanata magana, ita ma Hajian jin ta ambaci sunan Naja'atu sai gabanta ya tsananta faduwa ta zauna kusa da ita tare da dafa kafadarta tace""Maryam me yake faruwa da Naja'atu? jikina yana bani akwai mumman abinda ke faruwa da rayuwarta.""Aunty Maryam tayi qasa da kanta tana tunanin yanda zata fad'a mata maganar. Aure wata" uku kacal har anyi angama kuma saki har uku dan tsabar wulakanci a ganinta ko wane irin laifi naja'atu tayi bai cancani a wulakantata irin haka ba(Hausawa nacewa ciwon 'ya mace na 'ya mace ne) hakika "aunty maryam ta tausayawa Naja'atu sosai yarinya da quruciyar ta da komai maza sai katantawa suke da ita, koda yake na farko itace taqi to amma wannan a tunaninta ba daga gurinta bane kawai ta had'u da sharrin d'a namiji....Sai da ta dan samu nutsuwa tukkuna ta d'ago kanta cikin tararrabi da alhini tace""Hajia al'amarin ne babu dadin ji wallahi shiyasa kikaga duk jikina yayi sanyi Naja'atu ce ta kira ni" "take tabbatar min da cewar wai mijinta ya saketa saki har uku kwana uku da suka wuce.""" "Hajia tayi salati tana sanar da Ubangiji tace ""A kan me? me tayi masa yayi mata wannan wulakancin saki" "Uku!!? innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! Ai kafin kice kwabo palon ya cika da jama'ar da suke waje mafi akasari 'yan uwan Alhaji ne da hajian sai kuma Yaya Ramlatu! dukkanisu suka dinga tambayar ba'asin abinda yake faruwa, Aunty Maryam da hajia sukayi shuru domin sirrinta al'amarin, irin wannan maganar ba mai dadin fada bace shiyasa sukayi shuru Yaya Ramlatu tayi murmushi tana girgiza kanta" "tace"" Hajia meye abun 'boye magana nifa dama nasan sai haka ta faru shuru kawai nayi muku ban sanar miki da halin da ake ciki ba, kwana uku da suka wuce na samu labarin abinda ya faru da mijin data aura ashe d'an fashi ne 'barawo d'an shaye-shaye d'an Luwadi ne manemin mata! ke mutumin daj mugun mai laifi ne jam'ian tsaro sun jima suna nemansa sai a ranar dubunsu ta cika shida abokanan harkarsa sun shiga wani bank sunyi sata sun fito asirinsu ya tuno yanzu dai 'yan sanda sun samu nasarar kama abokan harkar tasa shi kuma ya tsere amma sun damqe mahaifiyarsa jiya na sake samun labarin cewar sunje har inda mahaifinsa yake sun damqe shi, yanzu dai sun baza binkice sosai dan gano inda yake shima su damqe shi! ai wallahi naso harda ita shegiyar suka damqe dama ai duk tsuntsun daya ja ruwa shi ruwa" "kan doka! makwadaita kawai gashi nan sun dauki 'yarsu saboda tsabar kwadayi sun aurawa 'barawo.""" Palon yayi tsit! kowa yana mamaki da salati a cikin zuciyarsa! Yaya Ramlatu ta cigaba tsinewa Baba malam dashi da zuriarsa tana kwashe musu albarka! Hajia da taga abun nata na nema ya wuce gona da iri sai ta tsawatar mata Yaya Ramlatu ta fita daga palon tana cigaba da surutai Hajia ta sallami kowa tace kowa ya koma ya cigaba da aikinsa. "Shuru palon yayi bayan fitar jama'ar hajia ta kalli anty maryam dake zaune da waya a hannu tace""Sake" kiran number data kira ki da ita.'' Aunty Maryam ta duba numbar da sauri ta shiga kira... swich up wayar "a kashe take! tayi ta kira ana ce mata a kashe take, cike da mamaki tace""Yanzu fa mukayi waya amma duba suna cewa a kashe wayar take.""" "A sanyaye hajia tace""To watakila babu chaji a wayar anjima kadan kafin ki tafi sai ki sake gwadawa" "mugani."" Aunty maryam tace""To shikkenan." Naja'atu bayan gama wayarsu da aunty maryam kwanciya kawai tayi tana kukan bakin ciki! gami da "nadama da dana sani! Hakika tasan duk abinda ya faru da ita itace ta janyowa kanta, gashi yanzu tazo" tana dana sani wanda hausawa ke cewa qeya ce! da tasan auran Bash ba zai tsinana mata komai ba data "hakura ta zauna a dakin mijinta data san Bash amanarta zai ci to da babu abinda zai sanyata ta fujirewa auran *MADADI* da iyayenta sukayi mata, hakika da tasan Bash ba mutumin kwarai bane to da babu abinda zai saka ta za'be shi a matsayin abokin rayuwarta...Data san ! data san! Data san! (babu wanda yasan gaibu sai Allah kuma komai ya faru da rayuwarki qaddara ce amma kuma akwai son zuciya da qin jin maganar magabata mafi akasari iyaye zasu za'bawa d'ansu abunda yake alkairi ga rayuwarsu sai su kuma 'Ya'yan fujire su nuna ga abinda suke so, hausawa nacewa abinda babba ya hango yaro ko ya hau" bishiyar rimi ba zai hango ba) Mmn Sajida data gaji da rarrashinta sai kawai ta fita gurin sana'arta ta qyaleta dan al'amarin Naja'atun tana gani kamar yafi karfinta. Mmn Sajida da wayarta ta fita tana so ta bayar a kai mata chaji kasancewar kwana biyu wutar unguwar ta lalace sai ta ajiyeta a kusa da ita ta cigaba da hada hada da jama'a! kawai wani d'an bana bakwai yazo siyan abinci ya dauketa yasa a aljihu a gurguje ya cinye abincinsa ya bar gurun.....Sim card din ya cire ya yar ya qara gaba abinsa. "Sai bayan jama'a sun tsagaita ta qwalawa Walid kira ya fito daga cikin gidan Mmn Ladi yana amsawa, ta" "laluba kusa da ita zata dauki wayar taji wayam! tashi tayi tana zazzage jikinta tana dubawa babu waya babu dalilinta, ta dudduba bata ganta ba sai tace""Shiga cikin gida ka tambayi Naja'atu ko wayar ta nan watakila dama ban fito da ita ba." "Yaron ya shiga gidan da sauri ita kuma ta cigaba da abinda take. Minti biyar Walid ya fito yace.""Mama" "wai tace baki wayar a cikin gidan ba da ita kika fito kika ce zaki bada chaji .""" "Mmn Sajida tace""Shikkenan sun sace yau kuma tsautsayin a kan wayata ya afka ai shikkenan Allah ya" "mayar min da alkairi."" Mutanan dake tsaye a kanta suka shiga jajanta mata, tace""Wallahi ni layina ma nake ji."" Da sauri daya yace''Bani numbar na kira muji."" Da sauri ta shiga fada masa yasa a wayarsa a take aka ce masa wayar a kashe take, ya dinga kiran yana sake bude hands free domin taji! Girgiza kanta tayi tace""qyale kawai ai duk wanda ya dauka dama ba zai barta a kunne ba yaje yayi min guzirin kiyama zai biyani a inda bashi dashi."" Mutumin yace.""Kinyi magana hajia Allah ya mayar miki da alkairi shi kuma" daya dauka Allah ya tona asirinsa. "Amma yana da kyau kije ayi miki swapping d'in layin naki saboda jama'arki."" Tace""Habu sai na samu" lokaci zanje kana ganin dai irin sana'a ta bani da lokacin kaina amma insha Allahu na samu lokaci zanje ayi min. "Naja'atu taji takaicin sace wayar da akayi, haka sukayi ta maganar kafin su hakura, Mmn Sajida ta cigaba" da sabgoginta kamar ma 'batan wayar bai dameta ba ita kuwa Naja'atu damuwa ta shiga sosai ta dinga tunanin hanyar da za tabi domin ganin ta taimaki kanta da kanta. "Aunty Maryam dai haka ta gaji da kiran waya ta hakura domun har ta zo tafiya wayar bata shiga ba," Hajiyar tace ta bari kawai tunda taqi shiga....Gabadaya da ita da hajiyan a sanyaye suka rabu da juna Tun a mota take so tayi wa mijin nata maganar tana jin tsoro dan akwai sanda ta ta'ba yi masa maganar "yarinyar ya nuna mata koda wasa kada ta kuskura ta sakeyi mata maganarta, ya nuna mata cewar shi babu ruwansa da yarinyar, a lokacin har sa'bani suka samu sabida hakan, ya daina mata magana tsayin kwana uku, al'amarin ya dinga bata mamaki! mutum da 'yar uwarsa ina laifinta dan ta nuna kulawarta a kanta zai dinga gaba da ita, sai itama ta fusata ta dauke masa wuta! kwana uku dan karan kansa ya sakko ya nemi shiri da ita to tun daga ranar bata sake yi masa maganar yarinyar ba...Sai yanzu da take ganin dole ta fad'a masa abinda ke faruwa tunda dai yarinyar babu wanda ta fara nema da maganar sai ita to tilas ta fad'a masa koda kuwa zai dauki gaba da ita kamar wancan karon Ta kalleshi a nutse tace""Wai" "kasan abinda yake faruwa da Naja'atu kuwa.? Abbah Magaji na driving yace.""Maryam ashe ban hanaki yi min maganar yarinyar nan ba.""? Tace"" Kamar yaya? wannan wai wace irin magana kakeyi Naja'atu fa kanwarka ce uwa daya uba daya duk abinda zanyi a kanta saboda kai zanyi amma sai ka dinga nuna wani" abu daban. "Yace.""To bana so na fad'a miki babu ruwana da yarinyar nan, kada ki sake ki tunzura min zuciyata duk" "abinda ya faru da ita itace ta janyowa kanta."" Murmushin takaici tayi tace""Au! ashe kasan abinda yake faruwa tsayin kwana uku kayi shuru da bakin ka ko.""? Yace."" Na sani asirin mijinta ya tuno wanda nasan dama komai daran dadewa dole sai haka ta faru dashi wannan yaron mugun mai laifi ne ni ganau ne ba" "jiyau ba shiyasa lokacin auran naqi saka kaina a ciki saboda nasan karshe ba zaiyi kyau ba.""" "Tace""To dai yanzu duk wata magana ta qare tashin ma maganar bacin rai ne dan Allah kayi hakuri ka" "yafe mata kuma ku duba halin da take ciki! Dazu ta kirani a waya tana kuka take sheda min cewar ya saketa saki uku! Tsabar tashin hankalin dana shiga a lokacin yasa na kasa tambayarta inda take, na kashe wayar, to kuma dana sake kira sai wayar taqi shiga nida hajia mun shiga damuwa sosai da sosai A nan ne nima nasan abinda ke faruwa a bakin Ramaltu Yace.""Maryam ki rabu da yarinyar nan dan Allah! ai" "tasan hanyar gida, tunda ya saketa to zaman me takeyi sai ta tattaro ta dawo gida. Buqatarta ta biya.""" Maryam shuru kawai tayi tana jimanta al'amarin Eh wannan itace shawara mai kyau tunda babu aure a tsakaninta da Bash din to zaman da takeyi a gidan bai da amfani ta tattaro ta dawo gida ta nemi gafarar iyayenta. "Washe garin ranar haka kowa ya wayi gari cikin alhini da damuwar abinda ya faru da Naja'atu, dan Hajia" kasa barin maganar tayi a ranta a daran ta samu alhaji ta sheda masa halin da ake ciki Alhaji Sama'aila "ya shiga tashin hankali gami da damuwar abinda ya faru da rayuwar Naja'atu, mutumin kasa bacci yayi a daran saboda alhini da asubah kuwa suna fitowa daga massalaci ya samu malam suka ke'be guri daya, kafin ya sheda masa abunda ke da akwai sai da yayi masa nasiha sosai sannan ya sheda masa rayuwar da Naja'atu take ciki Baba malam ya jima kansa a kasa yana kiran sunan Allah kafin ya d'ago kansa ya kalli" "Alhaji a nutse yace.""Allah yasa haka shi yafi alkairi a rayuwata, hakika na jima banji abinda ya tayar min da hankali irin wannan ba ashe dama yaron nan dashi da mahaifinsa ba mutanan arziki bane suka zo suka yaudaremu muka dauki amanar yarinya muka basu, to babu komai ai tunda da alkairi muka nufe su suka nufe mu da sharri ina rokon Allah yasa haka shi yafi alkairi."" Alhaji yace.""Wannan adduar itace abinda ya kamata sabida haka yanzu na yanke shawara cewa bayan anyi daurin auran nan hankali ya kwanta gobe da wuri zan sa direba ya dauki Hajia Rabi tunda ita tasan gidan taje ta dauko yarinyar ina" ganin wannan shine abinda yafi kamata muyi. "Baba malam yace.""To hakan yayi Alhaji nagode kwarai da gaske ina rokan Allah ya dubi gabanka da" "bayanka halinka nagari ya bika a duk inda kake."" Alhaji Sama'ila ya mika masa hannu tare da fad'in ""Babu" "komai malam Naja'atu tamkar 'yar cikina haka na dauketa dole ne na tsaya a cikin al'amuranta inayi mana fatan alkairi gabad'ayan mu.""" *ANGO* A shirya ya fito daga dakinsa yana sanye da wata dakakkiyar geznar milk color babbar riga da 'yar ciki da "wani irin sirfani mai kyau a wuyan babbar rigar! Kasancewar shadda mai haske ce yasa yayi amfani da baqar hula had'e da bakin takalmi sau ciki agogon dake daure a hannunsa na dama shima baki ne, kai hatta da links din da yayi amfani dasu masu duhu ne! Wani irin kamshin turare yake mai dadi irin na manyan mutane! Kallo guda nayi masa na tabbatar da cewar ya amsa sunansa na ango sai dai kuma" yanayin rashin walwala dake fuskarsa yasa na gane cewar akwai abinda ke damunsa. Koda ya fito bai tunkari ko ina ba sai dakin Halisa...Tana zaune kasan kafet abin duniya ya taru yayi mata "yawa, ga tarin magunguna nan a gabanta Halisa har yanzu taqi lafiya daga an toshe waccar matsalar sai wata ta bayyana yanzu wasu irin qananun kuraje ne suka feso mata a gabanta da matsematsin cinyarta kullum cikin susa take duk ta kwailaye fatar jikinta! Wannan dalilin yasa Abbah Abbas baya yarda wata mu'amula ta aure ta shiga tsakaninsa da ita ko toilet dinta baya shiga yayi wani uziri saboda a gabansa Dr Sa'adatu ta tabbatar masa da cewar Halisa na dauke da mugun sanyi wanda yayi masifar cin karfinta," wannan dalilin yasa ya janye jikinsa sosai da ita sai dai kuma duk wani abu da take bukata yana yi mata kuma yana tsaye kan duk wani maganin da Dr zata bada umarnin siya komai tsadarsa kuwa zai fitar da kudi ya siya sannan kuma ya jajurce a kan ta tayi amfani da maganin a kan ka'ida "Ganininta a firgice a lalace! yasa jikinsa ya d'anyi sanyi, Halisa sarkin kwalliya da gayu itace ta koma wata" iriya tamkar mara hankali! Tausayinsa yaji saboda yasan duk irin halin da ta jefa kanta a kansa ne wannan dalilin yasa ya sassauta fuskarsa ya shiga dakin ya zauna gefan gado yana kiran sunanta. Ta dago tana kallonsa wasu lafiyayyun hawaye suka wanke mata fuska! In da saboda ya saba da ganin wannan hawayen nata "Gyaran murya yayi a nutse yace.""Ina fatan kinsha maganin naki a kan ka'ida.""? Hanci ta shaqa! wasu" "hawayen na sake shararo mata, Yace.""Kiyi hakuri wannan koke koke bashi ne mafita ba a gurinki addua ce mafita ki roki Allah ya yaye miki sai dai kuma ba zan gaji da fada miki cewar kece kika siya da kudinki dan haka dole kiyi hakuri ki 'kar'ba! ni nayi miki al'kawari insha Allah daga dubu daya zuwa miliyan daya zan iya fitarwa a kan lafiyarki saboda haka ki kwantar da hankalinki! ki cigaba da rokan Allah ya baki lafiya .""( Lallai Abbah Abbas ka cika dan halak) Halisa hannu tasa ta goge hawayen fuskarta tace""Abbahn mufida nagode sosai dan Allah kada ka juya min baya."" Murmushi yayi yace""Halisa nasan fa duk wannan masifar da kika shiga saboda da ni ne to akan me zan sake ki ko na juya miki baya ni ba haka nake ba," "zaki cigaba da zama a matsayin matata har karshen rayuwarki.""" "Hanci taja ta sunkuyar da kanta a qasa tare da fadin ""Nagode Abban Mufida."" Mikewa yayi yana duba" "agogon hannunsa yace.""Ni zan tafi gurin daurin aure."" Ta kalleshi le'banta na rawa tace""To Allah ya sanya alkairi.""" Amin yace a takaice ya juya da niyar fita daga dakin Kallo ta bishi dashi hawaye wani na bin wani lallai babu shakka abunda yafi karfinka dole ka saka masa ido Yau mijinta da take bala'in so zai daura aure da dalleliyar budurwa tabd'ijam! ashe da ranta za taga wannan ranar. *To Alhamdullhi* An daura aure lafiya 'Bangaran Amarya suna cikin tsantsar farin ciki tare da taya 'yarsu 'yar uwarsu Zainab dace da samun miji nagari Yayin da kuma 'Bangaran ango dashi kansa angon suke cikin "damuwa da tararrabi al'amarin da yake damunsu, ha'ki'ka! Yanda suka nuna damuwarsu a kan al'amarin Naja'atu zaka fahimci cewar suna tsananin qaunarta gami kuma da tausaya mata, wannan dalilin ne" ma ya sanya bayan hankula sun kwanta suka ke'be kansu gabad'aya harshi angon suna tattaunawa "dangane da abunda ya faru, a nan ne Alhaji ya sake sanar musu da shawarar da ya yanke na tura Hajia Rabi taje ta daukota ...Gabad'ayansu sun amince da hukuncin da Alhajin ya yanke." Cikin gidan Alhaji ma hakane ya kasance Baba Talatu da Hajiya aunty Maryam su kad'ai ne suka san abinda ke zuciyarsu kawai dai sun sake ne suna hidima da jama'ar da suka tara. Ita kuwa Yaya Ramlatu "ta manta da wata Halisa yanzu ta amarya take, ta tara mutane a gefe guda sai hira suke suna shewa babu abinda ya dameta, burinta kawai a kawo amarya taga wace iri ce idan irin wacce za'a had'u da ita a rufawa kai asiri ce to za tayi kokarin riketa hannu biyu! Zata kuma yi kokarin ta d'orata a kan hanyar data d'ora Halisa a kai......Kwana biyu da Halisa ta daina daukar shawararta duk a dame take ga rashin kudi da yake damunta! a lokacin da suke tare da Halisa kudi basa yanke mata dan sosai Halisa take sato mata kudin mijinta ta bata, to cikin kwanakin duk a takure take, dan tayi tayi da Halisan akan tazo su sake komawa gidan Boka Halisa taqi amincewa shine take jin haushinta ta daina zuwa dubata! so take amarya" tazo su had'a kai su muzgunawa Halisan. *ANGO DA AMARYA* Abbah Abbas kasa Ta'bukawa amarya komai yayi saboda rashin nutsuwa da kwanciyar hankalin da yake "ciki, hakanan yana ji yana gani ya sanyawa dalleliyar amaryasa ido bayan sun gabatar da sallar ma'aurata sai kawai ya umarceta da taje ta kwanta! Zainab ta mike a nutse taje ta kwanta tana mamakin rashin walwalar angon nata, duk da bata da shekaru da yawa amma tana da wayo kuma tasan yanda ango ke rawar jiki a kan amaryarsa idan bata manta ba akwai wata kawarta mai suna Mariya da akayiwa aure ta dinga basu labarin irin rawar jikin da angonta ya dinga yi mata a daran amarcinsu. Kuma" itama ba saurayi bane zaiyi Abbah Abbas d'in! Dan har da sukaje gidan suka dinga sha'awar irin rayuwar da 'kawarsu mariya takeyi da sugar dady d'inta! lokacin itama taji tana sha'awar auran manyan mutane saboda taga yanda mijin Mariya ke kula da ita yanda ya kamata! To sai gashi burinta ya cika angon nata sai wani salalaf-salalaf! yake yi kamar wani mara laka a jikinsa sam baya wani nuna gand'okin sa a kanta......Haka tayi bacci cike da takaici da bakin ciki Da asubah ta gane a dakin ya kwana dan ganin "wayoyinsa a kan bed kusa da ita. Alamu sun nuna mata cewar ya tafi.massalaci. Sai ta mike ta nufi toilet," "tayi wanka da alwala ta fito ta shirya jikinta tsaf tsaf! ta hau kan dadduma ta gabatar da sallar! Sai da tayi addua sosai kana ta mike ta nufi mirror dinta dake shaqe da kayan kwalliya, Zainab ta zauna ta tsantsara kwalliya mai kyau da burgewa har dasu gashin ido sosai tayi kyau ta fito amarya sak! Zama tayi" kan bed tana jiran shigowarsa....Koda ya shigo dakin kasa dauke idonsa yayi daga kanta..Yaushe rabon "da yaga irin wannan kwalliya tun kafin Halisa ta kwanta ciwo, dama itace ke yi masa irinta Naja'atu dama" "can wannan kwaliye kwaliyen bai dameta ba! Shi kuma gashi yana san gayu! Zainab sarkin dubara da wayo ko a fuska bata nuna masa jin haushin abinda yayi mata jiya ba ta tsuguna har a qasa ta gaidashi, ya amsa yana mirmushi mai kyau da ma'ana, kanta ya dafa a nutse yace.""Allah yayi miki albarka! Ta amsa da ameen tana fari da idonta! saurin dauke kansa yayi yace""Tashi muje ku gaisa da Halisa da yaran ki ko."" Murmushi tayi a nutse tace""To Habibi."" Mikewa tayi ta yafa mayafi a jikinta sai murmushi take tana sunkuyar da kanta! Ya kama hannunta ya ri'ke a cikin nasa suka fita daga dakin Kai tsaye" 'bangaran Halisa suka nufa....... *Littafin na kudi ne...!* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake. Vip group #600 normal gruop#300.. accont number.. 0542382124...Binta Umar gtbnk. Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *******59 Baba Larai kad'ai suka samu a palon tana aikace akaice kamar ko da yaushe suka gaisa a "mutunce ya tambayeta kwanan yara tace""Sun tashi lafiya kalau."" Zainab ta dan risina cike da ladabi ta gaisheta, Baba Larai ta amsa cikin farin ciki tana jin dadin girmamata da yarinyar tayi lallai babu shakka duk inda ta fito gidan mutunci ne....Zainab din ya dan kalla yace.""Ki zauna bari na shiga gurin 'Yar uwar taki."" Tace""To tare da samun guri ta zauna kan kujera, Baba Larai ta juya domin cigaba da aikinta tana murmushi Lallai Allah ya musanyawa da Alhaji zankad'ed'iyar mata sarkin ado da kwalliya dama hausawa nacewa wani hanin ga Allah baiwa ne. Su saddiqa ne suka fito daga dakinsu ita da Mufida suna sanye" da Atampa iri daya shi kuma Mussadiq yana sanye da shadda blue color tsaf tsaf dasu suna gudanar da komai nasu cikin tsari da tarbiya dan sosai baba larai take tsaye a kansu da kula da tarbiyarsu. "A nutse suka gaishe da Zainab suna mata kallon rashin sani, ita kuwa Zainab sai murmushi take tana jan" "hannun Mussadiq har sai da ta samu nasarar zaunar dashi a kusa da ita tana masa magana, Baba Larai ta" "kalli Saddiqa tana murmushi tace""Naga sai kallon rashin sani kuke mata itace sabuwar aunty ku Amaryar" "Abbanku.""" "Saddiqa da Mufida suka shiga dariya suna 'boye fuska, Baba Larai tasa dariya tana fad'in ""Au! kunyarta" "kukeji? To amarya ga 'ya'yanki nan wai kunyarki sukeji.""" "Zainab na dariyar farin ciki tace""Haba dai meye najin kunyata ni mamanku ce ku saki jikinku dani kome" "kuke so kiyi min magana zanyi muku.""" "Mussadiq na murmushi yace.""Aunty ya sunanki.""? Tace.""Sunana Zainab."" Yayi qasa da kansa yana" "murmushi tare da fad'in ""Aunynmu munji dadin kasancewa dake muna miki fatan alkairi.'' Cike da nishadi ta amsa da ameen tare da dan rungumeshi a jikinta, aikuwa a kan idon Abbah lokacin da yake fitowa daga dakin Halisa tana biye a bayansa. Ganin yaransa na murmushi ga Mussadiq rungume a jikin" Zainab sai yaji wani farin ciki a cikin zuciyarsa yarinyar ta sake samun matsayi a zuciyarsa. Halisa ta "danji dama dama dan tayi wanka tayi kwalliya daidai gwargwado amma ganin amarya zainab sai da ya sanya ta shiga cikin halin damuwa, daurewa kawai tayi ta zauna tana dan kauda kanta daga kan yarinyar. (Kishin nan fa dole sai anyi) Itama Zainab din kafin ta gaida Halisan sai da ta dan jima tukkuna" "tace"" Aunt Ina kwana fatan kin tashi lafiya ya jiki kuma.""? Cikin dauriya tace""Lafiya lau jiki da sauki nagode sosai."" Shuru tayi da bakinta tana jin wani irin bakin kishi na taso mata a ganinta ai tunda ya samu wannan 'yar yarinyar magana ta qare tafi kowa sanin halin mijinta gurin son matan tsiya watakila ma tun daran jiya ya gama da yarinyar, sai taji hawaye na kokarin zubo mata. Ta riga ta tashi daga aiki a" "gurinsa tunda tsoron ma rike hannunta yake sabida kada ya dauki cuta(Kaico da wannan rayuwa da kika jefa kanki).....Abbah Abbas na qayataccen murmushi yake kallon Zainab yace.""Ina fata kun gaisa sosai da" "yaran naki.""" "Yarinyar ta wani wulkita ido tana gyara bakinta cikin wata iriyar magana tace""Wallahi mun gaisa dasu" "sosai kuma naji da dadi dana samesu masu tarbiya da girmama na gaba dasu a gaskiya Habibi family d'inka sun burgeni sosai ina rokan Allah ya albarkace ni da samun zuria da kai."" Palon yayi tsit!" Sakamakon maganar da Zainab take yi! Baba Larai da Halisa kasa 'boye mamakinsu sukayi sai da suka kalli yarinyar suna jimanta bud'ewar idonta kamar ba 'yar malamai ba gata 'karamar yarinya amma "sai firirita take gami da zaro zance ko kunyarsu ba taji."" Shi kuwa lafiyayyan murmushi ne a kwance a" "fuskarsa yace""Naji dadi kwarai da adduarki zainab Allah ya tabbatar mana da alkairi."" Ta amsa da amin tare da gyara zamanta a kan kujera" "Halisa ta daure zuciyarta sosai ta kalleshi a hankali tace""Abbah Mufida ina ganin zan koma na kwanta" "jikina bana jin dadinsa."" Yace.""Okey kafin ki kwanta ki tabbatar kinyi braek ki kuma tabbatar da kinsha maganinki."" Mikewa Tayi a hankali tare da fad'in.""Insha Allah ."" Zainab ta kalleta babu yabo babu fallasa" "tace""To aunty Allah ya sawaqe."" Ciki ciki ta amsa ta bar gurin, Abbah ya kalli Baba larai a nutse" "yace.""Komai ya kammala.""? Tace""Eh Alhaji."" Mi'kewa yayi ya kalli Zainab din da yaran yace.""Ku tashi muje mu karya."" Suka mike a nutse suka bi bayansa gurin cin abincin." To a takaice dai Abbah Abbas bai tunkari amaryarsa da wata magana ba har sai da tayi uku a gidansa "tukkuna ya tunkareta da wata bukata! sai kace wacce take jiran zuwansa ta kar'be shi hannu biyu, shi kuma ya shiga gwada mata soyayyarsa mai wahalar samu! Zainab itama ta dinga nuna masa fitinarta sai dai da akazo fad'an qarshe ne ta gane bata da wayo! dan ba wai tausayinta ya tsaya yi ba aiki yayi sosai ya zage a kanta ya bata kashi duk tarin sha'awar da ya tara ta tsayin wattanin da suka gabata ranar sai daya samu cikakkiyar gamusuwar da yake bukata da yarinyar...Zainab taji maza! ai lokaci guda ta shiga hankalinta ta daina rawar kai kullum a tsorace take da angon nata dan tun ranar daya mayar da ita cikakkiyar mace ya daina d'aga mata k'afa kullum sai ya biya bukatarsa har kwanaki bakwai d'inta suka" "qare, ta dinga murna tana godewa Allah zata sarara.""" ****** 'Bangaran Naja'atu kuwa abun babu dad'in ji dan tun ranar data samu labarin auran Abbah Abbas taqi "lafiya ciwon kai ciwon kirji da dai sauran ciwoka! Gashi sai 'boyewa Mmn Sajida take taqi ta bari ta gane bata da lafiya, to itama Mmn Sajidan da yake 'yar sabga ce bata fahimci komai ba sai dai sa'i da lokaci idan ta kalli Naja'atun takance"" Naja'atu duk kin rame kinyi haske dan Allah ki cire damuwa da fargaba daga ranki! wallahi nasan iyayenki nacan hankalinsu a tashe sakamakon rashin ganinki ke kuma sabida wata manufa taki kin'ki kije garesu, duk fa abinda ya faru da rayuwarki qaddarace iyayenki musulmai ne" "zasu kar'bi qaddarar da Allah ya dora miki ba zasu guje ki ba.""" Duk sanda Mmn Sajida tayi mata wannan maganar ba ta cewa komai sai da tayi murmushi tayi shuru da bakinta. Mmn Sajida haushi yasa ta tattarata ta qyaleta da taurin kanta. To kamar yanda suka yanke shawara kancewa Hajia Rabi zata je garin jos domin dauko Naja'atu hakane ya kasance Direba ya dauketa da wurwuri suka nufi garin Sai dai tun kafin direban yayi parking din motar suka hango gate din gidan garqame da 'katon kwado! Ga unguwar shuru babu wanda zasu tambaya. Hajia Rabi ba tayi qasa a gwiwa ba ta dauko wayarta ta kira mijinta domin sanar dashi halin da "ake ciki Alhaji Ya shiga mamaki mutuka yace.""Lallai su samu wani a unguwa wanda zasu tambayi domin" yayi musu qarayin bayani .......Direba ya fito ya tsaya jikin mota yana kallon yanayin unguwar...Cikin ikon "Allah wani bawan Allah yazo wucewa sai ya tsayar dashi da sauri ya miqa masa hannu suka gaisa yace.""Malam dan Allah ko kana da labarin mutanan nan gidan nan."" Ya fada yana nuna masa gidan" "Mutumin ya jima yana kallonsa kafin yace.""Amma ba a garin nan kake ba ko.""? Da sauri yace.""Eh kwarai" "kuwa."" Mutumin ya girgiza kansa gami da fara bashi labarin abinda ya faru da mutanan gidan ya rufe" "maganarsa da fad'in 'Wannan gidan da kake gani yanzu yana hannun bank dan haka tun wuri ku bar gurun nan tun kafin jama'a su ankara daku."" Da" Haruna Direba ya mika masa hannu yana masa godiya ya bude mota ya shiga...Ya kunna da sauri suka fita daga layin gidan Sai da suka hau titi sosai san Ya sanar da Hajia Rabi abinda mutumin ya fad'a "masa. A sanyaye tace""Wannan al'amari baiyi dadi ba ko kadan ko yanzu ina Naja'atu take? Kira ne ya" shigo wayar ta ta dauka da sauri dan ganin wanda ya kira. "Alhaji yace.""Ina fata kun samu cikakken bayanin inda Naja'atu take, a sanyaye ta shiga fad'a masa" maganar da mutumin nan ya fad'a dangane da gidan Aminu Dan jaridan....Alhaji yayi shuru yana tunanin inda zasu samu Naja'atun a cikin garin Jos. *ANA WATA GA WATA* Wani masifaffan amai ne ya tashe ta daga baccin da takeyi na safe! A guje ta dafe kirjinta ta nufi bakin rariya ta dinga kwararawa tana wani irin kakari tare da dafe kirjinta. Ta kai minti goma tsugune a "gurin kafin ta dan samu sassauci ta dauraye bakinta tare da mikewa tana dafa bango(garu) ta ciko buta da ruwa tazo ta wanke gurin data 'bata, tana tangadi ta koma daki ta zauna tana mayar da numfashi Bayan Mintina ashirin tana zaune a takure zazzabi na neman rufeta ta sake jin wani" "aman ya sake yunkuro mata da masifar qarfi! da sauri ta mike ta nufi bakin rariya ta tsuguna tana yi tana hawaye! tun tana amayo abinci har sai da ta dawo amayo ruwa shima ruwan ya daina fitowa sai miyau da majina ne kadai ke fita, kuka takeyi tana kiran sunan Allah ta samu gefan rariyar (kwata) ta kwanta tana wani irin nishi tare da janyo numfashi da kyar! Naja'atu haka ta yini kwance a bakin rariya daga taji yunkurin amai sai tayi ta kakari amma babu abinda zai fito sai miyau mai dacin gaske Haka Mmn" "Sajida ta dawo daga cefane ta sameta lokacin ma ta galabaita sosai dan jikinta yayi laushi duk ya saki Hankali a tashe Mmn Sajida ta shiga gidan Mmn Ladi suka fito tare, a daidaita sahu suka samo" suka kamata dakyar suka sata a ciki suka zazzauna a gefanta domin ri'keta asibitin kudi Mmn Sajida tace su nufa dan ganin yanda Naja'atun ta galabaita yasa ta yanke wannan shawarar tana jin tsoron kada yarinyar mutane ta mutu a hannunta a tuhumeta shiyasa take gani ko nawa ne zata iya kashewa domin samun lafiyarta. Gwajin farko Dr ya tabbatar musu da cewar tana da ciki dan kimanin sati tara! Wata biyu da sati daya! Mmn Sajida Da Mmn Ladi suka shiga cikin mamaki mai tsanani Ciki ciki! lallai Allah ya had'a Naja'atu da babbar qaddara........ *Littafin na kudi ne...!* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake. Vip group #600 normal group #300 accont....0542382124...Binta umar gtbank. Idan katin waya zaki tura sai kiyi min mgn ta wahsap da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *MANZIR _ALWAFIR ABUJA * _*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci magungunansu babu almundahana a ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu ko wace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye da akwai gruops na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rijistar dasu to kukanki ya 'kare idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_ "*****60 Mmn Ladi tace""Dama fa ni wallahi sai da jikina ya bani cewar haka zata iya kasancewa kawai" "dai dan yarinyar ta nuna bata san maganar ne yasa nayi shuru amma da tun farko ta dauki maganata da muhimanci munje asibiti sun dubata sosai a lokacin da sai mu san yanda zamuyi da cikin tunda baiyi kwari ba amma yanzu ciki har ya shiga wata na uku ai akwai matsala idan akace za'ayi wani yunkuri a kansa, gaskiya na tausayawa yarinyar domin haihuwa da irin su Bash matsala ne da da yanda za'ayi" kawai a zubar da cikin nan wallahi. "A sanyaye Mmn Sajida tace""Nima dai jikina yayi sanyi wallahi amma bari ta tashi daga bacci muji" "hukuncin data yanke."" Ajiyar zuciyarta da shashshekar kukanta sukaji." da sauri suka kalli gadon da take kwance! Ta bude idonta a hankali hawaye wani na bin wani ta kalli "Mmn Sajida murya na rawa tace""Ciki ne dani ko.""? A sanyaye Mmn Sajida ta daga mata kai" "Rintse idonta tayi hawaye suka cigaba da zubowa'' Innalilihi wa'ina ilaihi raji'un.""! Ta furta wannan" kalmar tare da sake bude idonta tana kokarin mikewa zaune. Mmn Ladi dake kusa da ita ta taimaka mata ta zauna tana goge hawayen fuskarta amma kamar bata gogewa wasu ne suke zubowa. """Allah na kar'bi wannan kyautar da kayi min ba zan sake yunkurin sa'ba maka ba Ubangiji Allah ka ingata" "abinda ke cikina Allah kasa ya zama cikon addinin musulunci."" Wannan maganar ta fad'a tana me tsurawa rufin dakin ido." "Mmn Ladi tace""Bamu gane me kike nufi ba Naja'atu yanzu sabida baki da hankali sai ki yarda ki haifi cikin" "nan to wane labari mai dadi zaki bawa d'an da kika haifa idan ya girma? ai kwanciyar hankalinki da samun nutsuwar ki kawai ki zubar dashi shine yafi alkairi a tattare dake.""" Girgiza kanta ta dinga yi tana kallonsu tana kuka kokarin tsayar da ruwan hawayen dake gudana a "fuskarta, tace""Bazan 'kara aikata kuskuran da nayi a baya ba Mmn Ladi koda ace wannan cikin ta hanyar banza na sameshi ba zan zubar dashi ba sai na haifeshi domin ban san munufar ubangiji a kansa ba." "Wallahi mutukar kinga ban haifi cikin nan ba to Allah ne bai nufa domin ni yanzu abinda zai kusantani da ubangiji nake so ba abinda zai nesanta ni dashi ba, a baya nayi kuskure wanda har yanzu nake cikin nadamarsa, to bana fatan na sake aikata wani kuskuran da Allah zai yi fushi dani ya tuhume ni a ranar" lahira kawai ku dai taya ni da addua kan Allah ya rabani dashi lafiya. "Wannan kalaman nata sune suka kashe musu jiki Mmn Sajida tace""To shikkenan Naja'atu zamu cigaba" "da taya ki addua kan Allah ya saukeki lafiya ya kuma kawo miki mafita a rayuwarki, ammafa yana da kyau ki koma ga iyayenki domin zaman da kike a tare damu bashi da wani amfani na fad'a miki duk inda iyayenki suke suna can hankalinsu a tashe suna neman inda kike me zai sanya ki dinga jin tsoro da" "tunanin wani abu daban.""" "Ajiyar zuciya ta sauke tace""Mmn Sajida ko dai kin gaji da zama dani ne? ko kin gaji da ciyar dani abincinki" "shiyasa kike wannan maganar.""? Mmn Sajida ta shiga girgiza kanta tana murmushi mai ciwo" "tace""Gaskiya Naja'atu ban ta'ba tsammanin jin wannan maganar daga gurinki ba Haba dan Allah meye" makwanci meye kuma abinci da har kike tunanin saboda su nake cewa kije ga iyayenki! To idan tunanin da kike kenan ki daina Mmn Sajida ba haka take ba duk wani abu da nake miki inayi miki ne tsakani da "Allah bada wata manufa ba.""" Naja'atu qasa tayi da kanta tana nadamar maganar data fad'awa Mmn Sajida dan sai bayan ta fad'i "maganar ne ta gane kamar bata kyauta ba, tasan halin Mmn Sajida macace mai karamci da mutuncin itace zata fad'awa wani hakan" Likita ne ya shigo dakin hannunsa rike da wata farar takarda! Ya mikawa Mmn Sajida da fadin duk wasu "bayanai na jikin takardar nan idan kun duba zaku gani."" Mmn Sajida da Mmn Ladi basa jin turanci sosai shiyasa basu fahimci rubutun da likita yayi a jikinta takardar ba." "Naja'atu ta kar'bi takardar tana dubawa, gabanta ne ya fad'i ganin kudin gadon data kwanta yini guda" dubo goma sai kudin magungunanta dubu bakwai da dari biyar. qasa tayi da kanta tana jin nauyin fad'a musu abinda ke rubuce a takardar. To a Ina Mmn Sajida taga dubu goma sha bakwai yanzu gabad'aya Jarin abincin siyar wa ta baifi na dubu ashirin ba dashi take ci take sha ita da 'yayanta yanxu idan ta sanadiyar ta ta ruguza mata sana'arta me zata ce.? jikinta ne yayi sanyi sosai ta tsirawa takardar ido tana tunanin yanda za'ayi. "Mmn Sajida tace""Naja'atu me Dr din ya ruboto."" A dan sanyaye tace""Mmn Sajida me yasa kuka kawo ni" "pravite hospital baku kaini na gomnati ba.""?" "Mmn Sajida tace""Naja'atu tsorata nayi da yanayin yanda ganki shiyasa na yanke shawarar kawo ki" asibitin kudi domin ayi gaggawar dubaki sanin da nayi cewar idan na gomnati mukaje kafin ma mu samu kati babban aiki ne sannan idan mukaje gurin ganin likita nan ma sai mun 'bata lokaci shiyasa kawai na "yanke wannan shawarar.""" Wasu hawaye masu zafi suka sauko a kumatunta gaskiya ta tabbatar da cewar Mmn Sajida masoyiyarta ce har ta mutu ba zata ta'ba mantawa da karamcinta ba. Shuru dakin yayi Mmn Sajida jikinta yayi sanyi itama tana jin tsoro da fargabar abinda ka iya zuwa ya "dawo...Tace""Nawa ne kudin gadon dana maganin insha Allahu ba zai gagara ba.""" "Ta kalleta tana girgiza kanta tace""Dubu goma sha bakwai da dari biyar."" Mmn Ladi ta ri'ke bakinta cike" "da mamaki tace""Dubu goma sha bakwai harda wata dari biyar a kai! Tabdijam! ko awa hud'u ba kiyi a kwance ba har kinci wannan kudin.""" "Naja'atu tace""Ba kudin gado bane kadai harda na magani."" Mmn Ladi tace""Duk da haka dai wallahi da" "tsada haba abin yayi yawa dubu goma sha bakwai fa ba kad'an bane gaskiya asibitin nan suna da tsada ta'bdijam.""! Mmn Sajida tace""Duk mu bar maganar dan Allah ko nawa suka rubuta ai hakkinsu ne tunda dai mu muka zo neman taimako kuma sun taimaka mana a lokacin da muke bukata bai kamata mu tsaya surutu ba, Yanzu ni abinda ke hannuna gabad'aya dubu bakwai ne dama na ajiyesu saboda wata matsalar, amma yanzu zan koma gida zan dauki buhun shinkafar dana siyo shekaran jiya zan kaiwa" maigari mai kanti ya siya nasan idan na siyar za'a had'a kudin "Girgiza kanta ta shiga yi tace""Kin san Allah Mmn Sajida ba zaki ruguza sana'arki kaina ba! Ban amince ki" "siyar da shinkafar ki ba."" Mmn Sajida tace""To ya kike so ayi? Kin san dai babu wanda zanje gurinsa da bukatar ya bani aron kudi ya bani kai tsaye mutane yanzu kwata kwata basa bada bashin kudin." Naja'atu shuru tayi tana tunanin yanda za tayi gaskiya ba zata bari Mmn Sajida ta rusa sana'arta a kanta "ba tunani ta shiga yi ko ta kira Abbah Magaji a waya ta fad'a masa halin da take ciki! Girgiza kanta tayi, gaskiya ba zata iya kiransa a waya ta fad'a masa cewa ya taimaka mata da kudin magani ba saboda tasan halin masifarsa, kuma bata manta cin fuskar da tayi masa ba tana jin kunya sosai 'Daya bangare na" zuciyarta yace mata kawai ki kira wayar Abbah Abbas zai taimaka miki tunda dama shi mai tausayi ne zai iya turo da kudi a biya asibiti kudinsu. Ajiyar zuciya ta sauke tana tunanin kamar wannan shawarar data yanke itace shawarar data dace dan gaskiya ba zata amince da shawarar Mmn Sajida ba. Suna tsaka da "tunanin mafita likita ya sake shigowa ya kalli Mmn Sajida da fad'in ""Hajiya ku muke saurara dan tuni mun sallameku ku biya asibiti hakkinsa." "Murya na rawa Mmn Sajida tace"" Dr kayi hakuri yanzu zan je gida insha Allahu kafin goma na dare zan" "kawo maka kudin.""" "Dr yace""Ni tara tana yi na tashi daga aiki wani ne zai maye gurbina kuma kuka kwana to kud'inku ya" "qaru zaku biya dubu ashirin da bakwai da dari biyar."" Mmn Ladi ta zare ido tana kallonsa! Ita kuwa Mmn Sajida mi'kewa tayi da sauri tana fad'in ""Insha Allahu yanzu zan dawo."" Dr ya kalli agogon hannunsa da" "fad'in ""Okey idan kika wuce tara baki dawo ba to ba zaki sameni ba."" Yana gama maganarsa ya juya da" niyyar fita. """Dr."" Muryarta ta katse musu hanzari daga shi har Mmn Sajidan da take kokarin bin yansa domun" "tafiya. Duk suka juyo suna kallonta, tace""Idan babu damuwa ina bukatar ka bani aron wayarka zan kira" "mahaifina da ita insha Allah za'a tura maka kudinka.""" Dr yayi kasaqe! yana kallonta kafin ya d'an d'age kafad'arsa ya dauko wayarsa dake gaban aljihun rigarsa "ta likitoci ya karasa har bakin gadon da take zaune ya miqa mata. Ta kar'ba a sanyaye, tana dubawa" dama kafin ya bata wayar sai da ya cire mata sucurity da yake kai Tana tararrabi da fargaba ta sanya numbar Abbah Abbas din a wayar ta shiga gurin kira gabanta na wani irin fad'uwa ta shiga kiran wayar. Daf da zata katse aka d'aga! ta sauke wata zazzafar ajiyar zuciya tana jiran taji muryarsa sai "kawai taji murya mace mai tafe da iyayi da feleqe! tana fad'in ""Waye yake magana.""? Gabanta ya dinga dukan uku uku! wacece wannan? Take tambayar kanta, tasan muryar Halisa kuma tasan muryar Saddiqa Mussadiq Mufida! muryar wannan me maganar ce bata tantance ba, Zuciyarta tayi saurin fad'a mata cewar amaryarsa ce! ji tayi idanunta na neman rufewa! tsabar fargaba! Tayi gum! da bakinta takasa magantuwa tana jin muryar Zainab sai magana takeyi amma uffan ta kasa cewa. Zainab tace"" To ikon" Allah waye wannan anata magana yana ji yayi shuru tsaki taja ta kashe wayar. Naja'atu ta shiga "rarraba idonta a dakin gumi! na tsatstsafo mata! Dr yace.""Ke nake saurare naji kamar an d'aga wayar ana magana kuma baki ce komai ba." "Da sauri ta dawo hankalinta tace""Yi hakuri Dr bari na sake kiran wayar bana ji sosai shiyasa na kasa" "magana."" Okey kawai yace ya zuba mata ido yana kallonta tamkar zai lasheta. Zainab hannunta r'ike" "da wayar ta kama hanyar fita palo inda Abbah Abbas din ke zaune yana hutawa.. tana daf da karasawa inda yake wani kiran ya sake shigowa, a maimakon ta kai masa wayar sai kawai ta d'aga tare da kara wayar a kunnanta da fad'in ""Waye yake magana."" Naja'atu ta daure da kyar tace.""Nice.""? Zainab jin miryar mace yasa gabanta faduwa tace""Kece wa.""? Abbah Abbas yayi saurin juyowa yana kallonta jin" yanda tayi maganar cikin izzah! da gadara! 'Bangaran Naja'atu kuwa ji tayi tamkar yarinyar ta soka mata wuqa a kirjinta jin yanda take wani daka "mata tsawa kamar uwarta! har ta hasala! sai kuma ta sassauta zuciyarta tace.""Naja'atu."" Zainab tayi shuru tana mamaki! Naja'atu Naja'atu? tasan sunan rad'au! a bakin yaran gidan kuma ta samu cikakken bayani a bakinsu da sauran jama'ar gari tunda dama hausawa nacewa ko haqa rami kayi ka bunne abu to wata rana sai ya fito an ganshi, duk labarin Naja'atu tasan shi daga farko har'karshe sai dai duk yanda take zungurar maigidan kan maganar koda wasa bai ta'ba bata wani labarin da ya dangace shi dashi da" "Naja'atun ba. ""Oh! nagane to wa kike nema.""?" "Naja'atu murmushin takaici tayi Kai tsaye tace""Ina neman mijinki ne idan yana kusa ki basa wayar zanyi" "magana dashi."" Zainab tace""Okey kada ki damu."" Sai kitt! ta kashe wayar ta nufi inda yake tana wata karairaya ga wani tsadaddan murmushi a fuskarta, zama tayi a kusa dashi tasa hannu a fuskarsa tana shafa gemunsa tare da wasa da karan hancinsa tace""Masoyinta sannu da hutawa."" Kafad'arta ya r'ike hankinsa na kan wayarsa dake hannunta ya kar'ba yana fad'in ""Waye ya kira ne.""? Tace"" Wata ce aka samu akasi ta kira number ka."" Abbah Abbas bai gamsu da maganarta ba ya 'kurawa number ido, wayarsa babba ce sosai shiyasa daga ko wane gari ko wace qasa aka kirashi sai ta nuna masa, ganin number daga garin jos ne yasa ya d'an shiga mamaki! Sai kawai ya tsinci kansa da kiran wayar...Lokacin Dr har ya kar'bi wayarsa zai fita kiran ya shigo, da sauri ya dawo da baya ya miqa mata wayar. Rai a" "'bace! ta daga wayar ta kara a kunnanta tace""Ke! dallah malama! ki bawa mai wayar abarsa mana wai ke" "amarya sai hauka kikewa mutane mtssw! ki bawa mai waya wayarsa zanyi magana dashi.""" Muryarta ta dinga dukan kunnansa yayi shuru yana sauraranta har sai da ta gama hayaniyar sannan yayi "gyaran murya a nutse ya kira sunanta. *""Naja'atu!!!*" "Wani irin yarrr! taji tun daga saman kanta har i zuwa tafin 'kafarta a sanyaye tace""Na'am Abbah Ina" "wuni.""? Ajiyar zuciya ya sauke da fad'in ""Lafiya lau ya kike ya maigidanki."" ? Ya nuna kamar bai san abinda ke faruwa ba." "Kuka tasa masa tace""Abbah bani da lafiya gani a kwance a gadon asibiti likita na bukatar kudi bani dashi" "bani da wanda zai biya min shine na kira ka ko zaka taimaka min kamar yanda Allah yake taimaka maka."" Jin maganar rashin lafiya yasa ya mayar da abin serious yace.""Baki da lafiya Baki da wanda zai biya miki kudin magani ina mijinki yake.""? Tana kuka tace""Ya sake ni ai.""? Shuru yayi dama abinda yake so kenan yaji daga gareta...Yace.""Yanzu kina ina.""? Cikin shashshekar kuka tace""Ina tare da wata mata mai kirki tana taimakona."" Girgiza kansa yayi yace""To Allah ya sawwaqe! Bani Likitan zamuyi magana dashi."" Tayi saurin miqawa Dr din wayar. Tana jinsu suna magana da Dr din yana tambayarsa abinda ke damunta" Dr yayi masa cikakken bayani sannan ya fad'a masa kudin da ake buqata. Yace Yanzu ya tura masa "account number nasa zai sa masa kudin Sallama sukayi da juna Dr ya kallesu a nutse yace.""To" "alhmdullhi zaku iya tafiya yanzu."" Mmn Sajida da Mmn Ladi sukace ""To mungode."" Da sauri Dr ya fita daga dakin su kuma suka shiga shirye shiryen tafiya gida......" *_Allah yasa cikin ya zube Aunty Binta ci kuma!!! dan Allah kada ta haihu da Bash Aunty Binta wannan pege d'in ya bani haushi Wato kuna so rabo ya kashe ni ko? To Yanda Allah ya saukar da ikonsa a kan Naja'atu nima 'yar kallo da addua ce........Alhamdullhi saqona na cikin littafin nan ya "soma isa, ha'kika wani baya ta'ba haihuwar d'an wani Allah ya qaddarta akwai rabo mai zafi a tsakanin Bash da Naja'atu shiyasa suka rabu da Abbah Abbas cikin 'kan'kani lokaci ta auri Bash shima suka rabu" "cin 'kan'kanin lokaci bayan ya saukar da ikonsa a kansu, babu wani wanda yasan gaibu sai Allah *" *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake Vip group #600 normal group #300 account....0542382124....Binta umar gtbank. Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan number. *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* "****61 Abbah Abbas shuru yayi da wayar a hannunsa yana tunanin maganar da dr ya fad'a masa," "Naja'atu na dauke da cikin wannan lalataccen yaron! hakika wannan al'amarin ya tsaya masa a rai mutuka, ba wai yana kishi ne da faruwar hakan ba yasan Allah ba yanda baya tsara al'amarinsa, yarinyar kawai yake tausayawa had'uwar jininsu da yaron da duniya tasan mutumin banza ne, koda yake Ubangiji kan saukar da shiriya akan bayinsa a lokacin da yaso, wannan dalilin ya sanya yaji zuciyarsa tayi sanyi sai kawai yayi addua a kam Allah ya shiryi Bash din ita kuma Naja'atun Allah ya sauketa lafiya ya sanya rabuwar auranta da Bash din shine alkairi Zainab kuwa kunya ce ta isheta tana jin tsoron kada ya" "tuhumeta a kan me yasa tayi masa karya bayan ta gane Naja'atu ce ta kira wayarsa, sai taga gabad'aya" ma hankalinsa da tunaninsa bayan kanta yana can wani tunani na daban. "Sai goma shaura na dare suka isa gida, Mmn Ladi kai tsaye gidanta ta wuce saboda tasan mijinta ya" "dawo kuma bata fad'a masa zata fita ba tunda bata da waya, yanzu babu laifi sun shirya sun daina fada sosai duk a sakamakon nasihar da Naja'atu tayi mata. Mmn Sajida ganin mutane sun cika rumfar" "kwanon siyar da abincinta yasa ta sallamesu da fadin yau babu abinci sai gobe idan Allah ya nufa. Dantalle ya nufo inda suke ya sha shaddarsa 'yar rini hannunsa rike da mukkulin lifan d'insa," "yana washe baki yace.""Mmn Sajida dama wannan qanwar taki tana nan.""? Mmn Sajida tace""Eh tana nan Dantalle ya gida ya iyali.""? Ya amsa idanunsa a tsaye a kan Naja'atu."" Yace."" 'Yan mata ya kike ya gari ya jin dadi.""? Naja'atu duk da halin ciwon da take ciki sai da ya bata dariya, wai shi dole sai ya burgeta ta lura mutumin yana so ya wuce gona da iri Tace""Lafiya lau jin dadi na gurinku.""' Dantalle dadi ya isheshi" "ya kalli Mmn Sajida yace yau babu abinci naga alamar ma kamar daga unguwa kuka dawo ko.""? Mmn" "sajida tace wallahi kuwa munje wani guri ne."" Yace.""To bbu laifi bari naje na dawo kada ku rufe gida da" "wuri."" Mmn Sajida tace""To shikkenan."" Ya juya da sauri ya nufi inda lifan dinsa yake Su kuma suka" "shiga gidan Mmn Sajida na fad'in ""Wahalalle kawai ya fito ya bar iyalinsa yana biye biyen gidajen abinci gabad'aya Dantalle baiyi ba wallahi."" Naja'atu murmushi tayi tace.""Ni kam gani nayi ma kamar sonki yake."" Mmn Sajida na kokarin bude dakinta tace""Ai ko maza sun kare a duniya ba zan auri dantalle ba" "Gwara nayi ta zama a haka.""" Walid da Sajida tuntuni sunyi bacci da yake Walid nada wayo shine yayi musu shimfida ya daura musu "net suka kwanta, ita kuma Mmn Sajida kicin ta nufa da sauri da yake tana da karamin gas sai ta fara kokarin d'ora ruwa ta dafa musu indomee sai kawai sukaji sallamar Dantalle daga waje Mmn Sajida" "tace""Naja'atu gashi can ya dawo ko zaki 'kokarta kije kiji dame yazo.'' Naja'atu tace""Rabani da wannan guy Mmn Sajida ki daure dai kije kada yace an masa wulakanci."" Mmn Sajida ta dauki mayafinta ta fita. Minti biyar sai gata ta shigo hannunta rike da manya manyan ledoji Dantalle yaje ya kashe musu" "kudi gurin siyayyar kayan ciye ciye gami da kayan masarufi."" Sosai Naja'atu ta dinga mamakin siyayyar tafi ta dubu biyar haka kawai bai ka gidansa ba yazo yana bawa duniya kai Allah ya shiryi mazan dakewa iyalinsu mugunta suna bayarwa a waje Mmn Sajida tace""Kadan kika gani in dai Dantalle ne kuma" wannan hidimar da yake yi da biyu yake wallahi ko shakka bana yi saboda dake yake yi. Naja'atu ta shiga girgiza kanta tana mamakin al'amarin wasu mazan........To Sai da suka zo kwanciya "Mmn Sajida take tambayarta dazu da wa tayi a waya a asibiti...Naja'atu kai tsaye tace mahaifinta ne anan Mmn Sajida tace na fada miki dama suma iyayen naki suna can hankalinsu a tashe dan Allah kiyi hakuri ki koma garesu ko kya samu nutsuwar zuciyarki idan kina zaune a gurina lalattatun maza irinsu Dantalle zasuyi ta kawo miki farmaki."" Tace""Mmn Sajida insha Allah zan tafi gida amma sai jikina ya warware tukkuna."" Mmn Sajida tace to Ubangiji Allah ya baki lafiya mai amfani kuma ya rabaki da abinda" "ke cikin ki lafiya.""" Bayan wata biyu cikin Naja'atu yayi wata hudu da 'yan kwanaki A lokacin ne Allah ya azurta Zainab da "samun nata cikin, murna a gurinta tamkar me! shima Abbah Abbas din sosai ya nuna farin cikinsa a kan karuwar daya samu, ya shiga lalla'bata gami da nuna mata so da kulawa, yarinyar ta samu sake sosai sai abinda take so takeyi a gidan Halisa ta sake shiga cikin wani irin hali na tashin hankali da damuwa dan" duk irin kokarin sauke hakkinta da maigidan yake yi gani take kamar baya adalci a tsakaninsu tana gani tamkar yafi fifita Zainab din a kanta lokaci guda tayi wata iriyar rama mara kyawun gani Zainab mai "wayo gami da so ta siye zuciyar mijinta ai tuni ta janye yaran sun koma bangaranta yanzu komai nasu na gurinta haka take kulawa dasu gami da sanyasu farin ciki, tuni yaran suka manta da wata Naja'atu saboda sun samu wacce ta maye musu gurbinta sai dai sa'i da lokaci Mussadiq yana tunawa da ita. Ranar wata Alhamis da yamma Yaya Ramlatu ta dira a gidan, kai tsaye bangaran Halisa ta nufa, ta" "zauna suna gaisawa! Halisa tace""Yaya Ramlatu sai yau aka tuna dani.""? Ta'be bakinta tayi tace""Halisa" kenan ai lamarin ki ne yake bani haushi wallahi dubeki dan Allah duk kin lalace yarinya qarama tazo ta "kwace miki miji da gida da yara kin kyaleta ba zaki dauki mataki ba.""" "Halisa tayi shuru tana nazarin maganar Tace""Yaya kenan ni yanzu ba tashin hankali ne a gabana ba" "ingantuwar lafiyata kawai nake bukata.'' Ramaltu ta ta'be bakinta tace"" ai shikkenan tunda kin mayar da kanki sususu!! ni kinga tafiyata."" Sai kawai ta miqe ta kama hanya ta futa." "Tana fitowa ta durfafi bangaran Zainab, lokacin suna zaune ita da yara a palo suna kallo suna wasa da" dariya! Kawai sai ganin mace tayi ta shigo mata babu sallama. Yaran duk sukayi tsuru-tsuru murya na rawa suka shiga gaisheta! Ramlatu ta samu guri ta zauna tana muzurai sai bin palon da kallo take tana watsawa Zainab kallon banza. Zainab dama a ciki take da matar domin ta tsani d'abiar da take mata kamar ba babba ba sai ta dinga shigo mata babu sallama...sai kawai ta dauke kanta taqi kallonta ballantana ma ta gaisheta. "Yaya Ramlatu ta fusata! sosai ! tace""Ke baki san matsayina bane da ba zaki gaisheni ki bani girma ba.""?" "Wani irin kallo Zainab tayi mata tace""Nasan matsayin ki mana kina so nayi miki sujjada ne.""?" "Ya Ramlatu tace""Ko baki yi min sujjada ba ai sai ki mutuntani a matsayina na yayar mijinki."" Zainab ta" "ta'be bakinta tare da dauke kanta. Wannan abun da tayi ya fusata Yaya Ramlatu mutuka, sai kawai ta" "shiga zaginta tana fad'in ""Ita bata daukar raini wallahi idan tace rashin kunya za tayi mata sai taci mutuncinta." "Zainab tace""Kinga dan Allah ki tashi ki fice min a gida ni ban gayyatoki ba haka kawai kizo kina min" "masifa me nayi miki kike zagin iyayena to bari kiji ni ba Naja'atu da kuka raina bace nasan daraja da mutuncin iyayena."" Ya Ramlatu ta miqe ta iska inda take tana zaginta hade da dungure mata kai tace.""Za kici ubanki zanyi maganin Kafin ta qarasa yarinyar ta miqe a fusace! ta wanke ta da mari!" "Tace""Wallahi ba zanji kunyar cin mutuncinki ba mutukar zaki ta'ba martabar iyayena." Yaya Ramltu ta dafe kumatunta jikinta na wani irin tsuma mamaki da al'ajabi kamar ya kasheta 'yar qaramar yarinya da bata wuce jikarta ba itace ta mareta! Sai kawai ta rufe ta da duka ta ko'ina! Zainab ta dinga ihu! tana kokarin kwatar kanta Ramlatu ta haye kanta sai jibga take. A kid'ime! Saddiqa taje ta "fad'awa Halisa halin da ake ciki sai gata sun shigo ita da Baba Larai! gabadayansu sun firgita da ganin duk da Ramlatu takewa Zainab! da kyar suka janyeta sai haki take tana fad'in ""Tunda take a duniya babu" wanda ya ta'ba marinta sai yarinyar na saboda haka sai ta dauki tsatstsauran mataki a kanta. Baba Larai ta bude bakinta za tayi magana ta buga mata tsawa da fadin tayi mata shuru bata son munuafurci. Yafan mayafinta ta gyara ta dauki jakarta ta kama hanyar fita sai zage zage take... Halisa ma juyawa tayi ta nufi gurinta uffan ba tace ba dama itama haushin zainab din take ji shiyasa taji dadin dukan da Ramlatu tayi mata Baba Larai ta taimaka mata ta tashi zaune tana kuka kamar ranta zai fita Baba larai ta rarrasheta gami da "yi mata nasiha akan ta zauna lafiya sannan ta fita daga sabgar Ramlatu tunda ba mutunci ne da ita ba, Zainab jinta kawai takeyi saboda haka tana fita ta dauki wayarta ta kira mijinta tana wani irin kuka ta shiga zayyane masa abinda ke faruwa tace tana kwance ta kasa tashi cikinta sai ciwo yake. Wannan" "al'amarin ya daga masa hankali sosai ashe Ramlatu ba zata kyaleshi ya huta ba! Dama yana jin haushin abinda tayi masa a kan Halisa kawai ya kyaleta ne, to yanzu kuma shine taje har gidansa ta daki matarsa da 'karamin ciki a jikinta wannan karan zai dauki mataki a kanta. Kasuwar ya bari ya nufi gidan, ya dauki" "Zainab sukaje asibiti aka dubata sosai komai lafiya ya dawo da ita gida tare da tarin siye siyen da yayi mata a hanya, yarinyar sai narkewa take tana kuka gami da riqe cikinta ya dinga rarrashinta yana bata hakuri da kyar ta barshi ya koma kasuwa. Koda ya tashi daga kasuwa, wani jami'in 'Dan sanda yaje" ya dauko a motarsa suka nufi gidan Ramlatu dake tudun wuzurci Tana zaune a tsakar gida tana gyara "kayan miya, yaro ya shigo yace.""Wai Ramlatu tazo su gaisa da dan uwanta yana waje. duk a tunaninta Alhassan ne saboda sa'i da lokaci yakan kawo mata ziyara, ta yafa mayafi ta fita, sai ganin Abbas tayi da dan sanda! jikinta a sanyaye take kallonsa yayi bala'in shan kunu tare da umartar d'ansandan ya daure mata hannu! Kuka ta fashe dashi taje ""Abbas ni zaka tozarta a kan matarka.""? Ko kallonta baiyi ba ya sake Umartar dansandan da maganar, Yaya Ramlatu ta juyo da sauri zata shiga gidanta shi kuma police din nan ya kama hannunta ta baya yasa mata takunkumi! Yara suka cika a gurin Sakina kishiyarta ta fito tana tambayar ba'asi! Abbah kuwa yana ganin an soma taruwa a gurin ya shiga mota ya sauke glass din motarsa mai duhu yana hango artabun da police din keyi da ita taqi sai turjewa take tana kuka da fad'in "" Dan uwana ne fa matarsa ce tasa yazo yaci mutuncina wallahi banyi laifin komai ba."" Jama'a sai kace kace ake a gurin ya cika sosai Abbah Abbas Yana kokarin jan motarsa ya bar gurun Salim yayi parking" "din motarsa ganin abinda ke faruwa yasa hankalinsa ya tashi har ya nufi inda mahaifiyarsa take Abbah ya dan sauke glass din motar ya kirashi Da sauri ya karaso gurin yana risinawa! Abbah yace.""Ina fatan" "ka kammala ayyukan dana sanya ka kafin barowa ta kasuwa.""? Yace.""Eh Kawu na had'a komai kamar yanda kace!."" Yace.""Okey jeka ce da wancan D'an sandan nace ya kwance mata abinda ya daura mata a hannu."" Salim yace.""Kawu wai meke faruwa ne.""? Yana kokarin kunna motarsa domin barin gurin yace kaje ka tambayeta zata fada maka."" Kawai yaja motarsa da sauri ya bar gurin ba tare da mutane sun" farga dashi ba Yaya Ramlatu ta muzanta mutu'ka kafin police din ya kwance mata hannunta ya qara gaba abunsa ita kuwa yara ne suka kewayeta suna surutai a kanta gami da qananun maganganu! Salim jikinsa a sanyaye yaja hannunta tana wani irin kuka na tsantsar kunya da takaicin tozarcin da dan uwanta yayi mata cikin unguwa a kan titi tunda gidan nata a kan titi yake shiyasa jamaa yara da manya suka cika gurin cikin gidan suka shiga ita da Salim rayukansu a mugun 'bace. 'Karya da gaskiya Ramlatu ta shiga fad'awa "'Danta tana kuka da fad'in ''Yana da kyau ya dauki mataki kan irin tozarcin da Dan uwan nata yayi mata, Salim ya fusata sosai bai ta'ba jin tsanar Kawun nasa ba sai ranar ko lokacin da ya auri naja'atu bai ji haushinsa ba kamar yanzu yace.""Kiyi hakuri Mama nagane abinda yasa mutumin nan yake miki wulakanci saboda Allah ya fifitashi a kanku yana da kudi yana da iko shiyasa duk wulakancinsa yake qarewa a kanki to insha Allah sai nayi miki maganinsa sai kinji mummunan labari wallahi sai na daukar miki fansar tozarcin da yayi miki a unguwa."" Ramlatu jin furucin da yaron nata yayi yasa ta tsagaita da" kukan da take tana qara tunzura masa zuciya a kan yabi ta qarqashin qasa ya tagayyara Dan uwan nata 'Bangaran Naja'atu sai dai godiyar Allah dan wannan cikin na jikinta da alama lafiyyye ne ya hanata sakat! "kullum cikin ciye ciye kwadayi iri iri idan ba taci kaza mai kuli kuli ba ji take tamkar zata mutu! al'amarin ya dinga bawa Mmn Sajida tsoro wannan wane irin d'an gayun ciki ne, duk kokarinta sai da ta gaza domin yau da gobe kayan Allah ne kuma tana jin tsoron saka Dantalle cikin harkar sabida kada ya nemi ya fanshe hidimarsa ta rasa bakin magana. Kawai sai ta shirya da sassafe tayi mata sallama tace zata je" "wani guri! Asibiti ta nufa, cikin ikon Allah kuwa ta hadu da Dr shima shigowarsa kenan, suka gaisa a" "mutunce kafin ta tambayeshi bukatar da ta kawo ta, Dr yace to Allah yasa bangoge numbar ba bari na duba dai."" Tace""To Allah yasa dai baka goge ba." "Ya jima yana dube dube a wayar tasa kafin yace.""Alhamdullhi kinga number nan. Ajiyar zuciya ta sauke" "tace to dan Allah rubuta min a takarda bani da waya wallahi."" Biro ya ciro a gaban aljihunsa ya bude wallet dinsa ya dan yagi jikin wata takarda ya rubuta mata number a gurguje ya mika mata ya wuce cikin asibitin Tana murna ta fita daga cikin asibitin ta danyi tafiya kadan ta samu masu communication" "tace""Dan Allah zanyi waya ta minti biyar ko goma nawa zan biya.''? Guy yace.""Kawo naira dari."" Ta bashi kudin had'e da miqa masa number yasa a wayar tana fara ringing ya miqa mata gurin ta bari ta samu inda babu mutane. Abbah Abbas na kokarin shiga toilet domin yin wanka yaji kira a shigo wayarsa" "dawowa yayi ya dauki wayar yana duba number, ganin sabuwar number daga Jos yasa yayi saurin dagawa tare da yin sallama Mmn Sajida ta gaishi a nutse ya amsa yana tambayarta wacece ita," "tace""Alhaji ni sunana Safiyya ina zaune a jos nice kuma wacce Naja'atu take zaune a gurinta dama na kira kane domin na fad'a maka halin da take ciki! Alhaji Naja'atu tana cikin halin taimako ga cikinta kullum sai qara girma yake a matsayinku na iyayenta yana da kyau kuyi hakuri ku gafarceta akan sa'ba muku da tayi ku dubi halin da take ciki kuzo ku dauketa dan nayi nayi da ita akan ta dawo gareku ta'ki! wannan dalilin yasa nace bari na kira ku a waya na fad'a muku halin da take ciki sabida bana so har lokacin haihuwarta yazo bata gaban iyayenta""........Ajiyar zuciya ya sauke bayan ya gama jin bayaninta yace.""Sannu da kokari Safiyya Allah ya baki ladan taimakon da kikayi akan yarinyar nan kuma naji dadi sosai da kikayi tunanin sanar damu halin da ake ciki Allah ya saka miki da alkairi mungode sosai Insha" Allah cikin satin nan zan turo da mota a dauketa watakila ma ni da kaina zanzo Okey dik dai yanda tayi "wu zaki bani cikakken address din inda kuke."" Tace""To shikkenan Alhaji insha Allah yanzu zan turo maka" "text za kaga address d'in idan ma baka gane ba kana shigowa unguwar sai ka tambayi Mmn Sajida mai abincin siyarwa insha Allah za'a nuna maka."" Yace.""To masha Allah mungode kwarai."" Sallama sukayi da juna Mmn Sajida tayi saurin tura masa text din ta mikawa mai wayar, ya duba balance da sauri yace sai kin ciko talatin kin qara minti uku akai."" Hamsin ta mika masa ya dauka ya bata sanjinta tayi saurin tarar" Napep ta shiga domin komawa gida. Shi kuwa Abbah Abbas bayan gama wayarsu da Mmn Sajida sai ya yanke shawara kancewa idan ya isa kasuwa zai samu abokinsa ya sheda masa fa halin da ake ciki yana ganin kamar alhakin komai yana kansu tunda yarinyar dai tuntuni ta bar hannunsa to kafin ya zartar da wani hukunci dole sai magabanta ta sun sani. Da wannan shawarar ya mi'ke ya nufi bandaki domin yayi wanka ya fita harkokinsa.... 62******Yau tsawon kwana uku kenan da Abbah Abbas ya sanar da abokinsa halin da ake ciki dangane "da maganar dauko Naja'atu dake can garin Jos, ya jima yana ta sauraran yaji ta bakinsa a kan a'lamarin Amma Abbah Magaji Yaja bakinsa yayi shuru yaqi cewa komai ballantana ya bada goyon bayan ayi tafiyar. Shi kuma a lokacin gabad'aya hankalinsa ya kasa kwanciya a tsakanin kwanaki ukun kullum" da yarinyar yake kwana yake tashi a cikin ranshi Shi kansa ya kanyi mamaki akan mai yasa yarinyar da cikin dake jikinta suka tsaya masa a zuciyarsa? To Yau daya isa kasuwar ko zama bai bari yayi ba ya nufi rumfar abokin nashi Koda Abbah Magaji "ya ganshi sai da yasha jinin jikinsa gaisawa sukayi a tsanake Abbah Abbas yace.""Wai ya ake ciki ne dangane da maganar da nayi maka kwanaki uku da suka wuce ina ta sauraron naji ta bakinka har yau" baka ce komai ba.'' "Abbah Magaji yace.""Dan Allah Alhaji Abbas ka cire kanka daga sabgar yarinyar nan wai shin meye ma na" "damun kanka a kanta yarinyar nan fa kai ta tozarta amma ka kasa dauke kanka daka kanta, bana so aje inda take a yanzu a rabu da ita duniya ta cigaba da koya mata hankali idan taji uwar bari da kafafunta" zata dawo gida. "Abbah Abbas ya girgiza kansa yana kallon abokin nasa yace.""Ban tsammaci jin wannan maganar daka" "bakinka ba wallahi! wato kana so Ubangiji yayi fushi damu akan rashin yarda da qaddara ko? to inaso ka sani Naja'atu bata isa ta tsarawa kanta rayuwar da take so tayi a duniya ba, komai ya faru da ita dama a rubuce yake daga Allah! Naja'atu ni tayiwa laifi kuma wallahi tuntuni na yafe mata babu wani 'kulli a zuciyata dangane da ita. Sannan naji kana maganar damuwa, dole na damu da yarinyar tunda ni yanzu" "a matsayin uba nake a gurinta, bayan haka kuma dole dani da kai da duk wani wanda ya shafeta ya damu da ita ya kula da ita saboda juna biyun da take dauke dashi, ina ganin akan wannan ma Ubangiji na" "iya tuhumar mu.""" "Abbah Magaji yace."" To tunda abun ya kasance haka kai kana iya zuwa ka daukota ko ka tura a daukota" "ni kam ina da uziri kai ko bani da uziri babu inda zanje wallahi.""" "Abbah Abbas ya fusata sosai yace.""Ashe haka kake da ri'ko! ? wai shin me yarinyar nan tayi maka me zafi" "da kake 'kinta haka gaskiya ka bani mamaki.""!" "Abbah Magaji na murmushi yana kallon abokin nasa dake huci! yace.""Laifin da tayi min bai isa yasa na" "yanke mata irin wannan hukuncin ba, kai tayi wa laifi ni kuma na ara na yafa amma naga kamar kana so ka watsa min 'kasa a ido.""" "Abbah Abbas ya mi'ke yana jan tsaki! da fad'in ""Idan kai baka yafe mata ba ni da tayiwa laifin na yafe" "mata kuma na fasa turawa a daukota da kaina zanje wallahi dana san wasa za kayi min da hankali da ban sanar maka da maganar ba sai dai kawai ka budi ido kaga yarinyar a gabanka."" Yana kar'e maganarsa" ya buge rigarsa ya kama hanyar futa. Abbah Magaji ya bishi da kallon Mamaki! to irin wannan fusata da abokinsa yayi anya kuwa ba so yake ya mayar da yarinyar gidansa ba? Girgiza kansa ya shiga yi yana mamakin al'amarin. "Yana tsaye a tsakiyar katuwar rumfar kasuwarsa yana magana da yaran dake qarqashinsa, Salim ya" shigo gurun.......Abbah Abbas sallamarsu yayi da fad'in kowa ya koma gurin zamansa. ya kalli Salim "fuskarsa babu walwala yace ""Zan tafi jos bayan azuhur insha Allah komai dare zan dawo ka cigaba da" "kula kamar yanda ka saba."" Salim yace.""Insha Allah zan kula amma Kawu ina da maganar da nake so muyi da kai." "Abbah ya tsaya tare da fadin ""Wace irin magana ce."" Salim yace dangane da abinda ya faru tsakaninka" da Yayarka ina nufin mahaifiyata.'' "Abbah Abbas ya sake tsuke fuskarsa yace.""Okey ta turoka ne kayi min rashin kunya."" Girgixa kansa yayi" "yace.""Wallahi ba ita bace nine kawai naga dacewar nayi magana kan hukuncin daka yanke gaskiya Kawu ba zan boye maka ba raina ya baci sosai ba kayi binkice ba ka yanke hukunci cikin 'bacin rai! Ashe ita" "aunty Zainab dince ta fara marin ta shine ita kuma ta kasa hakuri ta doketa.""" "Abbah shuru yayi yana nazarin maganar, yace kai waye ya fada maka Zainab ta mari mahaifiyarka.""?" "Yace.""Aunty Halisa da sauran yaran gidan sune suka tabbatar min da maganar. Abbah ya shiga mamaki" "mutuka ashe Zainab bata da kunya tunda har zata iya futar da hannu ta mari yayarsa gaskiya al'amarin ya bashi mamaki sosai komai zai dauki mataki a kanta. amma sai yace""Ni a ganina duk laifin na" mahaifiyarka ne a matsayinta na babba mai ya kaita zuwa gidan yara! ko shakka bana yi ita ta tunzura "zuciyar yarinyar har ta kai ga ta mareta.""" "Salim takaici da bakin ciki kamar ya kasheshi ya girgiza kansa tare da fadin""To Allah ya sawwaqe."" Abbah" "yace.""Abinda za'ace kenan amma al'amarin mata sai su." To kamar yanda ya fad'awa Salim cewar bayan yayi sallar a zuhur zai dauki hanya hakane ya kasance Abbah Abbas yayi sallama da yaran rumfarsa ya sake jaddadawa Salim ya kula sosai kana ya shiga motarsa ya dauki hanya ba tare da yayiwa abokinsa sallama ba dan har yanzu bai daina jin 'bacin rai dangane da abin da ya faru a tsakaninsu *Sharrin zuciya gami da kyashi da hassada!* Salim bayan fitar Kawun nasa murmushi yayi yana bin katafariyar rumfar dake ciki da kayan maqudan kudi da kallo! girgiza kansa yayi ya nufi wani qaramin daki dake cikin gurin yasa key ya bude a nutse ya shiga ya rufo kofa!. Wata drowar naga ya bud'e kudad'e ne bandir bandir anan suke shiryawa kafin motar banki tazo ta dauka. Yasa hannu ya dinga dauko dauri dauri! sai da ya d'auki dauri talatin ya "mayar da drowar ya rufe, ya samu wata 'bakar leda mai girma da 'kwari! ya loda kudin a ciki ya daure bakin ledar tamau! mikewa yayi ya fito daga dakin ya mayar dashi ya rufe. Yana jiran dare yayi ya" aiwatar da abinda ya tsara! A 'ka'idar kasuwar kafin magariba kowa ya tashi idan kaga mutum bai rufe rumfarsa ba to yana da baki sun ri'keshi ko kuma yana wani muhimin abu Kowa ya tashi sai d'ai-d'ai dan har masu gadi sun iso "domin fara aikinsu, Salim sai da yaga duhu ya shigo tukkuna ya fito daga cikin wannan dakin hannunsa rike da ledar kudin daya loda....Lokacin sauran yaran Abbahn sun tafi sai mutum daya, shima da yaga ledar hannun Salim din bai damu ba saboda ya saba ganin irinta wani sa'in Abbah ya kan sanya shi ya rage kudi ya kai masa banki shiyasa koda Abdulhamid yaga wannan ledar kudin bai damu ba. Tare suka" rufe rumfar sannan sukayi sallama kowa ya nufi inda motarsa take Salim yasa ledar kudin a bayan mota yayi saurin zama a mazauninsa ya figi motar yana d'agawa masu gadi hannu 'Karfe takwas da rabi na dare Abbah ya sauka a garin jos a daidai lokacin ne kuma al'amarin ya bayyana wata gagarimar wuta mai tafe da ba'kin hayaki ta dinga tashi a cikin katafariyar rumfar Abbah Abbas dake cikin kasuwar. Tashin hankali kenan! Hankalin masu gadi ya tashi mutuka suka doshi katon gate din daya rufe rumfar suna kokawar ya za'ayi su bude! "Kafin kice kwabo labari ya bazu a gari, tuni masu rumfuna a wajan gurin suka bazamo domin duba" "dokiyoyinsu...Salim yazo gurin hankalinsa a tashe yana ihu! kamar gaske ya durfafi gate din rumfar da yayi wani irin ja saboda wutar dake cinsa, ihu! yake da wai sai yaje ya bud'e! a take aka rirri'keshi Abbah Magaji da Abbah Alhassan suka janyeshi su kaishi can gefe guda suka ajiye! Kasuwar ta cika da 'yan a gaji kowa na iya bakin kokarinsa. a takaice dai sai da wuta taci ta cinye komai na cikin rumfar kasuwar" "Abbah sannan suka samu nasarar tunkarar gate din suka bud'e, nan ma sai da mutane uku suka fad'i suka suma! sakamakon shaqar hayakin da sukayi Ganin haka yasa jama'a da dama suka tsorata sai" kowa yaja da baya haya'ki ba'kikkirinn ya dinga fitowa daga cikin rumfar.. "Gidan Mmn Sajida baiyi wa Abbah wahala ba,dan da kansa yaje gidan bayan yayi tambaya a farkon layin" "wani matashin saurayi ya kwatanta masa, da yake akwai wutar nepa yasa hankulan Mutanan dake gurin ya dauke gurin kallon motar Abbah dake kokarin samun gurin yin parking." """Alhamdullhi ya furta a fili a nutse ya bud'e murfin motar ya fito, karaf! idanunsa ya sauka kan Naja'atu" "dake zaune kusa da Mmn Sajida da Plate din abinci a hannunta tana ci, ga wasu zaratan samari a tsaye a kansu da alama abinci zasu siya." "Ya dinga jin wani tsantsar bacin rai da takaici na kokarin fasa masa zuciyarsa, mutum ne shi mai tsananin" "kishi mussaman a kan abinda yake so, yaushe Naja'atu ta lalace haka? har take zama a kan hanya gaban maza tana cin abinci kamar tunkiya, gaskiya bai ji dadin wannan al'amari ba. Taku d'aya yayi da niyyar" "isa gurin sai kira ya shigo wayarsa, a nutse ya fito da ita yana dubawa ganin abokinsa ne yasa yaki dagawa, ya cigaba da tafiyarsa yana jin wani kiran na shigowa, dubawa yayi sai yaga Salim ne, sai ya kara wayar a kunnansa tare da yin sallama. "" Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un.""!! Wannan kalmar daya" "ambata itace ta dauki hankulan jama'ar dake gurin, Naja'atu ta miqe zumbur!! tana kallonsa tana so ta tabbatar da shi ne ko ba shi bane!! Jin muryarsa rad'au! na fad'in ""Ina fatan wutar ba taci kowa ba."" Salim yace babu wanda taci amma mutum uku sun suma sannan komai dake cikin rumfar ya kone harda" kudin da muka shiryasu a cikin drowar. "Yace.""Salim daina maganar kudi da sauran wasu abubuwa wannan duk a duniya na samesu nasan tunda" "me nema ne ni Allah zai mayar min da gurbin abinda na rasa babban farin ciki na shine wutar bata ci wani ba,nagode Allah da yasa wutar ta tsaya iya kan dukiya bata ta'ba wani ba." Salim jikinsa ne yayi sanyi baiso yaji haka daga gurinsa ba ya dauka zai gigice koma sitiyarin mota ya "k'wace daga hannunsa yayi hatsari! sai kawai yaji shi yana godewa Allah.A sanyaye yace.""To kawu Allah ya mayar maka da alkairi sai ka dawo kenan.? Yace.""Insha Allah gani a inda Naja'atu take kuma komai dare zan dauko hanya tare da ita."" Salim cikin zuciyarsa cewa yayi Allah yasa gurin hanyarka ta dawowa kayi accident kowa ya huta, a zahiri sai yace.""To Allah ya kawo ku lafiya Kawu."" Abbah Abbas ya amsa da amin kafin ya kashe wayarsa. Yana kallon gabansa yaga Naja'atu a durkushe kasan k'afafunsa tana" "shashshekar kukan da yayi mugun d'aga masa hankalinsa, damuwarsa a yanzu ganinta da yayi a tsakiyar" maza tsakiyar hanya gaban mai abinci ba wai damuwarsa wutar data cinye masa dukiya ba babban damuwarsa wannan hawayen da take zubarwa.......... * IKON ALLAH WAI DUK DUBARAR DA NAKE AKAN KADA A GANE BOOK DIN NAN KODA YA FITA SAI DA AKA GANE TO NA DAINA WAHALAR DA KAINA A BANZA WACCE TA KARANTA BATA BIYA BA ALLAH Y * *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake Vip gruop#600 normal group #300 account. Binta umar gtbank idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* "Mddbhrmbn63*******Kuka take sosai kukan da ya dinga jinsa har tsakiyar kwakwalwarsa, Cikin wani" "irin yanayi ya miqa hannunsa a hankali ya kamo hannunta ya miqar da ita tsaye suka tsirawa juna ido ita dashi dalilin hasken wutar lantarkin daya haske gurin yasa ya dinga kare mata kallo yana jin wani irin d'aci! a maqogwaronsa, Naja'atunsa lafiyayya mai san girma itace ta lalace ta zama tamkar qashi da rai" "ga wani irin haske da tayi tamkar mara jini a jiki, k'wayar idanunta kawai daya kalla shine ya nuna masa" "da cewar tana cikin jerin mutanan dake da bukatar jini a jikinsu, komai nata ya sanja a idonsa, wani irin" kallo yake mata wanda kai kana ganinsa kasan na tsantsar tausayi da jin kai ne. Kanta ta sunkuyar "qasa murya irin na wanda yaci kuka ya qoshi tace""Abbah Sannu da zuwa ya hanya.""? Ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya amsa kafin ya kalli agogon hannunsa yace.""Muje kiyi min jagora zuwa gurin uwar dakinki."" A sanyaye ta kalleshi tana so tayi magana ya rigata da fad'in ""Naja'atu nazo garin nan ne da niyyar na tafi dake bana so naji wata magana daga bakinki uwar ri'kon ki ta kira ni a waya kwanaki hudu" "da suka wuce ta sanar min da halin da kike ciki wannan dalilin yasa na yanke wannan shawarar a kanki.""" """Abbah dan Katse ta yayi ta hanyar daga mata hannu yace."" Meye amfanin zaman da kike a garin" mutane bayan wanda kike zaune dominsa ya sake ki wace irin rayuwa kike tunanin zakiyi a inda baki da kowa! sannan kinzo kin d'orawa wata nauyi a wannan zamanin da yayi wahala wa kike tunanin zai dauki lalurar ki kamar yanda wannan matar ta dauka! kiyi wa kanki fad'a Naja'atu duk rayuwar da kike tunanin "za kiyi a garin nan ba kamar kina gaban iyayenki ba.""" Wani irin kuka takeyi mara sauti! tana so tayi magana amma ta kasa saboda kukan daya ci karfinta sai kawai ta kama hannunsa ta riqe gam a cikin nata. a haka suka isa inda Mmn Sajida take "zaune. Jama'ar dake gurin duk suka zubo idanunsu suna kallonsu har suka karaso gurin, Mmn Sajida ta" miqe tsaye cikin karramawa takewa Abba barka da zuwa sai washe bakinta takeyi tana fad'in ya shigo "cikin gidan su gaisa sosai.'' Abbah cikin kulawa yace.""Tayi hakuri ba sai ya shiga ba tunda a kan hanya yake, ya umarci Naja'atu ta shiga gidan ta dauki abinda take ganin zata dauka ta fito su tafi!" "Mmn Sajida ta bita cikin gidan da sauri, shi kuma ya shiga nazarin gurin, matar na bukatar taimako ko ga" "yanayin sana'arta, barin gurin yayi saboda shi mutum ne da baya kaunar kallo a rayuwarsa sai yaje ya bude mota ya zauna yana jiran fitowarta. Mmn Sajida na kuka Naja'atu na kuka a haka suka fito, suka" shiga gidan Mmn Ladi sai gasu sun fito dukkaninsu su ukun suna kuka gwanin tausayi(sabo turken wawa ba) Mmn Sajida da Mmn Ladi sun shiga damuwa gami da alhinin tafiyar Naja'atu mutuka sun shaqu da ita mussaman Mmn Sajida gabadaya kasa magana tayi sai rintse hannun Naja'atu takeyi a cikin nata "A haka suka isa gurin motar, Abbah ya fito yana kallonsu sai kuka suke abun ya bashi mamaki sosai," "yace.""Kuyi hakuri ku daina kuka ba wai kun rabu da itaba har abada ba insha Allah zata dinga kawo muku ziyara sa'i da lokaci.""" "Mmn Ladi tace""Alhaji dole ne muyi kuka wallahi mun saba da yarinyar nan tana da hankali tana bani" "shawarwari masu amfani idan taga muna fad'a da mijina tayi ta bani hakuri tana kawo min misalai ni kam a rayuwar aurena ba zan ta'ba mancewa da wannan yarinyar ba."" Abbah Abbas ya shiga mamaki mutuka Naja'atunsa har ta iya sulhun aure kai alhamdullhi ashe zamanta a garin ya haifar da alkairai" amma yaji dadin wannan labarin. "Mmn Sajida tace""Ballantana kuma ni da muke kwana a guri daya mu tashi a guri daya kullum cikin nuna" "kulawarta take a kaina da 'ya'yana hakika ban ta'ba zama da mutum mai nutsuwa gami da iya mu'amula ba kamar wannan yarinyar kafin na saba da rashinta nasan zan sha fama.""" "Abbah yayi murmushi mai ma'ana kafin yace."" Duk maganar da kuka fada akan Naja'atu naji dadinta" kwarai da gaske inaso na sake jaddada muku kamar yanda na fada muku da farko cewar ba wai kun "rabu da ita bane har abada insha Allah ni nayi muku alkawarin kawo muku ita a duk sanda ta bukaci hakan ina fatan zaku kwantar da hankalinku baku rabu da Naja'atu ba.""" "Naja'atu share hawaye tayi ta kallesu murya na rawa tace""Mmn Sajida kamar yanda Abbana ya fad'a" "muku cewar muna tare har abada hakane ku daina kuka da damuwa kuna ganin kamar kun rabu dani wallahi bamu rabu ba, domin ba zan ta'ba mance alkairinku a gare ni ba, kun tallafe ni a lokacin da nake bukatar taimako baku qyamace ni ba kun jani a jikinki kun bani kulawa ni kuwa me zance muku ai idan na cika 'yar halak baku cancanci na tsawar daku a rayuwata ba insha Allah zan dinga kawo muku ziyara" "kamar yanda Abbana ya fad'a muku.""" To jin haka dasu Mmn Sajida sukayi sai hankalinsu ya kwanta suka daina kuke kuken da sukeyi...Abbah "ya bude mota ya shiga minti biyu ya fito hannunsa ri'ke da kudi yan dubu dubu sun kai talatin ya miqa wa Naja'atu da fad'in ta basu."" motar ya koma yana zauna yana qoqarin tashinta Mmn Sajida ta" "rungume Naja'atu tana zirarar da hawaye da kyar ta saketa Mmn Ladi ma tazo ta rungumeta sukayi sallama cike da alhini da damuwa Naja'atu ta bud'e mota ta shiga, suna tsaye a gurin suna daga musu hannu har sai da motar ta 'bace daga gurin Sannan suka juya da mataccen jiki, Mmn Sajida hada ido" "sukayi da Dantalle daya zubo mata ido yana kallonta shima tamkar yayi kuka! Yarinyar da yake qulafuci ashe ba tsararsa bace, yaso ya yaudareta da kudi da kayan kwadayi ya biya bukatarsa sai ya lura ba wannan ne a gabanta ba, sai yanzu ya qara tabbatar da cewar yarinyar 'yar manyan mutane ce ganin motar da'a kazo d'aukar ta yayi masifar sanyayyar masa da jiki da duk wani wanda yake mata kallon" banza a gurin.. Abbah gabad'aya hankalinsa nakan driving din da yake sai dai kiraye kirayen wayar da yake shigowa "wayarsa shine yake so yasa masa rashin nutsuwa a qalla an kirashi yafi sau ashirin bai daga ba, yasan dai labarin gizo baya wuce na'ko'ki duk wanda zai kirashi a yanzu zaiyi masa jajen abinda ya sameshi ne, wannan dalilin yasa ya'ki daga wayar kowa kawai ya mayar da hankalinsa kan driving din da yake. Naja'atu kanta a qasa nauyi da kunya gami da nadama ya hanata kwakkwaran motsi! a duniya" ita kuwa tana da masoyi wanda ya kai Abbahnta kuwa? Wai tambayar kanta takeyi (To nima dai a "ganina baki da masoyin daya wuce shi) Taji wasu hawayen na kokarin kwace mata data tuna zalintar kanta da tayi, yanzu data hakura ta zauna da auransa da tuni tana zaune hankalinta a kwance, da tuni" ma wannan cikin dake jikinta nasa ne zata haihu cikin nutsuwa da kwanciyar hankali ba tare da fargabar "abinda ka iya zuwa ya dawo ba, yanzu ya za tayi da d'an Bash idan ta haifeshi? wane namiji zata aura wanda zai ri'ke mata d'anta! hawayen da take ta kokarin dannewa suka shiga zuba a kumatunta. Inama ace ana dawo da abinda ya wuce a baya data gyara kuskuranta, ita da kanta tasan" ta aikata kuskure mai muni wanda har ta mutu ba zata daina nadama ba..............Wayar da yake ce ta dawo da ita hayyacinta. """Halisa bana gari a halin yanzu ku kwantar da hankalinku dukkanin abinda ya faru da sanin Ubangiji na" "samu labarin komai bayan tafiya ta jos wuta ta cinye d'aya daga cikin rumfunana to bana mamaki da ikon Ubangiji da kuma abinda ya saukar a kan dukiyata, kada ku manta shine ya bani ita lokacin da banyi tsammani ba, nasan idan yaga dama zai mayar min da abinda na rasa cikin lokaci kankani babban farin cikina wutar bata ta'ba kowa ba shine abinda yafi komai faranta min rai! Dukiya a duniya na sameta kuma anan zan tafi na barta to banga abin tashin hankali ba, kuma ba wai gabadaya abinda nake dashi ne ya 'kone ba akwai kaya masu yawa a sauran rumfunana ina da kudi a banki wanda ban san yawansu ba to me zai sanya na kasa tawakalli dan Allah ya zartar da ikonsa, inaso dukkaninku ku kwantar da" "hankalinku kuyi addua akan Allah yasa haka shi yafi alkairi.""" "Halisa jikinta yayi sanyi tace""To shikkenan gabad'ayanmu ma muna gidan Alhaji kowa hankalinsa ya tashi" "gashi babu wanda ka fad'awa inda kake sai da Salim ya dawo yake fad'a mana wai tun misalin biyu na rana ka tafi jos dauko Naja'atu.""" "Yace.""Eh nayi haka ne saboda wani dalili nawa amma yanzu gamu a kan hanya nida Naja'atun insha" "Allah kafin gari ya waye zamu sauka."" Halisa a sanyaye tace""To Allah ya saukeku lafiya."" Ya amsa da ameen tare da kashe wayar tashi gabadaya." Halisa a sanyaye ta shiga sanar dasu Hajia abinda yace mata Zainab ta cika ta batse sai haushi takeji kishi "kamar ya kasheta, akan me zai tafi dauko Naja'atu ya bar iyalinsa ai bashi ne yake da alhakin daukota ba tunda iyayenta da dan uwanta suna raye shi meye nasa, zainab sosai take kishin naja'atu dan Halisa bata gabanta tunda lura kamar ta tashi daga aiki Naja'atu a sanyaye ta kalleshi tace""Abbah wani abu ya" "faru da kaine naji kamar kana maganar gobara."" Ba tare da ya kalleta ba yace.""Eh bayan na dauko hanya da niyyar zuwa nan sai al'amarin ya afku wuta ta cinye babbar rumfata dake cikin kasuwa."" Jikinta yayi sanyi sosai tace""Allah ya mayar maka da alkairi Abbah Allah ya sadaka da rabo mai amfani."" Yaji dadin adduarta sai ya amsa da ""ameen ya Allah nagode sosai."" motar tayi shuru kowa na tunane tunane a cikin zuciyarsa, Abbah Abbas sosai yake gudu kan kwalta dan gabad'aya ba yaso su kwana a hanya dalilin da yasa kenan ya kashe dukkanin wayoyinsa ya mayar da hankalinsa guri guda. Sai gefin asubahi suka" "shigo garin kano a lokacin Naja'atu ta dad'e dayin bacci dan da yaga tana gyangyad'i sai tsayar da motar ya umarceta da ta koma bayan motar ta kwanta, Lokacin da ake kokarin shiga massalaci domin gabatar da Sallah asubahi yayi parking din motarsa a kofar gidan mahaifinsa, Allah ya godewa kafin ya bude motar ya fito da sauri ya nufi masjid din dake jikin gidan Alhaji, yana kokarin shiga massalacin Baba malam shima na kokarin shiga, sai sukayiwa junansu sallama suka shiga massalacin a tare, baba malam" ya wuce ciki shi kuma ya tsaya bakin famfo domin daura alwala. Naja'atu tun bayan fitarsa a motar ta tashi zaune tana muzarai gami da kalle kallen jama'ar dake shiga massalaci a gaban idonta Baba malam ya fito daga gida ya shiga massalacin ta dinga jin faduwar gaba da wani irin tsoro gami da kunya da nadama na damunta yanzu da wane ido zata kalli iyayenta da sauran jama'ar gari?.................. *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin littafin ga yanda abin yake Vip group #600 normal group #300 idan katin waya zaki tura sai kiyi min mgn ta whasap da wannan number...... *07084653262 BINTA UMAR ABBALE* 64*********Ta jima zaune a cikin motar kafin ta yanke shawarar budewa ta fito a hankali tana waige "waige, gidan alhaji ta nufa domin bata tunanin zata iya shiga gidansu dan bata san irin kar'bar da mahaifiyarta za tayi mata ba." "A sanyaye ta tura kofar palon hajia ta shiga da 'yar karamar sallama a bakinta, shuru palon babu kowa" "sai dai tana d'an jin motsi gami da magana sama-sama a dakin data zauna kafin auranta da Bash, A sanyaye ta zauna kan kujera tana takure jikinta ta kai minti goma a zaune babu wanda ya fito hajia na sama su kuma su Halisa da yaran na cikin wannan d'akin babu wanda yasan da shigowarta, ganin gari ya soma haske yasa ta yanke shawarar miqewa domin taje tayi sallah Dakin dasu Halisa suke ta nufa" tana tafiya salau salau wanda kana ganinta zaka fahimci karfin hali kawai take yi A hankali ta tura "kofar dakin ta shiga da sallama a bakinta, gabad'ayansu suka juyo suna kallonta, Mussadiq ya miqe a guje yaje ya rungumeta yana tsalle da murna had'e da kiran sunanta duk ya cikwikwiye mata hijabin jikinta" Mufida taje gurinta tana ta murna da farin ciki....Saddiqa kuwa tana zaune a inda take ba zaka tantance "yanayin da take ciki ba Naja'atu ta miqa mata hannu murya na rawa tace""Zo."" Saddiqa ta mayar da" kwallar dake kokarin zubo mata ta miqe a nutse ta nufi inda take "Zeey dake bacci sakamakon ihun! da Mussadiq yayi yasa ta miqewa zaune tana 'bata ranta, tana kokarin" yin magana Halisa ta fito daga toilet sai kawai idanunta ya sauka akan Naja'atu dake tsaye a bakin kofa ta rungume yaran sai hawaye take "Halisa tace""Naja'atu dama ke suka gani suke wannan ihun? ni ina bandaki naji ihu ina addua Allah yasa" "ba fad'a suke ba ashe kece."" Tace.""Nice aunty Halisa ya kuke ina fatan na sameku lafiya."" Halisa babu yabo babu fallasa tace""Muna lafiya gabad'ayanmu."" Daga haka sai ta wuce ta dauki dadduma da hijabinta ta tayar da sallah Ita kuwa Zainab komawa tayi ta kwanta tana jan qaramin tsaki ita dai tana" bala'in kishin Naja'atu mussaman yanda taga maigidanta gami da yaran sun damu ita. "Tace""To kuje ku zauna nayi alwala nayi sallah sai mu zauna mu sake gaisawa.""suka samu guri suka" zazzauna suna kallonta ta nufi toilet sai murmushin jin dadi suke. Mussadiq kasa hakuri yayi cike da "farin ciki ya nufi gurun Zainab yana fad'in ""Auntymu ki tashi ku gaisa ga Yaya Naja'atun ta dawo daga tafiyar da tayi.''" "Zainab idanunta a rufe tace"" Mussadiq bacci ne a idona idan na tashi a bacci zamu gaisa."" Yaron jikinsa" yayi sanyi dan baiji dad'in abunba jiki a sanyaye yaje ya zauna kusa da 'yan uwansa. Ita kuwa Halisa bayan ta idar da sallar carbi ta shiga ja tana istigifari ga Allah( Su Halisa an musulunta an koma ga Allah to Allah ya kar'bi tuban ta damu baki daya) Abbah Abbas da kyar ya samu kansa dan ana idar da sallah jama'a sukayi caaa! a kansa suna masa jajen "dangane da qaddarar data fad'a masa a kasuwa kowa sai fad'ar albarkacin bakinsa yake, to shi dai magana d'aya yake fad'a cewa komai ya sameshi daga Allah ne yana rokon Allah ya kare dukkanin musulmi da mugun ji da gani Sai kusan bakwai da kwata ya samu ke'bewa dasu Alhaji nan ya" "tabbatar musu da cewar ya dauk'o Naja'atu daga inda take kuma tana cikin koshin lafiya kamar kowa sai dai maganar cikin jikinta ya sanya duk jikinsu yayi sanyi suka shiga cikin halin jimami daga bisani suka barwa Allah ikonsa domin kuwa duk abinda Allah ya zartar a kan bayinsa shine daidai, babu wanda yasan abinda Allah yake nufi dangane da faruwar al'amarin shiyasa gabadayansu sukayi wa yarinyar adduar" sauka lafiya tare da adduar Allah ya inganta abinda zata haifa. Koda ya duba cikin motar yaga bata ciki bai damu ba saboda yasan bai kulle motar ba zata iya budewa ta shiga cikin gida. sai kawai ya nufi gidan Alhajin dan nan yake tsammanin samunta. Lokacin Naja'atu da yaran suna sama gurin hajia dan bayan tayi sallar jansu tayi domin suyi mata jagora zuwa gurin hajian masifar kunyar had'a ido take yi da ita shiyasa taja yaran domin su zame mata garkuwa. "Magana yaji 'kasa-'kasa a cikin dakin dasu Halisa suke, sai kawai ya nufi dakin dan yaji kamar muryar" "Zainab na magana. ""Nifa aunty Halisa jikina yay sanyi wallahi anya kuwa Abbansu Mussadiq ba mayar" da Naja'atun nan zaiyi ba? Kinga ni mahaifina malami ne amma ba malamin zaure ba malam ne mai fad'a akan abi sunna gami da dokokin ubangiji mu ba ma asiri da tsafi! amma tun kafin na auri mijinki muka samu labarin abinda ke faruwa ance shi wannan Baba malam din asiri yake yi ya asirce Alhaji dashi Abbansu Musaadiq din sannan kuma baya bari 'ya'yansa su wulakanta kullum cikin aiko musu da asiri yake shiyasa da waccar matar tasa ta rasu aka dauki qanwarta aka maye gurbin ta! wallahi ganin yanda "kowa yake rawar jiki akan Naja'atun nan yasa jikina ya mutu wani irin tsanarta nake ji a cikin raina.""" Halisa ta ajiye carbin hannunta tana wani irin murmushi kai da ganinsa kasan na takaici ne tace''Zainab "kenan to ni kam bansan abinda zance miki ba, tunda kin yarda da cewar Baba malam asiri yake sai kiyi takatsantsan da kanki kowa ya iya allonsa ya wanke ni yanzu duk ba wannan ne a gabana ba, maganar wai Abban Mufida zai dawo da Naja'atu gidanshi, ban sani ba, idan ma ya dawo da ita ni babu abinda ya" "dame ni ko wacce tata ta fishsheta.""" "Zainab tace""Aikuwa mu bama boka bama malam Allah kad'ai muka dogara dashi saboda haka banga" "asirin da wani boka zaiyi yayi tasiri a kaina ba.""" "Duk wannan maganganun a kunnansa, gaskiya yayi mamaki sosai! wai me yasa mutane suke hakane?" "duk wanda akaga babu ruwansa da duniya yana bin Allah sau da qafa sai a takura masa , tunda ya taso a unguwar kofar na'isa bai ta'ba jin wani yayi mummunar kalma akan Malam Sani ba, sai Halisa itace kullum ke kiransa da boka ko dan tsubbu to yau gashi an wayi gari itama Zainab tana kiranshi da wannan sunan duk kuwa da cewar ta fito daga cikin gidan da ba'a yarda da shirka da asiri ba gashi kishi yasa tana gazgatawa! duk akan ya tsaya a cikin al'amuran Naja'atu suke wannan surutan har suna zargin ko zai mayar da ita dakinta hmmmm! baya tunanin zai sake zaman aure da Naja'atu a yanzu duk wani abu da" "yake a kanta yanayi ne domin Allah da manzonsa da kuma lalurar cikin da take dauke dashi," "Gyaran muryarsa ne ya dawo dasu hankalinsu, ya shiga dakin da sallama a bakinsa, Zainab da sauri ta" "riga Halisa magana tana wani irin murmushi na iyayi da kissa tace""Habibi sannu da zuwa ina fatan ka dawo lafiya."" ? Ba tare da yayi mata cikakken kallo ba ya amsa yana kallon Halisa da tayi qasa'ke tana" kallon ikon Allah...Zainab ganin yanda ya amsa mata a banzace sai jikinta yayi sanyi tunda take dashi bai ta'ba yi mata irin hakaba. Halisa ta gaisheshi a nutse tana tambayarsa hanya ya amsa babu kyakkyawar walwala a tare dashi "yace.""Waye ya baku izinin zuwa nan gidan ku kwana.""? Sai sukayi tsuru tsuru suna kallonsa domin duk cikinsu babu wacce take da hujja."" Halisa da yake tasan halinsa idan yana fushi ba'a katse masa hanzari sai taja bakinta tayi shuru.....Ita kuwa Zeey sarki karambani tace""Habibi Hajia ce tac. Hannu ya d'aga" "mata da fad'in ""Rufe min baki sarkin magana! Hajia ce tace me? kina so kiyi mata karya ko.''? shuru tayi" "tana girgiza kanta, Yace.""Dama ai so nake na dawo na tambayeki dalilin daya sa kika fitar da hannu kika mari Yaya Ramlatu ashe dama baki da kunya da tarbiya.""? Halisa cikin zuciyarta tace "" Anzo gurun." "Zainab ta fashe da kuka tana kallonsa tace""Waye ta fada maka na mareta wallahi ni sharri akayi min" "yaushe ma zan mareta ba haba sai kace mara hankali itace fa kawai ta shigo gurina tana zagina amma ni ban mareta ba sai dai itace ma ta dokeni iya son ranta.""" "Yace.""Bakin daya fad'a min ba zaiyi min karya ba kin mare ta ko baki mareta ba.""? Zainab ta dinga rantse" ranste ita bata mareta ba sai kuka take tana neman mafita. Yana 'kokarin yin magana hajia tare dasu "Naja'atu suka shigo dakin Ganin Zainab na kuka yasa hankalinta ya tashi tace""To me yake faruwa haba" "kai kuwa daga dawowa sai ka aikata abunda bai dace ba ."" Yace.""Hajia yarinyar nan bata da kunya wallahi wai sun samu sa'bani da Yaya Ramlatu shine ta fitar da hannu ta mareta.""" "Hajia tace""Subahanallahi yaushe akayi hakan.""? Ya kalli su Saddiqa da fad'i! Saddiqa Zainab ta mari Yaya" "Ramlatu ko kuwa.""? Saddiqa da sauran yaran suka sunkuyar da kansu saboda basu iya karya ba.""" "Yace.""Yanzu kin tabbatar da ba sharri akayi miki ba ko, a gabansu kika tsinkawa uwarsu mari sabida baki" "da kunya ko me tayi miki ai sai ki bari na dawo ki fada min aa sai ki ka shirya karya da gaskiya kika kira ni a waya kika fad'a min to jiya Salim ya sheda min duk abunda ya faru a tsakaninku.""" "Zainab bakinta ya mutu murus sai hawaye dake zubo mata ta kasa magana ma ballantana ta kare kanta," "Hajia tace'' Idan ya kasance Zainab ta mari Ramlatu sai mu kira al'amarin da sunan hakkin wasu ne ya kama ta! Shin Ka tambayi dalilin zuwanta gidanka? Ramlatu ni na haifeta amma nafi kowa sanin halinta taje gidanka domin ta 'bata maka iyali da mugun halinta ni banga laifin Zainab ba sabida hausawa nacewa(Idan babba ya zubar da girmansa sai na qasa dashi ya hau kai ya taka) sabida haka idan za kayiwa yarinyar nan fada kayi mata akan wani abu daban ba'akan Ramlatu ba wacce idan ta samu damar da take so ba zata bari ma ka zauna da iyalin ka ba."" Jikinsa ne yayi sanyi kuma dajin maganganun hajian, Hakane tabbas Ramlatu ta samu damar da take so a kansa zata iya hanashi zaman aure da mugun halinta abinda yasa yake wa Zainab fada yana so ya nuna mata girma da mutuncin 'Yan uwansa kodan" gaba zata kiyaye aikata abinda ta aikata. Fita yayi daga dakin.... Hajia kuwa sai da ta tsaya ta rarrashin Zainab din kafin ta fita daga dakin. "Abbah Abbas yana zaune a kan kujera yana jiran fitowar mahaifiyar tasa su gaisa, a fakaice yake satar" "kallon Naja'atu dake zaune da yara suna magana, tayi wanka har ta sanja kayan jikinta sabuwar atampa hajia ta bata tasa a jikinta duk sai ta dawo hayyacinta, ya dinga satar kallonta ta'kasan idonsa yana mamakin uban haske da tayi a ganinsa hasken yayi yawa kuma baiyi kama dans ciki ba na rashin jini ne dan haka koda hajia ta fito suka gaisa yace yana ganin ko za'a kaita a asibiti a dubata dan yana tunanin akwai karancin jini a jikinta.....Hajia ta shiga duban Naja'atu tana nazarinta itama taga haskenta yayi yawa mussaman hannayenta da kafafunta, tace""To hakan ma nada kyau sai a bari sai zuwa gobe ko hajia Rabi sai ta kaita a dubata naga cikin nata ma yayi kwari."" Yace."" To babu laifi Allah ya kaimu goben lafiya. A nutse ya kalli Mussadiq yace.""Jeka kira Mommy da auntyku zamu tafi gida.""Yaron ya miqe da" sauri ya nufi dakinsu. Yaya Ramlatu ce ta shigo gidan tana kuka sai kace 'kan'kanuwar yarinya ta "wani fad'i gaban mahaifiyarta tana sheshsheka da fad'in ""Hajia na shiga uku na lalace! Ayuba ya cuce ni ya sake ni."" Sai ta fito da takardar sakin dake hannunta ta jefar da ita kusa da kafafunsa. Da sauri ya" dauki takardar ya warware ya soma karantawa......Da gaske Ayuba ya saki Ramlatu saki daya amma bai fadi dalili ba yace sai yazo yayi bayani. "Hajia ta shiga rud'ani sosai! to wai wace irin masifa ce ta rikito musu a cikin lokaci guda, Allah ta shiga" "kira a cikin zuciyarta tana ro'konsa ya kawo musu mafita. Abbah Abbas ya miqe a fusace! yace.""Wane" "irin sakin wulakanci ne wannan kawai babu laifin komai sai ya sake ki ai kamata yay yayi mana bayanin abinda yake faruwa."". Ramlatu za tayi magana sai ga Alhaji da Ayuban da Salim sun shigo palon kallo" "d'aya yayi musu yasha jinin jikinsa ganinsu yayi wani irin kamar wasu marasa lafiya suka nemi guri suka zazzauna, Ramlatu ta sake fashewa da kuka! Da fad'in ""Wallahi tallahi bani na tura shi ya aikata wannan" "aika aikan ba. Ya ma za'ayi na had'a baki da d'ana a cutar da d'an uwana.""............" *Littafin na kudi ne...!* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin ga yanda abin yake. p group #600 normal group #300 account....0542382124.....Binta umar gtbank..Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number... *07084653262...BINTA UMAR ABBALE* 65 Gabakid'ayansu hankalinsu ya koma kan Yaya Ramaltu dake wani irin kuka tana sake nanata maganarta ta farko na cewar ita ba itace ta tura Salim yaje ya aikata abinda ya aikata ba.... "Alhaji ya buga mata tsawa da fadin.""Rufe mana baki.mutuniyar banza mai ba'kin hali Ramlatu nayi" nadamar haihuwarki tun kina yarinya kike bani wahala na rasa a wane guri kika dauko wannan mummunan halin naki yanzu ki rasa wanda zaki cuta sai dan uwanki wanda kika sha nono kika bashi kike wa qeta shin me Abbas yayi miki a duniya wanda zai sanya ki had'a bakinki da d'anki ku sa masa wuta a "cikin dukiyarsa.""" "Abbah da hajia sukayi saurin kallon alhjin jin maganar da yake, hankali a tashe hajia tace""Wai shin me" yake faruwa ne ku fad'a min na rasa gane inda maganarku ta dosa. "Alhaji ya kalli Ayuba da fad'in ""Yana da kyau ka fad'i maganar data kawo ka a gaban kowa yaji cewar" "wad'annan mutanan ba mutanan arziki bane."" Yafada yana nuna Ramlatu da Salim dake zaune duk sun muzanta." "Ayuba yace.""Hakika na jima ban shiga tashin hankali da mamakin abinda kunnena yaji min ba a yau .Na" "dawo daga sallar asubah nazo gifta dakin Salim sai naji maganarsa da mahaifiyarsa sama sama nayi mamaki sosai dan na dauka yaron yaje sallah kamar yanda na shiga na tashe shi kafin na fita, ashe bayan fita ta mahaifiyarsa ce ta shiga dakin ta hanashi zuwa massalacin Lokacin da naji maganar da suke" "tattaunawa akai sai da na kusa fad'uwa sabida tsananin mamaki da al'jabi Salim na shedawa mahaifiyarsa cewar shine ya kunna wuta a cikin rumfar dan uwanta dake kasuwa, sai nayi shuru ina sauraran naji abinda zata ce. Kawai sa naji tana fad'in ""Ya kyauta mata hakan da yayi dama saboda dukiya Abbas ke wulakantata har da dauko mata police yazo har gida yaci mutuncinta saboda haka idan ma da akwai wata hanyar da yaron zai sake bi yaga ya kassara dan uwanta to ta bashi goyon baya yaje yayi ya kuma cigaba da nuna masa cewa shi mai kaunarsa har dai bukatarsu ta biya suga sun kai Abbas d'in k'asa! wannan al'amari ya d'aga min hankali mutuka dan ban san sanda na fad'a dakin ba, suna" ganina duk sai suka diririce alamun rashin gaskiya ya bayyana a idonsu. Cikin takaicin da tsananin bacin rai da damuwa nace musu duk naji abinda suka aikata ashe dama sune silar faruwar gobarar data cinye dukiyar Alhaji Abbas? sai dukkaninsu suka shiga rantse rantse cewa basu bane gabadaya ma ba maganar suke ba. Alhaji ku yafe min a lokacin ji nayi ina nadamar auran Ramlatu ina kuma nadamar hada zuria da ita! hakika tunda na auri wannan baiwar Allah na kasa samu nutsuwar zuciyata kasancewa ta matafiyi duk sanda zan dawo sai jama'ar unguwa makusantana sun kawo min "magana a kanta, cewar kullum a kan hanya take bata zama gida itace shiga can fita can! tun a wancan" lokacin zargi ya shiga tsakanina da ita sabida kowa akwai maganar da zai kawo min a kanta. Allah ya had'ani da mace tagari Sakina kullum itace ke hanani na aikata abinda nayi niyya akan Ramaltu Sakina mutuniyar arziki ce kuma tana kaunar zama da Ramlatu da shiriyarta shiyasa ta juri cin mutuncin da take mata. Ban ta'ba jin tsanar Ramlatu ba irin yau! jin mummunan aikin data tunzura d'anta yaje ya "aikatawa d'an uwanta wannan dalilin yasa naji kamar naje na dauko musu hukuma a tafi dasu dan gabadaya zama dasu annoba ne tunda sun zama 'yan ta'addah gwara suje su fuskanci hukunci sai kuma nayi tunanin cewar ai bani da hurumi yin hakan, wannan dalilin yasa ni na yanke shawarar rabuwa da ita dan gaskiya dama can zama hakuri kawai nake da ita, idan ina gurin sana'ata hankali kwata kwata ba a kwance yake ba saboda ina tunanin abubuwan da suke faruwa a gidana, jama'ar gari da abokaina gabadayansu babu wanda yake wa Ramlatu kallon mutuniyar kirki harda masu kiranta karuwa! wannan kalmar na daga min hankali mutuka! shiyasa na gaza samun nutsuwar zuciyata da ita gurin mu'amular aure. Ina rokon ku afuwa kan hukuncin dana yanke a kanta kamar yanda na rubuta mata saki daya" "jikin takarda hakane na sake ta saki daya idan ta samu miji tayi aurenta kai kuma Salim babu ni babu kai na yafe ka a duniya tunda ka zama butulu maci amana."" Ayuba ya kare maganar muryasa na wani irin" rawa. Gabad'aya palon shuru yayi kowa na mamaki da Tu'ajibun wannan al'amarin Hajia Kuka take tana Kallon Ramlatu tana so tayi magana amma tsabar damuwa da 'bacin rai ya hana ta iya cewa komai.........Wani sabon kukan suka ji da sauri suka kalli inda kukan ke tashi Halisa dake tsaye a bakin "kofar daki ta karaso cikin palon tana hawaye cikin tsananin damuwa gami da nadamar abinda suka aikata a baya, ta kalli Ramaltu tace""Nima babu abinda zance dake sai dai na had'aki da Allah ya saka min kin cuce ni kin cutar da d'an uwanki sannan kin cutar da baiwar Allah Halimatu wacce ba taji ba bata gani ba! wallahi tunda uwata ta haifeni ban ta'ba zuwa gurin wani boka ko malami ba wai dan yayi min duba ko yayi wa wani asiri sai da kika shigo rayuwata kika lalatani da zuwa gurin bokaye! wane gari ne baki jani kin kaini ba, har tsutsa sai da kika kaini gurin bokan da ya bani naci! a matsayinki na 'yar uwar mijina bai kamata kiyi mana hakaba kin cutar damu Allah zai saka min gashi garin biye biyen bokaye gami da shaye shayen maganin mata kinsa na had'u da lalura mai wahalar magani ni kuwa me zance miki a" "rayuwata wallahi Yaya Ramlatu kinci amanar zumunci.""!" "Yaya Ramlatu ta dinga kuka tana had'a hannuwanta guri da fad'in ""Ku gafarce ni nima ba laifina bane" "sharrin shedan ne wallahi kuyi min addua Allah ya gafarta min laifukana.""" Gabad'aya palon suka zuba mata ido jin maganganun da takeyi tana kuka. Naja'atu murya na rawa "tace""Salim idan ban manta ba ka ta'ba fad'a min wata magana a kan Abbah cewar a kwai lokacin da kake so ka rabu dashi bayan bukatarka ta biya a kansa! ashe wannan ne lokacin kana so ka cutar dashi ko?" yanzu meye ribar abinda ka aikata masa? kada fa ka manta Abbah yayi maka abinda iyayenka da suka haifeka ba suyi maka ba me yasa kake cin dunduniyarsa? kana nufin dan kasa masa wuta a kan dukiyarsa ya gama arziki kenan? lallai ashe baka da hankali kuma baka san waye Ubangiji ba! a lokacin da hassada da ganin kyashi sukayi yawa a kan mutum a lokacin shi kuma Ubangiji ke qara daukaka "darajarsa! wallahi wannan abun da ka aikata a banza domin duk zakaran da Allah ya nufa da cara sai yayi, daga karshe nake so in sake jaddada maka cewar ka samu nasarar raba tsakanina da Abbah ta hanyar zuga ni da nuna min aibunsa tare da tunzurani nayi masa rashin kunya to bukatarka ta biya amma ka sani duk abinda kayi mana mutukar muna da hakki sai Allah ya saka mana sannan kuma insha Allahu sai" "na koma dakina sai dai ka mutu da bakin ciki."" Cikin kuka mai wahala take maganar." Wannan tone tone da akeyi yayi masifar sanya shi cikin d'imuwa da tashin hankali...... *Ke duniya!!!* ina zaki damu? wai shin me mutane suka dauki duniya ne? duk yanda fa ka tafi da ita "haka zata tafi da kai! Jama'a su sakankance a duniya suyi ta shirya mugun abu kamar sun samu madawwama! me yayi wa mutane da dama da suke cin dunduniyarsa ba'a gida ba ba'a waje ba, Yanzu ashe dama da sanya hannun Salim gurin fujirewar Naja'atu gurin rashin so zama dashi, meye ribar abinda Salim yayi masa gashi nan da yake bashi da hakkin kowa tun ba'aje ko ina ba daga shi har uwar" "tasa asirinsu ya tuno shi kam me zaice da wad'annan bayin Allah.""" "Alhaji ya kalli Ayuba da fad'in ""Banji ciwo da takaicin sakin da kayiwa Ramlatu ba, shi aure anayin sa ne" "bisa amana da yarda da juna, kayi kokarin ma tsayin shekaru kana zaune da ita bayan kana zarginta! nima yanzu zargin nata nake saboda dukkanin abinda ka fad'a jama'ar gari suke a fad'a a kanta zata iya aikatawa saboda ba tsoron Allah take ba saboda haka kada ka sanya a ranka cewar ni Sama'ila zan" "qullace ka dan ka saki Ramlatu nayi maka farin cikin rabuwa da ita.""" "Ramlatu na kuka ta rarrafo gaban Alhajin tana kuka tace""Alhaji ka gafarce ni dan darajar annabi ka ro'ki" "Ayuba ya mayar dani wallahi duk abinda na aikata kuskurene da son zuciya hakika nasan nima ban kyautaba zuciyata ta tunzurani na cutar da dan uwana, sannan wallahi zargin da jama'ar gari suke min ba haka bane! ban ta'ba zina ba nasan dai kullum bana zama a gidana ina yawace yawace amma ba bin" maza nake ba *( qalubale gareku matan dake yawace yawacen banza da wofi haka kurrum ki kulle gidanki kiyi ta shige "da fice a unguwa to wallahi yanzu kiwon mutum ake ba dabbah ba, shashahar mace itake yawon bid'id'i! fakal fakal ko wane namiji na qarewa tafiyarki kallo ke idan aka samu 'yan iska ma kiji wani yay miki magana idan kince ke matar aure yace ya raina miki hankali yace ai ya dauka bazawara ce! hattara mata mu mutunta kanku sai Allah ya mutuntamu)*" Alhaji miqewa yayi ya kama hanya zai hau samansa dan zamansa a gurin yana kallon fuskar Ramlatu zai iya sanyawa jininsa ya hau dama ba lafiya gareshi ba. Ramlatu ta rarrafa gurin Dan uwan nata ta rike "masa kafafu tana kuka tace""Abbas ka gafarce ni wallahi sharrin zuciya ne ni kaina na rasa me yasa nake maka hassada duk da cewar babu abinda zan nema a gurinka ba kayi min ba, ka dauki d'ana ka ri'ke tamkar kai ka haifeshi kayi masa komai na rayuwa amma na kasa kyautata maka zuciya na ingixani akan na cutar da kai nima yanzu na gane zuciyata bata da kyau! kayi hakuri ka gafarce ni ka yafe min ka" "yafewa Salim abunda mukayi maka.""" Abbah ya ciro hankici a aljihunsa ya goge zufar goshinsa hularsa ya dauka yasa cikin wani irin yanayi na "damuwa da alhini yace.""Na yafe miki sai ki cigaba da neman gafara gurin Allah ina rokon Ubangiji yasa wannan tuban da kikayi na gaskiya ne."" yana gama maganarsa ya miqe! Salim cikin borin kunya gami da nadama Yace.""Kawu ka duba darajar Annabi Muhammad ka gafarce ni wallahi shedan ne! ya tunzurani cutar da kai yanzu na gane qarya da yawancin wasu abubuwa na mugunta basa lasting Idan mutum naso ya zauna lafiya a wannan duniyar to ya kad'aita Allah shi kad'ai kuma ya ri'ke gaskiya d'aya mutukar yayi" "haka to zai zauna lafiya kuma koda mutum ya nufe shi da mugun abu to Allah zai kareshi.""" Abbah Abbas ya jima a tsaye yana kallon Salim din dake hawaye kansa a kasa kunya ta hanashi ya dago "kai ya kalleshi, yace.""Salim kaima na yafe maka Allah ya yafe mana baki daya."" Ya kalli Hajia cikin wata iriyar murya da bata fita sosai yace ''Zamu tafi."" Hajia ta goge hawayen idonta cikin tausayi da jin kai irin na uwa da d'anta tace"" Ina rokon Ubangiji Allah ya ji'banci al'amuranka Abbas Allah ya kare ka ga miyagun mutane da aljanu, duk wanda ke nufinka da sharri Allah ya maida masa kansa, Allah ya daukaka darajarka daukaka mai amfani Ubangiji Allah ya shi maka albarka Abbas hakika ina alfaharin haihuwarka Allah ya albarkaci zuriarka."" Wannan adduar da mahaifiyarsa tayi masa itace ta wanke masa zuciyarsa tayi wasai gabadaya ma yaji ya daina jin takaicin abinda akayi masa. sai ya kasa 'boye farin" cikinsa ya dinga amsa adduar mahaifiyarta sa yana jin wani irin dadi yana ratsa shi. "To bayan tafiyar Abbah Abbas da iyalinsa Hajia ta kalli Yaya Ramlatu cikin bakin ciki da takaici tace""" "Ramlatu bana tunanin zan zauna dake a gidan nan sabida haka tun wuri ki nemi inda zaki je ki zauna, Idan ya kama dole sai kin zauna to ni ina iya bar miki gidan dan ni wallahi sharrin ki tsoro yake bani.""" "Ramlata cikin sarewa da al'amarin ta nufi mahaifiyar tata murya na rawa tace""Hajia dan darajar Allah" "kada kije ko ina a kaina kiyi zamanki a dakinki wallahi na tuba nabi Allah na gane abinda nayi ban kyauta ba insha Allah ba zan sake ba ki yafe min Naja'atu kema ki yafe min abubuwan da nayi miki."" Naja'atu ta goge hawayen idonta ta kalli hajia murya na rawa tace""Hajia dan Allah ki yafe mata tunda ta gane kuskuranta kin san adan adam ajizi ne kowa yana kuskure a duniya kinga shima wanda akayi wa laifi" "kafin ya tafi sai da ya yafe mata tukkuna."" Hajia tace""Humm! Naja'atu kenan har yanzu ke yarinya ce" kina ganin kamar abinda take fada har zuciyarta ne nafi kowa sanin halin Ramlatu da rantsuwa kan "karya.""" "Hajia Rabi dake kokarin shigowa dakin tace""Ke kuwa Hajia ki daina wannan maganar mana, kiyi addua" "kan Allah yasa tuban Ramlatu na gaskiya ne ni a jikina ina jin cewar karshen matsalarta ne yazo akwai mutane da dama da suke aikata mummunan abu wanda yafi nata su tuba su nemi gafarar Allah ya gafarta musu, kema don Allah ki yafe mata tunda shi Abbas din ya nuna komai ya wuce kuma dan Allah ki daina fad'in zaki fita ki bar mata gida wannan maganar bata dace ba."" Hajia tace""To shikkenan tunda kunce haka na hakura na barku da ita gatanan ta zauna idan halinta ne zaku gani ni tuntuni na dawo da" "rakiyar Ramltu shiyasa nake so tayi nesa dani da zuria ta.""" "Ramlatu tace""Hajia ashe har kin cire ni daga cikin zuriarki me yayi zafi hajia ki duba halin da nake ciki" "nice fa babbar 'yarki."" Hajia taja tsaki gami da miqewa da fad'in ""Kece babba kuma kece fitinanniya wacce bata kaunar zaman lafiya Allah dai ya shiryeki."" Tana kare maganarta ta mike tare da kallon kishiyarta tace""Hajia gobe idan Allah ya kaimu da safe zakuje asibiti da Naja'atu a dubata."" Hajia Rabi tace""To Allah y kaimu goben lafiya."" Hajia sama ta nufa ba tare da ta saurari magiyar da Ramlatu take mata ba. Hajia Rabi ta kalleta a nutse tace""Hakuri zakiyi Ramaltu ki cigaba da rarrashinta har ta sakko" amma hakikanin gaskiya ke da d'anki kun aikata mummunan aiki sai dai kawai ace Allah ya kyauta ya "kuma kiyaye gaba.""" Ramlatu tasa gefan zaninta ta share hawayen idonta jingina tayi jikin kujera tare da tsirawa kasan kafet ido tana tunanin yanda rayuwa ta juya mata baya. Naja'atu kuwa miqewa tayi ta shiga daki ta kwanta "tana zubar da hawayen bakin ciki, tana kallon Abbah Abbas ya tattara iyalinsa suka tafi banda ita wannan al'amarin yayi masifar tsaya mata a rai! sai ta shiga tunanin ita yanzu mecece makomarta." To washe garin ranar da wuri Naja'atu da hajia Rabi suka shirya direba ya daukesu suka nufi asibiti da yake pravite ne basu sha wahalar ganin likita ba. Dr ya tabbatarwa Da hajia Rabi cewar Naja'atu ita "da babyn dake jikinta lafiyarsu lau, hasken da fatar tayi ba matsala bane mafi akasari masu karamin ciki nayin irinsa, har scanning sai da yayi mata ya nuna musu tare da tabbatar musu da lafiyar babyn magunguna masu kyau ya rubuta a takarda sannan yace suna fita zasu ga gurin saida magani sai su siya. Hajia Rabi taji dadin bayanin da Dr yayi kan lafiyar Naja'atu da cikin jikinta, dan haka kafin su" nufi gida sai da suka tsaya a Pharmacy (gurun siyar da magani) suka siya kana suka shiga mota direba yaja suka nufi gida. Koda suka isa gida hajia rabi bata bari direba ya shiga da motar cikin gidan ba ta umarce shi daya "saukesu. Suna fitowa ta kalli Naja'atu a nutse tace""Zamu shiga gidan Baba malam ku gaisa ko.""?" "Naja'atu tayi kwal kwal tana shirin yin kuka tace""Hajia ina jin tsoron haduwata da Baba Talatu."" Hajia Rabi tayi murmushi tare da girgiza kanta tace""Ki saki jikinki kada ki damu bazan bari tayi miki fad'a ba!" Baba Talatu macace mai ilimi tasan qaddara daidai gwargwado saboda haka ki kwantar da hankalinki "nayi niyyar kaiki gurinta ku gaisa ba da wata munufa ba."" Naja'atu ta sauke ajiyar zuciya a hankali tace""Nagode hajia."" Hajia rabi tace""Babu komai ai."" Hannunta ta riqe kai tsaye suka nufi gidan baba" malam d'in......... *Wayyo hannuna Ayi hakuri da typing error babu editing Nagode * *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake. Vip group #600 normal group #300 account... 0542382124 Binta umar gtbank idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number.... *07084653262 BINTA UMAR ABBALE* 66****Baba Talatu na zaune a kan tabarma da karamar redio a kusa da ita tana sauraran shirin barka da "hantsi wanda tashar redio freedom ke gabatarwa a daidai irin wannan lokacin Baba Talatu ma'abociyar jin redio ce shiyasa kullum kanta yake a waye ta iya mu'amula da mutane bayan hakan kuma tana zuwa isilamiyya irin ta matan aure duk ranakun asabar da lahadi( sauraran redio nada mutukar tasiri a rayuwar d'an adam akwai muhimman shirye shiryen addini da wasu tashoshin gidajen redion ke gabatarwa wanda idan mutum na saurara zai qaru da wasu abubuwan masu amfani, redio tamkar" makarantar ce ta wanni fanni domin suna ilimantarwa ) Tunda suka shiga gidan Naja'atu take ra'be ra'be ta kasa sakin jikinta sai 'buya take a bayan hajia Rabi tana jin tsoron had'a idonta da mahaifiyartata. Baba Talatu ta gyara zamanta fuskarta da fara'a "takewa Hajia Rabi sannu da zuwa, redion kusa da ita ta dauke daga gurin ta sanja mata guri tana fad'in'' Hajia bisimillah zauna ga guri nan.""" Hajia Rabi ta zauna a nutse Naja'atu ta zauna kusa da ita sai sunkuyar da kanta takeyi Bayan sun "gaisa da juna Hajia Rabi ta kalli Baba talatu tace''Naja'atu na kawo miki ku gaisa da juna."" Baba Talatu" "tace'' Au ita bata da kafafu har sai anyi mata jagora.""? Hajia Rabi tace"" Haba ba dai haka bane wallahi" munje na kaita asibiti ne nace lallai sai na kawo ta ku gaisa da juna. Baba Talatu ta ta'be bakinta taja bakinta tayi shuru har yanzu tana jin ciwo da takaicin abinda naja'atu "tayi musu. Naja'atu ta dago kanta a hankali ta kalli gurin da mahaifiyar tata take a sanyaye tace""Baba" "ina kwana kunanan lafiya.""? Ba tare data kalleta ba ta amsa da ""lafiyarmu lau."" A sanyaye ta mayar da kanta qasa jikinta duk ya mutu da yanayin kallon da mahaifiyar tata ke mata. Hajia Rabi tace""Baba don" Allah ki yafewa yarinyar nan magana ta wuce nasan ke mai ilimin addini ce kin san qaddara daidai gwargwado dan haka ki sassautawa naja'atu taji da abu guda. "A sanyaye tace""Ai bani tayi wa laifi ba da kike wannan maganar ita tasan wanda tayi wa laifi shi zata" "nemi afuwarsa bani ba.""" "Hajia Rabi tace""Wallahi tuntuni Alhaji Abbas ya yafe mata da bai yafe mata ba ai ba zai tsaya a kan" al'amuranta ba nasan kina sane da cewar shine yaje har can garin da take ya daukota ko.'' "A sanyaye tace""Duk inada labarin komai wallahi ni kam na rasa wace zuciya ce da mutumin nan hajia" "Rabi ki duba kiga irin rashin arzikin da yarinyar nan tayi masa amma bai duba ba ba tare da yayi shawara da kowa ba yaje ya daukota daga wahala ai naso ya barta a can ta gane duniya ba rigar sanyawa bace.""" "Hajia Rabi tace""Haba Baba ya kike wannan maganar babu dadin ji idan rai ya 'baci hankali ake sawa ya" "nemo shi, kuma a duniyar nan babu wanda baya kuskure saboda haka dan Allah ki daina wannan maganar Baba kiyi hakuri da duk wasu abubuwa da suka faru a baya tunda shima wanda akayiwa laifin maganar ta wuce a gurinsa sai mu taru gabadayanmu muyi wa yarinyar nan adduar rabuwa da cikin" jikinta lafiya shine babban abinda ke gabanmu "Baba Talatu ta share guntun hawayen idonta tace""Wallahi tuntuni magana ta wuce a gurina kuma na" "yafe mata har abadah sai dai duk sanda na tuna al'amarin nakan ji rashin dad'i a zuciyata nida malam munso yarinyar nan ta zauna zaman aure da Alhaji Abbas amma ta watsa mana qasa a ido duk sanda na tuno wannan al'amarin nakan shiga 'bacin rai mai tsanani.""" "Hajia rabi tace""Gaskiya da akwai rashin dadi a cikin al'amarin amma bakya tunanin rabo ne ya fitar da ita" "daga gidan Alhaji Abbas din, dukkaninmu fa bamu san gaibu ba sai Allah wannan cikin dake jikinta ya ishemu ishara gabad'ayan mu.""" "Baba Talatu tace""Eh nima bayyanar cikin jikinta yasa na jingina al'amarin a matsayin abinda kika fad'a" "yanzu babu shakka idan rabo ya rantse to babu mahalukin da ya isa ya dakatar dashi, san nan kuma wani baya ta'ba haihuwar d'an wani koda da akwai sauran zama a tsakanin Alhaji Abbas da yarinyar nan" "to tilas sai taje ta auri wani ta haihu sannan ta dawo hannunsa.""" "Hajia Rabi tace""Yawwa nima abinda nake taso ki fahimta kenan watakila akwai ragowar zaman aure a" "tsakaninsu shiyasa Ubangiji ya yanke alaqar auranta da Bashir bayan ya saukar da ikonsa na samuwar cikin jikinta.""" "Baba Talatu tace""To Allah yasa dan wallahi nafi mata sha'awa ta koma dakinta akan ta sake wani" "auran."" murmushi hajia Rabi tayi a zuciyarta tace akwai yiwuwar hakan dan ganin irin kulawar da Abbas keyi wa yarinyar alamu sun nuna har yanzu yana muradinta." Mi'kewa tayi da niyyar tafiya ta kalli Naja'atu da kanta ke sunkuye tace''Zaki zauna ku sake gaisawa ko? "bayan sallahr azuhur rana tayi sanyi sai ki shigo gida.'' "" A hankali ta d'aga kanta tare da fad'in ""To shikkenan."" Hajia tace""Ga magangunanki nan idan kinci abinci sai kisha insha Allah idan na shiga gida" "zanyiwa hajia bayanin abinda dr ya fada sai ta kwantar da hankalinta.""" Murmushi ta d'anyi tana sake sunkuyar da kanta da tunanin yanda hajia ta damu da ita da cikin dake "jikinta ita kam babu abinda za tace da Iyalan gidan Alhaji sama'ila sun nuna mata zahirin kauna gami da kulawa a cikinsu babu wanda ya kyamaceta duk kuwa da cewar ita din mai laifi ce a gurinsu, amma sun" kauda kansu suna tattalinta gami da bata dukkanin kulawar data dace. Bayan fitar hajia Rabi da minti biyar ta dago kanta tana satar kallon mahaifiyar tata wada take ta kokarin "sanja tasha daga freedom ta mayar redio kanoAm a hankali ta matsa kusa da ita ta riqe hannayenta murya na rawa tace""Baba dan Allah ki yafe min wallahi nayi nadamar abinda nayi muku kuma ni kaina nasan nayi kuskure mai muni nabi son zuciyata na jefa kaina a wahala, sai dai kuma a duk sanda naji kuna maganar kan cewa qaddarata ce hakan sai naji sanyi a cikin raina, yanzu babban burina shine na haihu lafiya na koma dakin mijina dana bujirewa auransa hakika yanzu na gane alkairi kuke nufi dashi ba sharri ba, nagane kuma babu wani d'a namiji da zan aura yaso ni kamar yanda Abbah Abbas ke sona" "Baba ku taya ni addua akan Allah ya mayar da aurana dashi.""" "Baba Talatu ta ri'ke hannunta tace""Alhamdullhi dama ina adduar Akan Allah ya nuna min zuwan wannan" "rana da zaki gane muhimancin abinda mukayi miki *MADADI BA HARAM! BANE* kamar yanda kika dauka a baya kina ganin mun cutar dake saboda munce ki maye gurbin 'yar uwarki Halimatu Naja'atu mune muka haifeki ba zamu ta'ba cutar dake ba, cancanta da nagarta muka hango shiyasa muke miki shawarar auran wannan bawan Allahn, a yanzu dai zamu iya cewa rabon wannan cikin na jikin ki yasa abubuwa da yawa suka kasance, babu abunda zamu ce sai dai muce Allah ya sauke ki lafiya bayan nan kuma mu roki Allah ya daidaita auranku dake da Alhaji Abbas domin shine babban burin mu dani da" "mahaifin ki.""" "To har bayan la'asar Naja'atu na tare da baba talatu suna labari kamar babu abinda ya faru, sosai" "Naja'atu ta sake a gidan ta daina d'ari-d'ari dan abinci ma tare suka ci abin gwanin ban sha'awa, koda baba malam ya dawo ya tarar dasu suna hira sai yaji dadi sosai ya zauna kan abun zaman sa ana hirar dashi a fakaice yana yi mata nasiha kan zamantakewar rayuwa da yanda zata kula da kanta da duniyar baki daya....Sosai Nasihar malam take ratsa jikinta kafin ta bar gidan jikinta yayi sanyi sosai! ta dinga neman afuwarsa dangane da abubuwan da suka faru, lokacin baba malam ya nuna mata cewar shi dama duk abubuwan dake faruwa da rayuwarta bai qullace ta ba ya dauki al'amarin a matsayin qaddara wacce" ko wane d'an adam yake tafiya da ita. Daf da magariba ta fito daga gidan malam hannunta ri'ke da ledar magungunta kai tsaye gidan Alhaji ta nufa tana tafiya tana kallon kasa dan bata so ta dago kanta ta kalli fuskar wanda ta sani a unguwar gani take kamar ta zama abun kallo a gurin jama'a shiyasa ta sunkuyar da kanta. Sai data isa daf da gate "din gidan sannan ta dago kanta aikuwa suka had'a ido dashi yana kokarin fitowa daga mota, d'an tsayawa tayi a bakin gate din tana murmushi har ya karaso inda take ta d'an risina tana gaishe shi ya amsa a nutse tare da tambayarta daga inda take dan bai ga sanda ta fito daga gidan baba malam din ba. bayani tayi masa cewar tun bayan dawowarsu daga asibiti take gidan sai yanzu ta fito. Yace.""Ta" shiga gida idan ya fito daga massalaci zai shigo yaga magungunan nata. Cike da kuzari ta shiga gidan tana jin wani farin ciki na ratsa mata zuciya yanda ya amsa mata gaisuwarta "da sakin fuska shine yafi komai faranta mata rai! jikinta na bata har yanzu da sauran sonta a cikin zuciyarta watakila shima yana jira ne ta haihu ya mayar da ita gidansa, wannan tunanin ya sanya zuciyarta tayi haske." "Lokacin data shiga gidan hajia bata falo ta hau sama domin ta gabatar da sallah, sai kawai ta nufi dakin" "dakinta da take kwana, ta ajiye ledar maganin kan drowar ta cire hijabin dake jikinta ta shiga toilet domin ta dauro alwala..........Tana fitowa ta shimfida dadduma ta saka hijabinta ta kalli gabas. Bayan ta idar da sallar tana zaune kan dadduma tana jan istigifari a cikin ranta sai zuciyarta ta" shiga kwad'aita mata abubuwan ciye ciyen wanda ta saba ci lokacin da take jos gidan Mmn Sajida. Duk daran duniya sai taci kaza mai ku'li-ku'li dasu albasa da sauran kayan had'i! ta kan rasa a ina Mmn Sajida take sanyawa ana siyo mata wannan kazar mai dad'in tsiya. Yawun bakinta ne ya tsinke hankalinta yayi masifar tashi idan fa ba ta samu damar cin wannan gashashshiyar kaza mai quli quli ba akwai matsala! miqewa tayi tana jin jiri jiri ta nufi falo tana had'a hanya kamar wacce bata ganin gabanta. "Kujera ta samu ta zauna hawaye na kokarin kufce mata, idan ta tuno da gashshiyar kazar jos mai dad'i ji" "take kamar tayi tsuntsuwa taje taci Hajia ta sauko ta sameta a takure a guri guda..Tace""Naja'atu kin" "dawo kenan? nace ai yau kinyi yinin gidan malam ai naji dadin hakan sosai sannan Hajia Rabi ta sheda min bayanin da likita yayi a kanki gaskiya nayi farin ciki jin cewar lafiyarki lau dake da yaron dake cikinki.""" "Murmushi kawai ta iya yi tayi shuru tana kallon guri guda! Hajia tace""A'a yana ganki wani iri ko bakya jin" "dadi ne.""? Girgiza kanta tayi tana yar dariya tace''Aa wallahi lafiyata lau."" Hajia ta bita da kallo tana kokarin ta fahimci wani a tare da ita!" Yaya Ramlatu ce ta shigo ta samu guri ta zauna a kan kujera Yaya Ramlatu dai kunya tasa ta kasa zama a "gurin hajia sai ta gudu gurin Hajia Rabi can ta kai kayanta da Salim ya kawo mata sai dai ta shigo su gaisa. Hajia tace""Gaskiya ban yarda ba akwai abunda ke damunki kada ki 'boye min damuwarki" naja'atu ni uwarki ce ki sheda min damuwarki. """Murya na rawa tace"" Wallahi bani da damuwar komai hajia."" Taqi fad'in maganar ne domin kada suga" zaqewarta bata so ta dinga nuna musu kamar sun gaza dayi mata wani abun shiyasa takasa fad'a mata abinda take so "Abbah ya shigo ya tarar hajia na maganar, sai da suka gaisa tukkuna ya shiga tambayar abinda ke" "faruwa. Hajia tace""Gata nan dai tunda ta shigo na ganta cikin wani irin yanayi jikina na bani kamar" "akwai abinda ke damunta.""" Naja'atu ganin Abbah Abbas din ya sake karya mata zuciya sai kawai hawayen da take 'boyewa suka "shiga zubowa."" Tasa gefan hijabinta tana kare fuskarta...su hajia basu gani ba amma shi ya fahimci kuka take, gyaran murya yayi as'usul kafin yace.""Naja'atu kina da damuwa me yasa ba zaki fad'a ba shuru ba zai amfana miki da komai ba idan baki fad'i lalurar ki ba zaki cutar da kan ki duba da cewar ke d'in ba" "lafiya kika cika ba, idan wani abu ke damunki kiyi bayani insha Allah za'a san yanda za'ayi."" Falon yayi" shuru suna jiran suji ta bakinta. Ita kuwa kukanta ne ya tsananta dan da alama shagwa'bar data kwana biyu bata ta'ba ba yau ita za tayi. Al'amarin ya bashi mamaki ya kuma bawa su hajia mamaki sai kuka takeyi taqi magana. Yaya Ramlatu "cikin kokarin sake wanke kanta tace""Haba 'yar nan daga tambaya sai kuka dan Allah kiyi shuru ki daina kuka kada ki tayar mana da hankali wai shin meke damunki ne me kike so.""?" "Cikin shashshekar kuka tace""Yaya Ramlatu kaza mai yaji da quli-quli nake so naci.""" "Gabad'ayansu suka saki baki suna kallonta, danshi Abbah kasa 'boye mamakinsa yayi yana 'yar dariya" "yace.""Sabida kawai zaki ci kaza mai yaji da quli - quli sai ki dinga yiwa mutane kuka saboda shagwa'ba."" Hajia tace""nima dai abun ya bani mamaki wallahi haba Naja'atu meye abin kuka da damuwa da kin fad'a ai da tuni an siyo miki a bakin titi haba banji dadin wannan abuba wallahi bari na kira Dan azimi yaje" "*Murtala soya* ya siyo miki."" Kokarin miqewa take ya dakatar da ita da fad'in ""Zauna hajia bari na siyo mata da kaina."" Hajia ta koma ta zauna da fadin ""Yawwa dan Allah kayi sauri oh! ikon Allah ashe matsalar kenan."" Ya Ramlatu na murmushi tace""Ai hajia kin san dama wani cikin haka yake da azalzala" "idan yaso abu idan bai samu abunda yake so ba sai ya saka uwarsa a wani hali! na tashin hankali.""" "Hajia tace""To ba ita kadai ba muma gashinan ya samu wani halin ikon Allah kenan Allah to Ubangiji Allah" dai ya rabasu lafiya. Ya Ramlatu ta amsa da ameen tana jin dadin yanda mahaifiyar tata ta sake tana amsa mata maganarta. Abbah yana fita motarsa ya shiga kai tsaye ya nufi inda yasan zai samo mata irin kazar da take buqata! * Ikon Allah a gaskiyar magana wannan soyayyar za tayi wahalar samu* Ayi hakuri yau banyi posting a kan kari ba *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake. Vip group #600 normal gruop#300...account... 0542382124...Binta umar gtbank. Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 67****To tundaga wannan rana Abbah Abbas ya d'orawa kansa nauyin siyo kaza mai yaji da qul-quli "bama kazar kawai yake siyo mata ba harda sauran kayan kwad'ayi yake kawo mata, kafin kice kwabo Naja'atu ta sanja dik wannan ramar babu tayi qiba sosai saboda tana samun kulawa ta kowane bangare! Iyayenta kuwa rasa bakin magana sukayi danganin irin karamci da kulawar da 'yarsu take samu a gidan Alhaji Samaila ya sanya kullum basa gajiya dayi musu addua gami da fatan gamawa da duniya lafiya hakika Alhaji Sama'ila dashi da iyalinsa sun nuna musu kara gami da kauna sun dauki naja'atu sun ri'keta" tamkar sune suka haifata basu da abinda zasu yi musu face adduar dacewa da samun rahamar ubangiji. *Bayan sati biyu* Al'amuran sunyi wa Abbah Abbas sauqi katuwar rumfarsa wacce wuta ta cinye ta dawo sabuwar dal "kamar ma wani abu bai faru ba, a yanzu kayan da suke cikin rumfar sunfi nada yawa rumfar cike take da irin kayayyakin da jama'a ke bukata, kada ku dauka ko yaci bashi a gurin abokan sana'arsa ko daya Allah babu yanda baya zartar da ikonsa Abbah Abbas dalilin wannan abu da ya same shi ya janyo masa samun alkairi sosai daga gurin abokanan sana'arsa ta kwangila ita kanta gwamnatin garin sai da ta bashi tallafi dan ganin irin hidimar da yake mata hausawa dama suka ce wani hanin ga Allah baiwa ne, Abbah ya samu matasa wanda suka rasa aikin yi ya samar musu gurbi a cikin rumfunan sa dake kasuwar, Yanzu Abdulhamid shine a matsayin babban yaronsa ya yarda da yaron sosai ya amince da gaskiya da amanarsa shiyasa yaja shi a jikinsa yana nuna masa yanda harkokin kasuwanci suke saboda gaba baya so duk wanda yake karkashinsa ya dawwama a gurin yi masa bauta ya fiso kowa ya tsaya da" kafafunsa shiyasa ko kad'an baya yiwa yaransa mugunta ta kowane fanni suna jin dadin zama dashi *( Haka ake so shugaba ya zama adali mai kaunar cigaban na qasa dashi mafi akasarin abinda yake damun wasu 'yan kasuwar kenan kiga mutum kullum kansa ya sanyi daga zarar yaga wanda yake qasa dashi zai tashi sai ya mayar dashi ya dankwafe! kullum dai yafi so yayi ta zama a karkashinsa yana masa wahala.....Wannan ba adalci bane idan kana so kayi qarko jama'a su dinga fad'in alkairin ka to kada ka saka ganin kyashi da ganin ido a cikin al'amuranka idan ka samu abunda ka samu sai ka sakarwa na qasa da kai shima ya samu Allah ka karemu da ganin kyashi da hassada)* *BASH!* To Bash ya samu nasarar k'etara kasar Najeria inda kai tsaye ya sauka a 'kasar ghana tare da maqudan kudaden da suka sato a bank. Akwai abokansa a garin saboda haka yana sauka a airport ya kira daya "daga cikinsu, ko minti talatin baiyi ba a gurin wata zungureriyar bakar mota tazo ta daukeshi, koda ya shiga motar sai yaga duk guyz ne irinsa shi kadai ne musulmi ma a cikinsu dukkaninsu kafurai ne yawancin su ma had'uwa kawai sukayi da juna kowanne da kasar da ya fito." A daran sukaje gurin canjin kudi zunzurutun kudad'en da bash yaje musu dashi su sanja aka basu irin na 'kasar. Duniya sabuwa suka bud'e dama akwai 'yan garin guda biyu wanda suke da daurin gindi "kasancewar iyayansu 'kososhi ne a cikin gidan gomanati. shiyasa duk ta'addacin da suke babu wanda ke musu magana, suyi shaye shaye su kama yaran mutane suyi musu fyad'e komai kankantar yarinyar mutukar tsautsayi ya ritsa da ita to basa saurara mata, dan akwai lokacin da suka shiga wata bording skull a garin, suka haikewa yaran mutane sai da sukayi raping din sama da mata talatin suka fito suka barsu cikin jini da wahala, abun mamaki gwamnati ba ta wani dauki mataki mai tsauri a kansu ba. Bash yayi masifar jin dadin had'uwa da guyz d'in nan suka bud'e shafin iskanci irin wanda suke so," sace sace shaye shaye fyad'e Luwad'i da duk wani mummunar aikin da Allah ya haramta yi sukeyi Bash tuni ya kafurta kansa ya zama kafuri tunda yaje garin bai kalli gabas da sunan zai gaishe da Ubangiji ba sharholiyarsa kawai yake babu abunda ya dameshi. Munira kuwa tayi ciki da Muktar ya koreta daga gidansa yace tun wuri taje ta nemi uban danta kuma ya "fasa auranta domin abinda yake bukata a gurinta ya samu saboda haka idan ta sake zuwar masa gida sai ya karya mata kafafu! Munira ganin bata da gata yasa ta hakura ta kyaleshi ammafa taci kuka ta koshi kuma tayi nadamar wautar data tafka, yanzu tana gidan kanwar mamanta mai suna Hajia Zulai bakar wahala take bata a cewar matar lokacin da ludayin su yake kan dawo basu taimaka mata da komai ba dan haka bata ga wanda zai dauko wahala ya dora mata ba, Munira hakuri kawai take a gidan Hajia Zulai ita taci mutuncinta 'Ya'yanta su wulakantata watarana da yunwa take kwana ga ciki a jikinta Munira ta" gane duniya abar tsoro ce dan idan ta juya maka baya sai ka zama tamkar kashi a idanun mutane. Alhaji Aminu da matarsa kuwa suna can a kulle dan har yanzu ba'a yanke hukunci ba an dai rufesu a "kebantaccen guri, gwamnati tasa a cigaba da bukince inda Bash din ya fake dan tuntuni an yankewa sauran abokan nasa hukunci kisa bayan sun gama zaman gidan kaso na shekara goma......Tsanani tashin hankali Alhaji Aminu da Mommy suka shiga suka dinga kuka suna dana sanin abinda suka aikata na dora" "d'ansu a turba mara kyau, duk bayan sati biyu sai 'yan jarida abokanan aikinsa sunzo sun titsiye shi da" "tambayoyi kamar ma da gayya suke zuwa su turkeshi, takaicin hakan yasa ciwon hawan jini ya kamashi," yau da lafiya gobe babu. **** To zamantakewar gidan Abbah Abbas sai dai muce alhamdullahi dan a tsakanin Halisa da Zainab an "samu fahimtar juna duk ta dalilin jajurcewar jagoran nasu wato shi wanda ya ajiyesu a gidan, tuntuni Zainab ta daina rawar kai wanda ada take ta daidaita nutsuwarta yanzu ta kanta ma takeyi cikinta yayi wata hud'u! jikinta ya soma amsawa hankali ya fara shiga jikinta! gabad'aya sai tayi rauni ta kasa daukar lalurar mijin nata kamar wacce ta kusa haihuwa haka ta koma ciki wata hud'u, amma har ya fito kasancewar ta mai jiki da tumbi shiyasa cikin yayi saurin nuna kansa. Abbah nada tausayi sosai shiyasa" baya takura mata da fitina lalla'bata yake da dukkanin abinda take so burinsa kawai ta sauka lafiya. 'Bangaran Halisa ta samu lafiya sosai dan a jikinta ma tana jin hakan ta daina jin kyaikyayi ta kuma daina "zubar da ruwan da takeyi, sai ta fad'a masa cewar yana da kyau ta sake komawa asibiti su dubata domin su tabbatar mata da ingantuwar lafiyarta, da yake shima a cikin matsala yake sai ya dauketa da kansa ya kaita asibitin, Aikuwa kyakykyawan result ya fito Halisa kwayoyin cutar Gloria da take dauke dasu sun mutu yanzu mu'amula ta aure zata iya cigaba da gudana a tsakaninsu, amma dai duk da haka sai da Dr" Sa'adatu ta rubuta musu wani magani wanda 'ka'ida ita dashi ne zasuyi amfani dashi. Abbah Abbas yaji dad'in samun wannan kyakkyawan result d'in dan har sai da ya kasa 'boyewa ya nuna "a fuskarsa kyautar kudi masu kauri yayi Dr din suka kama hanya suka tafi, Dr Sa'adatu ta dinga murmushi" tana jin wani iri a jikinta hakika mutumin na burgeta mutuka tana adduar Allah ya bata miji mai irin halinsa. Tun daga ranar Abbah da Halisa suka d'inke Halisa aka dawo amarya aka dinga gwangwajewa da ango "ana biyan bukatar juna, sai dai bangaran mutumin naku daurewa kawai yake amma ba wani daidai yake ji ba dan ya tsani yaji ya shiga gurin yaji shi sakwaf-sakwaf! Halisa ta riga ta gama bud'ewa magungunan gurin 'yar Sa'adu sunyi mata mummunar illah! Haka dai yake hakuri yana biya wa kanshi bukata ba tare da ya nuna mata wani abuba, sai duk sanda takaici ya ishe shi kasa hakura yake a cikin kwananta zuwa yake gurin Zainab ya baje kolinsa yanda ranshi yake so sai bayan ya samu nutsuwa zai dawo yana da ya sani dan Zainab kwana takeyi tana kuka da fad'in cikinta ciwo yake hankalinsa ya tashi da kyar yake" rarrashinta. Salim abin duniya ya isheshi ya rasa makama kullum yana gida a kwance yana tunani gabadaya yanzu "kunyar fitowa yake saboda irin kallon da Jama'ar gari ke masa! Ya kai sati biyu a gida baya fitowa sai da daddare nan ma baya dadewa zai dawo gida ya kwanta, mahaifinsa kuwa har ya koma bakin sana'arsa baya amsa gaisuwarsa fushi yake dashi sosai da sosai Ranar Lahadi ya shirya tsaf domin zuwa" "gidansu Salimat budurwasa wacce aka kai kudin aure da sa rana, ya fito da key din motarsa simi simi ya" fita daga gidan kai tsaye motarsa ya shiga ya nufi gidansu Salimat.......... "Salimat ta sameshi a cikin mota a zaune ta bude ta shiga ta zauna ta kalleshi tana ta'be bakinta tace""Wai" "dan Allah kwana biyu me yake damunka ne naga duk kabi ka susuce ka ma daina zuwa gurina kullum kuma idan na kira wayarka sai naji ka a cikin hali na damuwa wai ko ka daina sona ne.""? Salim ya girgiza kansa yana kallonta yace""Ba haka bane salimat kwana biyu bana jin dadi wallahi shiyasa kika kasa gane" "kaina amma yanxu naji sauki sosai inaso ki fad'a min meye damuwarki.""" "Ta'be bakinta tayi tace""Kasan bani da wata damuwa sai ta kud'i yanzu ma inaso ka sanja min waya" "sannan na kwana biyu banyi ciye ciye ba inaso muje ka siya min kayan kwalliya da sauran abunda nake bukata.""" "Yace.""Okey shikkenan kada ki damu."" Motar ya kunna kai tsaye suka fita daga cikin unguwar. Kafin su" "tafi shopping din sai da suka tsaya a P.O.S tana kallo Salim ya bada atm dinsa da accont number nasa, suka bashi abun yasa nambobin sirrin sa duk akan idonta kudin da yake bukata suka miqa masa ya kar'bi" atm dinsa suka fita daga gurin.... Lokacin da suka shiga motar ya manta bai mayar da atm din cikin wallet dinsa ba ya fad'i kasan site a kan "idonta sunayi parking a daidai gate din Jujin lambo ya bude motar ya fita ita kuma tana ganin fitarsa tayi saurin sunkuya ta lalubi atm din tasa a cikin pose din dake hannunta ta bude motar tabi bayansa cikin gurun Siyayya yayi mata sosai da sosai suka fito da kaya a hannunsu, kafin ya kaita gida sai da ya siya" "mata kayan ciye ciye irin wanda take so sannan ya kaita gida, to yaso su danyi abun da suka saba kafin" "su rabu taki bashi damar hakan tace ita ta gaji gobe ya dawo da wuri zata bashi mamaki! yace shikkenan, sallama sukayi da juna yaja motar yayi gaba. A ranar Salimat kasa bacci tayi saboda tunanin yanda" "za'ayi ta cire kudaden dake cikin account din Salim gashi ita ba account ne da ita ba, sai ta samu Yayanta Mai suna Naburago mugun dan son banza ne Naburago baya gudun Allah ya isa duk inda yaga bashi sai yaci bashi da sana'a sai buge buge da ita suke rufawa kansu asiri kasancewar su marayu ubansu ya mutu shine kuma namiji shiyasa wahala tayi yawa a kansa, talauci yasa Salimat lalacewa maza babu irin wanda bata sani ba shi kuwa Naburago rigima ko ta uwar uban waye saka kansa yake a ciki ayi ta fafatawa dashi a rabu dashi dan idan yaci bashi aka zo aka turkeshi ya biya sai ya mayar da abun wasa idan mutum ya kaishi gurin 'yan sanda kai tsaye yake fad'a musu bashi da kudin da zai biya bashi idan kuma ana kar'bar shekaru zai lissafa shekarunsa ya biya. Su kansu 'Yan sandan sun sallamawa Naburago shegen kansa" gashi da kwarjin tsiya komai takatsantsan di'nka a kan kayan sana'ar ka idan yazo kar'ba bashi mutum baya sanin sanda yake dauka ya bashi Salimat shi ta samu da maganar ta fada masa abunda ke "faruwa, Naburago yayi tsalle da juyi a dakinsa yace.""Bani atm din jeki kwanta ki huta kudi zasu koma" "account d'ina wahala ta yanke mana."" Salimat ta fad'a masa numbobin sirrin na Salim din yace to" magana ta kare. Alwala yayi ya yay sallah ya fita da atm din cikin aljihunsa. A ranar Naburago ya kwashe kudaden account din Salim tas ya mayar nasa accont din Salim sai shigowar alert kawai yaji yana dubawa yaga a'lamarin daya afku babu abinda ya fara dubawa sai wallet d'insa ya nemi atm dinsa ya rasa a gigice ya nufi motarsa ya shiga dubawa sako da loko babu atm! cikin tsantsar tashin hankali ya shiga motar ya kunna a guje ya nufi P.O.S din da sukaje kawai ya fad'a musu guri kamar mahaukaci yana dube dube. Ai a take wani Police dake gurin ya damqe shi a cewarsa yaga yayi yanayi da masu laifi dan yanda yaga ya shigo gurin a kid'ime ya nuna masa hakan! aikuwa jama'ar dake gurin suka gazgata hakan dan ganin yanda Salim din ke muzurai yana wani irin gumi! sai rawar baki yake ya kasa magana. Yana ji yana gani aka sashi a mota aka tafi dashi police stion kamar wanda aka daurewa baki ya kasa cewa komai zufa ce kawai ke tsatstsafowa daga jikinsa.......... _*Yau tafe nake da 'yar tsaraba ta *_ *'Kawata matso kiji wata muhimiyar magana A kwai gurare masu daraja da muhimanci a jikinki 1 Headquarter naki...2 Hamtarki....3 qasan nonuwanki 4 Tsakanin cibiyarki! Wad'annan guraran nada mutukar mahimanci a gurinki yana da kyau ki kula dasu ki mutunta su. Na farko dai ke kanki kin san "barin gashin hammata dana headquarter babbar matsala ce a gurinki waccan ka iya janyo miki imfaction gami da rashin jituwa da miji kullum ya kasance kin zama abar kyama a gurinsa, barin gashin hammata a gurinki sam! bai dace ba, ba dan komai ba sai dan ansan ita mace daban take da namiji kada kiga mijinki da gashin hammata kice kema ba zakiyi aski ba a kull! ke daban shi daban! ke ai abun kunya ne a gurinki ki d'aga hammatar ki a ga gashi! Wallahi duk ranar da kikayi kuskure kika bar mijinki yaga d'audar hammatarki kin cuci kanki sannan kika sake mijinki ya shaqi warin hammatarki kin zubar da qimarki duk da kasancewar yanzu muna lokacin sanyi kada kice ai yanxu sanyi ne ba'a wari kiqi yin aski wallahi duk turaran da zaki saka sai yaji warin jikinki saboda haka kiyi hattara. Warin qasan" "nono na mussaman ne ba ko wace macece ke kula da da wanke qasan nononta ba, to bari kiji mutukar kika ga mijinki a lokacin da kuke sex yana kauda kansa daga gurin nono ki to wallahi wannan warin yake damunsa, ina amfani ace kinyi wanka baki d'aga nonuwanki kin wanke ba ai kamar ba kiyi wanka ba k'awata! Kisa sabulu ki wanke kasan nono tas kisa masa turare na mussaman sai kiga maigida na zumud'in kai kansa gurin Ramin cibiya yana tara daud'a saboda gurin a tsuke yake baida spece" "sosai, yana da kyau kullum idan kinzo wanka kina sa bakin soso a hankali a hankali kina wankewa kada ki" bar ramin cibiyarki da daud'a domin hakan na iya janyo miki matsala mai girma. Wannan tsarabar tawa ba ta mantan aure bace kawai har daku 'Yan mata da zawarawa 'yan kwalisa To sai mun sake had'uwa daku a fita ta biyu * Vip gruop #600 normal group #300 account numbar....0542382124...Binta umar gtbank. Wahasap number. 07084653262 *BINTA UMAR ABBALE* 68******Salim har yamma yana police station a gar'kame hankalinsa yayi masifar tashi ganin duhun "magariba ya gabato sai kawai ya fara zubar da hawayen nadama! babu shakka wannan al'amari daya faru dashi hakkin Kawunsa daya zalinta ne, yasa hannu ya dauko hankici a cikin aljihunsa ya goge idanunsa tare da sake ri'ke 'karfen da yayi masa katanga da ma'aikan gurin, zare ido kawai yake yana fad'in ""Oga dan girman Allah ka saurari maganata wallahi ni ba 'barawo bane inaso kazo kaji uzirina ni" "abun a tausayawa ne qaddara da tsautsayi ne suka afka min.""" "'Daya daga cikinsu ya doki! tebur din dake gabansa yace.""Rufe mana baki munafiki kai har kasan" "qaddara irinku ai ba imani ne daku ba kazo sata sai Allah ya tona maka asiri dama irinku muke nema duk muyi maganinku yanzu D.P.O muke jira yazo mu zartar da hukuncin da zamuyi maka.""" "Salim ya sake rikicewa cikin tsantsar tashin hankali yace.""Wallahi wallahi bana daya daga cikin wa'yan" "nan mutanan da kuke magana a kansu, ku taimakeni kamar yanda Allah ya taimake ku wallahi ban shiga gurin nan da sunan sata ba Atm dina naje nema a gurin kasancewar kwanaki uku da suka wuce naje na cire kudi a gurun Tiryan tiryan ya fad'a musu abinda ya faru, yace""Idan kuna so ku tabbatar da" maganata to ku duba waya ta zaku ga text din da banki suka turo min cewar gabadaya kudin dake "account d'ina babu.""" "Da sauri wanda wayar ke hannunsa ya shiga dubawa, aikuwa da text din yaci karo cike da mamaki ya" "shiga nunawa 'yan uwansa sai duk jikinsu yayi sanyi, wanda key din cell din ke hannunsa ya miqe da sauri yaje ya bude shi yace.""Kayi hakuri kaji ko Allah ya mayar maka da alkairi.""" Cikin tsananin damuwa da tashin hankali ya kar'bi wayarsa da key din motarsa ya kama hanya ya futa "daga gurin, sai suka bishi da kallon tausayi kud'i kimanin miliyan daya da rabi an kwashe masa ai dole su jajanta al'amarin Salim na fita daga station din kai tsaye gidansu Salimat ya nufa, yayi parking a kofar" gidan cikin damuwa ya kira wayarta. Salimat ta fito cikin shiga ta alfarma kamar yanda ta saba ta bude "mota ta shiga, ganinsa a burkice yasa tasha jinin jikinta, ya kalleta dan jan ido yace.""Salimat 'barayi sun" kwashe min kudin accont dina yanxu bani da ko kwabo Atm dina ya fad'i a lokacin dana kaiki shopping "ban ankara ba sai da naga bank sunyi min alert sannan na duba naga abunda ke faruwa...Hakika ina cikin tashin hankali mai tsanani.""" "Cikin alhini tace""Innalilihi wa'ina ilahi raji'un Salim yanzu ya zamuyi da wannan qaddara sai kawai ta" "fashe da kukan munafurci Naburago ne ya fito daga gidan, yasha shaddarsa harda hula kamar" "mutumin kirki kai tsaye motar ya durfafa. Dama sun riga sun gama shirya plan dinsu tun a gida. hannu yasa ya kwankwansa gilashin motar. Da sauri Salim ya sauke gilas din ganin Naburago a tsaye yasa da sauri ya miqa masa hannu suka gaisa Naburago ya gyara tsayuwarsa yana kallon Salim din yace.""A matsayina na wakilin wannan yarinya Salimat na yanke shawara kancewar mun fasa baka auranta dan sabida munyi kyakkyawan bunkice a kanka mungane kai d'in azzalimi ne macuci maha'inci mun samu labari daga bakunan mutane da yawa kancewa kaine ka kunnawa ubangidanka wuta a cikin dukiyarsa wannan dalilin yasa muka yanke shawarar dawo maka da kudin auranka."" Yana gama maganarsa ya kalli Salimat din cikin tsawa! yace.""Maza ki fito daga motar nan ki shiga gida babu ke babu wannan" "macucin.""" "Salimat ta bude mota da sauri ta nufi gida tana kuka kamar gaske, Naburago yasa hannu aljihu ya dauko" "kudin Salim dubu Hamsin yasa masa a jikinsa yace ""Ga kudinka nan babu mu babu kai kada ka kuskura na sake ganin kafarka a kofar gidan nan."" Yana gama maganarsa ya bar gurin." Salim jikinsa ji'kewa yayi da gumi! tsabar tashin hankali makogwaronsa bushewa yayi qamas ya rasa ma wane irin tunani zaiyi sai kawai ya kifa kansa akan sitiyarin mota yana zubar da hawayen nadama. **** "*'Yar Sa'adu* ta jangwalowa kanta masifa, matar wani babban soja za'ayi mata kishiya sai ta samu" labarin *'Yar Sa'adu* da magungunanta sai kawai ta wanko kafarta ta ciko jakarta da kud'i taje 'Yar Sa'adu ta had'ata da magungunan mata iri iri Matar ta tafi gida ta dinga shan magani babu qa'ida ta dinga cusa maganin matsi wai ita lallai sai gabanta ya matse dan saboda kada amarya ta fita a gurin miji... "Aikuwa matsalar data afku da Halisa irinta ce ta afku da ita, Soja mazan fama ya bud'e mata wuta danshi" "har da duka ma ya had'a mata dashi yace sai tayi masa bayanin yanda akayi al'amuranta suka kasance a haka! Ganin rufa rufar da take bashi da amfani sai kawai ta fad'a masa yanda al'amarin ya kasance, takaici yasa shi yayi mata dukan tsiya da blet kuma ya daina kulata, ashe duk hukuncin da yayi mata bai" hakura ba mota ya cika da sojoji ya sata a gaba suka nufi gidan *'Yar sa'adu me kayan mata*. 'Yar sa'adu na tare da baki kawai sukaji ihun yara ga unguwar ta cika da kururuwar motar sojoji ai babu shiri "ita da matan da take a gidan suka fito waje, ganin zaratan sojoji sun durfafo kofar gidanta yasa ta kusa sakin fitsari a wando! a tsaroce tayi nufin komawa cikin gidan gabanta na wani irin faduwa ganin matar sojan data zo ta hada mata magani makwanni biyu da suka wuce babu shakka akwai abunda ke faruwa, takalmin kafarta ne ya gurde ta tsaya zata gyara matar soja da sojojin dake bayanta suka karaso gurin ba tare da jin tsoron komai ba matar ta nuna 'Yar Sa'adu da fad'in ""Gata nan itace matar da siyar da" "magunguna kan kudi masu yawa.""" "'Yar sa'adu ta diririce ta hau inda inda, Sojan dake kusa da ita ya taska mata mari da fad'in ""Kece kike" "cutar mata ko kin zama 'yar damfara ki tara mata ki dinga kar'be musu kudi kina siyar musu da abunda zai cutar dasu ko to yau sai kin gane kuranki."" doguwar bundigar dake hannunsa ya dora mata a wuya a tsawace! yace.""Wuce muje yau kin fad'a komar mu sai kin gane baki da wayo."" Yar Sa'adu kuka ne ya kufce mata jikinta ya shiga kyarma! sai ta shiga d'aga hannunta sama tana basu hakuri Kafin kice" "kwabo gurin ya cika da jama'a, su kuwa matan da suke tare da ita ganin an shigar da ita mota yasa da" sauri kowacce ta fece! tsoro da tashin hankali duk ya cika musu zuciya. **** Watannin Naja'atu biyu da dawowa gida inda ya kama wattanin cikinta shida kenan yanzu cikin nata ya "fito ana d'an ganinsa amma ba sosai ba kasancewarta doguwa yasa cikin bai bayyana kansa ba sai dai amma ita kadai ta san abinda take ji a jikinta, kusan kullum sai ta 'buya a daki taci kukanta ta koshi haka kawai Bash ya had'ata da wahala ya gudu ya bar mutane da jigilar d'ansa duk sanda ta tuno wannan al'amari takan kwana ta yini cikin kunci da damuwa, mussaman idan taga yanda Abbah Abbas ke hidima da ita da cikin jikinta duk sai hankalinta ya tashi ta shiga nadamar abinda tayi masa a baya, itace ta zama sanadiya gurin lalacewarsa cikinsa gashi ita taje ta dauko ciki ta kawo masa wahala, yanzu saboda ita kullum da safe kafin ya tafi harkokinsa sai yazo ya kofar na'isan sannan bayan ya dawo daga kasuwa ya sake dawowa gabad'aya jama'ar gidan sun fahimci saboda ita yake wannan sintirin dukkaninsu su gane ya damu da yarinyar da cikin jikinta, sai hankalinsu ya kwanta mussaman hajia da Alhaji burinsu kawai yarinyar ta haihu lafiya sai ai maganar kome domin su a ganinsu yanda yake nuna damuwarsa a kan yarinyar suna ganin kamar yana so ya mayar da ita gidansa ne. wanda shi kuma kwata kwata ba haka bane a cikin zuciyarsa haka kawai take bashi tausayi da ita da abinda ke cikinta shiyasa ya mayar da hankalinsa a kanta duk da bashi ne keda alhakin kula da itaba , a yanzu dai cikin zuciyarsa bai dauki" Naja'atu a matsayin komai ba face 'Yarsa. Yau asabar yana zuwa da wuri dalili kenan daya sa takasa komawa baccinta na safe ta fito palo ta zauna "tana jiran zuwan nasa, lokacin daya shigo hajia na sama ita kadai ya samu a zaune tana kallon tashar" "sunna tv Malam Aminu Daurawa na gabatar da shirin tambaya mabudin ilimi, a nutse ta amsa masa" sallamarsa ta dan gyara zamanta a hankali tana gaishe shi Ganin yanda take ya mutsa fuska ne yasa ya "mayar da hankalinsa kanta a nutse yace.""Ina fatan kina lafiya ya jikinki.""?" "Kamar za tayi kuka tace""Da sauki inasu Mussadiq."" Yace.""Suna gida lafiya lau ina hajia.""? Tana sama.""" "Tafada tana kallon kasan kafafunsa, kai tsaye saman ya nufa sai ta bishi da kallo tana girgiza kanta ita kam a duniya akwai mutumin dake sonta irinsa kuwa? gaskiya babu." "Ya kai mintina goma sha biyar a saman ya sakko da sauri yana duba agogon hannunsa, dan kallon gefan" "da take zaune yayi ba tare da yace wani abu ba ya kama hanyar fita. Da kyar ta kira sunanshi, tsayawa" "yayi yana kallonta. Murya na rawa tace.""Ina so mu gaisa dasu Mmn Sajida matar nan data taimaka" "min.""" "Jim! yayi kafin yace.""Yanzu dai sauri nakeyi ana jirana idan nazo da yamma sai ayi yanda kikace.""" "tace.""To Abbah Allah ya bada sa'a.""Ya amsa yana kokarin futa daga falon." Sai bayan futarsa ne ta shiga tunanin yanda za'ayi ma tayi magana dasu Mmn Sajidan tunda lokacin data "barsu daga ita har Mmn Ladin babu me waya a cikinsu , wannan dalilin ya sanya jikinta yay sanyi taso da hanyar da zata sadata dasu da sun gaisa da juna ta 'kara yi musu godiyar abinda sukayi mata." To koda ya dawo gidan da Yamma batai masa maganar ba shima al'amuran dake gabansa sun mantar "dashi, sai kawai ya ajiye mata abubuwan da ya saba siyo mata ako wace rana yay tafiyarsa gurun iyalinsa." Bayan kwanaki biyu da faruwar hakan Yana tsaka da shiryawa domin tafiya kasuwa kira ya shigo "wayarsa, Zainab yasa ta miqa masa wayar ya daga tare da karawa a kunnansa. Mmn Sajida dake" "d'aya bangaran ta sauke ajiyar zuciya tana godewa Allah da sauri tace""Sannu ina kwana sunana Mmn Sajida daga jos."" Sai yayi saurin duba number yana so ya tabbatar, ya mayar da wayar kunnansa yace."" Lafiya kalau Mmn Sajida na gane ina fatan kuna lafiya.""? Ta amsa da lafiya lau Alhaji muna fatan kunje gida lafiya."" Yace.""Lafiya lau alhmdullhi."" Tace.""Dama na kira ne idan da dama inaso a bani Naja'atu mu gaisa wallahi har yanzu alhinin rabuwa da ita bai sakemu ba."" Yace.""Ayya! kada ki damu insha Allahu anjima kad'an idan naje Inda take zan bata wayar ku gaisa."" Tace.""To Alhaji mungode sai anjima."" Yace.""To masha Allah."" Kashe wayar yayi ya ajiye kan drowar dake gefansa, Zainab tunda taji ya ambaci" sunan Naja'atu ta sanja fuska dan har sai da ya fahimci sauyawarta alhalin labari take bashi amma lokaci guda yaga ta 'bata rai! kwanciya ma tayi ta juya bayanta kishin Naja'atu naso ya dargagaza mata zuciya. "Sai da ya gama shiryawa tsaf ya juyo yana kallonta a nutse yace.""Zainab lafiya dai ko.? ba tare data jiyo ba tace.""Lafiya lau bacci zanyi shiyasa na kwanta."" Yace.""Okey ni zan fita."" Tace""A dawo lafiya."" ya amsa a nutse ya bude kofar dakin ya fita, mikewa zaune tayi tana jan tsaki! kai gaskiya ta gaji da wasiwahsi gami da takurawa zuciyarta dole yau idan ya dawo ta tambayeshi tsakaninsa da Naja'atun nan da ya" damu da ita idan mayar da ita zaiyi gwara ya fad'a musu su ya daina wani 'boye-'boye........... *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar karanta littafin ga yanda abin yake. Vip group #600 normal group #300 account.... 0542382124...Binta umar gtbank. Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 69*******Lokacin daya isa gidan Alhajin Naja'atu na daki tana baccinta na qa'ida dama idan tayi sallar asubahi komawa take ta kwanta tayi ta bacci watarana hajia da kanta take shiga dakin ta tashe ta sannan fa tayi break fast tunda cikinta yayi kwari take wannan bacci mara qa'ida daddare ma tana idar "da sallar isha'i take kwanciya, hajia da taga abun yayi yawa cewa tayi aje asibiti a dubata, Yaya Ramlatu tace"" Lafiyarta lau kawai yanayin cikin nata ne yazo a haka dama ana samun ciki mai sanya baccin tsiya ta ce ta kwantar da hankalinta bacci lafiya ne. bana cuta ba to wannan maganar da Yaya Ramlatu tayi itace tasa hajian ta kwantar da hankalinta amma dai duk rintsi da daddare bata barinta ta kwanta sai ta" tabbatar ds taci abinci ta koshi tukkuna. "Koda ya shigo gidan bai samu kowa ba, wai ashe sun tafi jana'izar 'yar 'kanin Hajia Rabi dake mandawari," "da yake mutuwar ta dare ce shiyasa bashi da labari sai daya ya shigo gidan tukkuna maigadi ke fad'a masa. Juyawa yayi da niyyar fita daga gidan sai kuma yayi wani nazari, yana tunanin ko zasuje" "gidan mutuwar bai zama lallai suje da ita ba shima yasan a daidai lokacin take baccin data saba, dan" wani lokacin idan yazo baya samun ganinta sai dai kawai ya tambayi hajia lafiyarta. "Shuru falon lokacin daya shiga, bai jira komai ba ya nufi dakin da take. Kallon sharia yayi mata yayi" "saurin kauda kansa, yanayin kwanciyar da tayi taso ta saka shi cikin wani yanayi yayi saurin kawar da abun daga cikin ranshi Ya karasa bakin gado tare da tsayawa saitin kafafunta yana kallon fuskarta dake" "kallon rufin dakin, da yake irin kwanciyar da ba'a masu ciki suyi ita tayi (rigingine) ta tayar da kafafunta sun taka gadon kana ta d'ora dukkanin hannayenta a saman cikin nata. Sunanta ya shiga kira yana" korar shad'en d'in da yake ra'barshi idan da baiyi wa Mmn Sajida al'kawari ba da yana ganin tafiyarsa zaiyi dan tsayuwarsa a dakin na nema ta haifar masa da matsala. Kamar a mafarki taji muryarsa na kiran sunanta! ta bud'e idonta da sauri! shi take gani dishi dishi a "idonta, shi kuwa yanayin yanda yaga idanunta sun sauya yasa ya dauke kansa yana kallon gefe guda, yace.""Tashi ku gaisa da Uwar dakin ki ta jos dazu ta kira waya tana so ta dubaki.""" Da sauri ta miqe zaune jin cewar Mmn Sajida ta kira waya...Wannan gaggawar miqewar da tayi yasa "yaron dake cikinta ya kai mata wani irin naushi! yayi fushi! ya samu guri guda ya dunkule mata! Rintse! idonta tayi murya na rawa tace""Wayyo cikina.""! Kafin kice me zufa ta tsatstsafo mata a saman goshi!" "Rikicewa yayi yay saurin ajiye wayar a kan drowar dake gefan gadon, be san sanda ya zauna kusa da ita" "ba yana kokarin kamo hannunta. ""Wayyo Allah cikina ya 'kulle a guri d'aya.""Abinda take fad'a kenan" tana janyo zanin gadon da hannayenta. Kamota yayi yasa a jikinsa yana shafa bayanta a hankali a "hankali duk ya rasa nutsuwarsa ita kuwa sai kokarin cire jikinta take tana kiran cikinta! Yace.""Me yasa kikayi irin wannan kwanciyar bayan kin san masu ciki ba'aso suyi sannan me yasa kike gaggawa a cikin al'amuranki kin jima a kwance rigingine gashi kin tashi cikin gaggawa dole shima yayi fushi! ya zauna miki" "a guri guda, sannu ki dinga kula kinji ko.""" "Wannan maganganun yake mata yana dan shafa bayanta a hankali a hankali! Shuru tayi a jikinsa, tana" jin yanda yaron ke motsi inda ya d'aure yana saki a hankali a hankali cikin nata ya koma daidai ta daina jin ciwo A sanyaye ta cire jikinta a nasa ta sunkuyar da kanta tare da kokarin gyara botiran "rigarta. Daidaita nutsuwarsa yayi ya dauki wayar daya ajiye yana kallonta yace.""Ina fatan cikin ya daina" "ciwo."" Kanta ta d'aga tana jin nauyin abinda ya faru Yace.""To sai ki kiyaye gaggawa kuma ki daina irin" "wannan kwanciyar cikinki yayi kwari yanzu kiyi hakuri kina kwanciyar da yaronki zaiji dadi kema ki inganta lafiyarki.""" "A hankali tace""Wallahi bana sanin sanda nakeyi nafi jin dadin irin kwanciyar."" Dan murmushi yayi" "yace.""Baki damu da lafiyarki ba shiyasa kike biyewa son zuciyarki kisa a ranki kin daina irin kwanciyar sai kiga kin zauna lafiya."" Tace""To shikkenan insha Allah.""" Dakin ne yayi shuru Abbah na traying din number Mmn Sajida tana fara ringing ta dauka yay saurin "miqa mata, gani yay ta fad'ad'a fuskarta da fara'a tana dariyar farin ciki tace.""Mmn Sajida ina kwana ina Mmn Ladi.""? Mmn Sajida cikin da walwala da farin ciki ta amsa da fad'in ""Ga Mmn Ladi a kusa dani muna tare Naja'atu ya kuke je gida? Ya kuma jikinki muna fatan duk komai lafiya."" Tace""Wallahi" alhmdullhi Mmn Sajida gaskiya naji dadin jin muryarki ina nan ina kewarki ki bani Mmn Ladi mu gaisa "insha Allahu idan na haihu zanzo nayi muku kwanaki.""" "Mmn Sajida tace.""Muma muna nan duk kewarki ta ishemu dan Walid ma sai da yayi zazzabi Sajida kuwa" "kullum sai ta kira sunanki tayi kuka."" Najaatu murya na rawa tace""Ayya Allah sarki Walid dan Allah kice ina gaishi da kyau Sajida kuma kice mata idan zanzo zan zo mata da kayan wasa irin wanda take so." "Mmn Sajida tace""To insha Allah zan fad'a mata ga Mmn Ladi ku gaisa."" Mmn Ladi na washe bakinta ta" "kar'bi wayar da fad'in ""Naja'atu 'yar albarka mai gyara sinnar ma'aiki ai ni kam babu abinda zance miki daba dan keba da tuni na dade da rabuwa da Saleh wallahi yanzu zaman lafiya muke da juna yanzu ina hakuri da duk abinda ya bani kuma na daina yi masa rashin kunya yanzu Saleh daidai gwargwado yana" kyautata min muna zaune lafiya da 'ya'yanmu. "Naja'atu tace"" Amma gaskiya naji dadin wannan labarin naki Mmn Ladi Allah ya qara muku zaman lafiya" "sannan kuma inaso in tuna miki cewar kada ki manta da al'kawarinmu insha Allah idan nazo garin zan tallafa miki ki fara sana'a kema.""" "Mmn Ladi tace""To nagode kwarai da gaske Naja'atu Allah ya saka da alkairi Allah kuma ya sauke ki" "lafiya."" Ta amsa da amin tana jin wani irin farin ciki a cikin ranta." Abbah na zaune yana kallonta sai dariya take Mmn Sajida ce take bata labarin halin da Dantalle ya shiga "bayan tafiyarta harda kuka ya dinga yi Naja'atu ta dinga kyalkyala dariya tana fad'in ""Lallai Dantalle to" "ki bashi hakuri yaje ya rungumi matanshi ya kyautata musu shine abinda ya dace yayi"". Kallon" "agogon hannunsa yayi yaga lokaci yaja a qallah sun dauki minti ashirin suna wayar gyaran mirya yayi tayi saurin kallonsa, hannunsa ya miqa alamun ta bashi wayar. Da sauri tace"" Mmn Sajida nagode da" "karamci Abbah zai kar'bi wayarsa insha Allahu idan na haihu lafiya zaku ga nazo muku."" Mmn Sajida" "tace""To Naja'atu Ubangiji Allah ya raba lafiya sai anjima."" Sallama sukayi cike da farin ciki da kewar juna." "Tana miqa masa wayar tace""Abbah don Allah kayi serving number ta Mmn Sajida ce."" Wayar yake" "dubawa a tsanake ba tare da ya dubeta ba yace.""Waye Dantalle.""? Sai tayi saurin kallonsa. Hankalinsa" "nakan wayar yana kokarin serving din number Ya sake maimaita tambayarsa. A sanyaye tace""Wani" "mutumi ne a garin tun zuwa na na farko yake naci wai sona yake.""" "Miqewa yayi tare da mai da wayarsa aljihu Yace.""Okey na fahimta to Allah ya tabbatar da alkairi a" "tsakaninku Wannan number kuma nayi serving insha Allah gobe ko jibi zan kawo miki waya sai ku dinga gaisawa idan kin haihu sai ki fad'a musu dan na fahimci matar tana kaunarki sosai.""" Maganar Allah ya tabbatar musu da alkairi da Dantalle itace duk ta ragargaza mata duk wani farin ciki da annushuwar da take ciki! sai ta shiga tunani gami da nazarin inda maganar tasa ta dosa! Me yake nufi ne?? Bayansa tabi da kallo har ya fice daga dakin bata samu damar yin wata magaba ba Jiki a masifar sanyaye ta koma ta kwanta ai sai hawaye suka 'balle mata suka dinga fita tamkar wanda "aka kwance famfo yanzu idan yace ba zai mayar da ita ba to wa zata aura? waye zai riqe mata d'anta? Waye zai tallafa mata kamar yanda yake mata, gaskiya idan yaqi mayar da ita gidansa ya cuceta dan ta riga ta gama sa rai ganin irin wahalar da yake mata shiyasa ta sakankance da cewar yana jira ne ta haihu" ya bijiro da maganar da kowa yake tunaninta a kansa Shi kuwa yana fita motarsa ya shiga a gurguje ya nufi gidan mutuwar domin yayi gaisuwa ya wuce "harkokinsa, gabad'aya bai sanya lamarin Naja'atu a cikin ransa ba ballantana ya dameshi yana fitowa daga inda take ya ajiyeta a gefe guda ba zaije ko'ina da damuwarta ba bare ta hanashi gudanar da abubuwan da suke gabansa." "Koda su hajia suka dawo kasa gane kanta sukayi, hajia ta dinga tambayarta ko wani abu na damunta," "girgiza kanta kawai takeyi tace""Babu komai baccin data yini tanayi ne ya sanya yanayin ta ya sanja to hajia dai taji ne amma bata amince da maganar ba, haka yamma tanayi data fahimci ya kusa shigowa gidan sai kawai ta shige daki ta kwanta bata so ta ganshi saboda gudun abunda ka iya zuwa ya dawo" tana ganin zata iya fashewa da kuka mutukar zata kalli fuskarsa. To shima a nasa 'bangaran bai damu da rashin ganinta a falon ba bayan sun gaisa da mahaifiyarsa sai "kawai ya ajiye ledojin hannunsa wanda ita tasan ko na menene kayan ciye ciyen Naja'atu ne wanda yake siyo mata kullum ta Alla. Sallama yayi mata yace.""Idan ya fito daga massalaci gida zai wuce ba zai dawo" "ba. Hajia tayi masa fatan alkairi tare da bashi saqon gaisuwarta gurin su Saddiqa, ba tare da damuwar" komai ba ya bar gidan. "Koda ya isa gidan nasa kai tsaye gurin Halisa ya nufa duk da cewar ba itake keda girki ba, sai da ya duba" ta sosai sannan ya fito ya nufi gurin Zainab Ita da yaran suna zaune a falo gwanin sha'awa sukayi masa "sannu da zuwa ya amsa a sake, yana kallon Zainab yau tayi kwaliya sosai sai dai babu walwala a tare da ita, bece mata komai ba ya nufi dakinsa, ta mike tabi bayansa tana wani cika da batsewa." Ya tu'be kayan jikinsa yana kokarin shiga wanka ta shigo dakin sai ya tsaya yana kallonta har ta qaraso ta "samu guri ta zauna tare da fadin."" Abban Mufida sannu da zuwa."" Ya amsa yana sake nazarinta yace.""Da alama yau akwai abunda ke damunki na karanci rashin walwala a fuskarki ina fatan ba yaro na bane yake" "takura miki.""" "Girgixa kanta tayi tana dan ta'be bakinta tace""Idan shine yake takura min ai da sauqi Abban mufida" "zuciyata ta kasa nutsuwa kwana biyu sai tunani nake da wasiwahsi dan Allah kada ka dauki maganata da wata manufa naga kamar kana so ka dawo da Naja'atu gidanka saboda dawainiyar da kake mata har taso tayi yawa wani abun ma sai dai mu samu labari, nida aunty Halisa kullum cikin tunani muke idan dawo da ita za kayi gwara kawai ka fad'a mana mu sani dan ina ganin kamar 'boye-'boyen da kake mana sam" bashi da wani amfani.'' Tunda ta soma maganar ya zuba mata ido yana kallonta mamaki yana kasheshi! shi dai tunda Allah ya had'ashi aure da qananun yara yake ganin rashin kunya iri iri Wai Zainab ce ta turkeshi take kokarin sai "ta 'kure shi a ganinta yana 'boye musu abinda ke tsakaninsa da Naja'atu, idan tunaninsu kenan to babu" shakka zai basu mamaki! Dauke kansa yayi daga kanta ba ta tare da yace mata komai ba ya nufo toilet cikin d'umbun mamakin yarinyar. *NA DAWO * *'Kawata matso kiji wata magana mai muhimanci nasan kin san da cewar yanxu muna lokaci na sanyi jiki na bushewa kammani na sauyawa to bari kiji wata magana maza a irin wannan lokacin jaraba da "fitinarsu take tashi, me ya kamata kiyi domin ganin kin gyara kanki da kowane lokaci mijinki na samun" nutsuwa dake Kada ki mayar da hankalinki kacokan kan gyaran fatar jikinki baki inganta ni'imarki ba Ina amfanin fatar ki tayi luwai luwai kina gayu da tunkawo kuma sai dare yayi maigida yaji guri a bushe kada ki sake haka ta faru 'Kawata! kamar yanda zaki kula da fatar jikinki to ki kula da Ni'imar ki ya kasance kullum idan maigida yazo yaji zam!zam kada kiyi wasa da shan ruwan kaninfari had'e da shan kayan marmari ina ganin koga wannan kika tsaya zaki gamsar da maigidanki Wannan itace tsarabar da nake tafe da ita * Vip gruop#600 normal group #300 account.. 0542382124.//Binta umar gtbank .....WhatsApp number.... 07084653262 *MADADI* 70Zainab na zaune tana sa'kawa da kwancewa ya fito daga toilet yanda taga fuskarsa a had'e! shine "yasa jikinta mutuwa gabanta ya dinga fad'uwa, tana kallonsa har ya kimtsa jikinsa ya kama hanya ya fice daga dakin ba tare da ya tanka mata ba...Jikinta a mace ta miqe salo salo tabi bayansa falon gurin cin abinci ta sameshi a zaune yana duba karamar wayarsa Saddiqa na kokarin zuba masa abinci." "Da sauri ta karasa gurin, cikin kokarin wanke kanta ta kar'bi plate din dake hannun Saddiqar tace taje ta" zauna. "Abbah duba wayarsa kawai yake yi bai kalleta ba har ta gama zuba masa abinci ta ajiye masa a gabansa," ya ajiye wayar a nutse ya dan yanyo plate din gabansa yayi bisimillah kamar koda yaushe ya fara cikin abincin. "Ta kalleshi a sanyaye tace""Abban Mussadiq naga kamar maganata ta 'bata maka rai dan Allah kayi hakuri" "wallahi ni haka nake bana iya ajiye abu a raina.""" "Yayi mata wani kallo mai kama da harara yace.""Surutu da fad'i ba'a tambaye ki ba shine yake damunki" "ba abinda kika fad'a ba, Okey zan kira Halisa yanzu itama naji ta bakinta akan maganar da kika fad'a min tunda kun dauke ni munafiki wanda ke 'boye muku tsakaninsa da Naja'atu.""" "Da sauri tace""Wallahi ba haka nake nufi ba shiyasa fa tun farko kafin na fad'i maganar nan sai da nace ka" "fahimceni amma meye sai an kira anty Halisa dan Allah kada ka kirata.""" "Yace.""Ai a inda ba qasa nan ake gaddamar kokawa tunda kince keda ita kuna cikin wasiwahsi kullum" "kuna tunani da zargina kan na 'boye muku wani abu to dole itama tazo ta fad'a min da bakinta kamar yanda kika fad'i naki.""" "Zainab idonta ya ciko da kwalla! Tunda suke basu ta'ba zancan Naja'atu da Halisa ba, tunda ta ta'ba yi" mata maganar a gidan Alhaji Halisan ta nuna bata son maganar bata qara tunkararta ba ita kadai abun ke damu kawai ta sako sunan Halisa a cikin maganarta ne wai ko zai dauki abun da muhimanci ya fad'a musu abunda ke zuciyarsa. Yana kammala cin abincinsa ya barta a gurin yaje ya zauna kan kujera yana kiran wayar Halisa. Zainab "kasa motsawa tayi tana zaune a inda take har Halisa ta shigo falon.....Umartar su Saddiqa yayi dasu je su kwanta, yaran suka miqa da sauri suka nufi dakinsu." "Halisa ta zauna kan kujerar dake fuskantarsa itama tunda taga yanda yasha kunu sai tasha jinin jikinta," barka da dare tayi masa taja bakinta tayi shuru. "Ba tare daya juya ba yace.""Zainab zo nan."" Ta miqe a hankali taje ta zauna nadama da dana sani kawai" takeyi data san tozartata zaiyi a gaban kishiya da ta daure ba tayi masa maganar ba. Ya kalli Halisa a "kaurare yace.""Ashe idan bana nan munafurcina kukeyi? Har kuna zargina akan ina 'boye muku tsakanina da Naja'atu shin idan nace zan dawo da ita akwai wacce ta isa ta hanani dawo da ita a cikinku.""!" "Halisa ta bud'e bakinta cike da mamaki da tsoro tace""Yaushe akayi hakan Abbah Mufida wallahi duk" "wanda ya fad'a maka maganar nan karya yake ni meye nawa a ciki idan ka dawo da Naja'atu gidanka gaskiya ka 'kara yin bunkice a kan maganar nan..""" A tsanake ya kalleta ya kalli Zainab da tayi tsuru tsuru nan ya tabbatar da cewar 'karya yarinyar tayiwa "Halisan, yace.""Ba wani ne ya fad'a min ba Zainab ce gata nan tana jinki abunda yasa kuma na yarda da maganarta saboda ina ganin zaki iya aikata hakan tunda kema ba qaunar Naja'atun kike ba.""" "Halisa tace.""To ikon Allah idan da ranka kasha kallo ina zaune anyi min sharri yanzu ke dan Allah dan" "annabi Zainab yaushe mukayi wannan maganar dake ashe kin manta maganar da mukayi dake a gidan alhaji, haka kawai zakiyi maganarki sai kisa sunana.""!" "Ganin yanda Halisan ta hasala! ne yasa ya daga mata hannu yace.""Ya isa! kina nufin ba kiyi ba kenan.""? A" "fusace! tace""Wai dan Allah wace irin magana kakeyi? da da yanzu ba d'aya bane kai kanka ka san yanzu na gyara kuskurena sannan naji kana wata magana wai bana qaunar Naja'atu shiyasa zan zauna da Zainab mu zageta! a kan wane dalili ni Naja'atu da iyayenta basuyi min komai ba wallahi saboda haka ko" "yau ka dawo da ita gidanka ina maraba da ita.""" Tana gama maganarta ta miqe rai a 'bace! ta fita daga falon Maganganun da Halisa tayi ya nuna "masa gaskiyar abinda ke cikin zuciyarta, kuma yaji dadin hakan Halisa ta daina adawa da Naja'atu ta barwa Zainab, a nutse ya juya yana kallonta tayi tsilli tsilli kunya da nauyi duk sun rufeta sai yanzu ta gane itama wauta da kuruciya na damunta to idan ba haka yaushe ma zata turkeshi da irin wannan" maganar. """Zainab."" Ya kira sunanta tare da tsira mata idonsa, ta amsa murya na rawa. Yace."" Saboda ina yiwa" "Naja'atu hidima kike ganin kamar zan dawo da ita gidana."" Fashewa tayi da kuka tace""Aa wallahi."" Yace.""Hakane mana! kina kishi da Naja'atu alhalin zama bai ta'ba had'aki da ita ba, to ki kwantar da hankalinki kinji ko dik wata hidima da kika ga inayi mata inayi ne dan Allah da manzonsa da kuma tausayawa abinda ke cikinta, amma babu maganar na sake zaman aure da ita! saboda haka ki samu nutsuwa ki daina wasiwahsi kamar yanda kika fad'a! Sai dai da kowane lokaci zan iya kawo muku abokiyar zama dalili ni mutum ne meso ya cikasa sinnar ma'aiki Annabi Muhammad (slw) inaso kafin Allah ya dauki raina na had'a mata hudu a gidana su haifa min tarin yara masu albarka saboda haka kisa" "a ranki cewar akwai sauran abokanan zamanki da zasu zo mutukar Allah ya qaddara min hakan.""" Zainab shuru tayi tana goge hawaye itakam wauta da rashin dubara na damunta amma daga yau tayi "alqawari zata dinga kiyaye harshenta domin gudun abunda ka iya zuwa ya dawo, dan gaskiya itama ba" "laifinta bane kishin naja""atu ne ya tunxura mata zuciyarta amma dai za tayi kokarin ganin ta dauke kanta akan dukkanin abinda zata gani ko taji labarin yayiwa Naja'atun.." To kamar yanda yayi mata alkawarin zai siya mata waya hakan ya faru dan Abbah Abbas waya mai kyau "da tsada ya siya mata sabuwa dal a kwalinta, ranar da ya bata wayar tayi ta murna da farin ciki tana masa godiya. babu wanda ta fara kira da wayar sai Mmn Sajida. suka shafe mintina da dama suna hira A gaskiya Naja'atu tayi farin ciki da samuwar wayar a hannunta dan sabida tasan ba qaramin kewa zata" d'ebe mata ba. ****** """Kaga Salisu ina jin tsoron ranar da asiri zai tuno ni dai da zaka bi ta shawarata da kaje ka samu mutumin" "nan kayi masa bayani watakila ma yace mu rike kudin tunda nasa ne ."" Mahaifiyar Naburago ce take wannan maganar" "Gyara zamansa yayi yana kallonta yace.""Haba Mama ki daina tsoro mana babu ta yanda zaayi asiri ya" "tuno kudi sun riga sun shigo hannuna."" Tace.""A'a ni daina nafi so kaje kayi masa bayani wannan kudin ba zasuyi maka albarka ba tunda na sata ne kaga kenan sata ta saci sata kaima idan da tsautsayi wani sai ya damfare ka tunda dai kasan inda zaka samu mutumin nan to kaje kayi masa bayani ka bashi hakuri ni na" "fada maka ba zaice komai ba watakila ma yace ka rike kudin.""" "Naburago yace.""Mamma wannan shawarar taki gurguwa yace yama za'ayi na samu kudi a sama kice" "naje fad'awa wanda yake dasu ni ba zanje ba wallahi, na riga na shirya tsaf akwai sana'ar da nake so na fara dasu sana'a ce mai inganci kuma ina da ya'kinin zata kawo min kudi dan lokaci guda zan zama multi mollonia."".. Girgiza kanta kawai tayi tace.""Shikkenan ai tunda kaki daukar shawara."" Miqewa yay ya kama hanya ya fita, kai tsaye ya hau sabon babur dinsa wanda ya siya dubu dari biyu da hamsin, sannan yayi sabbanin d'unkuna ya kuma bibbiya bashin da ake binsa, daga haka sai kawai ya cigaba da facakarsa da kudin, dan ita kanta wacce tayi sanadiyar samuwar kudin da kyar yake bata wani abu, Naburago ya tattare kudin yayi bukatarsa dasu yanzu saura dubu dari takwas dasu yake so ya fara sanar cah-cah dan yana ganin yanda sana'ar take sanya mutane da yawa suyi mahaukanta kud'i to shima dama rashin kudi a hannu ne yasa bai fad'a harkar ba tunda yanzu ya samu dama to zai shiga a dama" "dashi, babur dinsa ya hau ya nufi mahad'arta su." ***** 'Bangaran 'Yar Sa'adu kuwa sai da tayi sati a barikin sojoji suna azabtar da ita sannan suka saketa ta "dawo gidanta a mutukar galabaice jikinta duk yayi rud'u rud'u da shatin bulala abinka da farar mace ko'ina yayi tabo a jikinta, haka ta kwanta ciwo duk a cikin matan dake mata fadanci a kara rasa wacce zata zauna tayi jinyarta, sai da ta dan samu sauqi ta tattara komatsanta ta tafi garinsu tana ganin ba zata iya cigaba da zama ba haka kawai tana zaune wata ta sake janyo mata masifa gwara ta koma" garinsu ta cigaba da harkokinta a can. **** "To kwanaki na tafiya wattani na shiga suna mutuwa, komai na tafiya ne da ikon Allah da kuma" "amincewarsa Naja'atu al'amuranta sun tsananta dan dab take da haihuwa cikinta ya shiga wata na tara har yayi kwanaki! gabadaya hankalin wanda yake kusanci da ita ya tashi saboda tunda cikin ya shiga wattanin haihuwarsa ta kumbura mussaman qafafunta, duk da Likita ya dubata ya tabbatar musu da cewar babu matsala hankalinsu bai kwanta ba. Abbah Abbas da hajia sunfi kowa tada hankalinsu a kan al'amarin Baba malam da baba talatu kawaici da alkunya yasa duk damuwar da suke ciki game da 'Yar" tasu sun kasa nunawa gabad'aya ma Baba talatu d'auke kanta tayi da kanta sai dai kullum cikin yi mata addua take......B'angaran Abbah Abbas kuwa gudun zargin da mutane ke masa yasa yake boye damuwarsa akan halin da Naja'atu take ciki amma zahirin gaskiya yana cikin tsanani da damuwa mussaman idan yazo gidan ya ganta a jibge a kan kujera! sai dik jikinsa ya mutu kullum haka yake yini ya kwana cikin alhini da jiran tsammani yanda ma ya damu da haihuwar Naja'atu kamar bai damu data Zainab ba su kansu matansa sun fahimci hakan sai dai kowacce na kokarin dauke kanta akai amma hakikanin gaskiya abun yana damunsu mutukar aka cigaba da tafiya a haka to suna cikin matsala gwara ya dawo da ita gidan hankalinsu zaifi kwanciya akan ya dinga shiga halin damuwa akanta. Ranar Alhamis da daddare ta farka da ciwon haihuwa mai tsanani dama tun sanda cikin nata ya tsufa "Yaya Ramlatu take kwana da ita a daki, jin motsinta yasa ta tashi da sauri tana tambayarta, Naja'atu na zufa tana kiran sunan Allah tace""Watakila haihuwa zanyi dan ciwon da nake ji yafi na kullum."" Ya Ramlatu tace""To ikon Allah bari na kira hajia sannu kinji ko."" Fita tayi daga dakin da saurin gaske Tare suka dawo dakin da hajia da sauri ta d'ago ta ta rungumeta a jikinta, tana mata sannu!" "Yaya Ramlatu ta shiga hada kayan haihuwa! Hajia t""Ta kalli Ramlatu da fadin''Ki sanar da hajia Rabi Naja'atu na kan gwiwa."" Ya Ramlatu da sauri ta futa daga dakin Hajia ta rike ta sosai tana tofa mata" "adduoi lokacin ita Naja'atu, ciwon ya tsananta dan dab take da haihuwa, shiyasa ta kasa tsugunawa" sai kawai ta silale a gurin ta kwanta tana wani irin kifkif da idanunta! hannunta tasa ta janyo na hajian tana jan salati! Hajia ta shiga tashin hankali ganin irin abinda Naja'atun takeyi sai hawaye ya soma zubo mata addua take Allah y yanke mata wahala.....Hajia Rabi da Ramlatu na shigowa faya ta fashe! sai yunkuri kawai sukaji tana wani irin nishi!! da sauri suka rufu a kanta kowanne na iya bakin kokarinsa. Naja'atu Ganin Yaya Ramlatu itace mai kwari a cikinsu sai kawai ta d'amko ta ri'keta gam! gam! a tare suka dinga nakud'ar suna nishi! tare! Sosai Ramlatu taji jiki ta kuma tabbatar riqon bana Naja'atu bane na mala'iku ne. Cikin ikon Allah da hukuncinsa yaro ya fad'o a cikin zanin da suka rufa "mata, sai kawai kukansa sukaji Ajiyar zuciya suka sauke dukkaninsu suka had'a baki gurin fad'ar" """Alhamdullhi.""" *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin littafin ga yanda abin yake. Vip group #600 normal group #300...account... 0542382124...Binta umar gtbank. Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *BA HARAM BANE!* 71 Yaya Ramlatu ce tayi dubarar d'auko babyn dake ta tsanyara kuka alamu sun nuna cewar yaron yana "da qoshin lafiya dan tunda ya sauka ya cika musu kunne da kuka.........Hajia Rabi tace""Namiji ne ko mace.""? Yaya Ramaltu na murmushi tana sake riqe yaron a hannunta tace.""Namiji ne gashinan tubarkallah masha Allah."" Hajia ta rike Naja'atu sosai a jikinta tana fad'in ""To Allah ya raya shi tafarkin addinin musulunci."" Suka amsa da amin amin Yaya Ramlatu ta nad'e yaron a towel ta ajiyeshi kan" gado da sauri tazo ta taimakawa hajia Rabi gurin rirriqe Naja'atun dake ta wani irin nishi!!! 'Yan dabaru suka shiga yi mata domin mahaifa ta fad'o amma abun yaci tura Hajia ganin lokaci yana ja mahaifar taqi ta fad'o sai kawai ta yanke shawara akan su tafi asibiti zaifi "kwanciyar hankali......... Hankali a tashe Ramlatu ta bude wardrobe cikin sauri ta dauko riga da zani na atampa, hajian ta kar'ba tana kokarin sanya mata Allah sarki Naja'atu Idan kuka ga Naja'atu a lokacin sai kun tausaya mata dan tayi masifar galabaita kokarin kwanciya ma takeyi hajia na hana ta. Hajia Rabi" "ce ta shigo d'akin da sauri ta kalli Ramlatu da fadin "" Taimaka mu kamata yanzu nasa 'Dan Azimi ya fito" "da mota."" Sai suka fara kokarin miqar da ita, tana lanjarewa kuka take da fad'in su yafe mata mutuwa za" "tayi, lokacin da take wannan maganar gabad'ayansu jikinsu mutuwa yay Hajia kuwa da yake mai saurin" kuka ce tuni hawaye sun 'balle mata. "Ya Ramlatu tace""Ba zaki mutu ba Naja'atu insha Allah zakiyi dogon zango a duniya kiyi hakuri kinji ko ita" "haihuwa haka take da sammatsi muna zuwa asibiti zasu taimaka miki.""" Girgiza kanta kawai take tana karanto sunayen Allah dari ba d'aya a zuciyarta. "Hajia tace""Yana da kyau aje a sanar da iyayenta halin da ake ciki."" Ya Ramlatu tace""Hakane bari nasa" "Dan Azimi ya buga musu kofa.""" Naja'atu riqe hannunta tayi tana girgiza mata kai magana takeso tayi amma bakinta yayi nauyi wani irin "ciwo mararta yake mata, Hajia Rabi ta riqeta a jikinta tana tofa mata Addua duk sun rasa yanda zasuyi ita ba miji ba ballantana a kirasa yazo ya dauketa yasa a mota. Cigaba sukayi dayi mata taimako irin na" "gida, cikin ikon Allah ta dinga wani irin yunkuri kamar wacce zata sake sabuwar haihuwa mahaifar ce ta" fad'o kafin wani uban jini ya biyo bayanta. Gabad'ayansu suka shiga godewa Allah dan ganin yanda ya gajarta musu wahala basu sha wahalar zuwa asibiti ba amma a zahirin gaskiya haihuwar tazo da tangard'a! amma dai tunda Allah ya raba lafiya sai su gode masa. Kafin gari ya waye komai yayi tsaf! Hajia Rabi da Yaya Ramlatu sun gyara maijego "da babynta mai kama da ubansa, dakin yayi tsaf dashi sai qamshin turaran wuta yakeyi Da Asubah" "Hajia ta sanar da Alhaji haihuwar ya dinga murna da farin ciki yana Allah Allah a idar da Sallar ya sanar da Mahaifin yarinyar, to shima Malam yayi farin ciki dajin cewa yarinyar shi ta haihu cikin koshin lafiya," cike da farin ciki ya shiga gida domin ya sanarwa da matarsa halin da ake ciki. Yaya Ramlatu itake tsaye a kan Naja'atu da yaronta dan da gari ya waye ma itace tayi wa yaron wanka ta shiryashi cikin kayan sanyi sannan ta kai Naja'atu toilet ta gasa mata jikinta sosai tasa ta ta zauna a cikin ruwan d'umi! Naja'atu ta dinga mamakin irin dawainiyar da Ramlatu keyi mata ko a mafarki bata ta'ba tunanin hakan na iya faruwa ba. "Kafin takwas na safe Naja'atu tasha gayu tayi kyau tamkar ba ita ba, Ya ramlatu ta taimaka mata ta" "shirya jikinta cikin wani Swiss les mai kyau! Hajia kuwa da kanta ta shiga kicin tayi mata abun kari na mussaman sannan ta zauna a kusa da ita sai data tabbatar da taci ta koshi tukkuna ta fita daga dakin Bayan kowa ya gama shige da ficensa a dakin, Naja'atu a hankali ta kai hannu inda yaron yake" "ta daukoshi ta riqe a hannunta, tsira masa ido tayi kawai tana kallonsa, yaron kamar sa daya da ubansa tamkar Bash yayi kaki! ya tofar, wasu irin hawaye ne masu zafi suka shiga zobo mata, wai yau itace ke dauke da d'an Bash a hannunta, ashe dai sai ta fara haifawa Bash d'a kafin ta haifawa Abbah Abbas, gabanta ne ya fad'i Data tuna irin kauce kaucen da Abbah Abbas din ke mata, to yanzu dai gashi ta haihu lafiya kome zai biyo baya oho! itakam idan Abbah bai mai da ita gidansa ba to tana jin ita da aure har" abadah! "Hawayen take sharewa wasu na sake kwararowa, cikin wannan halin ya shiga dakin ya sameta." "Bata san ma ya shigo ba sai qamshin turaransa ne ya sanar mata shigowar tasa, da sauri ta dago kanta" tana kallonsa suka tsirawa juna ido.........Dauke kansa yayi daga kallonta cikin nutsuwa ya zauna gefanta tare dasa hannunsa ya kar'bi yaron yana dubashi. Tausayinsa da tsantsar kaunarsa suka sake karya mata zuciya sai kawai ta dukufar da kanta ta cigaba da rera kuka wanda na rasa ko na menene! Abbah bakinsa yasa kunnan yaron dama da hagu yayi masa kiransa sallah sau uku sannan yasa masa kalmar shahada duk dai a kunnuwan nasa ya d'ago kanshi cikin nutsuwa ya tsirawa fuskar yaron ido Hausawa sukace labarin zuciya a tambayi fuska ni kaina a lokacin dana kalli fuskarsa sai dana "tausayawa masa, dan kallon fuskar yaron tasa yasa ya tuno da abubuwan da suka shud'e yana tunanin da Naja'atu na gidansa da tuni wannan yaron dake riqe a hannunsa nasa ne, kallon fuskar yaron tasa ya tuno da fuskar ubansa duk da sau daya ya ta'ba ganin Bash amma baya ta'ba tunanin zai mance" "kammaninsa," "Tamaza! yayi yayi saurin aro dauriya da jarumta ya kalleta tare da fad'in ""Sannu ina fatan babu abunda" "ke damunki.""! shuru tayi masa ta kasa magana saboda kukan da yaci karfinta" "Gyaran murya yayi a nutse ya kira sunanta."" Naja'atu."" Dago kanta tayi tana kallonsa hawaye na sake" "zubowa, ""Kukan me kikeyi bayan Allah ya sauke ki lafiya ai sai ki gode masa.""" "Murya na rawa tace""Abbah tausayin ka nake ji wallahi dan Allah ka gafarta min abunda nayi maka" "wallahi ban zubar maka da ciki ba."" Kawai sai ya tsaya yana kallonta, Kafin yayi murmushi ya dan sunkuyar da kansa yana nazarin maganarta, wai tausayi shi maganar ma dariya ta bashi" "Yace.""Cikina daya zube a jikinki dama haka Allah ya hukunta, maganar tausayi kuma ki daina nima na" "kusa samun k'aruwa ko baki da labarin amaryata nada ciki."" Yafad'a yana kallonta ido da ido" "Sai taga maganar tasa kamar akwai cin fuska a ciki, a sanyaye tace""Na sani Allah ya rabasu lafiya."" Ya" "amsa da ''ameen ya Allah Wane suna kike so a sakawa yaron ki.""Da sauri ta kalleshi, yace.""Eh inaso nayi masa hud'uba ne kafin na tashi." "Tace""Ko wane suna asa masa." """A'a kina da ikon ki za'bi sunan da kike so a saka masa dan haka ki duba dai." "Kai tsaye tace"" Kasa masa sunanka tunda a yanzu kai ka zame masa uba.""" "Girgiza kansa yayi yace.""Kece 'Yata shi wannan sai dai a kirasa da jika na, dan haka ba sunana ya kamata" "a saka masa ba na Malam za'asa masa ko kuma a saka masa sunan babansa Bashir.""" "Da sauri tace""Abbah dan Allah kada kasa masa sunan wannan mugun mutumin azzalimi wanda ya" "kwashe kayansa daga gaban ma'aiki, ni sunanka nakeso kawai kasa masa." "Yace.""Ki daina tsine masa kina kwashe masa albarka yana a matsayin uban danki sannan ita shiriya ta" Allah ce watakila Allah ya shiryeshi ya dawo ku daidaita kanku. Fad'ar wannan magana da yayi sai ta sake tunzura ta dinga zazzagin Bash din tana tsine masa albarka da fadin Sai dai ta mutu babu aure akan ta koma gidan Bash har da cewa insha Allahu ba zaiga annabi ba. Abbah da kyar ya sata tayi shuru a maimakon ta tsaya ta cigaba da sauraran nasihar da yake mata kawai sai ta kwanta ta juya masa baya zafafan hawaye na zubo mata Yaron ya ajiye mata a kusa da ita ya fita daga dakin yana mamakin al'amarin Kafin ya tafi harkokinsa "sai ya tsaya ta tambayi hajia ko da akwai abinda ake bukata, hajia ta fad'a masa duk abinda ake bukata yace insha Allahu zai turo yaronsa" Aikuwa wajejan sha biyu na rana Abdulhamid ya kawo uban naman rago gami da kaji gyararru da kayan tea da uban cefane mai yawa...........A take Hajia ta umarci Yaya Ramlatu data taimakwa Jummai mai aiki da suyi wa Naja'atu miya irin ta masu jego. Sai bayan la'asar iyalin Abbah Abbas suka sauka a gidan dukkaninsu har da yaran tinda washe garin "ranar haihuwar jumaa ce sun taso daga makaranta da wuri yaran sai murna sukeyi zasuje suga d'an jinjiri......To bayan sun gaisa da hajia kai tsaye dakin da maijego take suka nufa...Naja'atu da aunty Maryam suna hira sukaji sallamarsu, halisa kamar ba itaba ta karasa cikin dakin da faraa a tare da ita take fadin""Lallai haihuwa da lafiya abar alfahari ce gaskiya na taya ki murna naja'atu Allah ya raya ya" "baki lafiya.""" "Aunty maryam ta amsa da ameen tana miqa mata yaron, Halisa ta karba tana dariya kamar ba itaba suka" "gaisa da Aunty maryam din cikin sakin fuska, aunty maryam ta dinga mamakin al'amarin, Zainab kuwa sai dauke kai take tana ya mutsa fuska, aunty maryam tace ""Sannu uwar biyu kema ai kin kusa Allah dai" "ya raba lafiya.""" "A hankali ta amsa da ""Ameen."" Najaatu ta dan kalleta na minti biyu ta kau da kanta ta rasa me yasa" gabad'aya Zainab din ke bata haushi iyayinta shine abinda tafi tsana a tare da ita "Halisa ta gama duba yaron ta miqawa Zainab da fad'in ''Gashi ki daukeshi kema kisa albarka."" Zainab ta" "ya mutsa fuska da fad'in aunt Halisa bana iya daukarsa ni kai dai nasan abunda ke damuna Allah yasa masa albarka.""" Babu wanda yaji dadin abinda tayi ai ko yaya ne ta daukeshi koda kuwa bata jin dadin jikinta...Naja'atu taji haushi sosai sai dai ta bawa zuciyarta hakuri ta cigaba da amsawa Halisa maganar da suke. Su Saddiqa ne suka shigo dakin suna murmushi. "Aunty Maryam tace""Yawwa dama tun dazu 'kaninku yake neman ku da har yayi fushi na bashi hakuri.""" "Da sauri mussadiq ya karasa kusa da Halisa yana dariya yana leqa fuskar yaron, Halisa tace zauna nasa maka shi a jikinka." Ya zauna da sauri tasa masa yaron ya rungumeshi su Saddiqa na leqen fuskarsa! Aunty Maryam ta kalli "Mufida da fad'in ""Albishirin ku."" Mufida tace""Goro."" Aunty maryam na dariya tace""To dai yaro yaci sunan Abbanku dan sunan da mamansa ta za'ba masa kenan."" Ai gabad'aya sai yaran suka shiga murna da farin ciki Halisa na 'yar dariya tace""To ikon Allah ashe sunan maigida aka saka masa gaskiya dole na" "fito da kyau ranar suna."" Aunty Maryam ta dinga dariya tana fad'in ""Aikuwa hakan nada kyau." Zainab kamar ruwa ya cinyeta a dakin tayi d'if bakin ciki kamar ya kasheta jin wai sunan mjinta ta sakawa yaronta yasa ta sake jin wani sabon kishi na taso mata Gabadaya zaman dakin ne ya gundureta "mutukar zata waiwaya ta kalli Naja'atu shar da ita tana dariya da farin ciki to ji take kamar zata mutu saboda bakin ciki Miqewa kawai tayi ta kama hanya fita, dukkaninsu suka bita da kallo har ta futa babu" wanda yayi mata magana a cikinsu. To aunty maryam dai da Halisa ba yara bane dukkaninsu sun gane abinda ke damun yarinyar itama Naja'atun taso ta fahimci wani abu kawai ta share abun ne dan a zauna lafiya amma zahirin gaskiya irin halin ko in kulan da Zainab ke nuna mata yana yi mata ciwo. "Zainab falo ta fito ta zauna ita kadai abun duniya ya isheta, ita kuwa Yaya Ramlatu sai shige da fuce" takeyi a tsakanin Dakin maijego da kicin tana sakin habaici ga Zainab din( mai hali baya fasa halinsa "hausawa suka ce idan ka kwana biyu ba kaga mutum ba to kana ganinsa ka fara tambayarsa halinsa) Zainab muzanta tayi kwarai da gaske sai ta shiga data sanin fitowa falon , sunkuyar da kanta tayi kuka na" kokarin kufce mata. Yaya Ramlatu bata qyale Zainab ta sarara ba sai da taga hajia ta sakko tukkuna ta rabu da ita. Har yamma suna gidan aunty maryam kuwa ganin yamma tayi yasa tayi musu sallama ta tafi gidanta. Halisa da Zainab suka zauna jiran zuwan mijinsu domin haka yace su zauna su jirashi idan yazo sai su tafi tare. Daf da magariba Abbah da Abbah magaji suka shiga gidan Alhajin Abbah Abbas da "kansa ya jagoranci Abokin nasa har dakin da maijegon take ya shiga ya duba yaro da mamansa, Naja'atu kasa hada ido tayi dashi sabida kunya kuma tayi mamakin yanda ya dauki yaron nata yayi masa addua sosai, ta dinga jin wani iri a jikinta tana tuno irin rashin arzikin da dinga yi musu a lokacin auranta da" Bash! tana can tunanin abinda ya shud'e suka fita daga dakin ba tare da ta sani ba. *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar karantawa ga yanda abin yake. p gruop#600 normal group #300 account... 0542382124....Binta umar gtbank. Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* "Takwara nima ina bayanki gaskiya abun na Abbah Abbas yayi yawa, haba yace shi ba mayar da ita zaiyi" ba to me yasa yake damun kansa a kan al'amuranta hidimar tayi yawa kuma Zainab macace dole tayi kishi tunda halak ne! itama Halisa ruwa ne ya daki babban zakara shiyasa tayi sanyi......gaskiya Zainab da Halisa suna da hakuri Nafisat maganarki haka take Najaatu dawa ta dogara da har takewa wata al'kawarin zata bata jari Kawai ta samu mutum sai tatikeshi take koda yake ai yace saboda Allah da Annabi yake mata hidima! hummm! to maji ma gani dai wai an bunne tsuhowa da ranta *MADADI* 72*****Naja'atu sai wajajen tara na dare da samu sukunin kiran wayar su Mmn Sajida ta fad'a musu ta "haihu! Mmn Sajida kamar ta fasa wayar dan murna a gurguje ta shiga gidan Mmn Ladi ta sheda mata, Mmn Ladi na murna da farin ciki ta kar'bi wayar tana mata barka tare da fatan Allah ya raya abunda aka samu Sun juma suna hira da juna kafin tayi musu sallama cike da jin kaunarsu a cikin ranta. To a" takaice dai Sai da Naja'atu ta kwana uku da haihuwa tukkuna Baba Talatu tazo ta duba taga abinda ta haifa daukar "yaron tayi tai masa addua daidai gwargwado tabbas komai qinka da abu idan Allah ya qaddara faruwarsa babu yanda za'akayi, babu shakka rabon wannan yaro ne ya raba auran *MADADIN* da suka daura amma suna fatan Allah ya mayar dashi da alkairi...............Bayan ta gama zancan zucci da take sai ta kalli Naja'atun a nutse tace"" 'Dazu Magaji yake fad'a min cewar wai kin za'bawa yaro suna hakane ko.""? A sanyaye tace""Eh Baba nace ayi masa hud'uba da sunan Abbah Abbas dan ganin yanda yake hidima nasan babu abinda zanyi na biya shi dawainiyar da yake dani amma hausawa na cewa yaba kyauta tukwici a" "ganina sunansa yafi cancanta a sakawa yaron.""" "Baba Talatu tace""Lallai kinyi tunani mai kyau Naja'atu kuma nayi farin ciki sosai da wannan yaro yaci" "sunan Alhaji Abbas ina rokon Allah yasa ya gaji irin halinsa."" Kanta a 'kasa ta amsa da ameen ya Allah."" Baba malam ma da yaji sunan da Naja'atu ta za'bawa yaron yaji dadi sosai saboda haka" A daran ranar da Baba Talatu ta fad'a masa maganar ya aika aka dauko masa yaron yayi masa hud'uba da sunan Abbas kamar yanda Naja'atun ta buqata.. 'Bangaran Abbah Abbas kuwa koda ya samu labarin anyiwa yaro huduba da sunansa beyi mamaki ba saboda dama kafin hakan ta kasance sunyi maganar da ita kawai sai yayi fatan alkairi tare da yiwa yaron adduar shiriya maidaiciya. Washe garin ranar yana zuwa Kasuwa ya kira Abdulhamid ya umarce shi "daya shiga kasuwa ya had'o kayan baby duk wani abu da yasan masu haihuwa na bukata ya siyo idan ma bai gane ba yayi tambaya a gurin yace a hada masa set biyu, yana nufin dana Naja'atu dana Zainab duk da ita bata haihu ba yana ganin idan ya siya ya huta tunda itama a kan hanya take cikinta yanzu yana" wata bakwai. "Abudulhamid ya nufi kasuwar wambai dama dan wajejen ne, kai tsaye gurin masu siyar da kayan bebis" "ya nufa, yace a had'a masa kayan jarirai. Mutumin ya tambayashi namiji ko mace.""" "Da sauri ya dauko wayarsa ya kira Abbah Abbas din ya tambayeshi, yace A had'a na maza duka duk da" bawai amincewa yayi da scanning din Zainab ba yasan hasashe ne abun bai zama lallai ta haifi Namiji ba kamar yanda suka fad'a! ya dai siya kawai idan mace ta haifa ya sake siyan wasu. Sannan yace masa ya wuce da kayan gida ya kai b'angaran Zainab zai kirata a waya ya fad'a mata. Tsaf aka had'a kaya saiti biyu iri daya Abdulhamid ya shiryasu a mota ya nufi gidan Ubangidan nasa Abbah na gama waya da Abdulhamid ya kira Zainab ya fada mata cewar Abdulhamid zai zo da kayan jarirai sai ta za'bi wanda take so ta barwa Naja'atu nata. Zainab ta rasa inda maganarsa ta dosa sai kawai ta amsa da to sukayi sallama. Abdulhamid yazo ya jibge mata kaya a bakin gate din gurinta bayan fitarsa ta tsirawa kayan ido ikon "Allah komai iri d'aya komai biyu sai kace kayan tagwaye sai ta shiga zargin anya kuwa ba shine uban yaron ba, to idan ba hakaba ya za'ayi ya dinga daidaitashi da d'ansa." "Kamar za tayi kuka ta nufi gurin Halisa, taje ta tattagota suka zo suka tsaya a gaban kayan suna" "kallo. Halisa ta sauke ajiyar zuciya tana dudduba kayan tace"" Saura ragon suna shine kawai abunda ya" "rage amma wannan hidima tayi yawa, ni kam banta'ba ganin mutum mara zuciya irin Abban Mufida ba wallahi."" Yanda ta fadi maganar zaka fahimci a fusace take, dan duk abinda yake akan Naja'atun bai ta'ba qular da ita irin yau ba, haka kawai saboda rashin zuciya ya dinga daukar yaro yana daidaitashi da" nasa gaskiya abunda yake yayi yawa wallahi "Zainab kuwa fashewa tayi da kuka da fad'in ""Kin san Allah aunty Halisa hakuri na ya kusa 'karewa nifa ba" "zan iya jurar wannan wulakancin ba wallahi!...Yama za'ayi ya dinga daidaita ta damu muna a matsayin matayensa komai zaiyi mana sai yayi mata ke wata hidimar ma da yake mata bayayi mana, ba dole muyi zargin akwai wani abu qasa ba ni wallahi bana son namiji munafiki ki duba kiga kwanaki yanda ya fitittuke yana kokarin ci mana mutunci a kanta ina dalili wallahi bazan zauna hawan jini ya kama ni ba.""" Zainab na kuka ta qarashe maganarta. "Halisa tace""A'a Zainab kibi hankali kusan wata takwas kina zaune da mutumin nan amma har yanzu kin" "kasa gane halinsa Abbahn Mufida idan yasa kansa abu babu wanda ya isa ya hanashi, kuma wallahi ki iya bakinki rashin kunya babu inda zata kai ki ki kyaleshi kawai muga iya gudun ruwansa ai shi dai da bakinsa yace ba dawo da ita zaiyi ba to duk ranar da yazo mana da maganar zai dawo da ita mu kuma a ranar zamu mayar masa da martani Sannan ki daina sakar masa fuska nima zai daina ganin walwalata kwana" biyu haba abun ya wuce gona da iri kawai saboda yaga munyi masa shuru sai ya dinga yi mana abunda "yaga dama.""" "Zainab tace""Nifa aunty Halisa ban iya 'boye abu a raina ba shiyasa ko gidanmu sukeyi min kallon mara" kunya a gaskiya idan ba'a nan din ba to babu a inda za'a dinga cimin fuska na haqura ki duba kiga "wannan aikin dan Allah kawai an kama an siyo min kayan haihuwa da wata mtssw!."" takarashe maganar" tare da jan tsaki. "Halisa ta'be bakinta tayi tace""Allah y kyauta na fad'a miki ba tsayayya zakiyi masa ba ki 'bullo masa ta" "bayan gida idan kika ce zakiyi masa rashin kunya duk abin arzikin da yake da mahaifinki bai hanashi ya kora ki gida ba.""" "Zainab jikinta yayi sanyi jin maganar da Halisa tayi, gaskiya tana jin tsoron faruwar hakan saboda tasan" "halin mahaifinta bashi da wasa idan ma yaji kan abinda take rigima a kai zai iya hukuntata, tana ganin zata 'bullo masa ta bayan gida kamar yanda Halisa ta bata shawara. Wuce wa tayi ta bar gurin ba tare data ta'ba komai a cikin kayan ba............Hasken solar daya haske harabar gidan nasa baisa ya lura da kayan dake gibge a guri guda ba, kasancewar girkin Halisa ne sai ya nufi gurin zainab din ya gurguje" domin ya dubata. .A kwance ya sameta a dakinta yara suna falo su kadai Yayi mamakin hakan kasance duk dare tana zama tare da yaran a falo har sai ya shigo gidan ita kuwa Zainab tana jin shigowarsa dakin sai ta shiga baccin karya yayi ta kiran sunanta tana ji taqi "magana, kawai sai ya qyaleta da tunanin anjima kafin ya kwanta ya sake shigowa ya dubata watakila lokacin ta tashi." "To koda ya shiga gurin Halisan ma bai samu tar'ba mai kyau ba, ta bashi abinci amma bata zauna ta bari" "ya gama ci ba ta bar gurin...Zuwa tayi ta kwanta ta bacci ya dauketa. Abbah bai kawo komai a ranshi ba," "daya gama dube dubensa a loptop kamar yanda ya saba sai ya sake komawa gurin Zainab din nan ya tarar har ta kulle kofar falon daga ciki kamar tasan zai dawo, kasa hakuri yayi yana tsaye a gurun ya kira wayarta lokacin bata kwanta ba kuma bata kashe wayar ba amma tana kallo yana kira bata daga ba."" Girgiza kansa yay ya kama hanya da niyyar barin gurin yana nazarin wani abu a cikin zuciyarsa. Cin" karo yayi da abu yayi saurin kuna hasken wayarsa yana dubawa. Ya kai minti biyar yana nazarin kayan kafin ya gane kayan daya sa Abdulhamid ya kawo ne! to meye amfanin barinsu a waje? tambayar kansa yake! wannan ya nuna masa cewar Zainab duk abinda tayi masa a yanzu tana da manufa! takaici al'amarin yasa shi jan karamin tsaki ya bar gurin tare da tunanin halin quruciyar yarinyar yasan dai duk abunda takeyi akan Naja'atu take yinsa. "To al'amarin su Halisa fa ya tsananta kwana biyu sun had'e masa kai babu wacce ke sakar masa fuska," "tun abun na bashi dariya da mamaki har ya dawo bashi haushi! daya gaji da bibiyarsu sai shima ya dauke musu wuta ya shiga sabgarsa da yaran sa idan ya dawo gida yayi abinda zaiyi ya shige dakinsa ya kwanta ba wacce yake cin abincinta, kayan jirajirai kuwa daya fahimci akansu suke jin haushi, sai ya sake qudurtar kuntata musu bai dauki kayan ya kai gidan Alhajin ba sai da yasa aka kawo masa manya manya atampopi guda uku da legos less masu tsada biyu sai wani boyel mai uban kyau da tsada da saitin takalmi da jakarsa, a falon Zainab ya ajiye kayan sabida yasan dole zata kira Halisa ta gani, aikuwa a ranar kasa komai sukayi a gidan kowacce al'amarin yafi karfinta! wato fushin da suke yi ma kamar tunzurashi suke. Zainab cutar karya ta kirkira ta dinga kuka tana lanjarewa darajar abinda yake cikinta" ya kulata..Ita kuwa Halisa shareta yayi ya daina shiga sabgarta. Ranar suna da sassafe ya dauki yaransa "ya kaisu gidan yayi tafiyarsa sabgarsa, Halisa taga al'amarin na nema ya zama babba sai ta shirya tsaf da" turaman atamfofinta guda biyu ta nufi gidan Alhajin...Ita kuwa Zainab cewa tayi babu inda za taje bata da lafiya. Halisa bata saurareta ba ta tafi tare da daukar alkawarin bashi hakuri dangane da abunda sukayi masa........... *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya ga yanda abin yake Vip group #600 normal group #300 account... 0542382124...Binta umar gtbank. Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *BA HARAM BANE!* 73****To alhamdullilahi duk wani abunda ake bukatar ayiwa mai haihuwa Abbah Abbas da iyayensa "sunyiwa Naja'atu sun tsaya a kanta sun mata gata fiye da wacce take da miji anyi suna cikin walwala da farin ciki Naja'atu har kuka tayi a ranar sunan ganin yanda kowa yake nuna mata kauna ita da d'anta, a gaskiya kafin samun mutane masu karamci irinsu Alhaji da Hajia sai an bincika, dama kuma barewa ba za tayi gudu danta yayi rarrafe ba, babu shakka Abbah Abbas shine zai zama magajinsu dan gabad'aya shine yake kwatanta hallayar iyayen nasa Abbah Abbas kwata kwata abin duniya bai rufe masa ido ba" "shi har so yake ma mutum yazo neman abu a gurinsa ya dauka ya bashi, a kasuwa kuwa bai san iya" "adadin mutanan daya yafewa bashika ba, shiyasa gashinan kullum Allah qara daukaka darajarsa yake" yana samun addua ta kowane bangare. "Halisa jiki a sanyaye ta dawo gida tana ta mamakin yanda al'amura suke kasancewa, mijinta ya siyawa" "mejego raguna biyu manya manya sannan ya siyi wanda akayi miyar suna duk a bakin Ramlatu take jin maganar, hakikanin gaskiya jikinta yayi sanyi da irin qaunar da yakewa yarinyar tana ganin dawo da ita gidansa shine yafi masa alkairi sai kawai ta yanke shawarar watsar da makamanta za ta kuma tunkareshi" da maganar Naja'atun taji mai zai sake cewa. "Ranar dama itace take da girki ta fito falo ta sameshi yana abunda ya saba, da kyar ya saurareta dan har" "yanzu haushin abinda sukai masa yake ji Yace.""Ai kin bani mamaki Halisa ina tunanin kece ta farkon" "wacce zata fadawa wani halina, meye a cikin abubuwan da nakewa Najaatu da duk zaku tayar da hankalin ku akai har kuna had'e min kai saboda baku da hankali! to inaso na tuna miki abunda kika manta, Naja'atu bata da wanda ya fini tunda tun tana shekara hudu take a hannuna nine na rainata tana riqe ta tamkar 'yar dana haifa a cikina ni ta sani duk wani nauyi nata yana kaina, koda iyayenta nada halin daukar d:awainiyarta to bazan bari ba saboda tun farko sun dauke ta sun bani ita, wannan dalilin ya sanya nake kokarin ganin na sauke nauyin amanarta dake kaina, duk ki ture ta wasu abubuwan da suka faru a tsakanina da ita, ni ba mutum ne me riqe abu a cikin ransa ba, da ina da wannan d'abiar to na tabbata ba zan kalli inda take ba, ballantana na 'batar da kwabona a kanta, sannan idan banda abunku ai Najaatu abar ku tausaya mata ne duba da halin da take ciki menene abin ganin k'yashi da kishi" "dan na taimaka mata.""?" "Halisa tace""Duk naji bayanan ka amma dai kasan kishi halak ne ko.? Shuru yay yana kallonta ta cigaba" "da cewa""Nifa wallahi idan zaka dafa al'kur'ani ba zan yarda cewar baka son yarinyar nan ba."" 'Bata fuska yay yana dan harararta Tace""Ai gaskiya ce abunda kakeyi yay yawa haba kowa ya d'ora zarginsa akanka nasan ita kanta yarinyar tana ji a jikinta ko zaka mayar da ita gidanka ne, dan haka nima wallahi nafi" sha'awar ka dawo da ita dani da kai da ita Zainab din dukkaninmu sai hankalinmu yafi kwanciya "Ya jima kafin yay magana yace""Na fad'a muku ni ba zan dawo da Najaatu gidana ba amma kun'ki yarda" "da maganata, magana ce mukeyi a kan cikinta da haihuwarta to tinda Allah yasa ta haihu lafiya ai abunda ake bukata kenan daga haka kuma me zai sake shiga tsakanina da ita idan ba gaisuwa ba, amma tunda na lura zama ku biyu ne bakwaso zan fara neman aure shikkenan sai hankalinku ya kwanta." "Murmushin takaici tayi tace""Ba sabon aure ya kamata kayi ba Najaatu ya kamata ka dawo da ita dan" "wallahi ko sabon auran kayi ba zaka samun nutsuwar da kake bukata.""" "Yace.""Haka dai kike gani ni Najaatu bata gabana wallahi kune dai kawai kuke zargina akanta zaku" "wahalar da kanku ne a banza."" Yana gama maganarsa ya cigaba da duba laptop din gabansa. Halisa" "takaici yasa ta bar gurin, kwanciya taje tayi tana tunanin maganganunsa itafa ba yarinya bace ballantana ya raina mata hankali." "Tunda akayi suna ya daina zuwa gidan da safe, ya dawo zuwa da yamma kamar yanda ya saba kuma" babu ruwansa da shiga sabgar Najaatu gaisuwa ce kawai take had'ashi da ita yay abunda ya kawoshi ya "tafi, ba Najaatun ba su kansu su hajia sai da suka fuskanci sauyawarsa sai duk jikinsu yayi sanyi kada fa yay musu bazata ya nuna musu abunda suke zargi ba haka bane a gurinsa." *BASH!* "Abunda sukeyi dashi da abokansa ya wuce tunanin masu tunani, yanzu harkar siyar da hodar ibilis suke" "da turawan america, Bash ya had'a kansa da manya manya yahudawa suna ta aikin sa'bo! Yayi masifar kudi irin wanda yake b'ukata gabad'aya idan kun ka ganshi ba zaku ganeshi ba saboda dukkanin kammaninsa sun sanja ya samu duniya sosai duniya tasan da zamansa kuma abokanansa sunaji dashi saboda yana brain sosai yana kawo musu cigaba a cikin harkokin da sukeyi a 'boye. to hausawa" "sukace rana dubu ta barawo rana guda ta me kaya Ranar Asabar Allah yay nufi tona musu asiri sun shirya shida abokanasa suka nufi Cameroon domin shigar da musu da kayan sana'ar tasu, lafiya lau suka sauka a filin jirgin garin suka soma saukowa kowa na goye da wata katuwar jaka a bayansa, wani ma'aikaci ya dakatar dasu, yace su ajiye jakkunan dake bayansu, cikin turanci Bash yace idan zaiyi bunkice a kansu yayi su ba zasu ajiye jakarsu ba, mutumin sabon ma'aikaci ne mai aiki domin kishin qasarsa, kawai yace azo a tafi dasu tunda sun sa gaddama sunqi suyi abunda ake bukata suyi Jin haka" da sukayi kawai sai Bash yayi dubarar dauko k'aramar bundiga dake cikin jakar bayansa ya harbi ma'aikacin nan a gwiwa kafin kice kwabo guri ya hautsine! ganin haka yasa da saurin gaske shima ya "saita kafafun Bash din ya harbi daya Bash ya zube a gurin yana ihu hade da riqe kafarsa data jiqe da jini," abokansa suka nemi hanyar tserewa Jami'an tsaron da suka iso gurin suka damqe su. sai da sojoji "sukayi bunkice sosai a gurin kafin su bari kowa ya fita daga airport din, tashin hankali su Bash suka raina kansu lokacin da jamian tsaro suka ga abubuwan dake cikin jakkunansu, tun a airport din suka fara jibgarsu kafin su sasu a mota su tafi dasu.......tsayin sati guda suna binkice a kansu kafin su san kasar da kowanne daga cikin su ya fito, jamian tsaro na kasar Cameroon sun samu cikakken bayani akansu Bash cewar mugwayen 'Yan taaddah! ne wanda suka addabi mutane da gomnati dama kullum cikin bukince ake a kansu da abubuwan da suke aikatawa tunda Allah yasa yanzu suna hannu sai a yanke musu" "hukuncin daya dace. Koto aka shiga dasu, alqali yaji ya kuma tabbatar da dukkanin abunda ake" zarginsu dashi tsabar wahala yasa dukkaninsu basu karyata ba sabida sun riga sun saddaqar da cewa karshensu ne yazo A take mai girma mai sharia ya yanke musu hukuncin kisa domin barinsu a doron duniya had'ari ne hukuncin da aka yankewa su Bash babu wanda bai sa farin ciki ba lokacin ne 'yan jarida suka samu aikin yi suka dinga daukar hotonan su da muryoyinsu Allah Sarki Bash sunkuyar da "kansa kawai yake yana hawayen nadama, dan da wani dan Jarida yazo yana masa tambayoyi kasa magana yay ya dago kansa kawai hawaye na zuba a kumatunsa magana biyu kacal ya iya fad'a. ""Iyayane sune silar lalacewata babu abunda zance musu sai dai nace zamu hadu a gaban Allah." "Magana ta karshe da zanyi a kan wata yarinya ne dana yaudara sunanta Najaatu Ina fatan maganar nan da na keyi tana ji kuma tana kallonta, Najaatu ina rokon ki daki yafe min abunda nayi miki ba ke kadai bama da duk wanda na zalinta ina rokonsa ya yafe min ni tawa takare a duniya."" Sai kawai yayi qasa da" kansa hawaye na cigaba da zubowa daga idansa Lokacin da labarin abunda ya faru ya isa kunnan iyayen Bash sun shiga tsananin tashin hankali da "nadamar abunda suka aikata, dan jin bayanin da Bash yayi yasa jamaar gari sun sake gazgata maganar dama kowa yana tunanin sune suka dorashi a kan hanyar banza gashi yanzu sunzo suna nadama, 'Yan jarida kuwa ai kewaye Alhaji Aminu sukayi wai lallai sai yayi musu qarin bayani dangane da jawabin da" Bash din yayi kafin mutuwarsa. Najaatu kuwa al'amarin yayi masifar d'aga mata hankali tayi kuka sosai tayi nadamar rayuwa hajia "kasa gane kanta tayi a gidan, sai da ta dinga yi mata nasiha gami da kawo mata misalai sannan ta daina kukan da takeyi ammafa kullum da daddare sai ta rungume 'Danta taci kukanta ta koshi!! sannan take jin sassauci bata ta'ba tunanin zata auri Mutum mai miyagun halaye ba sai gashi ta auri bash wanda ya tara munanan halaye harda albarka haihuwa a tsakaninsu hakika ta tabbata wannan al'amarin da ya faru da rayuwarta qaddarace dan da tasan abinda zai faru kenan da bata bujirewa auran da iyayenta sukayi mata ba, A duk sanda zata kalli fuskar d'anta ji take zuciyarta na karaya ta dinga tunanin halin da zai shiga idan ya girma yaji labarin ta'addacin da ubansa ya aikata kafin a kashe shi, wannan tunanin yasa ta dinga wata iriyar rama kafin tayi ar'bain duk ta fige kullum cikin tunani da nazarin yaya rayuwar d'anta zata tashi take. tunda wanda take tunanin zai tallafeta shima ya daina sakar mata fuska ya nunawa duniya cewa ba zai mayar da ita ba dan yanda yake nuna mata halin ko'in kula yasa kowa ya fahimci munufarsa ita dashi gaisuwa ce kawai ke had'a su watarana har yazo gidan ya tafi bata sani ba, dan zaman daki ta aura yanzu tafi so ta kadaice ita kadai tayi tunanin abinda zai fishsheta. Allah Sarki" "Ramlatu itace ke hidima da (Daddy) sunan da suke kiran yaron dashi kenan, Tayi masa wanka ta shiryashi ta goya shi a bayanta mutukar kinga yaron a hannun uwarsa to nono zai sha, Najaatu tana jin" dadin yanda Ya Ramlatu da sauran mutan gidan ke nuna kulawarsu a kan yaronta To haka rayuwa ta cigaba da tafiya yau fari gobe baki Najaatu nata hakuri da halin ko'in kulan da Abbah "Abbas ke nuna mata, ita abun sai ya dinga bata mamaki ya damu da d'anta amma ita kallo bata isheshi ba ko gaishe shi tayi baya kallonta yake amsawa amma wani sa'in idan yazo za taji shi suna maganar Daddy da Yaya Ramlatu wani lokacin ma har daukar yaron yake yay masa wasa kafin ya tafi. sai tayi ta mamakin al'amarin wallahi ita ta dauka dukkanin irin kulawar da yake nuna mata a baya yana so ta" haihu ne ya mayar da ita sai gashi ya juya mata baya lokaci guda ko kallonta ma baya yi. "Yau kwanan ta sittin da uku da haihuwa, hankalinta gabad'aya yana kansu Mmn Sajida dan kullum sai" sunyi waya ita Mmn Sajida har fushi tayi saboda dukkaninsu suna lissafe da kwanakin haihuwarta tace saboda taga suna so su ganta da abunda ta haifa shiyasa take ja musu rai shikkenan zasu cireta daga rayuwarsu kamar yanda ta watsar dasu. "Wannan maganar da mmn sajida tayi ta tayar mata da hankali sosai taji tana sha'awar zuwa gurinsu, sai" ta yanke shawarar sanar da Abbah Abbas din domin taji me zaice akan tafiyar. Lokacin data kira wayarsa yana tare da Zainab da cikinta ya tsufa dan kamar ma naquda take a tsaitsaye dan dai haihuwar fari ce shiyasa basu gane ba amma dai bata da cikakkiyar lafiya. Zainab ta dauki "wayar tana dubawa, My dota ta gani na yawo a fuskar wayar, tasan Najaatu ce sai tace""Abbah Mufida Najaatu na kiran wayarka. Domin ya sake nuna mata babu wata alaqa a tsakaninsa da ita yace ""Dauka" "mana."" Da sauri ta daga wayar tana sallama, Najaatu taji rashin dadin jin muryar Zainab sai dai ta daure" "tace""Dan Allah ki bawa Abbah wayar zanyi magana dashi." "Zainab tace""Kada ki damu shine yace na dauka ina sauraranki."" Najaatu taji kanta ya sara! da kyar" "tace""Aa ki dai bashi wayar."" Zainab murmushi tayi cikin sigar kuntatawa tace""Wallahi da gaske nake miki gashi ma yana kimtsawa zai fita kuma da umarninsa nake magana dake ki fad'i maganarki dani dashi duk daya ne."" Najaatu ta dinga jin kamar ba'a guri guda take ba dan wani irin jiri ne ya shiga d'ibanta, sai kawai ta kashe wayar ta jefar da ita lafiyayyun hawaye suka shiga zobowa a kumatunta, wannan wulakanci dame yay kama? Lallai Abbah Na shirin ya dasa mata ciwo a cikin zuciyarta, ashe bai san yanda take bala'in jin kishin matarsa ba zai ce ta daga mata waya aikuwa ba zata qara kiransa ba, kuma" tafiyarta zatayi tunda dama ba zamansa take ba Sai da taci kunanta ta qoshi tukkuna taje ta sanar da hajia maganar zuwa jos din Hajia tace'' Hakan yana da kyau sai ta fara shiri. Bangaransa kuwa koda ya gama shirinsa bai tambayi zainab komai ba tunda hands free wayar take duk "yaji komai ya kar'bi wayarsa yayi tafiyarsa harkokinsa, ita kuwa Zainab a ranar yini tayi cikin farin ciki da annushuwa dan duk ciwo ciwon da take ji a jikinta daina ji tayi sabida abunda tayiwa Najaatu na" quntatawa kuma taji dadin yanda ya bata goyon baya d'ari bisa d'ari. "Bayan kwana uku Naja'atu ta shirya kayanta tsaf hajia ta shirya mata tsaraba mai yawa, tace ta kai musu" "domin sun cancanci abinda yafi haka, a ranar da zata tafi ta shiga gidan Baba Malam da wurwuri tayi musu sallama itama Baba Talatu ta bata abubuwan tsaraba tace ta kai musu, sannan tayi mata fatan" dawowa lafiya. "Sai da zata tafi hajia tace""Kinga ikon Allah ko na sha'afa wallahi duk zuwan da Abbansu Saddiqa keyi ban" "fada masa ba ko kin kirashi a waya ne.""? Da sauri tace""Eh shekaran jiya na fada masa."" Hajia tace""To" shikkenan dama dan dai kada ya samu labarin tafiyar daga baya ne yasa nayi maganar to Allah ya saukeku lafiya a gaishe mana dasu da kyau. Naja'atu tace zasuji insha Allahu Hajia. Tare suka fito harabar gidan suna tsaye suna kallonta ta shiga mota direba yaja suka fita daga gidan Abbah Abbas lokacin daya samu labarin tafiyar ranshi yayi "masifar 'baci! ya za'ayi saboda rashin hankali ta dauki yaro karami a lokacin sanyi tayi tafiya mai tsayi dashi, shifa gabad'aya garin jos bai masa ba shiyasa bai ta'ba yi mata zancan zuwa ba, ashe jira take ta haihu ta dauki kafa ta tafi ba tare da ta sanar masa ba(Matarka ce ita da zata tsaya fad'a maka ) Hajia ta dinga tausarsa da fadin ita bata san bai sani ba wallahi amma ai ba wani abu bane dan taje ta nunawa mutanan abunda ta haifa saboda sun cancanci hakan Yace.""Hajia ba hana zuwa anyi ba a qalla dai ta" "bari yaron bayanta yayi kwari ki duba kiga yanda ake busa iska a gari tana iya zuwa da yaron ya samu wata matsalar yanayin gidan da zataje bashi da kyau da tsayin katanga akwai matsala sosai."" Hajia ta dinga mamakin maganarsa tace""To ai lalura a ko'ina ma daukarta akeyi kuma ta tafi da kayan sanyi" nasan zata kula dashi. "Shuru kawai yay ya miqe tare da fadin shi zai tafi.Hajia tace to a sauka lafiya, hanyar futa ya kama ta" bishi da kallo tana mamakin son 'ya'yansa. "Kasa hakuri yay yana driving ya shiga kiran wayarta, lokacin har ta sauka tana tare dasu Mmn Sajida sai" "gaishe da juna sukeyi, su Walid da 'Ya'yan Mmn Ladi sun kewayeta tana ta basu tsarabar da taje musu da ita." "Koda ta duba wayar taga number sa ce sai ta cigaba da abunda takeyi, taki dauka sai da ya kira sau uku" "tukkuna ta daga, tana kokarin gaisheshi ya dakatar da ita. ""Ashe baki da hankali Najaatu wa kika" "tambaya wanda ya baki izinin tafiya wani gari? ashe kina nan da halinki na taurin kai ko.""" "Kai tsaye tace""Abbah yi hakuri dan Allah kwana hudu da suka wuce na kira wayarka na tambayaka sai" "dai idan mantawa kayi.""" "Yace.""Ke bana son karya yaushe kika kira ni kika tambaye ni ai saboda kin san bazan bari ba shiyasa kika" "'ki sanar dani."" (Takwara zo kiga karfin hali Tace""Wallahi na kira wayarka Zainab ta dauka kuma na fad'a mata maganar sai dai idan itace bata fad'a maka ba.""" "Shuru yay yana tunanin maganar. "" To Gobe Dan Azimi zai zo ya dauke ki dan haka duk wanda kika" "san zaki gaisa dashi a garin kiyi kokarin gaisawa dashi kafin gobe."" Yana gama maganarsa ya kashe wayarsa.........." *Littafin na kudi ne...!* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abun yake Vip group #600 normal group #300 account... 0542382124....Binta umar gtbank...idan katim waya zaki tura kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* _Abbah Abbas ka janyo 'yan group yau na caccakar ka Mum Basma tace idan ka tsaya kallon ruwa "kwado zaiyi maka kafa, ita kuma Sakina tace"" Kana ruwa sistar Habiba tace Dantalle ya shigo kawai" ayi dashi tunda kai ka tsaya wasa! To nima dai nace ka ajiye makaman ka dan idan ka tsaya jan aji za'ayi maka shigar sauri Najaatu dai a yanzu allura cikin ruwa ce (mai rabo ka dauka)_ *MADADI74* "Najaatu shuru kawai tayi tana bin wayar da kallo, mamakin maganarsa take wai zai turo Dan Azimi gobe" ya dauketa lallai aikuwa yanda yazo haka zai koma domin kuwa bata tunanin zata bishi to wai nauyin waye a kanta da zaice lallai sai ta dawo gida me za tayi masa bayan baya kulata sannan kullum yana tare da iyalinsa ita kuma sai ya hanata zuwa inda zata ji sassauci zuwanta gidan Mmn Sajida ya saukar mata "da nutsuwar zuciya ko babu komai zatai kwana biyu bata saka shi a idonta ba, domin watarana ganinsa" yana janyo mata abubuwa da dama hakuri kawai takeyi tana bin rayuwa a yanda tazo mata. "Mmn Sajida ta kalleta a sanyaye tace""Najaatu naga jikinki yay sanyi ashe ba'a sani ba kika zo.''? Kallonta" "tayi tace""Waye ya fad'a miki haka.""? Kai tsaye tace""Gashinan mahaifinki ya kira waya yana miki fad'a."" Mmn Ladi tace""Eh ai nima shiyasa kika ga jikina yay sanyi wallahi." "Najaatu murmushi tayi a nutse tace""Wai ku waye ya fad'a muku Abbah Abbas mahaifina ne.""? bude baki" "sukayi suna kallonta, ta sunkuyar da kanta tana dan murmushi wanda ya tsaya iyakacin lebenta." "Mmn Sajida tace ''To idan bashi ya haife ki ba waye shi a cikin rayuwarki.""? Tana girgiza kanta tace""Shine" mijina na fari wanda na baku labarinsa farkon zuwana garin nan. "Suka tsira mata ido suna mamakin maganarta, kwallah ta cika mata ido tace""Kuna mamaki ko? ni kaina" "ina mamakin kyautayi da tausayi da kyautatawa irin nasa dukkanin irin abubuwan da nayi masa bai sa ya watsar dani da al'amurana ba, yana tsaye a kaina da dukkanin bukatuna."" Mmn Sajida tace""Lallai Najaatu kin tafka babban kuskure a baya waye ya fada miki ana samun nagartattun mutane irin wannan mutumin? yanzu dama a kan an aura miki shi kika gudo garin nan yanzu dan Allah meye aibunsa meye kuma abun'ki a tattare dashi.""? Tana kuka tace""qaddara Mmn Sajida qaddarar wannan yaron dake hannuna ce ta kawo ni garin nan har na had'u daku Wallahi har bana so na tuno abubuwan da suka" "faru a baya Mmn Sajida ni da kaina nasan na tafka kuskure babba! wanda yanzu nake nadamar aikatashi, yanzu gashi inaji ina gani Abbah yafi karfina sai dai na kalleshi da ido Mmn Sajida a yanzu ne nake masifar so nayi zaman aure dashi shi kuma yana nuna baya so, wallahi bansan iya adadain son da nake masa ba a cikin zuciyata saboda mutumin ya cancanci a soshi duk wata sadaukarwa yayi min yana kanyi min babu namijin da zan aura na samu nutsuwar da nake bukata, Mmn Sajida ba zan 'boye muku halin dana ke ciki ba wallahi saboda halin ko in kula da yake nuna min yasa naji zaman garin ya gundureni na" "tattaro na tawo nan kuma bana tunanin zan koma a kurkusa sai na huta tukkuna.""" "Mmn Ladi ta sauke ajiyar zuciya tace""Gaskiya Najaatu naji miki haushi da takaicin rasa wannan mutumin" to amma tunda kin jingina al'amarin a matsayin qaddara muma zamu jingina shi a hakan ammafa wallahi kema da akwai son zuciyarki wanda shine ya kara sanyawa kika kai kanki ga wahala! saboda haka ni dai shawarar da zan baki wallahi ki lalla'ba da wayo da siyasa ya mayar dake dan nima na tabbatar da cewar a gurinsa ne kadai zaki fi samun nutsuwa da kwanciyar hankali saboda yanzu duniya kowa kansa ba kowane namiji ne zai yarda kije masa da d'anki ba. """Mmn Ladi wane dabaru zanyi ya mayar dani ni bazan iya fada masa baki da baki ba, na hakura zan" "cigaba da rainon yarona har Allah yasa ya girma, shikkenan idan na samu daidai dani sai na aura." "Mmn Sajida tace."" Ni kuma sai nake ganin kamar yana jira yaron ki yay wayo ya bijiro da maganar kome" "din kin san fa koda zai mayar dake gidansa ba zai mayar dake kina da d'anyan jego ba, wallahi ko kaffara ba zanyi ba yana sonki dan da baya sonki ba zai dinga yi miki wahala ba, haba ki duba fa ki gani shine yazo ya daukar ki anan sannan lokacin da kika kwanta a asibiti kina kiran wayarsa ko minti ashirin ba'ayi ba ya turo da kudiin da'a ka bukata. Duk da kin kasance mai laifi a gurinsa hakan bai hanashi kula" "dake ba, ki kwantar da hankali da kansa zaiyi miki maganar ki koma gidansa amma kema dole ki dan yawaita kwalliya da gyaran jikinki da kowane lokaci ya dinga ganinki tsaf tsaf zaki janyo hankalinsa" "sannan kina kiransa a waya kina gaisheshi.""" "Najaatu murmushin takaici tayi tace""Mmn Sajida sau nawa zan kira wayarsa yasa matarsa ta dauka! a" "gabanki ma fa hakan ya ta'ba faruwa Abbah wani irin mutum ne wanda baka gane gabansa da bayansa.""" "Mmn Ladi tace""Kome baud'ewar halinsa mace na iya sanja shi saboda haka idan kika mayar da hankali" "akan shawarwarin da muke baki zasu taimake ki.""" "Najaartu shuru kawai tayi tana sauraran maganganunsu, tana daukar na dauka tana watsar dana" watsarwa bata tunanin zata tunkareshi da maganar ya mayar da ita gidansa idan ya tausaya mata da yaronta ya mayar da ita haka take so idan kuma yana ganin bashi da ra'ayi sai ta hakura ta barwa Allah. "Sai bayan taci abinci ta nutsu tukkuna ta shiga fito musu da tsarabar data kawo musu , kowacce turmin" atamfa biyu da mayafi da takalmi sai sabulai na wanka dana wanki da kayan kwalliya irin na mata. "Sosai suka shiga yi mata godiyar hidimar da tayi musu, ashe da sauran godiya, dan kudinta na haihuwa" data samu kimanin dubu saba'in da wani abu a ciki ta dauko dubu hamsin ta kawo musu Mmn Sajida ta miqawa tace su raba. Mmn Sajida ta riqe kudin a hannunta tana kallonta cikin d'umbun "mamaki! Murmushi tayi ta kalli Mmn Ladi tace""Mmn Ladi naki kudin sai kiyi kokarin ki fara sanaa dasu kafin naga abunda Allah zaiyi anan gaba insha Allahu idan na samu yanda nake so zan qara miki wasu." "Mmn Ladi fashewa tayi da kuka ta rungumeta tana fad'in ""Wallahi Najaatu na rasa bakin da zan gode" "miki ashe ke din alkairi ce a tare damu muna mutukar alfahari da sanin da mukayi miki wallahi Kinyi min abunda d'an uwa na jini baiyi min ba, a cikin 'yan uwana akwai masu hali amma babu wanda yay tunanin dauko kwabonsa ya bani da sunan naja jari nayi sana'a sai ke da Allah ya had'ani dake kin gyara min aurena kuma kin dauki kudi kin bamu, kin kawo min babban zani irin wanda banta'ba daurawa ba, babu" abinda zance sai dai nace Allah ya saka miki da alkairi ya biya miki dukkanin bukatunki. "Naja'atu tace""Haba Mmn Ladi meye abun kuka wallahi wannan ba komai bane a gurina idan ina da" "abunda yafi haka zan baku domin kuma kun taimakawa rayuwata a lokacin da nake bukatar taimako saboda haka ki daina kuka kina gode min Allah ne ya had'amu ina fatan zumuncin mu ya d'ore har 'ya'ya da jikoki."" Mmn Sajida tace""Insha Allahu Najaatu Allah zai cika mana burin mu kuma kamar yanda muke" "zumunci insha Allah 'ya'yanmu suma za suyi.""" Da wannan addua ta Mmn Sajida suka rufe maganar suka shiga hirar Bash da hukuncin da'a ka yanke masa. "Laifin Najaatu ya shafi su Halisa a tunzure ya shiga gidan, girkin Halisa ne ganin yanda ya shigo yana shan" "qamshi yasa bata tunkari inda yake ba gudun wulakanci yasa taje tayi kwanciyar a dakinta tana kallo, har ya gama abinda yake a falo ya shigo yay shirin kwanciya, zama yay gefan gado da wayarsa a hannunsa." Number Najaatu ya nema Lokacin dare yayi dan goma da rabi ta wuce duk sunyi shirin kwanciya Mmn Sajida dalilin zuwan "Najaatun yasa bata fita sana'arta ba, suna hira sama sama kiran wayarsa tasa ya shigo." "Ta dauka tana dan tunani to me ya kirata yace mata? Shawarar dasu Mmn Sajida suka bata ta tuna, sai" "kawai ta daga wayar tana wani maqale murya tace""Hello Abbah! barka da dare."" Wani irin yarrr! yaji a jikinsa sakamakon jin yanda muryarta ta ratsa jikinsa, tamaza yay yayi gyaran murya as'usul yace.""Barka dai ina fatan kin suturta yaron nan da kayan sanyi saboda kin san dai yanda ake sanyi gashi na lura" "gurin da kike bashi da tsaro da sauransu.""" "Dan murmushi tayi tana kallon Mmn Sajida, ta sake kashe murya tace"" Abbah ni baka damu dani ba" "kenan kana tambayar na suturta Mai sunanka nima ai ina jin sanyi sosai a jikina.""! Cikin shagwaba ta k'arasa maganar." "Shuru yay na minti biyu kafin yace.""Ke ai kin girma sanyi ba zai miki lahani ba kamar shi so sabida shi na" "kira wayarki sannan kuma na sake tunasar miki da abinda na fad'a miki d'azu! gobe da wurwuri Dan Azimi zai zo ya daukeki.""" "Kamar za tayi kuka tace""Allah ni bazan dawo gobe ba, Abbah wa na'ajiye a garin kano da zan takurawa" kaina dawowa ni dai dan Allah ka bari na kwana biyu a gari jos dan ina jin dadin garin sosai da sosai.'' "A hasale yace.""Ke! ashe baki da hankali wannan garin duk babu mutunin arziki a cikinsa ashe kina so ki" "sake haduwa da wani mara tarbiya kenan( Afuwa mazauna wannan garin banyi da niyyar naci muku fuska ba labari ne yazo a haka a gafarce ni garin jos akwai masu tarbiya sosai ga misalin irinsu Mmn Sajida nan nayi). Tace""Haba dai Abbah ba duka a ka zama d'aya ba Wallahi su Mmn Sajida suna da" kirki da tarbiya kuma ni da naje ziyara mai zai had'a ni da wani saurayi ko bazawari babu ruwana dasu. "Yace.""Ni dai na fad'a miki gobe ki zauna cikin shiri domin hankalina bai yarda da zamanki a wannan gari" "ba."" Kashe wayar yay bai saurari ta bakinta ba. Halisa ta miqe zaune tana hararar bayansa ji take" "kamar ta makeshi! saboda haushi yana yaudarar kansa yana yaudararsu to meye nasa na damuwa dan ta tafi jos da har zai ce zai tura a daukota. tsaki taja a zuciyarta kafin tace""To wai kai meye na damuwa dan ta tafi wannan gari? babu fa nauyin kowa a kanta da kake cewa ta dawo haba ai ka kyaleta ta huta su" "gaisa sosai da wannan mutanan da sukayi mata hallaci.""" "Yana jinta yay shuru sai ma ya fara kokarin kwanciya yana kokarin rufe kafafunsa, Halisa bata san sanda" "taja tsaki ba tace""Abban Mufida kenan ka tsaya wasa wallahi sai dai kaji anayi dan Najaatu a yanzu allura cikin ruwa ce da d'anyan jegon da take dashi ba zata rasa me auranta ba. Fad'in wannan magana da" "Halisa tayi sai ya fusata! ya miqe zaune ya dinga zazzaga mata masifa da fad'in ""mahaukacin Namiji ne" zai auri mace da d'anyan jego saboda haka kada ta kuskura ta sake yi masa irin wannan magana. "Halisa itama ta fusata tace"" To itama kada ya sake zuwa gabanta yayi waya da Najaatu tunda abun nasa" "ya zama rainin hankali, haka suka dinga cacar baki tana fad'a yana fad'a dan gabanyansu a tunzure suke kowa yana ganin ba'ayi masa daidai ba.......Gabad'ayansu Haka suka kwanta suna jin haushin juna....." *Infaction* _Ko wace mace kaji tace miki tana fama da infaction wai shin ya zamuyi mu kare kanmu daga wannan laluran mai wahalar magani? Idan kina da sanyi koda mijinki bai dashi sai ya samu Ko kuma ke baki "dashi mijinki nada shi to sai kin samu, idan ya kasance duk kuna dauke da lalurar sai ku durfafi shan magani a tare! dan idan daya yasha daya bai shaba to akin banza kukayi ciwon yana nan babu inda zaije. Kina budurwa kina kyaikayin gaba da zubar da farin ruwa gashi an kusa bikin ki kinja bakinki" "kinyi shuru baki fadawa mamanki ba, to zaki haifarwa da kanki matsala babba dan idan kikaje gidan mijinki da wannan ciwo kika shafa masa zai miki mummunar fahinta ya dunga yi miki wani irin kallo na daban saboda haka mutukar kina da matsala irin wannan maza ki sanar da mahaifiyarki kafin ki" sanar dani mahaifiyarki itace mafi kusa dake kuma ita ta haifeki babu kunya a tsakaninku! Ki fada mata komai zata kaiki gurin mai magani Ni shawara ce kawai a tsakaninmu._ *Idan da tsumma kike using a lokacin da kike jin al'ada to ya kasance kullum kina sanjawa sau uku ko sau "hudu, sannan idan kin wanke tsumman ki dinga sashi a rana ya bushe kwayoyin cutar zasu mutu. mutukar kina barin matuncin ki da danshin ruwa to ba zaki rabu da kyaikyayin gaba ba," wannan guri an fiso kullum ya kasance a bushe. Idan da pad kike using lokacin haila yana da kyau kina sanjawa a kai kai kada kisa tun safe ki barshi sai dare dole gabanki yayi miki kyaikyayi daga haka kuma "kwayoyin cuta su shiga jikinki, wannan kyakiyayin masifa ne, saboda haka dan Allah muyi hattara *" Vip group #600 normal group #300 accont...0542382124....Binta umat gtbank...WhatsApp number... 07084653262 _Yau mura ta hana ni nayi muku post akan lokaci duk naga adduoin ku dana pravite dana group Nagode sosai Binta tana tare daku insha Allah _ *BHRMBN 74_75* "Da maganar Halisa ya kwanta bacci ya kuma tashi da maganar a cikin ransa, ya jima yana nazarin" maganar da tunanin abinda zai biyo baya a jos din mutukar an san ita din bazawara ce to tabbas "maganar Halisa na iya kasacancewa a samu wanda zai ce yana sonta duk da jegon da take dashi, dan" "haka yana dawowa daga masallaci ya nemi number wayar Dan Azimi suka gaisa da juna yace.""Ina fatan dai ka shirya ka tafi da wuri bana so kuyi shigowar dare." "Dan Azimi yace.""Eh gani nama fito Insha Allahu yanzu zan tafi, Yace."" to Allah ya kiyaye hanya inda ka" "sauka sai ka kira ni ka sanar dani ."" Dan Azimi yace.""Insha Allah ranka ya dade."" Sallama sukayi ya kashe wayar ya miqe ya fita falo zama yay kan kujera yana jiyo motsin Halisa a kicin, tsabar 'bacin rai Halisa" "ko gaisheshi ba tayi ba, yana kallonta ta fito daga kicin ta nufi dakinta ko kallonsa ba tayi ba, miqewa yay yana girgiza kansa ya nufi gurin Zainab, babu kowa a falon lokacin da shiga sai ya nufi dakin yaran sa domin duba su, suna tare da Baba Larai tana taimaka musu da shirin makaranta, a nutse yaran suka gaishe shi ya amsa cikin kulawa shima ya gaishe da Baba larai ya tsaya suka danyi maganar yaran da ita" kafin ya fita daga dakin. Zainab tana zaune kan dadduma tunda tayi sallah ta kasa motsawa daga inda take marar ta ce take wani "irin ciwo Cikin mawuyacin hali ya sameta, hankalinsa ya tashi ya taimaka mata ta miqe tsaye, yana" "tambayarta abinda ke damunta, cikin halin ciwo ta fada masa cewar mararta ke ciwo, zaunar da ita yay gefan gado yace.""Bari na kira Baba Larai ta dubaki ko haihuwa za kayi....Fita yay daga dakin sauri, koda baba larai taga yanayin Zainab a take ta fahimci cewa haihuwa za tayi, tace""Alhaji haihuwa yarinyar nan za tayi amma yana da kyau aje asibiti domin a sake tabbatarwa, Yace.""Okey bari na sanar da Halisa....Halisa jin cewa zainab zata haihu yasa ta biyo bayansa halin da taga Zainab a ciki yasa jikinta sanyi, kayan haihuwa kawai suka hada suka nufi asibiti Zainab duk ta rikice da ihu! gabadaya ta manta da addua sai ihu take tana kiran a taimaka mata gabadaya hankalinsu ya tashi harshi Abbah Abbas din" dake driving hankali a tashe ya kara karfin motar suka isa asibitin nasarawa. Zainab bata dade tana doguwar naquda ba Allah ya sauketa lafiya inda ta haifi 'ya mace mai kama da ita "sai dai ta dauko hasken fatar babanta, Abbah yayi farin ciki sosai ganin yanda Allah ya raba lafiya maijego da babynta lafiyarsu lau Kafin su bar asibitin Abbah ya sanar da duk wanda ya dace ya san" "haihuwa, awa biyu kacal sukayi a asibitin aka sallamesu Suna koma gidan suka tarar da 'yan uwan" "Zainab sun cika gidan, Abbah ya tsaya suka gaisa a gurguje ya fita ya basu guri" Bangaran Halisa ya koma domin ya kimtsa jikinsa. Allah sarki Halisa ganin yanda yake ta murna da "haihuwar zainab din yasa itama taji tana sha'awar haihuwa tunda ta haihu sau biyu bata sake haihuwa ba, mufida yanzu shekaranta goma sha uku amma ko 'batan wata ta sake ba, zama tayi ta zabga tagumi" abin duniya ya isheta. Ganin ya shigo dakin ne yasa ta miqe ta fita ta basa guri gabad'aya duniya tayi mata zafi tana ta nadamar cutar da kanta da tayi tana tunanin ko magungunan turawan data dinga d'ubga ne ya toshe mata mahaifa gaskiya dole ma taje asibiti a dubata tunda ba wuce haihuwa tayi ba. Zainab na tsakiyar 'yan uwanta suna ta zugata ita kuma ta saki baki sai fad'a musu karya da gaskiya "takeyi...Wata yayarta tace""To yanzu ai duk wani abu da kika san kina bukata ki rubuta masa kuma kada ki sake kiyi amfani da kyan babyn nan ya sake siya miki wasu, sannan kice kina so ya siya miki set gold" zakiyi fitar bikin suna dashi. "Zainab tace""Duk abinda nake so yana kaina ke har mota nima sai ya siya min tunda na tabbatar wacce" aunty Halisa take hawa shi ya siya mata. "Yayar tata tace""Ato idan kika tsaya wasa sai ki zama koma baya tunda kin haihu dashi ai kin zama kujera" a gidansa....Zainab murmushin jin dadi tayi ta juya ta kalli babynta dake kwance a gefanta. Yaya Ramlatu da Hajia Rabi da Baba Talatu ne sukayi sallama a dakin. "Da sauri Yayar zainab ta miqe tana musu barka da zuwa ta basu guri suka zauna suna gaisawa, Babyn ta" "dauko ta miqawa baba talatu da fadin ""Ga bakuwar duniya mai kama da babanta."" Baba Talatu ta karbi yarinyar tana murmushi cikin nutsuwa tace""Masha Allah Allah yayi mata albarka babu shakka yarinya ta dauko gida Allah y raya mana ita." suka amsa da amin. Baba talatu ta miqawa Hajia Rabi itama ta karbe ta tayi mata addua sannan ta miqawa Yaya Ramlatu. "Yaya Ramlatu tayi murmushi idonta a kan babyn tace""Yarinya dai ta dauko hasken fatar gida amma" "kuma kammaninta sak na uwarta."" Zainab tayi saurin kallonta tana mamakin maganarta, ita kuwa yayarta cikin ya'ke tace""Aikuwa baki ji bahaushe yana cewa kyawun d'a ya gaji uwarsa ba."" Ya Ramlatu tayi dariya cikin sigar kuntatawa tace"" Kyawun d'a ya gaji ubansa ake cewa yarinya ta gaji ubanta gurin" "haske fata kammani kuma na uwarta ne Allah yasa kada ta dauko halinta.""" "Hajia rabi tace""Wace irin magana ce wannan.""? cikin takaici Ramlatu tace""Hajia duk sanda zan kalli" "yarinyar nan sai na tuna sanda ta wanke ni da mari ni kam a tarihin rayuwata ba zan taba mancewa da ita ba.""" "Jin wannan magana yasa 'yan uwan Zainab jikinsu yay sanyi kunya duk ta dabaibayesu, Zainab kuwa tuni" ta fashe da kuka gabanta sai faduwa yake Ramlatu tazo ta tona mata asiri a gurin 'yan uwanta "Yayar Zainab tace""Dan Allah kiyi hakuri 'yar uwa maganar tone tone duk bata taso ba alheri da farin ciki" ne ya kawo muku gidan nan saboda haka idan zainab tayi miki wani wanda bakiji dadinsa ba ki gafarce ta akwai kuruciya a tare da ita "Ramlatu tace""Iskanci dai ba kuruciya ba, ai magana ni ta wuce a gurina wallahi kawai dai idan na tuna" "al'amarin raina yake baci.""" "Cikin fusata! Yayar zainab din tace"" Ashe dama abunda kike yi kenan yanzu kamar wannan matar tana a" "matsayin yayar mijinki ki fitar da hannu ki mareta to Sai ki bata hakuri tunda ke baki da mutunci.""" "Zainab na kuka tace""Yaya Ramlatu ki gafarce ni wallahi tsautsayi ne."" Cike da takaici tace ""Dena kuka ai" "na yafe miki tuntuni saura kuma idan ya dawo ki fada masa ga abinda nazo nayi miki kisa shi ya kawo min rundunar sojoji."" Zainab tace""Wallahi ko wancan karan ma bani nasa shi ba kiyi hakuri.""" "Baba Talatu tace""Ke kam Ramlatu abu baya wuce wa a gurinki ne? yarinyar nan ta baki hakuri magana ta" kare dan Allah. "Yaya Ramlatu tace""Magana ta wuce baba insha Allah bazan sake tada ita ba.""" "Karfe uku saura na rana Dan Azimi yayi parking din mota a kofar gidan Mmn Sajida, sai dai me? yana" fitowa yaga katon kwado kulle da kyauran gidan Ya jima yana mamaki kafin ya bude motar ya zauna "ya shiga kiran wanda ya aikoshi, ya sheda masa abunda yake faruwa." Abbah jin abinda dan Azimi yake fad'a masa yasa ko gama sauraransa baiyi ba ya kashe wayar da sauri ya "nemi number ta......Lokacin suna gidan bikin sunan k'anwar Mmn Ladi, dan da zasu tafi cewa tayi ba" zata zauna ita kadai a gida ba sai ta shirya tsaf sukayi tafiyarsu bayan tasan da maganar zuwan Dan Azimi. Hayaniyar jama'a ya hanata taji abinda yake cewa sai kawai ta kashe wayar ta ta ajiye tasan dai maganar zuwan Dan Azimi zaiyi mata ita kuwa ba taga dalilin da zai sanya ta koma gida a yanzu ba. Abbah ya shiga mamaki mai tsananin gaske yau shi Najaatu ta kashewa waya! to wai shin ma ina ta tafi a garin da bata da kowa hakika yarinyar nan na nema ta d'ora masa ciwon zuciya. Wayar ya sake kira sai ta miqe daga cikin mutane ta samu gurin da babu hayaniya sosai ta daga a "sanyaye tace""Abbah ina kwana wallahi ina cikin jamaa ne shiyasa bana jinka sosai.""" "Yace.""Kina ina Dan Azimi tuntuni yazo daukar ki bakya nan to har in dai na isa dake duk inda kike kiyi" "maza ki koma yana zaman jiran ki."" Abbah dan Katse ta yay da sauri yace.""Kina so ki 'bata min rai ko?" na fad'a miki bana son zamanki a wannan garin nasan dai daga jiya zuwa yau duk wanda kika sani a garin kin gaisa dashi to zaman me za kiyi kuma gashi nan kwana d'aya kacal da zuwanki kin fita yawo shin me kike so ki zama? saboda haka na gama magana idan na isa na fad'a miki kiji to ki tabbatar kin biyo Dan Azimi kun "n dawo gida a tare."" Kashe wayarsa yay bayan ya gama maganarsa." "Tun kafin ta zauna Mmn Sajida ke kallonta, tace""Najaatu yana ga jikinki a sanyaye ina fata ba wata" "matsala bace.""" "A sanyaye tace""Abbah ne ya kira wai yanzu haka Dan Azimi nacan kofar gidanki yana jirana yace lallai" dole sai na bishi mun koma gida a tare ni kuma wallahi bana jin zan iya binsa sai dai idan ya gaji da zama ya tafi bari ma kawai na kashe wayar ta kada ya sake kira. "Mmn Sajida tace""A'a bada ni za'ayi wannan rashin hankalin ba, Najaatu ba zaki had'a kai dani ki 'batawa" "wannan bawan Allahn rai ba, tunda yace ki tafi to gaskiya yana da kyau kibi umarninsa kada ki nuna masa bai isa dake ba, haba keda kike nema ya mayar dake gidansa me zai sanya ki dinga yi masa gaddama akan dukkanin abinda zai umarceki kawai ki tashi mu tafi na tayaki hada kayanki ai mun gaisa" kuma insha Allah muma zamu inda kike. "Murya na rawa tace""Mmn Sajida korata kike a gidanki? Wai shin dan Allah idan na koma me zanyi masa" "zama fa kawai zanyi a gida shi kuma kullum yana gurin iyalinsa to ba gwara na zauna na samu nutsuwa ba.""" "Mmn Sajida tace""Lallai ta yaro kyau tace bata qarko wallahi Najaatu baki da wayo har yanzu Mutumin" "nan dafa baya sonki ba zai damu dake haka ba, yanzu dama kika samu a hannunki wacce zaki sake janyo hankalinsa kanki ta hanyoyi daban daban, baki da wayo wallahi har yanzu kiyi tunani akan shawarwarin" dana baki jiya da daddare wallahi mutukar kin dauki shawara ta baza'a ja dogon lokaci ba zai kawo kansa gurinki. "Najaatu tayi shuru tana nazarin maganar da Mmn Sajida keyi, "" A sanyaye tace."" Shikkenan Mmn Sajida" "zan gwada Daukar shawararki nagode sosai da kulawarki a kaina.""" "Mmn Sajida tace""Babu komai wallahi aike yanzu 'kanwata ce duk abinda nayi miki ban fadi ba, saboda" "haka yanzu tashi muje ki shirya kayanki.""" "Miqewa sukayi suna gyara mayafi, Mmn Ladi ta fito daga dakin mejego ganin sun miqe tace""Aa ina" "zakuje naga kun miqe.""? A takaice Mmn Sajida tayi mata bayani...Mmn Ladi tace""Eh lallai haka shine yafi alkairi dake Naja'atu mungode kwarai da ziyara kuma insha Allah muma muna kan hanyar zuwa. Tare" suka fita daga gidan Mmn Ladi har bakin titi ta rakasu sai da ta tabbatar sun hau adaidaita sahu sannan ta koma cikin gidan Dan Azimi na ganin saukar su Najaatu daga a daidata sahu ya shiga murna dama tun dazu wanda ya turo shi yake ta kiransa a waya yana tambayarsa yanda ake ciki sai bayan sun shiga gidan ne yay saurin kiransa ya fada masa cewa gata nan ta dawo nan ba da jimawa ba zasu dauko hanya. "Abbah Abbas ajiyar zuciya ya sauke kafin yace.''To Alhamdullhi Allah ya kawo ku lafiya."". Najaatu" "cikin kunci da damuwa ta fito Mmn Sajida tasa mata jakar kayanta a motar dukkaninsu idan ka gansu za kagane suna cikin alhini na rabuwa da junansu Mmn Sajida sai daure zuciyarta take tana kwantar mata da hankali, sai bayan data shiga motar ne hawayen da take 'boyewa suka shiga zuba, hannu kawai ta daga mata ta kauda kanta gefe guda. Dan Azimi na jan motar Mmn Sajida ta juya da sauri ta shiga" "gidanta tana goge hawayen daya 'kwace mata, Allah kenan mai had'a mutum da mutum." Dan Azimi sai hira yake mata ta shareshi haushinsa takeji kamar shine yay mata laifi to shima daya lura bata son hirar sai yaja bakinsa yay shuru kawai ya cigaba da fafara gudu a kan kwalta. "daidai sanda suka shiga zaria Abbah ya sake kiran wayar Dan Azimin yana tambayarsa hanya," "Yace.""Gamu a zaria ai mun kusa isowa gida insha Allah.""" "Abbah ajiyar zuciya ya sauke tare da fad'in ""Allah ya saukeku lafiya.'' ya kashe wayar yana jin tamkar" "wanda aka yayewa dukkanin damuwar dake damunsa tabbas Tafiyar Najaatu garin jos ta daga masa hankali sosai dan gani yake kamar zata sake had'uwa da wani dan ta'addahn! ya yaudareta, shi da kansa a yanzu ya gazgata abinda ke damunsa a kan yarinyar ya daina wahalar da kansa da yaudarar kansa a kan cewar shi ba son aure yake mata ba so yake mata irin na uba da 'yarsa! Gaskiya da yayi nazari sosai ya gane ba irin wannan son yake mata ba, yarinyar ita da d'anta sunyi masifar tsaya masa a rai! kuma ya yarda da maganar Halisa inda take cewa samun nutsuwar sa Najaatu na kusa dashi, hakane tunda tun jiya yake cikin tararrabi gami da rashin kwanciyar hankali saboda tayi nesa daga inda" "yake, gabadaya haihuwar Zainab bata dameshi ba akan yanda ya damu da lallai sai Najaatu ta dawo gida." Sai wajejen tara da rabi na dare suka sauka. Dama tuntuni ya gayawa Hajia cewa ya tura Dan Azimi ya "daukota hajia ta dinga mamakinsa, sai dai tayi shuru kawai tana binsa da dukkanin abinda yake tsara mata akan tafiyar. Najaatu kukan takaici ta zauna ta nayi Hajia ta zauna tana ta rarrashinta da bata" hakuri ita kuwa Yaya Ramlatu d'an ta dauka ta goya tana taya hajian rarrashin da take. A ranar dai Najaatu bakin ciki da takaici tayi bacci dan taji bala'in haushin abun dan dai babu yanda za tayi ne. "Sai da safe take jin labarin haihuwar Zainab a bakin Ramlatu tace Allah Ya raya abunda aka samu, Hajia" "tace""Idan anyi la'asar sai muje nima banje naga 'yar ba." "Tace""To shikkenan Hajia Allah ya kaimu lafiya." To kamar yanda hajia ta fada hakane ya kasance bayan sunyi sallar la'asar a gida suka shirya tsaf suka "nufi gidan masu jegon......Gate din Zainab cike yake da 'yan uwanta tamkar ma ranar ne suna Zainab famliy nasu suna da yawa shiyasa tunda akayi haihuwar suke shige da fice a gidan, mutum uku ma a gidan suka kwana kuma duk da auransu kawai daular gidan Zainab din ce take d'ibarsu suka zauna suna d'orawa da saukewa, 'Ya'yan sheik Nazifi 'Ya'yan malam kaqi halin malam ne yawanci su basu da hali mai" "kyau mazajensu na hakuri dasu mutuka, kuma mafi akasari almajiransa suke aure shiyasa suke rashin" mutuncinsu iya san ransu sabida mazajen nasu najin kunya da nauyin tunkarar shehin malamin da wata "magana, a cikinsu Zainab ce karama kuma itace ke auran Alhaji (mai kudi) shiyasa tunda suka zo suke zugata ga yanda za tayi ta gina kanta a gidan.......Harabar gurin Zainab yayi kaca kaca da kayan miya gefe" katon kasko ne akan murhu wuta sai ci take anata soya nama tamkar ranar sallah. Ganin shigowarsu Hajian gidan yasa suka dan shiga nutsuwarsu cikin girmamawa suke shiga yi mata "barka da zuwa, Babbar yayar su zainab din itace ta jagorance su har inda maijego take. Zainab taci" kwalliya tamkar wata amarya da babynta a hannu tana shayar da ita cike da murna takewa hajian barka da zuwa. Hajia Abu ta samu guri ta zauna a nutse Najaatu ma ta zauna kusa da ita tana kokarin kwance Daddy dake motsi a bayanta. Zainab ta miqawa Hajia yarinyar kana cikin neman gindin zama ta tsuguna har qasa tana gaishe "ta....Hajia cike da farin cikin ganin Zainab da 'yarta kalau ta amsa tana fad'in ""Sannu Zainab Allah ya qara miki lafiya tare da abunda kika haifa naji dadin ganinki kalau keda yarinyarki Allah ya rayata tafarkin" "addinin musulunci."" Zainab na dan murmushi ta amsa tare da komawa ta zauna a gefan gado." Dakin ne yay shuru Zainab 'Yar rainin hankali wai jira take Najaatu ta gaisheta tayi mata "barka. Najaatu kuwa tunda tayi mata kallo daya ta dauke kanta,babyn kawai ta kar'ba hannun hajia" "tana dubata gami da sa mata albarka, a tsakaninsu babu wacce ta kulawa kowa. Hajia tayi mamakin" al'amarin kwarai da gaske kuma ta fahimci abinda yake da akwai sai tayi shuru da bakinta ba wai dan bata da abincewa ba sai dan ganin kamar shuru din da tayi shi yafi alkairi. Sun kai kimanin Mintina ashirin a dakin Zainab din kafi su miqe Hajia tace zasu shiga gurin halisa su "gaisa."" Zainab tace""To hajia nagode sosai Allah ya qara girma."" Hajia ta amsa da ameeen sannan suka fita daga dakin." "Yanayin yanda suka samu Halisa cikin damuwa yasa daga hajian har Najaatun suka tausaya mata, Halisa" "bata 'boyewa hajia abinda ke damunta ba sai da fad'a mata komai Hajia tace""Kada ta damu insha Allahu ita da kanta za tai masa maganar zuwa asibitin insha Allahu kuma za'a dace idan anje dan haka ta daina damuwa."" Halisa taji dadin zuwan hajian sosai da sosai kuma tasan tunda tace zatayi masa magana to zai dauki al'amarin da muhimanci........Hajia da Najaatu basu jima sosai ba sukayi mata sallama suka fito, Halisa har bakin mota ta rakasu sai da direba yaja motar sannan ta koma gurinta tana jin sassauci a cikin zuciyarta amma hakika abinda 'Yan uwan Zainab sukeyi a gidan ya fara bata haushi 'barna da samun gurin da sukayi yayi yawa basu da hankali ko kadan kuma sun fito da kwadayinsu a fili kamar ba 'ya'yan" fitaccen malami ba. To har dai yanzu abinda ke faruwa a tsakaninta dashi shike faruwa tunda ta dawo gaisuwa ce kawai a "tsakaninsu daga ita babu wata magana sai dai kallo, watarana idan yazo tana zaune a falo barin falon takeyi bayan sun gaisa dan ta tsani munafikin kallon da yake mata wanda daga zarar yaga zasu had'a ido sai yay sauri ya dauke kansa, haushin hakan yasa take barin gurin inda shi kuma yake jin haushin hakan" yafi so ta zauna yana dan kallonta ko yafi fahintar abunda suke tattaunawa da mahaifiyarsa. Ranar kwana biyar da haihuwa yasa Abdulhamid ya kai kayan barka gidan Alhajin kamar yanda hajia ta "umarceshi....akwati uku manya shaqe da kaya sai kace amarya, akwatin babyn ma guda daya ce amma na Zainab har uku. ita kanta hajian sai da tayi mamakin abun harda set din gold masu nauyi da" "tsada!. Ya Ramlatu ta dinga masifa da fad'in ""Wannan kayan sunyi yawa kuma basu dace da yarinyar ba" haba sai kace hauka bayan lefan da akayi mata saboda ta haihu sai a sake yi mata wani. "Hajia ta katseta da fad'in "" Ke bana son ganin ido dan Allah ko wace haihuwa da goshinta meye dan anyi" mata ai haihuwar fari ce saboda haka kada na sake jin wannan magana duk abinda zainab ta samu rabonta ne. "Ramlatu tace""Hajia duba fa kiga wannan uwar sarqa ki daga kiji nauyinta anya Abbas yana sane yake" "'barnatar da dukiyarsa bayan ga 'ya'ya ya fara tarawa abun yay yawa."" Hajia tace""Ni dai nace ki bar maganar nan kome zainab ta samu rabonta ne saboda haka ki hada komai a inda yake anjima da yamma sai kuje ku kai musu.""" Ramlatu shuru kawai tayi tana mamakin al'amarin To itama Najaatu nata 'bangaran sai da taji wani iri daurewa kawai tayi tana kokarin cire kanta daga abinda be shafeta ba amma ita kanta wannan set din gold din ya bata sha'awa sosai.... *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya ga yanda abun yake. p gruop#600 normal group #300 account... 0542382124 Binta umar gtbabk WhatsApp number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *MADADI 76_77* Abinda su hajia basu sani ba shine tun ranar kwana biyu da haihuwar Zainab ta tisa shi a gaba ta dinga "lissafa masa abubuwan da take so, Allah sarki Abbah sarkin adalci sai yace to ta fada masa iya adadin kudin da take bukata, bata fada masa a ranar ba sai ta bari babbar yarta tazo ta fad'a mata inda ita kuma kai tsaye tace""ki fada masa dubu dari biyar zai baki. Zainab tayi shuru tana mamakin uban kudin da yayartata ta tsuga! tace.""Anya aunty kudin basuyi yawa ba.""? Murmushi tayi tace""Idan miliyan kikace kina bukata yana da ikon da zai baki mijinki fa yana da kudi ne wanda be san a dadinsu ba meye a ciki dan ya baki dubu dari biyar 'ya guda fa kika haifar masa darajar dan mutum yafi komai."" Zainab tace""To" zan gwada nagani anty bana so yaga rashin hankalina wallahi. "Tace""Baki da wayo zainab na fada miki fa yanzu ne lokacin ki amma tunda kina ganin kamar wani abu" "shikkenn kanki zaki cuta ba wani ba, yanzu idan ya baki kudin nan sun isa ki siyi komai na qawa da kece raini ke har sai sunyi miki saura sai ki ajiye a account dinki kyayi wata bukatar dasu" "Zainab tace""To shikkenan bari ya shigo da daddare zan fada masa.""" Zainab tayi mamaki lokacin data fada masa a dadin kudin da take bukata yace babu matsala zai saka mata a account dinta in yaso duk abunda take bukata baby ke bukata sai tasa 'yan uwanta su cire kudin su siya mata. Zainab yana fita ta dinga murna da farin ciki kanta na sake girma tana tunkaho da cewar "ita din 'yar gaban goshi ce wannan zunzurutun kudin da ya bata tayi hidimar haihuwarta yasa ta daina jin haushin abubuwan da yayi wa Najaatu a lokacin data haihu, ta tabbata kyauta da hannun bayarwa a jinin jikinsa yake koda yan uwanta suka zo ta nuna musu shedar kudin a wayarta sai suka dinga" "mamaki! wasu daga cikinsu har sai da hassadar su ta fito fili, babbar yarsu aunty Hauwa tace""To sai ki bani Atm din ki naje da kaina zan had'o miki kaya na alfarma wanda zaki fita kunya dashi ranar suna."" haka kuwa akayi aunty Hauwa yayar Zainab itace duk ta had'o kayan barka saboda tsabar rashin hankali" duk ta qarar da kudin gurin siyawa 'yar uwarta kayan banza da wofi amma baby ta tashi da akwati daya itama ba wasu kayan kirki ne a ciki ba. Ita kanta Halisa da aka kai kayan ta shiga ta gansu sai da tayi mamaki! daurewa kawai tayi ta dudduba "tasa albarka ta nufi gurinta, aikuwa tana fita 'yan uwan Zainab suka shiga dariya kowa na fadin albarkacin bakinsa akanta wai 'yar bakin ciki ce hassada tasa ta kasa zama ta duba kayan a tsanake, ita kuwa zainab sai wani figala take tana fad'in ita waye yasan abunda akayi mata a baya saboda haka taje tayi ta hassadarta idan ma mutuwa za tayi ta mutu babu ruwanta.'' Babu wanda yay mata fadan arziki sai ma qara zugata da suke idan tayi arbain tace ya siya mata mota. kai tsaye tace""Dama ai yanzu abinda" "yake gabana kenan naga ina hawa babbar mota wacce tafi ta Halisan kudi da girma.""" "Halisa kuwa sa masa ido kawai tayi taga iya gudun ruwansa, shin ita da yara me ya tanadar musu na fitar" "suna ai ko turaman atamfofi ya kawo musu suma su sanya, tun ranar da sukayi cacar baki akan Najaatu suke sama sama da juna dan haka ana ya gobe suna ta same shi yana shiryawa zai fita tace""Naga kayan" "barka na Zainab sai nace to mu ina namu kayan fitar suna ni da yara.""" "Ba tare da ya kalleta ba yace.""Kinyi magana kina bukata ne? Tace""Sai nayi magana zaka san abinda ya" dace a qallah dai ai muma ka kawo mana namu ba sai nayi magana ba tunda muna da hakki. "Yace.""Itama bani naje nayi mata siyayya ba dan bani da lokaci kudi na bata kuma kin san dole ayi mata" "hidima tunda haihuwa tayi."" Tace""Ina ruwana da haihuwa tayi ni ina maka maganar akan hakkina da yara na."" Afusace! yace.""Ke! Halisa ba zanyi ba! uwata ce ke zaki sani a gaba kina nuna min abunda ya dace to ba zanyi ba nace! kusa wanda kuke dashi."" Yana gama maganarsa ya buge rigarsa tare da daukar wayoyinsa ya qara gaba. Halisa ta jima tana mamakin wannan al'amarin ta dinga tunanin hukuncin da" "zata dauka a kansa, miqewa tayi a guruguje tayi wanka ta fito ta shirya key din motarta ta dauka ta kama" hanyar fita Daidai kofar gate din Zainab ta dinga jiyo hayaniyarsu sai shewa sukeyi da fad'in gobe har d'an asharrale "zasu dauko su cashe! Motar ta kawai ta shiga ta fita daga gidan, kai tsaye kofar na'isa ta nufa." Lokacin data isa gidan Hajia da Ramlatu na zaune a palo suna hira Najaatu na daki tana bacci Halisa ta "samu guri ta zauna fuskarta a ba'ce! Hajia tace""Halisa Allah yasa dai lafiya na ganki da tsakar rana ina fata dai ba wata matsala bace. Halisa kasa magana tayi sabida tunda take bata ta'ba kawo kararsa" "gurin iyayensa ba ba dan bayayi mata laifi ba kawai tana hakuri ne amma hakika yau ya kaita bangon makura. Ta gaida hajian murya na rawa ta shiga sheda mata abunda yake faruwa, Tace""Saboda nace ya" mayar da Najaatu gidansa yake jin haushina kullum babu kalma mai dadi to yau dan nayi masa magana "akan hakkina dana yara ya farfad'a min magana iya son ransa Hajia wallahi ina hakuri da halin Abban mufida ina ganin zan tafi gida kawai na bashi guri.""" "Hajia tayi shuru tana nazarin maganar Ramlatu kuwa hasala tayi tace""Ai wannan yarinya fitinanniya ce" wallahi watakila ma ita ta hanashi yay muku komai aini tunda ta zugashi ya dauko min police ta fita daga "raina, kuma haka kawai saboda kin bashi shawarar arziki sai ya dinga jin haushinki to meye da Najaatun da yake gudunta.""" Najaatu jin hayaniya a falo yasa ta fito daga daki ta samu guri ta zauna tana kallonsu da so ta fahimci "inda maganar ta dosa. Halisa tace""Wallahi kuwa Yaya Ramlatu Abban Mufida wani iri ne yana son abu" "amma sai ya dinga nunawa baya so saboda nace idan ya tsaya wasa wani zai aureta duk da jegonta shine fa yake Jin haushina."" Hajia tace""Duk dai yanzu magana ta kare kiyi hakuri ki koma gida kada ki tafi gidanku idan yazo da yamma zanji dalilinsa na danne miki hakki maganar zuwa asibiti dama munyi dashi" "kancewar sai bayan suna hankali ya kwanta zai kaiki yace watakila ma dubai zakuje a dubaki sosai.""" Jin wannan magana da hajia tayi yasa Halisa taji sassaucin akan bacin ran dake zuciyarta sai ta miqe tana "gyara mayafinta da fadin ita zata tafi."" Hajia da Yaya Ramlatu suka sake tausarta akan kada tace fa zata je gida ta koma dakinta, nan ta tabbatar musu da cewar gidan zan ta koma insha Allah Bayan fitar" Halisa Najaatu tunani ta shigayi ta fahimci maganganun da Halisa takeyi a kanta wato saboda tace masa ya mayar da ita yake gaba da ita to ita kuwa wace iriyar kiyayya yake mata da har zai dinga gaba da wani a kanta. Allah sarki Halisa ashe yanzu tana kaunarta tunda gashi har tana cewa mijinta ya dawo da ita. jin hawaye na kokarin su zubo mata ne yasa ta miqe da sauri ta bar gurin. "Hawaye na sauka a kan kumatun ta ta zaune gefan gado tana tunanin abinda zai taimake ta, gabadaya ji" "tayi zaman gidan Alhajin ya fita daga ranta, ba dan komai sai dan tayi nesa dashi da duk abinda ya shafe" "shi tana ganin idan ya daina ganinta sai tafi martaba da daraja a idonsa, me yay zafi da har zai dauki fushi" da gaba akanta ashe dama haka kiyayyar ta tayi girma a zuciyarsa. yanzu idan tace zata koma "gidan Malam su hajia hankalinsu zai tashi kuma ba zasuji dadi ba sannan zasu dinga tunanin ko wani abun suke mata na rashin kyautawa yasa take gudun zama dasu, amma da badan hakaba da wallahi barin gidan za tayi domin ba taga amfanin zamanta a ciki ba" Tana wanka tana tunanin maganarsu da Mmn Sajida. Itafa gani take dukkanin wani abu na jan hankali "da za tayi masa bai zama lallai ya kalleta da qima da daraja ba , amma dai tana ganin zata kwatanta yin wasu abubuwan ko Allah zai sa a dace." "Shiryawa tayi tsaf! ta fito ta samesu har yanzu suna falon suna tattauna maganar, sai ta nuna tamkar ba" "taji abinda suke magana a kai ba. Hajia tace""Ya na ganki da hijabi ko gidan Malam zaki shiga.""?" "Tace""Eh inaso na shiga mu gaisa bayan na dawo daga gidan Lalle ('Kunshi) inaso nayi kwalliyar suna."" Hajia tace""Aikuwa yana da kyau hakan to da akwai kudi a gurinki ne."" Tace""Eh akwai wanda zasu ishe ni."" Yaya Ramlatu tace""To ko zaki bar Daddy a gida kyafi samun nutsuwa gurin zaman kunshin."" kokarin kwanto yaron take daga bayanta tana fadin "" Aikuwa kin kawo shawara mai kyau Yaya Ramlatu dan yana iya rikice min da rigima ya hana lalle na yayi kyau. Yaya Ramlatu ta kar'be shi da zanin goyonsa ta miqe tana kokarin goya shi a baya tace""Ai har kyaje ki dawo yana baya idan ya tashi a bacci sai a dama masa madara."" Hajia tace""Duk da haka dai kada ki zauna kada a shiga hakkinsa."" Tana kokarin fita tace""Insha" Allah bazan jima ba zan dawo. Gidan Lallen kabuga ne kuma lokacin da taje akwai mutane dan ma mai lallen kawar Salimat ce "budurwar Salim wacce a lokacin auranta da Bash yasa ta gane gidan.....Dalilin wannan sanayyar yasa Bilki mai kunshi ta tsallake mutanan dake gabanta ta kama kafafun Najaatu tana yi mata, aikuwa jamaar dake gurin suka dinga surutu kowa na ganin an shiga hakkinsa. Tace"" Dan Allah kuyi hakuri na" "bar karamin yaro ne a gida kuyi min uziri.'' jin haka yasa wasu suka daina magana wasu kuwa fushi sukayi suka tafi.....Bilki ta dauki lalle mai tsayi da ado da yawa, Najaatu tace""Bilki da kinyi min takaitacce tunda kinga akwai jamaa a gabanki."" tace""na riga na dauki mai ado dole kema sai kin jure zama.'' shuru" kawai tayi ta zubawa kafafunta ido wanda bilki ke zane su da jan lalle. Kafafuwa da hannuwa akayi mata jan lalle mai kyau da burgewa sosai kunshin ya dauki hankulan jamaar dake gurin suka dinga so ayi musu irinsa. Sai bayan biyar da Rabi na yamma sannan ta cire lallen ya wani fito rad'au a kafafunta na hannun ma "yayi abun burgewa, Najaatu sosai tayi farin ciki da yanda Bilki ta fito da ita kamar wata amarya. Dubu" biyar ta bata saboda jin dadin abinda tayi mata bayan haka kuma zuwanta yasa wasu costoms din sun "tafi shiyasa ta bata wannan kudin Ta jima a bakin titi tana neman abun hawa bata samu ba, da" "yake yamma tayi duk 'yan kasuwa sun tashi tun daga mandawari ake fama da goslow har titin kabuga gurin ya had'e sosai masu motocin gida dana haya kowa na kokarin wuce wa, da kyar ta samu a daidaita sahu wanda zaije kofar na'isa amma kuma duk maza ne a ciki su biyu Ganin bata da mafita" "yasa kawai tayi kundubala ta shiga, aikuwa samarin nan suka dameta da hira da yake aboki da aboki ne duk a tunaninsu sun dauka budurwa ce wai dan Allah ta basu number wayarta, Najaatu shuru tayi musu tayi bala'in shan kunu! na kusa da ita ne ya kalli hannunta data dora a jikin k'arfen adaidata sahun yace""Baby wannan lallen yay kyau nawa ne kudinsa na biya gaskiya kina da kyau gaki da aji wallahi kin" "burgeni kuma ina shaawar auranki.""" "Tace""Kai dan Allah ku kyaleni da surutu lalura ce ta fito dani kuma ni ba budurwa bace matar aurece." "Dariya kawai sukayi suna fadin""Aikwai 'yan mata irinki da yawa masu kiran kansu da matan aure amma" basu bane matar aure ta fita daban baby Takaici yasa tayi musu shuru tana Allah Allah ta sauka. kawai sai taji suna cewa mai adaidata sahun kada ya saukesu a inda zasu sauka suna so su "rakata gida....Gabanta ya fadi ta kallesu rai a bace tace""Wallahi zaku janyowa kan ku wato na fada muku ni matar aure ce kuna gaddama ko okey."" Daga haka sai kawai taja bakinta tayi shuru ta kyalesu tana jinsu suna ta dariya da surutai a kan maganarta." Ana kokarin shiga massalaci domin sallar magariba adaidaita sahu ta tsaya a kofar gidan alhaji Motar "Abbah Abbas da taga ni a fake a inda ya saba ajiyewa yasa gabanta ya tsananta faduwa. Tana kokarin dauko kudi a jakarta ya fito daga gidan Alhajin fuskarsa tamkar hadarin dake dab da zubar da ruwa, tunda yazo gidan ya samu yaro na kuka da neman uwarsa ransa ya 'baci ya tambayi Yaya Ramlatu ina take? tace Ta tafi gidan kunshi Ai sai ya shiga surfa mata masifa kamar ubanta harda cewa rashin" "hankali ne da zata kama d'aukar yaro ta rabashi da uwarsa yini guda saboda haka ai sai ta daukeshi ta kaiwa uwarsa kada su kashe shi."" Ya Ramlatu ta dinga mamakin tsawar da yake buga mata sai so take ta fahimtar dashi yaki fahinta wai itama ta mayar da kanta karamar yarinya mara tunani, Hajiya da taga abun nasa naso ya wuce gona da iri tace""To wai kai ina ruwanka ne? ko auran yarinyar nan kake da zaka takura mata kunshi ta tafi domin ta gyara kanta kuma bamu dauka yaron nan zai tashi ya dinga rigima irin hakaba itama watakila rashin abun hawa ne ya tsayar da ita dan haka abar maganar haka uwar yaron itama nasan tana can hankalinta a tashe. Cikin wannan 'bacin ran ya fito daga gidan sai kuma" yaci karo da wani dan samarin nan sun kewaye ta sun hanata wucewa wai sai ta basu number. Ganinsa yasa ta kid'ime! pose dinta ta fad'i ta sunkuya dauka saurayin shima ya tsuguna hannunwansu ya hadu guri daya. tana dagowa ta wanka masa mari jiki na kyarma ta dauki pose dinta ta barsu a gurin Komai a "kan idonsa ya faru yana kallonta tana tawowa yana ji kamar idan ta karaso yayi wurgi da ita saboda jin wani mahaukacin kishi dake taso masa, gifta shi tayi da sauri ta tura karamar kofar gidan ta shiga gabanta sai wani irin bugawa yake matasan samarin nan kuwa adaidata sahun suka shiga takaici" kamar ya kashe su su basu samu number ba gashi sun sha mari amma babu komai tunda sunga inda ta shiga watarana zasu kawo mata ziyara dansu basu yarda matar aure ce. Abbah sai da yaga Adaidata sahun ya bar gurin sannan ya wuce cikin massalaci yana jin wani irin zafi a cikin zuciyarsa. Najaatu na shiga gidan taji yo muryar daddy nata zabga ihu! da sauri ta shiga falon ta tarar dasu sunyi cirko cirko hajia rabi na rike da waya a hannunta tana kokarin nemo number. Sallamarta yasa duk suka "kalli bakin kofar shigowa Ya Ramlatu ta karasa gurinta da sauri ta miqa mata yaron da fadin""Kar'beshi kada azo a tafi dani yanzu yanzu aka gama cin mutuncina.""" "Hajia Rabi tasa dariya da fad'in ""Wallahi Ramlatu baki da dama waye zai tafi dake.""? Rike baki tayi tace""" Haba Hajia kina kallonsa fa ya dinga zazzaga kamar zai doke ni ke kyace shine yake gaba dani wallahi Abbas ya raina ni sosai amma babu komai. "Najaatu taji tausayinta ya kamata tace""Dan Allah Yaya Ramlatu kiyi hakuri wallahi dana san zan dade" "gurin k'unshin nan da na tafi da yaron nan yau goslow akayi sosai da kyar ma na samu abun hawa."" Hajia tace""Nima sai da na zargi haka wallahi to me yasa baki kira Dan Azimi yazo ya daukeki ba."" Tace""Gabadaya hankalina bai kai nayi tunanin hakaba wallahi." "Hajia Rabi tace gashinan kuwa kwalliya ta biya kudin sabulu kunshin yayi kyau sosai da sosai."" Najaatu ta" "nemi guri ta zauna tana kokarin ciro nono tasawa yaron a baki tace""Wai ma duk da haka akwai wanda suka rigani darajar Salimat budurwar Salim naci akayi min da wuri."" Hajia Rabi tace"" lallai zuwa gidan 'kunshin sai mutum yayi da gaske...Hajia tace""Aikuwa dai kafin ayi kwalliya sai an ji jiki mu lokacin mu idan muka daure kafafun mu da lalle shikkenan bukata ta biya mu wayi gari rad'au damu amma zamani yanzu komai ya sanja Allah ya kyauta."" tana ta gama maganarta miqe da niyyar zuwa tayi sallah Yaya Ramlatu da hajia Rabi ma tafiya sukayi sallah suka barta ita kadai a falon tana shayar da d'anta tare da tunanin irin kallon da taga Abbah Abbas nayi mata a d'azu! yanda taga fuskarsa a murtuke yasa dik" hankalinta ya tashi tana tsoron ya shigo yay mata fad'a. Tana kokarin barin falon ya shigo Tayi saurin sunkuyar da kanta gabanta na fad'uwa. Nasa 'bangaran "ganin nonota guda a bayyane yasa hankalinsa ya tashi sai yaji gabadaya ma yana nema ya rasa karsashinsa. Najaatu sam ta manta tana shayar da d'anta nono shiyasa bata gyara ba, Da kyar ya karasa" "shigowa yana ta bin ta da kallo 'kunshin dake kafafunta da hannayenta ya tsirawa ido, yayi masa kyau a ido, dauke kansa yay daga kallon kafafunta yay gyaran murya kamar koda yaushe Yace.""Najaatu wane irin rashin hankali da rashin imani ne yasa zaki tafi yawon banza ki bar yaro karami irin wannan a gida yay ta kuka kin san hakkin d'an adam kuwa.""? A kausashe yay maganar. Ta dan kalleshi tana zum'bura" "baki tace""Abbah ba yawo naje ba naje gurun 'kunshi ne."" Da sauri yace.""Wa kika ajiye da zakiyi wa kwalliya ko kina da miji ne.""? Gabanta ya fadi ta kalleshi tace""Sai ina da miji zanyi kwalliya ai mace da" "ado aka santa.""" "Yace."" Sam Ban san da wannan maganar ba kawai dai kin fita ke kad'ai ne dan ki samu samari kuma na" gani kin samo to mutukar yawo zaki dinga fita kina barin yaro zan samu Baba malam na sheda masa abinda kikeyi nasan shi zakiji maganarsa tunda ni kin raina tawa maganar saboda kina samun daurin gindi a gurinsu hajia! dan haka wannan itace maganata ta karshe da zanyi miki kada ki kuskura ki kara "barin yaro a gida ki fita yawon zagayen samun zawarawa.""" "Kuka take sosai tace""Wai dan Allah Abbah wannan wace irin magana kake kana kallon 'kunshi fa a" "kafafuna amma kake cewa ina tafiya yawon samo zawarawa ashe har sai na fita zagaye bazawari zai biyo ni ni ba'irin wannan zawarawan bace ko yanzu nayi niyyar aure sai nayi saboda inada wanda zan aura a hannu."" Ta fadi wannan maganar ne danta tunzura shi, aikuwa ya tunzuru ya dinga zazzaga mata fad'a da fad'in ""kamar shi zata sashi a gaba tana yi masa rashin kunya to zai fita harkar ta tunda ta zama 'yar" "kanta, fad'a yake mata sosai harda miqewa tsaye kishi na nema yasa ya fad'i a gurin." "Hajia ta sauko daga sama da sauri tana fad'in ""me yake faruwa ne wannan fad'a da kake yi kwana biyu" "ya isa fad'a a gida fad'a a inda bai dace ba to ita kuma Najaatu mai tayi maka.""?" "Zama yay kan kujera yana numfarfashi, ya cire hularsa ya ajiye kawai ya shiga girgiza kafafunsa. Najaatu" daukar d'anta tayi ta bar gurin tun kafin zuciyarta tayi bundiga. Hajia ta kalleshi tana so ya samu sassauci ta fad'a masa hukuncin data yanke dan ta gaji da wannan hargagin da yake....... "78***Hajia sai da ta tabbatar da cewar ya dawo cikin hayyacinsa sannan ta fara magana kamar haka.""" "'Dazu da safe Halisa tazo gidan nan cikin 'bacin rai tare da qudirin tafiya gidansu akan abubuwan da kake a gidanka na rashin kyautawa to naji ta banki ta kuma na rarrasheta tayi hakuri ta koma gida inaso kai ma yanzu naji ta bakinka kan abunda ke faruwa a tsakaninka da ita.""" Shuru yayi yana mamakin maganar Halisa ta kawo shi qara gurin mahaifiyarsa akan wani dalili me yay "mata mai zafi da zata kawo kararsa gaban mahaifiyarsa, Hajia ganin yay shiru yasa tace""Kai nake saurare.""" "Ajiyar zuciya ya sauke kafin yace.""Hajia a zahirin gaskiya ni ban san abinda nayi mata wanda ya sanya" har ta kawo miki ka'ra ta wannan shine dalilin da yasa kika ga nayi shuru ina mamakin maganar saboda d'azu da safe lafiya lau muka rabu na tafi kasuwa. "Hajia tace""To ita kuma tace min akan tace ka mayar da Najaatu gidanka ne kake jin haushinta wanda" "dalilin wannan maganar da tayi maka yasa kake gaba da ita sannan baka siya mata abin futar suna ba.""" Shuru yay bakinsa ya mutu lallai Halisa bata da kirki shi zata tonawa asiri baiyi tsammanin zata iya kawo "kararsa akan wannan dalilin ba, tabbas daya san abinda zata aikata kenan toda ya tsaya ya saurareta sun rabu lafiya, duk sanda zai tunu da furucinta a kan Najaatu sai yaji wani irin mugun haushinta ya rufeshi shiyasa ya watsar da lamarinta ya'ki siya mata komai ya kuma ki bata kudi duk da yasan zata bukace su" domin tayi hidimar haihuwar Zainab dasu. Hajia ta cigaba da cewa''Yanzu meye laifin Najaatu da har zaka dinga gudunta haba kai kuwa! wallahi mu "duk mun dauka kana da qudirin mayar da ita dakinta dan ganin irin hidimar da kake mata ashe kai ba haka abun yake a zuciyarka ba, menene abun gudu a tare da yarinyar kayi hakuri ka tausaya mata ita da" d'anta ka mayar da ita dakinta komai ya wuce ni a matsayina na wacce ta haifeka nake baka umarni akan "haka Najaatu matar arziki ce sannan dukkanin abunda ya faru tsakaninka da ita qaddara ce da rabon wannan yaro da take goye dashi, dukkaninmu idan yarinyar nan ta koma dakinta sai munfi farin ciki akan ta sake wani auran.......Sannan sai magana akan Halisa inaso itama kayi mata abunda ya dace duk da ba itace ta haihu ba yana da kyau kayi mata wani abun wanda zai faranta zuciyarta haka akasan adalin" "namiji.""" Abbah Abbas kasa cewa komai yayi dan gabadaya Hajia ta gama kashe masa jikinsa da maganganunta "tabbas bashi da yanda zaiyi ya bijirewa umarninta dole ne ya mayar da Najaatu dakinta tinda ta riga ta umarce shi Hularsa ya dauka yasa yace.""Shikkenan Hajia tunda kin bukaci da ayi hakan za'ayi insha" Allah ina rokon Allah yasa hakan shine alkairi maganar Halisa kuma idan na koma gida zan zauna da ita insha Allah. "Hajia tayi murmushin jin dadi tace""To nagode sosai da wannan alfarmar da kayi min baka bijirewa" umarnina ba naji dadi kwarai da gaske ina maka fatan alkairi tare da samu farin ciki har karshen rayuwarka. Ya amsa da ameen ya rabbi hajia babu wani abu da zaki nema a gurina na kasa yi miki saboda nasan kome na zama a duniya ta dalilinki ne da tasirin aduoin da kike min saboda haka insha Allah Najaatu zata koma dakinta kamar yanda kika bukata amma inaso yaron yay wayo tukkuna sai ayi maganar daurin "aure.""" Hajia tayi shuru tana nazarin maganarsa Eh hakan kamar shine maslaha amma kamar za'a ja dogon "lokaci Tace.""To shikkenan hakan yayi Allah ya nuna mana lokacin da zata yaye yaron sai a d'aura auren" "ko kuma dai za'a daura auran kawai sai tayi zamanta a gida idan ta yaye yaron sai ta tare.""" "Yace.""A'a bari dai ta yaye shi tukkuna ina ganin hakan kamar sai yafi.'' Baya so taje ta dauki ciki ga" k'aramin goyo yaron zai iya lalacewa shiyasa yace haka. To itama hajian ta fahimci abinda yake nufi sai "tace""To Allah ya nuna mana....Miqewa yay tare yi mata sallama, a sauka lafiya tayi masa tare da bada sakon gaisuwarta gasu Saddaqa........lokacin daya shiga gidan samun Halisa yay a qame a kujera tayi kici" "kici da fuska, tsaf ta shirya masa da duk wani tashin hankalin da zai shigo dashi" Ganinta cikin shirin ko ta kwana yasa ya sassauta fuskarsa domin baya neman wani bala'i yaji ma da "wanda ya shigo dashi gidan, sai kawai ya shige dakinsa ba tare da ya tanka mata ba." K'wafa tayi tana girgiza kanta ta dauka zai shigo da bala'i sai taga akasin hakan tayi murmushi cikin "zuciyarta tace""Ashe abun rainin hankali ne da samun sake to daga yanzu idan kayi min abunda be" gamsar dani ba xan tunkari mahaifiyarka na fada mata magana ta qare...'Kin tashi tayi tabi bayansa har "ya gama abunda yake ya fito cikin jallabiya ruwan toka Kusa da ita ya zauna yana kallonta yace.""" "Abunda kikayi kin kyauta kenan? abunda ba kiyi da kuruciya ba shine yanzu saboda shashanci zakiyi gabadaya kishi ya rufe miki ido kin manta ke irin abubuwan da nayi miki a baya sabida kawai kinga kayan haihuwar Zainab kin tashi hankalinki harda zuwa ki fad'awa hajia laifina bana muamular arzki dake saboda kince na mayar da Najaatu naqi shine nake gaba dake ko? Kallonsa tayi tace""Ai ba qarya nayi ba baka kulani baka cin abincina"" Yace ""cikin nida dake waye gaba da wani? wa ya cancanci ya d'urkusuwa" "dan uwansa""." "Murmushi tayi tace"" Abinda yake faruwa kenan tsakanin ma'aurata wai dan Allah Abban mufida me yasa" kuke da iko ne sau nawa ina maka magana ina girki ina ajiye maka baka ko saurarata ballantana kaci abincina akan kawai na baka shawarar arziki ashe kai so kake nai ta binka ina baka hakuri alhalin ni na nayi maka alkairi ka mayar min da sharri wallahi banga laifin da nayi maka ba wanda zai sanya nayi ta "baka hakuri ba.""" "Yace.""Ya isa haka! maganar dawo da Najaatu ce dai duk ta janyo wannan abu to sai hankalinki ya kwanta" "hajia ta bani umarni na dawo da ita shikkenan magana sai ta qare.Tace""Abbahn mufida kenan koda hajia bata baka umarni ba to kai zaka bawa kanka umarni dan haka kamar yanda kace a bar maganar an barta kai da Najaatun ina muku fatan alkairi tare da zaman lafiya mai d'orewa. Cikin ransa ya amsa da ameen" "kafin gurin yay shuru na minti uku. Gyaran murya yay yace.""Yanzu me kike bukata."" Tace""Yanzu kuma" "lokaci ya qure ai gobe suna mai zanyi da kudi.""" Yace duk da haka hakkinki ne ai ko bayan suna zaki iya amfani dasu ta wata hanyar sabida haka kema "zan sa miki kudi a account d'inki shikkenan na fita kada ki sake zuwa kice ina tauye miki hakkinki dan ni duk neman da nake akan iyalina nake banga abunda zai hanani na faranta muku rai ba.""" "Halisa akayi murmushi ana wani girgiza jiki ""To nagode sosai Allah ya qara budi na alkairi."" Amsawa yay" da amin ya miqe tare da fad'in zai shiga gurin Zainab ya dubata. "Ba tace masa komai ba har ya fita daga dakin, lallai zuwa gurin hajia yayi mata amfani tunda gashi nan ya" zauna suna maganar arziki babu hayaniyar daya saba. "Zainab maijego tayi shar shar da ita, mai kitso da lalle ('kunshi) har gida tazo tayi mata kitson" attaccement mai uban yawa sannan akayi mata jan lalle da baki gabadaya faratan ta tasa musu (jan farce) sai kace wata inyamura dan gabadaya kammanin ta sun sanja. Tana zaune ita da masu taya ta zaman jego sai hira suke tare da shirye shiryen yanda shagalin bikin suna zai kasance dan har sun biya "mai d'an Asharrale (DJ) kudi zai zo da yamma ya baje kolinsa, abunda sukeyi tamkar ba 'Ya'yan shehin malami ba." Ganin ya shigo dakin yasa suka shiga gaisheshi suka fita daga dakin da sauri. "Zama yay kusa da ita yana kallonta cike da mamaki yace.""Wannan wane irin kitso ne akanki irin na arna" "shin nauyin abinda akayi miki kitson dashi baya damunki sannan kin saka wani abu a faratanki ko kyau ba suyi miki ba, dan Allah idan za kuyi kwalliya kusan irin wacce zaku dinga yi." Zainab jikinta yay sanyi jin yanda ya gwale mata kwalliyarta sam bata dauka zai ga rashin kyawunta ba kasancewar ta sanshi shi ma'abocin san ado ne. "A sanyaye tace""Ai sabida nasan bana sallah yasa nayi kitson attachment sannan nayi ado da jan farce." "Yace.""Duk da haka zaki gayyato shedanu jikinki wannan kwalliyar da kuke ita kesa sanyawa abubuwa da" "yawa su faru daku ina laifi ma da kikayi 'kunshi amma meye na rufe farcenki da wani jan abu.""" "Zainab tayi shuru yace.""Gobe da safe ki kankareshi dan baiyi miki kyau ba sannan wannan uban gashin" "dokin da kika sa a kanki ana gama taron suna ki kwance shi bazan lamunci shigowar shed'anu gidana ba. Tace""Abbah Mufida kitson nan ansha wuya kafin ayi kuma dubu kusan ashirin na biya akayi min ya" za'ayi kace na tsefe! "Yace.""Babu ruwana da kudin da kika biya ni dai umarni na baki."" Zainab ta shiga halin damuwa, babyn" "dake kwance a kusa da ita ya dauka ya dubata sosai ya ajiye ta tare da miqewa hanyar futa ya nufa....Tace.""Abbah Mufida dama ina so na fad'a maka cewar su aunt Hauwa sun gayyato mai DJ zai zo" "yay mana da yamma.""" "Yace.""Waye me DJ. ""? Kai tsaye tace"" Ina nufin mai Dan Asharrale inaso ka bani kudin li katse ta yay" "da sauri yace""A gidan nawa za'a buga min DJ.""? Dawo yay ya tsaya a kanta ya wani tamke fuska yace""Wai shin Zainab kin manta daga inda kika fito ne na lura gabadaya dake da 'yan uwanki duk shagalallu ne kun fito daga tsatso mai kyau amma kuna neman ku shagala wannan abubuwan da kuke na tabbata Ya sheik bai sani ba to ni da kaina zan sanar masa dan ni ba irin shashashan mazan da 'yan uwanki ke aura bane in banda rashin hankali har ki dube ni kice zaki kawo min 'Dan Asharrale yazo yay me? To kada ki kuskura wallahi tun wuri su da suka gayyoto shi su dakatar dashi dan mutukar yazo min gida sai na daureshi sannan kema na baki mamaki."" Zainab ta dinga kuka tana bashi hakuri tsabar 'bacin rai yasa ko sauraranta baiyi ba ya kada kansa ya fita da dakin yana mamakin al'amarin ashe da yarinyar nan bata fad'a masa ba da sai dai ya samu labarin zuwan Dan Asharrale gidansa. da kuwa ya dauki" tsatstsauran mataki a kanta dan ba zata kawo masa bidia a gida ba. Washe gari ranar suna yarinya taci sunan kakarta Hajia Zainab (Abu) sai ya kasance Yarinyar ta amsa sunan mamanta da kakarta amma dai shi uban 'yar sunan babarsa yasa kai tsaye kuma yace a dinga kiranta da Ummi Hajia taji dadin samun takawara ta dinga murna tare da adduar Allah ya raya mai "sunanta..........Bangaran Najaatu kuwa da tayi alkawari kan cewa babu inda za taje, sai kuma daga" baya tayi wani tunani tayi sauri tayi shiri na mussaman ado da kwalliya tayi mai k'ayatarwa ta fito falo tana zabga kamshi turarruka masu kamshi da daukar hankali... Nan ta samu Ya Ramlatu da wasu daga cikin Family din Hajia suna zaune ta gaisa dasu a mutunce! Ta "kalli Ramlatu da fad'in."" Ba yanzu zamu tafi bane.""? Ya Ramlatu tace""ko kawai kibi hajia Rabi ku tafi kada rana tayi ni zan jira zuwansu Hajia Rakiya sai mu had'u gabadayanmu mu biyo bayanku." "Tace""To shikkenan, sama ta hau tayi sallama da hajia ta sauko Ya Ramlatu tace"" Daddy tunda yay bacci" a bayana to ki barshi kawai na tawo dashi. "Tace""Kada fa ya tashi yayi miki rigima irin na jiya." "Dariya ta d'anyi tace""Ba zai tashi ba insha Allah ai su Hajia Rakiyan suna hanya muma ba zamu dade ba" zamu biyo bayanku. Tace to shikkenan sai kin tawo. Naja'atu tana sane ta yafa qaramin mayafi mara sirri ga yanayin dinki jikinta riga da siket sun matseta swiss les ne mai tsada amma tasa anyi mata matsatstsan d'inki! tana sane tasa kayan saboda tasan baya son suyi irin shigar su fita da ita.. "Taji dadin ganin dukk motocinsa a harabar gidan da alama bai futa ba, kai tsaye bangaran maijego suka" nufa. 'Yan uwanta ne duk a gurin suka gaisa a tsaitsaye suka wuce ciki. Zainab tayi kyau har ta gaji kana ganinta kaga matar Alhaji gold yaji a ko'ina ga wata uwar shadda tasa "wacce taji uban surfani irin na manyan mata...Najaatu kallo daya tayi mata ta dauke kanta, kishi ne yake taso mata tana danneshi...To itama Zainab din nata bangaran ganin zahirin Najaatun ya firgitata jikinta yay sanyi dan bata ta'ba tsammanin cika da kasaitarta ya kai hakaba ashe cikakkiyar macace abar" alfaharin ko wane da namiji lallai hijabi ba karamin sururta mace yake ba. Ta dinga satar kallon Najaatun tana jin wata shakkarta gabad'aya bata so ta had'u da mijinta dan kada ya 'kyasa (Maman Hanan kinga mutuniyar ki ko sai kace tsinken sakace sai iyayin tsiya) Najaatu na "hankalce da irin kallon da take mata sai kawai ta miqe da fad'n ""Hajia bari na shiga gurin Aunty Halisa mu gaisa." "Hajia Rabi tace"" To shikkenan nima zan shigo yanzu insha Allah."" Najaatu ta juya tana wata iyar tafiya ta" taqama! Zainab kasa dauke idonta tayi daga kanta har ta fita daga dakin. "Da sallama a bakinta ta tura kofar falon ta shiga, Abbah Abbas na tsaye a tsakiyar falon yana magana da" Saddiqa Halisa kuma na zaune a kan kujera tayi ado daidai misali Mussadiq da Mufida na kusa da ita a zaune. Ganin shigowarta yasa yaran suka ruga a guje suka rungumeta suna murna...Halisa na murmushi "tace""Najaatu ke kika fara zuwa kenan sannu da zuwa karaso ki zauna." A nutse ta riqe hannun Mussadiq suka karasa falon ta samu guri ta zauna a nutse ta kalleshi yana tsaye a "inda yake yana mata wani irin kallo mai kama da harara ita tasan ko kallon menene sai ta basar tace""Abbah ina kwana? 'kin amsawa yay ya kalli Saddiqa da fad'in ta tashi maza taje gurin Zainab tace ta duba masa gilas d'insa a dakinta, Saddiqa tayi saurin miqewa domin tafiya aiken da yayi mata, Najaatu ba tayi zuciya ba ta sake gaishe shi, a dakile ya amsa ya bar gurin... murmushi kawai tayi ta juya suka" cigaba da magana da Halisa...... *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abun yake Vip gruop#600 normal group #300 account..... 0542382124...Binta umar gtbabk...Idan kati zaki tura kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number. *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* "79******Halisa na murmushi tace"" Ya kuma naganki a haka ina kika baro maigidan nawa.""? Tace""Yana" "goye a bayan Yaya Ramlatu lokacin da zamu tawo yana bacci shine tace na kyaleshi kawai ta tawo dashi."" Halisa tace"" Ayya amma kin shiga gurin maijegon ko.""? ""Eh Hajia Rabi ma can na baro ta."" Shuru falon yayi kowa yana tunani a cikin ransa. Kamshin turaransa ne ya sanya dukkaninsu suka dago kai" "suna kallonsa, Najaatu kallon sharia kawai tayi masa tayi kasa da kanta tana jin wani irin yanayi a jikinta," "a duk lokacin da zata kalleshi sai sonsa da kaunarsa sun sake karuwa a cikin zuciyarta, Abbah Abbas" "kwata kwata baya tsufa kullum kara masa kuruciya ake babu wanda zai kalleshi yace yayi shekara hamsin a duniya saboda shi mutum ne dan gayu mai kula da kansa, Yanzu ma yayi ado cikin wani had'addan filtex irin na maza dark blue abinka da farin mutum sai yayi masa wani irin kyau, hula mai farin zanen zare yay amfani da ita, kafarsa sanye da takalmi sau ciki baki sai shaninig yake, farin gilashin da yake sakaye a idonsa yayi masa masifar kyau, Najaatu ta dinga jin wani irin sanyi na ziyartar jikinta sha'awarsa ce take taso mata a jikinta sai ta shiga tunawa da irin zazzafar soyayyar da ya dinga nuna mata a lokacin da suke tare.......Muryarsa taji yana magana...""Yau ma kin bar yaron nan a gida ko ashe ke ba'a isa a fad'a miki magana guda kiji ba? yanzu meye amfanin saka wannan mayafin na jikinki da kin" sani kin yar dashi a hanya dan bashi da wani amfani tunda gashinan a zahiri komai na jikinki ana gani. Shuru tayi ta kasa magana ba wai dan bata da abinda cewa ba kawai tana ganin kamar shurun shi yafi amfani saboda gudun kada ta fada masa wata maganar yace tayi masa rashin kunya. "Halisa tace"" Ni sai nake ganin ai ba wani abu bane dan ta bar yaron a gurin Yaya Ramlatu tunda yanzu" zasu zo maganar hijabi kuma ka ajiyeshi a gefe yau daya dan tasa mayafi ai ba laifi bane tunda bata da nauyin kowa a kanta kuma ni wallahi banga abunda mayafinta ya nuna ba. tana yar dariya ta karashe maganar. "Yace."" Ni na gani ai tunda ke baki gani ba, sannan ni nasan tana da wata munufa ta yafa mayafin tunda" "keda ita duk kun san bana son irin wannan mayafan marasa sirri saboda haka idan zaku tafi ki kar'bi hijabi gurin Halisa ki suturta jikinki baki burgeni ba idan dani kikayi Halisa tace""Ikon Allah shikkenan" "sai tayi kwalliya dan kai kad'ai bazawara ce fa kuma kowa yasan zawarawa da 'yan mata gurin ado da kwalliya me zai sanya ka damu kanka. Yace.""Ai shine abinda nake so ki fahinta ta bud'e tsaraicinta ne" "dan ni ko wani a waje ya gani yaji sha'awa to ni duk irin wannan basa burgeni.""" "Jin abinda yake cewa ne yasa tace""Haba Abbah yanzu dan Allah ina tsaraici anan.""? Tafada tana cire" "mayafin jikinta tare da gyara zamanta a kan kujerar. Saurin dauke kansa yay sakamakon ganin tudun nonowanta da suka fito ta saman riga. Aunty Halisa tace""To nima dai haka na gani wallahi."" Najaatu ta" "cigaba da cewa""Wallahi ni banyi kwalliyata dan kowa ba dan kaina nayi kuma Aunty Halisa ni bazan fitar" "da tsaraicina saboda na samu mijin aure ba saboda nasan ko yanzu na bukaci aure zanyi tunda ni nasan kaina ba k'aramar mace bace.""" "Halisa ta dinga dariya tana kallonsa yana tsaye yana kallonsu, kowa dai yay zagi a kasuwa yasan da" "wanda yake, shuru kawai yay musu ya zauna kan kujera mai cin mutum daya, agogon hannunsa ya duba, ya kalli Mussadiq dake fama da game yace""Jeka gurun Zainab kace tazo amma tazo da baby Ummi.""" Yaron ya ajiye game din da sauri ya tafi aiken da akai masa. "Abbah shuru yay yana jin Halisa na fad'in ""Najaatu kin birgeni wallahi ai dama nace ke ba k'aramar mace" "bace koda baki sa mayafi ba ya kasance kullum a cikin hijabi kike na tabbata ba zaki rasa miji ba haba ai ido ba mudu ba yasan 'kima.""" Shiru yay bai tanka ba dan ya lura Halisa naso ta tona masa asiri a gurin yarinyar shiyasa yaja bakinsa yay shuru ya shiga girgiza kafafunsa. Halisa kallonsa take a fakaice tana 'boye dariyarta ita wallahi idan yana muzurai a kan rashin gaskiya dariya yake bata wai shi lallai ba zai fito fili ya nuna cewar ya damu da yarinyar ba alhalin duk gashinan ya nuna alama a zahiri kowa ya gani. Zainab ta shigo falon rugume da 'yarta ganin Halisa da Najaatu na hira cikin fahimtar juna yasa taji "haushin hakan, dauke kanta tayi ta nufi gurun mijinta. Baby Ummi ya kar'ba daga hannuta ya" "rungumeta a gefan hannunsa na hagu sai ya janyo zainab din ya d'ora a cinyarsa, ya rike kungunta da hannunsa na dama wayarsa ya bata yace tayi musu hoto Wannan al'amari ya duguzunma zuciyar" "Najaatu da Halisa ba kamar najaatu da taji gurin na juyawa da ita, Ita kuwa Halisa d'aga murya tayi" "tace""Me yasa ba kaje can gurinta kunyi hoton ba ai ina ganin kamar hakan sai yafi armashi.""" "Yace.""Akwai jamaa a gurun ne ko banda ikon nayi abinda nake so a inda na gada dama."" Ta'be bakinta" "tayi tace""Aa kayi komai babu damuwa ai.""" "Ya kalli su Saddiqa da fad'in su taso suzo gurinsa, yaran suka kewaye shi Zainab na zaune daram! a" "cinyarsa tana ta daukarsu a hoto farin ciki kamar ya kasheta hakika tayi farin ciki da yanda ya nuna musu cewa ita mai muhimanci ce a rayuwarsa, in da shi kuma anasa bangaran da biyu yake haka duk dan ya cuzguna musu, aikuwa ya hango tsantsar kishi da tashin hankali a idanun Najaatu dan har ja idanunta sukayi saboda tsabar bacin rai da takaici Sai da suka gama dauke dauke hotonsu sannan yazo inda" "suke zaune da yake duguwar kujera ce sai ya shiga tsakaninsu, Najaatu kamar ta miqe ta bar gurin haka taji sai dai ta daure ta matsa gefe saboda jin yanda ya takureta. Baby Ummi ya kar'ba ya riqe yasa su" "Saddiqa suka shigo kowa ya tsaya, sannan ya umarci Zainab din ta daukesu, hakan be mata ciwo ba saboda tasan ita ya fara nunawa muhimanci.....Zainab tayi musu kusan biyar ta miqa masa wayar, tare da fad'in ""Zata koma gurin 'yan uwanta! Babyn ya miqa mata tare da fatan a tashi taro lafiya. Ta 'karbi" 'yarta ta tafi ba tare da ta kula kowa a gurin ba. Shima tana fita ya miqe daga tsakiyarsu ya kama "hanyar futa, babu wanda ya kulashi sai yaransa sune sukayi masa adawo lafiya." Ya amsa cike da walwala da farin ciki yasan yau da Halisa Da Najaatu dukkaninsu ba zasu yini cikin farin "ciki ba, wato harshi zasu sa a gaba sunawa dariya sun mayar dashi sakarai shiyasa yay musu haka. bayan fitarsa Najaatu mamaki take sosai da yanda Halisa tayi sanyi yanzu gabadaya ta mayar da rayuwa ba wani abuba, idan da lokacin baya ne ai bai isa yayi mata irin wannan rashin kyautawa a falonta ba gaskiya kamar da akwai cin fuska a ciki sai taga kamar ma ita ta fita jin haushin al'amarin amma dai" yanda ta dauke kanta daga kan abunda yayi yasa taji ta burgeta mutuka Taron sunan Zainab yayi kyau ya kuma k'ayatar anci ansha maijego ta fito sosai dan sai da tayi shigar kaya kala goma cikinsu duk babu na yarwa abunda yay musu cikas kawai rashin Dan Asharrale amma dai duk da haka ba suyi bikin Lami ba sai da suka saka (Mp) mai kid'an tsiya suka dinga jin wakokin *Gwanja* suna cashewa sai rawa suke suna murguda mazaunai maijego dadi ya isheta ta dinga yi musu liki Gabadaya d'abi'un 'yan uwan Zainab na banza ne 'ya'yan malam ne amma kuma sunqi halin malam rashin arziki kawai suke yanda ransu yake so. *BAYAN SATI BIYU* "Al'amura suna ta gudanawa yanda ya kamata, ta bangaran Najaatu ta bude wuta sosai da ado da" "kwalliya da ta daidaici lokacin zuwansa gidan zata fito ta zauna kan kujera tana baza kamshi tururuka...Ita kanta hajia sai da taji dad'in salon da yarinyar ta tsiro dashi tasan tabbas yin hakan zai sake janyo hankalinsa kanta, aikuwa dai a tsakankanin kwanakin daurewa kawai yake yi amma yarinyar na mutukar galabaitar da zuciyarsa dan dai kawai mutum ne mai dauriya da dauke kansa a kan abu shiyasa baya bari kowa ya gane halin da yake ciki, duk sanda zai shiga gidan yakan sakaye idanunsa da gilashi gudun kada kwayoyin idonsa su nuna abinda yake zuciyarsa. Najaatu halin ko'in kulan da yake nuna" mata bai dameta ba kwalliya da sauran abubuwa ba zata daina ba tunda ta fahimci suna tasiri a tare dashi..... Da yake tana da yawan gashi mai kitso har gida take zuwa ta 'bata lokaci gurin tsantsara mata kunshi kuwa da ya goge zatayi wani Al'amarin daya sanya shi tunanin sanja shawara akan wacce "sukayi da hajia yana ganin kamar d'aura auran a kurkusa shine kwanciyar hankalinsa idan yace zai cigaba da zama tsayin watanni yana ganin yarinyar hankalinsa na tashi to babu shakka zai iya shiga halin ni 'yasu dalilin daya sa ya yanke shawarar tunkarar abokinsa da maganar. Abbah Magaji yace""To" "tunda kana ganin hakan yayi maka shikkenan sai kawai ka sanya a ranar da kakeso a daura auran."" Yace.""Yau insha Allah idan na shiga unguwar zan zauna da Malam da Alhaji a kan maganar."" Abbah" "Magaji yace.""To shikkenan Allah ya sanya alkairi yasa anyi kenan."" Ya amsa da ameen ameen." Najaatu duk wani abu da ake bata da labarinsa dan tunda aka tsayar da maganar daurin aure shi bai "kirata ya fada mata ba kuma har yanzu babu wata kyakkyawar alaka a tsakaninsu, tana dai jin maganar sama sama a gurun hajia da Yaya Ramlatu suma kuma babu wacce tace mata komai a kan al'amarin Ranar Lahadi da safe yazo gidan, Hajia na sama tana sallar walha Yaya Ramlatu da Hajia" "Rabi sun tafi asibiti duba Salim ashe tun ranar da Naburago ya watsa masa kudin auransa ya kwanta ciwo kamar ba zaiyi rai ba, sai da aka kwantar dashi a asibiti sannan Sakina ta aiko aka sanar da mahaifiyarsa shine fa Alhaji yace maza maza suje su duba jikin nasa ai hannunka baya ru'bewa ka yanke" "ka yar........Tana daki tana gyara jakar kayanta yay sallama a dakin, gabanta ya fadi dajin miryarsa," daidaita nutsuwarta tayi ta dan juya tana amsawa Idonsa kuri kan gashinta wanda akayi mata wani "irin kitso mai kyau jelolin gashin sun dan sauka bayanta, Najaatu nada gashi daidai gwargwado gashi baki mai daukar ido. Ganin yana mata wani irin kallo ne yasa ta lalubi dankwalinta ta daura, a sanyaye" "tace""Abbah sannu da zuwa.""" "Da sassauci a tare dashi ya amsa tare da neman guri ya zauna yana kallonta, gaishe tayi ta dan gyara" zamanta tana jira taji da abinda yazo dashi. "Gyaran mirya yay as'usul yace.""Naji gidan shuru tunda na shigo banji motsin mutum ba ina fata dai" "lafiya.""? Tace""Wallahi tun safe Alhaji da Hajia Rabi yaya" "Ramlatu suka tafi asibitin gadon kaya wai ashe Salim ne bai da lafiya yana can a kwance, ita kuma hajia" "na sama tana sallar walha."" shuru yay na minti biyu kafin yace.""Tun yaushe ne baida lafiyar.''? Tace""Wallahi ban sani ba jiya Matar babansa ta aiko aka fad'a.""" "Allah ya sawwake."" yafada yana me tsurawa yatsun hannunta ido Dakin yay shuru kowa na tunani," "Abbah tunanin ta inda zai fara yake, da kyar ya iya kiran sunanta." Ta daga kanta ta kalleshi kafin ta mayar dashi kasa """Kina da labarin maganar daurin auramu ranar jumaa mai zuwa kuwa.""? Gabanta ya fadi tayi saurin" "kallonsa, girarsa ya daga mata ya lumshe idonsa, a hankali yace."" Naso na bari yaronki ya kara kwari amma na kasa saboda ni kadai nasan yanda nake jinki a cikin zuciyata, Halisa tace ba zan ta'ba samun nutsuwa ba sai dake sai nake kokarin k'aryata maganarta saboda ina ganin ke baki isa ki tauyemin rayuwata ta kowane fanni ba, ashe so ba haka yake ba, dalilin yin hakan da nayi yasa ya mayar dani sakarai mara nutsuwa gami da saninan muhumacinsa, hakika a cikin 'yan kwanakin nan ni kadai nasan irin azabtuwar da nake a kanki Najaatu zan sake auranki a karo na biyu inaso ki bani hankalinki da nutsuwarki da dukkanin kulawarki bana so a yanzu dani dake muyi auran Madadi inaso muyi aure naso" "da kauna wanda zamu rayu a cikinsa cikin farin ciki da walwala har karshen rayuwarmu.""" "Wani irin farin ciki ya ciki mata zuciyarta hawayen farin ciki ya shiga sauka akan kumatunta, mirya na" "rawa tace""Abbah ka daina kokwanto akaina a yanzu zan aureka na zauna da kai tsakani na da Allah, Wallahi ban ta'ba kaunar wani namiji ba kamar ka, Abbah bani da za'bi sai naka bani da bakin godiya a gareka kayi min dukkanin sadaukarwa a rayuwata inaso yau na fad'a maka da bakina cewar ina sonka wanda ban san iya adadinsa ba, ina rokonka daka yafe min abubuwan da suka faru a baya kuruciya ce da" "kuma qaddara yanzu zan zauna zaman aure da kai tsakani da Allah da kuma so da kauna insha Allah.""" "Ya dinga wani murmushin farin ciki da jin dadi yana wani lumshe idanunsa a kanta, mirmushi tayi ta" "sunkuyar da kanta k'asa tana wasa da hannayenta yace.""Nayi farin cikin jin wannan magana taki Najaatu" "ashe yanzu ina da babban matsayi a cikin zuciyarki ban sani ba, a gaskiya dole wannan karon nayi shiri" "mai kyau inaso na nuna miki ni daban nake da sauran maza sai kin kasance a matsayin matata zaki gazgata hakan."" Yakare maganar yana jifanta da wani shu'umin kallo...Kunya ce ta rufe ta da sauri ta rufe" fuskarta tana dariya. *ALHAMDULLILAHI FAD'AN MASOYA HUTU NE INJI BAHAUSHE* "Salim zazza'bi typoid ne yaci karfinsa inda har ya ta'ba masa hanjin jikinsa,wannan bayanin likitan dake" kula dashi yayiwa Alhaji hankalinsa ya tashi Yaya Ramlatu kuwa kuka kawai take tana fad'in ''Yanzu wata da wattani d'anta yana kwance yana ciwo a kasa fada mata wato da sai dai taji labarin mutuwarsa "kenan, babu shakka abunda Sakina tayi mata bata kyauta ba" Ita dai Sakina hakuri kawai take bata dan gabadayan su Hankalinsu ya tashi jin cewar hanjin cikinsa ya 'bule dole sai anyi masa aiki. "Abbah Abbas ma da yazo dubashi sai da hankalinsa ya tashi, a take yasa hannu ya kuma biya zunzurutun" "kud'aden da asibitin ke bukata yace maza a shiga dashi teater , Allah sarki Yaya Ramlatu kuka kawai take dan gani take tamkar gawarsa za'a fito mata da ita, sai dai kuma ba a nan take ita cuta ba mutuwa bace mai lafiya ma yana iya mutuwa ya bar wanda yake da shekara goma yana jinya. Lafiya lau aka fito da" Salim anyi aiki cikin nasara yanzu abinda yay saura kula da shan magani akan 'ka'ida. ***** Alhaji Aminu Dan jarida da kyar ya samu gurin zama bayan fitowarsu daga prison sai kowa ya gudunsu "dalilin daya sa kenan ya harhada 'yan kudaden da suka rage masa ya gudu k'yauyen zaria shida iyalinsa ya samu ya siyi wani lalataccen gida, sauran kudin suka siyi kayan abinci Mommy ta fara sanar sai da" gwanjo a cikin kyauyen sai ta shiga cikin gari ta siyo tazo ta baza a kofar gidan jama'ar garin na siya da wannan sanaa suke rufawa kansu asiri. A lokacin Munira ta dade da haihuwa inda ta haifi Da namiji a hannun kanwar Momynta Laila. 'Kaskanci da "wulakanci babu irin wanda Munira bata gani ba, taci wuya sosai wanda sai da ta kai ta kawo ta daina fitowa waje dan da ta fito za'a soma yi mata waka mai cikin shega babanta karto d'an uwanta 'barawo wasu yaran ma har jifanta suke wannan dalilin yasa take zama a gida taci kukanta ta koshi Lailah ta ta cigaba da azabtar da ita. Tunda ta samu labarin dawowar iyayenta ta gudu ta koma gurinsu, dan gwara" tayi rayuwa a cikin kyauyen da suke a kan azabar da Laila take gana mata. *RANAR JUMA'A* Ranar aka daura auran Abbah Abbas da Najaatu a karo na biyu daurin auran yayi albarka sosai dan ya samu halartar manya manyan mutane daga bangaran Alhaji Abbas mai girma governor dashi da mukarrabansa ma sun samu hallatar daurin auran Abbah Abbas ranar kasa rufe bakinsa yay sai murmushi yake yana gaisawa da jamaa cikin walwala da farin ciki.........Najaatu ta sake zama matarsa a karo na biyu ai dole ya nunawa Ubangiji farin cikinsa.. *'Kawata kada kiyi wasa da wanke bakin ki domun ana saurin gane tsabtar mutum ta ha'koransa. Akwai damuwa ace wai idan kikayi brush da safe ba zaki sakeyin wani ba sai wata "safiyar to idan kuna marking lov da oga yana muradin ya sha bakinki yaji wari ko datti abinci kina tunanin zai sake marmarin kusantar bakin ki tsotsar bakin juna gurin mu'amula ta aure na qarawa ma'aurata amarshi da son kasantuwa da junansu, duk wata macen da mijinta baya had'a baki da ita ta bunkici kanta, rashin gyara da kula da kanki zai janyo miki babbar matsala k'awata. Idan kinyi" "bursh da asubah da safe kafin ki karya ki sake yin wani, da daddare kafin ki kwanta kiyi wani ki dauki" "kaninfari guda biyu kisa a bakinki kina tsotsa, kaninfari yana da mutukar sirri a tare dake kada kiyi wasa" "dayin amfanin dashi, dan Allah kada kiyi saken da zai sanya mijinki ya dinga gudun had'a baki dake *" *BINTA UMAR ABBALE* *07084653262* 80*******A tsakanin gidan Baba malam da gidan Alhaji ban san wanda yafi wani murna da farin cikin "zuwan wannan rana ba, ta ko wane b'angare hidima akeyi sosai 'yan uwa da abokanan arziki nata shige da fice a tsakanin gidajan, duk dai da yawa daga cikin wasu mutanan unguwar gulma ce take kawo su ba abun arziki ba, amma haka hajia da Baba Talatu suka dinga kar'bar jamaa har dai taro ya watse lafiya" kowa ya koma muhallinsa. Bayan sallar isha'i Baba malam yasa aka kira masa amaryar domin ya zauna da ita...Najaatu a sanyaye ta nufi gidan Malam din tana boye fuskarta cikin hijabi dan gabadaya a "daki ta yini saboda Dangin Hajia da alhaji da suka cika gidan, kunya tasa ta zauna a daki ita kadai haka jamaa suka dinga shigowa d'akin wai zasu ganta, ta dinga data sanin zama a gidan tana ganin da gidan Malam ta gudu daya yafi, to yanzu ma data fito akwai sauran jamaar da basu tafi ba sai kallonta sukeyi ita kuma kallon ne bata so tabbas ba zata dawo gidan ba ta fita kenan dan yanzu ita kanta hajiar" kunyarta takeji. Tana zaune gaban mahaifin nata yana mata nasiha mai ratsa jiki nasiha yake mata kan biyayyar aure "gami da riqeshi a hannu biyu baba malam ya nuna mata cewar mijinta a yanzu shi yake da iko akanta saboda haka duk wani abu da zai umarce ta dashi tayi kokarin bin umarninsa mutukar bai sa'bawa sharia ba, sannan ya sake jadadda mata cewar sai tabi mijinta sau da qaba san zata samu aljanna dan haka sai ta zage dantse tayi koyi da Nana Fadima d'iyar manzon Allah (slw) bayan haka kuma tayi koyi da 'yar uwarta Halimatu wanda har Allah ya dauki rayuwarta mijinta na shi mata albarka gami dayi mata" kyakkyawar addua. "Bayan Baba malam ya gama Baba talatu ta d'ora nata, Najaatu na kuka tace""Insha Allah ba zan baku" kunya ba nayi al'kawarin zan zauna da mijina har karshen rayuwata sannan zanyi masa biyayya kamar yanda Allah ya umarce ni da nayi sannan ina kara rokon ku da ku yafe min abinda nayi muku a baya da yardar Allah wannan karon ba zan baku kunya ba. "Baba Talatu da baba malam sun ji mutukar dadi da maganarta, Baba malam yace.""Allah yay miki albarka" "ya baki zuria mai albarka."" Miqewa yay yasa takalmansa ya fita, Baba Talatu tace"" Ki shiga dakina wajan gado zaki ga wasu kaya a cikin leda viva Hafsa 'yar gidan Yakumbo ce tace idan kin shigo a baki ban dai bud'a naga ko menene a ciki ba." A sanyaye ta miqe ta nufi dakin....Kayan ta d'auko a nutse ta shiga fito dasu kayan mata ne zuma cikin "wata jarka sai tsumi shima a jarka sai kuma garin magani irin wanda akesha da nono ko madara roba kusan biyar ko wanne da nau'insa, Hasken wayarta ta kunna tana dudduba maganin gami da bayanin dake jikinsa, Murmushi tayi a hankali tace lallai akwai dirama bari na fara da wannan biyun." Zuma ta dauka kawai ta bud'e bakin abin ta kafa kai tana kwankwad'a! sai da tasha da yawa tukkuna ta "dauki jarkar tsumi din a maimakon ta samo kofi ta tsiyaya shima bude murfi kawai tayi ta kafa kai tasha yanda take so ta rufe. Tana kokarin mayar da kayan cikin ledarsu taji sallamar aunty Maryam, tace ashe" "bata tafi ba, tana jin sanda take tambaya baba ina take, tace mata tana cikin daki Kafin ma ta gama" mayar da kayan cikin ledarsu ta shigo dakin. """Aunty Maryam baki tafi ba dama.""? Aunty maryam ta samu guri ta zauna tare da ajiye fulas din dake" "hannunta, Tace"" saboda ke na dawo ai, ga kazar amarci nan ba zan tashi daga gurin nan ba sai kin cinye tas kin tsotse kashin." "Dariya tasa tace""Lallai aunty Maryam kema gudumawar da zaki bani kenan kinga fa wasu maganin da" "Aunty Hafsa ta Yakumbo ta kawo min.""" "aunty maryam ta shiga duba maganin tana murmushi tace""Lallai ta gwangwaje ki sosai sai ki mayar da" "hankali kina sha a kai a kai! zasu taimaka miki sosai.""" "'Yar dariya tayi tace""Ni wallahi aunty maryam da kun barni haka sai yafi meye duk sai kun tashi hankalin" ku nifa ina da ni'ima daidai gwargwago ba sai nasha wani magani ba. "Aunty maryam ta harareta tare da fadin ""Mara wayo kawai to ko kina da ni'ima sai akace ba zaki 'kara" "wata ba, okey da haka kike so kije masa babu gyara yaji ki lami! humm to wallahi ba kunyar ki zaiji ba zai iya barinki ya tafi inda zai samu gamsuwa saboda haka kiyi hattara da gyara kanki har wani cewa kike kina da ni'ima a'ina kikayi ni'imar mtwws! Najaatu ban san sanda zakiyi wayo ba wallahi, zaki zauna tsakanin kishiyoyi idan suka fiki kula da kansu kin shiga uku gwara ki san yanda al'amarin yake tun yanzu....Duk wata mace mutukar tana da kishiya to burinta ta fita a gurin miji kiyi kokarin ganin kin" zama tauraruwa akan kishiyoyinki idan kuma kin zauna sakarci shikkenan Najaatu jikinta yay sanyi Zainab ce kawai ta fad'o mata ta lura yarinyar nada wayo sosai dole ne ma ta zage damtse a kanta dan ta fahimci shima yana ji da ita ko ga yanayin yanda yake kula da ita da sauransu. Fulas din gaban aunty maryam din ta janyo gabanta ta bude kamshi ya bigi hancinta kamshin tattasai dana magani amma dai maganin yafi yawa a ciki Hannu tasa tayi bisimillah a nutse ta soma ci tana had'awa da ruwan roman "Najaatu tas ta cinye kazar ta shanye roman aunty Maryam ta rufe fulas dinta ta miqe tare da fadin""to ni" zan tafi sai gobe idan munzo rakiyar amarya. "Najaatu mikewa tayi tana sud'e hannunta tace""Wai dan Allah da gaske gobe zan tare aunty Maryam" "wallahi bana so na tare gobe nafi so adan kwana biyu tukkuna."" Aunty maryam harararta tayi tace ""Sai kiyi ai ni har gidan da zaki zauna ma na gani a waya. Gidanki daban mai kyau da burgewa babu abinda" "babu a ciki gaskiya yay kyau sosai wallahi."" Gabanta na faduwa tace""Wane unguwa ne ni wallahi daya sani ya had'ani dasu Aunty Halisan zaifi.....Aunty Maryam tace""Aa gwara ki zauna ke kadai yafi mutumci" watakila shima yana da manufarsa akan hakan saboda haka ki kwantar da hankalin ki gidanki na rijiyar "zaki wajejan massalacin jumaa na d'an sarari."" Najaatu shuru kawai tayi tana addua Allah yasa haka shi" yafi alkairi amma dai da za'a bi son ranta to da tafi so ta zauna gida daya dasu Halisa. Aunty maryam na kokarin fita daga gidan Yaya Ramlatu ta shigo da Daddy a hannunta yana kukan a mutunce suka gaisa da juna kafin ta shige cikin gidan da sauri Najaatu na wanke hannunta tayi saurin karasawa ta "kar'beshi da fad'in ''Ashe ya tashi lokacin dana fito na barshi a daki yana bacci."" Ya Ramlatu tace""Ai ina tunanin baki dade da fita ba ya tashi, na bashi costand ya'ki kar'ba nono kawai yake bukata. Baba" "Talatu ta fito daga kicin tare da fadin ""Ai yay kokari ma ace yaro ya tashi a bacci sama da awa guda bai" ci abinci ba ai dole yayi kuka ai sai ki zauna ki bashi yasha. "Da sauri ta zauna gefan tabarma ta fito da nono tasa masa a baki, aikuwa ya kama da sauri ya shiga" tsotsa yana sauke ajiyar zuciya "Yaya Ramlatu tace"" Bari naje sai kin shigo."" A sanyaye tace""Yaya Ramltu da kyar idan zan dawo wallahi" "kunya nake ji mutane tun dazu suke kallona."" Ramlatu ta bude baki tana kallonta cike da mamaki tace""To ai tuntuni kowa ya kama gabansa mu kadai ne a gidan" "Shuru tayi tana nazari kafin tace""Allah kunyar hajia nake kice mata sai gobe zan shigo."" Ya Ramlatu tayi" "murmushi tace""Bakiyi laifi ba Najaatu dan dama dole haka zata iya kasancewa shikkenan bari na kawo miki abubuwan da zaki bukata ko.""" Kasa tayi da kanta kunyar matar takeji sosai sam bata gajiyawa dayi mata hidima ga wahalar d'anta da take kullum daddy na goye a bayanta a mafarki ba ta ta'ba tsammanin Yaya Ramltu zata bautata mata ba. "Baba Talatu ta fito daga daki tare da fad'in "" Ke abinda kikayi a ganinki shine daidai? me yasa tunda bakiji" kunyar su ba sai yau bana son munafurci ki gama bashi nono ki tashi ki tafi. "Kuka tasa tace""Allah ba zan iya komawa gidan ba Baba ki kyaleni kawai na zauna anan tunda nace miki" "kunya nakeji da gaske nake wallahi."" Baba talatu shuru tayi tana kallonta, tace""Ai shikkenan tunda a ganin ki haka shine ya dace."" Redion ta ta kunna ta shiga sauraran shirin ko wane gauta a tashar freedoom redio Allah sarki Ya Ramlatu duk wani abu data san Najaatu da danta zasu bukata sai da ta" kawo mata Baba Talatu ta dinga yi mata godiya Najaatu kam nauyi da kunya yasa ta kasa cewa komai ita kanta mamaki takeyi wai yau itace ke jin nauyin hada ido da Ramlatu da Hajia babu shakka abun babbane "Karfe goma da rabi tayi shirin kwanciya ta shirya yaronta tare da kwantar dashi gefan katifa, kwanciya" tayi tana duba wayarta. A lokacin ne taga kiran Mmn Sajida har guda bakwai da yake saboda hayaniya "tasa wayar a silent ""Allah sarki Mmn Sajidata."" Miqewa tayi zaune tana duba gogo, gaskiya dare yayi data kirata ta bata hakuri tasan sun kira wayar ne suyi mata Allah ya sanya alkairi tunda suna da labarin duk abinda ke faruwa ta fada musu komai babu abunda ta rufe musu, tabbas data san zasu kira da bata rufe wayar ba, amma insha Allah gobe itace zata tashe su a bacci da wuri zata kirasu ta basu hakuri..........WhatsApp ta shiga ta danyi dube dube kafin ta fita number angon nata ta nema tana so" ta kirasa tayi masa bangajiya......Tana fara ringing aka d'auka. Muryar Zainab ce ta daki dodon kunanta Gabanta ya fadi ta miqe zaune tana kara rike wayar a hannunta. Zainab cikin dusasheshiyar murya "tace""To me kika bugo kice masa ai kya bari a kai masa ke tukkuna yanzu dai lokacin mu ne dan haka sai anjima."" Sai kawai ta kashe wayar, ta barta da tata a maqale a kunne." "Mutuwar zaune tayi ta kasa motsi sai tunanin hukuncin da zata dauka kan Zainab take, tabbas fa idan" tayi sake yarinyar nan zata samu galaba a kanta idan da ta daga mata waya to a lokacin babu aure a tsakaninta da mijinta a yanzu bata isa ta daga mata waya ta fada mata maganar banza ta kyaleta ba.......... """Wai Zainab me Najaatu tayi miki ne kika damu kanki a kanta? Saboda na dawo da ita shine kike ta kuka" "kina da jego amma ki yini babu abinci a cikin ki shin kashe kanki kike so kiyi kome.""?" "Tana kuka tace."" Wallahi dole na damu sabida tun ba yau ba nasan irin son da kake mata, gabad'aya" "labarin abunda ya faru tsakaninka da ita babu wanda ban sani ba, amma tunda nake da kai baka ta'ba cewa yau ga laifinta ba duk da ta kasance mai laifi a gurinka amma kullum cikin kyautata mata kakeyi ko makaho ne ya shafa yaji zai san irin kaunar da kake mata, ni kam wallahi daka dawo da ita gwanda ka sake sabon aure sabida nasan da kyar idan zata bar mu zauna a gida. Katse ta yayi a fusace! yace.""Ke" "bana son hauka da rashin hankali shin Najaatu ce ke aurana ko kuma nine ke auranta da har zaki dinga tunanin shigowarta rayuwata zai sa na rabu dake? wai me yasa bakya aiki da Iliminki ne! nasan gabadayan'ku keda ""yan uwanki kuna da sani akan abu amma kuke takewa ba, kinyi saukar al'kur'ani har sau biyu kin san hadisan annabi da sauran littafan musulunci to me yasa kike adawa da abinda Allah ya hallata ? mahaifinki mata hud'u gareshi kuma idan ban manta ba kwanaki na fad'a miki cewar ba zan zauna daku ku biyu ba, shin me Najaatu ta isa tayi miki da har kike tunanin idan ta shigo k'arshen ki yazo. wannan rashin hankali ne, Najaatu a karkashina take kamar yanda kuke a karkashina duk so da kaunar da nake mata bata isa ta ta'ba martabarku na kyaleta ba saboda haka kada ki sakeyin wannan maganar."" Zainab ta dinga share hawaye tana jin wani katon abu ya tokare mata a kirji, itafa Najaatun ce kawai bata so amma da zai auri mata biyu a rana ba zai dameta ba. Kira ne ya shigo wayarsa dake" "kusa da ita, Yasa hannu ya dauka yana dubawa. Sunan my dota ya gani yana yawo kan screen din wayar," "Ya sasaauta muryarsa sosai ya d'aga tare dasa wayar a kunnasa, a kasalance ta amsa masa, tace""Abbah" "barka da dare! dama na kira wayarka ne nayi maka ban gajiya."" Murmushi yayi yana jin yanda tsigar jikinsa take tashi, hanyar fita ya kama da wayar a maqale a kunnansa yace.""Nagode my wife Amma ni yanzu ba Abbah bane Darling ne sannan kuma naji dad'in wannan bangajiyar da kikayi min ina fatan kinyi min tanadi mai kyau dan ni na riga na gama kimtsawa ke kawai nake jira"" Yana kokarin fita daga dakin yake magana..............Zainab ta bishi da wani irin kallo bakinta a sake hawaye na sharara a" kumatun ta *Allah sarki har ta bani tausayi * *Malam Bahaushe dai yace Amarya ko tabuzuzu ce dole ayi Zumud'in ta To ballantana wannan dalleliyar amaryar daya san zai gwangwanje ai sai abinda hali yayi......Zainab sai a tanadi maganin hawan jini * *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake. Vip group #600...Normal group #300 account... 0542382124...Binta umar gtbabk. Idan katin waya zaki tura sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* "81********Najaatu cikin jin kunya da jin nauyin maganar da yayi tace.""Humm! Abbah kenan wallahi" "har kasa naji kunya."" Murmushi yayi ya samu kan kujera ya zauna yace"" Ai gaskiya na fada miki nasan da" "cewar amare na shirya jikinsu domin tar'ba ango shine dalilin daya sa nayi wannan maganar. amma nasan ke koda ba kiyi wani kintsi ba zaki gamsar dani irin yanda nake bukata ko ba haka bane.""" "Najaatu ta dinga jin kunyar maganarsa tana 'yar dariya da fad'in ""Abbah kenan."" Yace.""Na fada miki ni ba" "Abbah bane a yanzu inaso ki tanadi suna na mussaman da zaki dinga kirana dashi amma bana son wannan Abbahn.""" "Shuru tayi tana sauke wane irin numfashi, tsabar feelings ne yay mata yawa yasa ta janyo fillo ta" rungume wannan d'an kalaman da yake mata yasa gabadaya sha'awarta ta tashi ta wani takure jikinta guri guda. "Jin shuru yasa yace.""Najaatu kina jina kuwa kodai kinyi bacci ne.""! A sarqe tace""Ina jinka Abbah baccin" "ne dai ya soma daukana."" Yace.""Okey to ki kwanta kiyi bacci amma kafin nan ki tabbatar kinyi addua kin shafe jikinki.""" "Tace""To insha Allah Ab kasa karasawa tayi saboda maganarsu ta d'azu, mirmushi yayi yace.""Zan kashe" "waya yanzu amma inaso kafin gobe kiyi tunanin suna na mussaman daya dace dani."" Yana gama maganar sai ya kashe wayarshi Najaatu ta jima da wayar a hannunta sai sakin murmushi take tana juyi" "a kan katifa shin wane suna ya dace ta dinga kiransa dashi, gaskiya itama za taji nauyin kiransa da Abbah" tunda a yanzu tasan babu wannan alaqar a tsakaninsu bayan haka kuma tana so ta siye zuciyarsa da kalolin soyayyarta dole ne ma tayi tunanin suna na mussaman da zata dinga kiransa dashi. "A hankali ta miqe ta fita tsakar gida, ruwa ta zuba a buta ta shiga bandaki, ikon Allah wai wannan 'yar" "wayar da sukayi tasa zubar da ruwa, koda yake ai ta banki zuma da tsumi dole sha'awarta ta tashi to" "koda ma babu zuma da tsumi Najaatu nada karfin sha'awa, wanke jikinta tayi ta mayar da pant dinta ta fito a hankali ta ajiye butar ta shiga daki da sauri ta turo kofa bata so Baba talatu taji motsinta" Bayan ta idar da sallar asubahi ta jima kan dadduma hannu a sama tana rokon Allah ya dawwamar mata "da zaman lafiya da kwanciyar hankali a zamantakewar auranta ta roki Allah sosai akan ya bata zaman lafiya da mijinta da abokanan zamanta, iyayenta da sukayi silar samuwar farin cikinta suma tayi musu addau kan Allah yasa su cika da kyau da imani, Hajia da Alhaji suma bata manta dasu ba ta jima tana" musu addua sannan ta rufe da fatiha ta shafa a fuskarta "Gefan katifa ta zauna tare da cire hijabin jikinta ta duba Daddy bacci yake bai tashi ba, kwanciya tay ta" dauki wayarta ta kunna. Numbersa ta nema ta rubuta masa sakon gaisuwa kamar haka. "_Annur Barka da safiya ina fatan ka tashi lafiya ya kwanan iyali.""?_" "Tura text din tayi tasan mutukar ya kunna wayarsa zai gani, Annur (Haske) shine sunan da take ganin ya" "dace ta dinga kiransa, domin yanzu shi kad'ai ne kesa zuciyarta tayi a haske, bayan soyayyar manzon Allah to babu wanda take so kamarsa bayansa iyayenta da suka biyo baya.(Soyayya ruwan zuma ) Abbah na bude wayarsa da text din yaci karo yana karantawa yana murmushi had'e da shafa gemunsa, iyeee! ashe shi dan gata ne an sa masar masa da suna mai dadi da ma'ana! (Haske) sunan ya kyatar dashi sosai, kawai ya dingi karanta text din yana murmushi sai kace wani shashasha! Halisa dake kwance a bayansa ta motsa, da sauri ya kashe wayar ya juya yana kallonta tamkar wani mara gaskiya, Halisa kuwa gyara kwanciyarta tayi ta cigaba da baccinta dan bayan ta idar da sallar asubah komawa tayi ta" kwanta abunta. To shima rufe wayar yay ya kwanta rigingine tare da tsirawa rufin dakin ido lumshe idonsa yayi da kyakyawan murmushi kwance a fuskarsa ya shiga tunanin yanda zata kasance a tsakaninsa da yarinyar idan sun had'u a daki daya. *Naburago* Ya fantsama harkar cah-cah! inda 'yan kudin da suka rage a accont dinsa ya dinga zuwa yana sasu a caca "wani lokacin yayi sa'a wani lokacin kuma a 'kwamushe shi, mahaifiyarsa ta sake zama dashi tana masa fada akan ya daina wannan harkar domin kuwa bata da riba tunda dai yace ba zai mayarwa da mai kudi kudinsa ba to abinda yay saura a hannunsa yaje ya kama shagon haya ko chajin waya ya dinga yi, Naburago ya shafawa idonsa toka yace shifa yana kallon sana'a mai romo irin wacce take kawo kudi da wuri ba zai je ya wahalar da kansa gurin tada gen da zura chaza a jikin waya ba, dan haka idan ma zata" daina wahalar da kanta ta daina ba zai bar sanar caca ba. A ranar Salimat ta fusata ta farfada masa magana tare dayi masa gori akan kudin ita tayi silar samuwar kudin amma ko kwabo ya hanata sai biyan bukatarsa yake dasu Naburago ya fusata sosai ya zare blet "ya dinga laftar ta sai da yayi mata jini da majina ya farfasa mata jikinta sannan ya kyaleta, ko ajikinsa ya fita ya bar gidan." Bank yaje ya ciro gabadaya kudin da sukayi saura a ciki Yau zasu buga da wani guy yana adduar Allah "ya bashi nasara a kansa ya k'wamushe shi, parking din babur dinsa yay ya shiga gurin, kai tsaye yaje ya samu gurin zamansa, guy shima yazo ya zauna al'kalai suka kewaye su. Basu ja dogon lokaci ba suka" "fara bugawa. Da farko guy nan sakarwa Naburago yayi yana ta kwamushe shi, sai da akazo karshe" "tukkuna yay masa kwaf daya duk uban kudin da Naburago ya zuba guy ya k'wamushe Naburago ya fusata kawai sai ya zaro key din babur dinsa yasa aka cigaba da bugawa, ai ba'a wani ja dogon lokaci ba guy nan yayi winning d'insa. Naburago yayi tsuru tsuru zufa sai yanko masa take, ya akayi yau rana ta" "'baci dashi an K'wamushe dik abinda yake dashi, shikkenan ya tashi a tutar babu, yana kallon guy nan na" dariya da farin ciki yana had'a kan kudinsa abokansa na taya shi. Hannu ya kai zai wafci kudin d'aya daga cikin abokanan guy ya zaro bindiga kai kace ta gaske ce amma copy ce suna yawo da itane saboda barazana! Naburago a gigice ya miqe tsaye yana daga hannunsa. Daya daga cikin al'kalan gurin ya buga masa tsawa tare da nuna masa hanyar fita. Naburago simi simi ya kama hanyar fita gumi duk ya jika masa rigarsa. 'Bangaran Salim kuwa sai dai munce alhmdullhi dan a tsakanin kwanaki bakwai da yay a kwance a asibiti "jikinsa yayi kyau sosai Sakina matar Babansa ce take jinyarsa ita kuma Yaya Ramlatu na zuwa kullum tana dubashi yanzu tsakaninta da Sakina mutunci ne da ganin girman juna saboda ta gane cewar ko wane mutum yana da rana gashi dai duk irin cin zarafin da takewa Sakina bai sa ta guji Jininta ba, babu" abinda zata ce akan wannan abinda tayi mata sai dai kawai ta roki Allah ya saka mata da alkairi. Najaatu tayi mamakin yanda ya kashe kudi guri k'awata mata gidanta kayan kyale kyale iri iri kamar ma "abin yaso yay yawa, duk wanda ya shiga gidan Najaatu ba zai so ya fito ba gidane madaidaici amma yanayin tsarin ginin da akayi wa gidan tun daga waje zaka gane cewar an kashe kudi gurin ginashi Babban abinda ya kara bata mamaki shine ganin jerin akwatina mai shida a bedroom dinta," wai kayan lefenta ne. kawai sai jin saukar hawaye tayi a fuskarta ita kuwa ina zata kai wannan farin "cikin.....Aunty Maryam ta rarrasheta ta kuma sheda mata cewar mijinta ne ya basu kudi ita da Halisa sukaje sukaje sukayi mata siyayyar kayan lefenta. Tace""Aunty Maryam dole nayi kuka wallahi na rasa" wane irin kauna Abbah keyi min kiga yanda ya 'kawata min gida ni kadai sannan sai kace wata budurwa "yayi min lefe har akwati shida abin yana bani mamaki.""" "Aunty maryam tayi murmushi tace""Sai ma kin bude kinga abubuwan dake ciki dan gaskiya duk babu na" banza kudi masu yawa ya bayar aka shirya miki kayanki ni banga komai ba dan yay miki ai aure duka aure ne da bazawara da budurwa mutukar mutum nada iko babu laifi dan ya auri bazawara yayi mata lefe irin na budurwa karshe dai shi za tayi kwalliya da kayan. "Tace""Hakane maganar ki aunty maryam kema sannunki da kokari nagode sosai da abubuwan da kikeyi" "min.""" "Aunty Maryam tace.""Haba ai babu komai an riga an zama zama d'aya." Najaatu bayan tafiyar aunty Maryam ta jima zaune a gefan gado tana sa'kawa da kwancewa tunanin "yanda zata tar'bi angon nata take, tana mutukar sha'awar kasancewa dashi sai dai kuma tana jin tsoron abinda zaije ya dawo......Wanka tayi ta shafe jikinta da humra mai k'amshin gaske, kayan bacci tasa farare masu taushi da hularsu sai ta d'auki katon hijabi tasa ta nemi gefan gado ta zauna. da wayarta a" hannunta tana duba lokaci goma da rabi har ta gota bai shigo ba. Abbah Abbas lafiya lau yay sallama da Halisa tayi masa fatan alkairi ita kuwa Zainab ai taqi sauraransa "sai zum'bure zumbu're take tana share hawaye, shi kuma ganin yanda ta shiga damuwa yasa ya zauna yana tausarta wallahi shi bai ga abin damuwa da daga hankali ba, shi suke aure kuma ko wacce yana kokarin sauke hakkinta dake kansa to me zai sanya ta damu kanta, abinci ma da kyar take ci yanzu" yarinyar ta ba sosai take samun ruwan nono ba. "Yace.""To naji duk abinda kikace na kuma amince da maganarki duk domin a samu daidaito da zaman" "lafiya idan na gama kwana ukuna da amarya za'a cigaba da yanda aka saba, ma'ana ke kwana biyu Halisa ma haka Najaatu ma haka ina fatan dai shikkenan.""?" "Tace""Eh shikkenan nafi so da kagama kwana ukun ka ka dawo gurina, tunda dai ai na kusa ar'bain.""" "Yace.""To shikkenan sai ki sallami masu tayaki zama dan ba zan dinga sintiri a gaban mutane ba."" Tace""Ni" "yau ma zan sallemsu su tafi.'' Mikewa yay cike da takaicinta yace.""Ni zan tafi sai da safe."" Da kyar tace Allah ya bamu alkairi."" Abbah ya juya ya fita daga dakin (Kunga mutuniyarku ko da d'anyan jego take" gayyato miji sai kace wani abun arziki zata iya yi ) "Sha daya da kwata na dare ya shiga gidan, ya fito daga mota a nutse maigadin gidan ya karaso har kasa" ya durkusa ya gaishe Abbah ya amsa cikin sakewa tare da bashi umarnin ya rufe gidan Motsin bude kofarsa ne yasa ta nutsu ta tsirawa kofar dakin ido kusan minti biyar da jin motsinsa sannan taji "ya turo kofar dakin ya shigo, ajiyar zuciya ta sauke tasa masa ido tana kallonsa tare da kyataccen mirmushi a fuskarta, Abbah lafiyayyan kamshin humrar daya cika dakin shine ya saukar masa da kasala," "ya karasa inda take tare da zama gefanta ledojin hannunsa ya ajiye a gabanta a hankali yace.""Amarya.""" "Dan mirmushi tayi tana wasa da hannunta tace Abbah sannu da zuwa."" Yasa hannu ya dago fuskarta tare da tsira mata ido yace.""Ina sunan da kika saka min? naji kin kirani da Abbah."" Yana 'bata fuska yayi" maganar. "Ta dan ji kunya a hankali ta cire fuskarta daga hannunsa tace""Annur.""! Yaji wani sanyi ya sauka acikin" "zuciyarsa mirmushi yayi mai ma'ana yace""Naji dadin wannan sunan da kika saka min ina rokan Allah ya dawwamar mana da haske a duniya da lahira.""" A hankali ta amsa da ameen ya Allah. "A nutse ya juya bayansa yana kallon Daddy dake bacci cikin net dinsa, Yace.""Ina fata kinyi masa addua" "ko."" kanta ta daga a hankali tace""Eh."" Yace.""Masha Allah. To yanzu ga kayan amarci nan na kawo miki kici sosai sai kizo ki bani labarai masu dadi Dan mirmushi tayi gabanta na faduwa tace""Naci abinci a" "gida. Kashingida yay yana mata kallon kasan ido yace.""Wannan na mussaman ne dole kici ko yayane sai" mu miqa godiyarmu ga Allah daya sake hadamu zama a karo na biyu bayan nan kuma sai mu fuskanci abunda yake gaba. A hankali ta sauka kasa ta bude ledar robar yught ta dauka ta bude tasha rabi ta "ajiye, yace.""Ai baki ci sauran ba.""" "A sanyaye tace""Ai kace ko yaya ne naci shiyasa nasha yogurt. "" Yace.""Okey to jeki yi alwala ko."" Mikewa" "tay ta nufi toilet ya bita da kallon sha'awa, tana fitowa ya shiga ya daura tasa ya fito Nafila sukayi" "irin ta sababbin ma'aurata, Abbah ya jima yana addua kafin ya rufe da fatiha, ya shafa a fuskarsa itama ta shafa. Kai tsaye daya miqe zuwa yay ya kashe haske dakin. Ya karaso inda take zaune, lalubarta yay" "ya miqar da ita tsaye, hijabin jikinta ya cire ya rungumeta 'kam a jikinsa." A haka suka isa bakin gadon... zama yayi gafen bed din ya dorata a cinyarsa tare da rad'a mata magana a "kunnanta......""Ya zakiyi da abokina ne ina ganin ki sanja masa gurin kwanciya kada mu danneshi."" yana nufin Daddy. Najaatu" "Ta dinga jin wani irin abu na yawo a jikinta kunya duk ta isheta, a sar'ke tace ""Aa kawai a barshi a gurin" "ai."" Sai tayi shuru yace.""Ai me? humm! aikin ai bana wasa bane dole a janza masa gurin kwanciya dan kada kina cikin yanayi ki kai masa duka baki sani ba.""" "Rufe fuskarta tayi tace""Kai dan Allah.""! Abbah yasa dariya kasa kasa tare da sumbatar gefan fuskarta," Bedlamp ya kunna yayi dubarar janyo net din da yaron yake kwance ya sauke shi kasan gadon ya gyarashi sosai kana ya dawo gareta. kamar kwai ya kwantar da ita kan bed din yasa hannu ya kashe "bedlamp din, jallabiyar jikinsa ya cire yasa hannu a hankali ya dagota rigarta ya cire mata yasa hannu jikin dogon wandon dake jikinta tay saurin dora hannunta akan nasa. Abbah wani irin salo ya shiga yi" mata wanda yasa ta saki hannunsa bata sani ba.. gabadaya sai da ya rabata da komai na jikinta ya wani maqale mata a jiki yana shashshafa guraran da yake da muradi.....Najaatu jikinta ya saki sosai ta riga ta "gama kawadituwa shiyasa duk inda ya kai hannunsa take bashi gudumawa da goyon baya,ita dashi sun" riga sun shiga yanayi sai shafa junansu suke suna tsosar kansu da kansu nishinsu ne kawai ke tashi a dakin Abbah babu inda bai tsotse a jikinta ba mussanan HQ nata yasha tsotsa kamar me har kuka "sai da tayi saboda tsabar shau'ki da kanta ta kamo jijiyar tasa data wani kumbura ta dinga wasa da ita a gabanta, wannan salon yasa shi kusan zautuwa sunanta kawai ya shiga kira yana sake nane mata a jikinta, Najaatu ita da kanta tasa jijiyar a jikinta ta d'aga masa sosai ya fara safa da marwa a ciki.............." *Abbah Allah yasa kwallonka ya shiga raga * *Littafin na kudi ne. * Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar biyan kudi ga yanda abun yake. p group #600 normal group #300 accont number.... 0542382124.....Binta umar gtbabk. Idan kati zaki tura kiyi min mgn ta whasapp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* ****82 Zainab da 'kyar ta iya rintsawa a daran ranar saboda mummunan kishin daya tokare mata "ma'koshi, daga zarar ta rintse idonta Najaatu take hangowa tare da mijinta yana gwada mata soyayyarsa" "mai wahalar samu, tana jin baby Ummi na kukan neman nono taki daukarta har sai dai daya daga cikin masu taya ta kwana ta tashi ta kunna fitila tana kiran sunanta." """Zainab ki tashi fa yarinyar nan tun dazu tana kuka da alama yunwa takej. Sheshshekar kukanta ne ya" "katse ta da sauri tace"" Zainab Lafiyarki kuwa.""?" """Aunty Balaraba wallahi na kasa bacci tun dazu hankalina gabadaya yaki nutsuwa sai hango abunda yake" "faruwa a tsakaninsu nake, aunty Balaraba wallahi yana sonta irin son da baya yi mana nida aunt Halisa shiyasa gabadaya na tsaneta bana kaunarta ko kad'an sabida ina ganin kamar tafi ni a gurin mijina bayan haka kuma ubanta malamin zaure ne a tsaye yake a kanta ba zai ta'ba bari ta wulakanta ba ni yanzu" "tunani na ya za'ayi na janyo hankalinsa kaina ya daina rawar jiki da zumud'in da yake a kanta.""" "Aunty Balaraba ta gyara zamanta da murmushi a fuskarta tace""Lallai kina da kishi Zainab sabida kina" tunanin abinda zai faru tsakanin mijinki da kishiyarki kika kasa rintsawa. Humm koda yake kusan duk "'yan gidanmu haka suke da kishin tsiya amma gaskiya naki yafi na kowa, ni lokacin da Idiris ya 'kara aure ban hana idona bacci ba kwanciya nayi nai baccina na more ban tashi hankalina ba saboda nasan a shirye nake da zuwan shegiya sharri da makircina kadai ya isheta, kin san dai ko wata uku Amina ba tayi a gidana ba tayi waje, har sharrin zina sai da nayi mata sharrin sata ke abubuwa iri iri gefe guda na dinga had'ata da mijinta, dan haka kema ki kwantar da hankalin ki duk wasu dabaru zan koya miki babu boka" babu malam da kafafunta zata fita. "Zainab ta sauke ajiyar zuciya tace""Wallahi har na d'an ji sanyi a zuciyata aunty Balaraba nagode sosai" "yanzu dame kike ganin zamu fara so nake a rikirkita musu hankali gabad'aya wannan kwanaki ukun bana so suyi cikin nutsuwa saboda naga alamar zumudi a tattare dashi Aunty Balaraba tace""Na fahimci" yana da son 'ya'ya asubah nayi ki kirashi ki sheda masa cewa 'yarsa bata da lafiya sai da ta suma sau uku a dare. "Zainab tace""Yawwa aunty Wallahi wannan shawarar taki tayi min dadi nasan duk abinda yake yi yaji" "cewar Ummi babu lafiya sai ya bari yazo."" Aunty Balaraba tace""Dole mana gashi dama sunanan babarsa ne da yarinyar kawai ki kwanta kiyi baccin ki lafiya sai mun rikitashi dashi da amaryarta sa.." Zainab kwanciya tayi tana murmushin jin dadi gami da Allah Allah asuba tayi. 'Bangaran ango da amarya kuwa sun jima suna raya daran amarcin nasu kafin dukkaninsu su samu gamsuwa mai inganci sukayi wanka a tare kana suka kwanta tare da rungume junansu bacci sukayi mai dad'i irin wanda suka jima basuyi irinsa ba.. Abbah koda ya dawo daga sallah jallabiyarsa ya cire ya zauna gefan gado tare da tsira mata ido tana zaune kan dadduma cikin hijabi ta idar da sallah tana karatun al'kur'ani Ganin ta dauki sura mai "tsayi yasa a hankali ya kira sunanta. ta juyo a nutse tana kallonsa, ganin irin kallon da yake mata ne yasa tayi saurin sunkuyar da kanta k'asa Yace.""Rufe al'kur'anin kizo ki bani kulawar ki."" Shuru tayi gabanta na fad'uwa, jiya fa ya kai awa biyu a kanta yana sarrafata ashe da akwai saura, al'kur'anin ta rufe ta kasa" motsawa daga inda take. "Sunanta ya sake kira, ta dan kalleshi taga ya wani wargaje akan bed din ga jijiyarsa dake cikin gajeran" "wandonsa har ta fara miqewa, saurin dauke kanta tayi, tana jin shigar 'bakon yanayi a jikinta, ganin shi a haka yasa itama sha'awar ta bijiro mata," "A hankali ta miqe taje ta kashe haske dakin, kafin ta karasa bed din ta cire hijab din jikinta ta ajiye...Kusa" "dashi ta zauna, ya miqe da sauri ya janyota jikinsa, a haka ya rabata da kayan jikinta, ya matseta a" "kirjinsa ya shiga shafa ilahirin jikinta.....Najaatu ta dinga taimaka masa gurin sake tayar masa da sha'awa, dan nipples d'insa ta dinga matsawa tana tsotsa! Abbah ya shiga cikin wani irin yanayi na tashin hankali da tsananin bukatuwa, da sauri yasa hannunta cikin wandonsa aikuwa ta kama ta shiga murzawa tana sama da kasa da hannunta akai Ya dinga sakar mata wasu zafafan kesses masu hautsina" lissafi....Gabadaya ita dashi sun fice daga hayyancinsu babu abinda suke muradi a lokacin sai jinsu suna biyawa junansu bukata. Abbah Yay kwance a bed Najaatu na saman sa wannan karon ma itake "kokarin sakawa....a daidai lokacin kiran Zainab ya shigo wayarsa, babu wanda ya saurari wayar a cikinsu tuni sun lula duniya ta mussaman shiyasa duk 'karar da wayar take bai damesu ba, ni dai cikin Najaatu da Abbah ban san waye yafi wani ba, Dan Najaatu taji masifar dadin style din shiyasa ta riqe wuta sosai ta kusa ta sumar da bawan Allah! sai da yayi ta maza tukkuna ya nuna mata akwai aiki a gabanta dan birkitar da ita yay ya dogare kafafunta kan kafitar wuyanta ya rike da hannunsa ya fara kokarin zurkud'a mata jijiyarsa da takai ta kawo Har zuwa a lokacin Zainab bata fasa kiran waya ta kira ya kai saura" goma ba'a daga ba kamar mayya ta cigaba da kira. Abbah cikin fitar hayyaci ya sauka dan yana ganin zai iya shafe awa bai ji yanda yake so ba shiyasa kawai ya yanke shawarar duba wanda ke kiransa idan ya gama wayar sai ya koma ya cigaba. wayar ya dauka ba tare daya duba ko wanene ba ya kara a "kunnansa, maganarsa ma sam bata fita sosai yace.""Salamu alaikum.""" "Zainab ta fashe da kuka! tare da fad'in ""Innalilihi wa'ina ilaihi raji'un!."" Abbah Abbas na jin muryar Zainab" tana kuka da salati nutsuwa ta shigeshi ya bude murya sosai yana kiranta da tambayar abinda yake faruwa "Cikin wani irin kuka mai nuna tsantsar tashin hankalin da take ciki tace""Abban Mufida Baby Ummi bata" "da lafiya kwana mukayi a zaune nida su aunty Balaraba wallahi kafin gari ya waye sai da ta suma su uku gabadayan mu muna cikin tashin hankali.""" """Innalilihi wa'ina wa'ina ilahi raji'un.""! Abinda ya fad'a kenan tare da miqewa tsaye da sauri yace."" Ganin" "zuwa muje asibiti."" Ya kashe wayar da sauri ya juya ya kalli Najaatu dake kwance tana takure jikinta sabida tsabar sha'awar dake cinta daf take da samun satisfaction kiran wayar ya katse mata hanzari shiyasa duk jikinta ya saki Jallabiyarsa yasa yace.""Zainab ce ta kira waya baby Ummi babu lafiya kina ji" "kafin gari ya waye sumanta uku.""" "Ta d'an tsira masa jajayen idonta da suke buge da tsantsar sha'awa da bukatuwa tace"" Allah ya sawaqe.""" "Daga haka bata sake cewa komai ba taja bargo ta rufe jikinta takaici kamar ya kasheta Wannan Maganar Karyace dan gabad'aya jikinta bai bata cewa da gaske yarinyar ce bata da lafiya ba, Zainab ta shirya mata" iskanci ne duk domin ta ruguza mata farin cikinta. "Tana kallonsa ya nufi toilet tamkar zai tashi sama yayi wanka ya fito nan ma a gurguje ya shirya jikinsa," "ya tsaya kanta tare da kiran sunanta, Share shi tayi ta rufe idonta ruf kamar mai bacci Sai ya tsammaci" "da gaske baccin takeyi, da sauri ya bude kofar dakin ya fita.Bude idonta tayi tare da miqewa zaune, lallai Zainab bata da mutunci wato ita kuma nata salon iskancin kenan? Humm! ta lura sai ta tashi a tsaye a kanta sannan zata kyaleta zata gane bata da wayo dan wallahi itama sai ta rama iskancin da take" mata. Miqewa tayi ta nufi toilet domin tsarkake jikinta. "Abbah a gigice ya shiga gurin Zainab, ikon Allah sai akayi katari da lokacin yarinyar nata tsandara ihu! ana" sa mata nono a baki tana 'kin kamawa zuciya tayi dan tayi kukan tayi har tagaji saboda Zalinci aunty Balaraba tace kada Zainab din ta bata nono sai sun daidaici zuwansa. Yana shiga dakin su aunty Balaraba suka gaisheshi kamar wasu mutanan arziki suka fita daga dakin "Zainab na kuka tace""Ka gani ko Abban mufida nono ma taqi kamawa tun jiya babu komai a cikinta. Ya" "zauna kusa da ita tare da kar'bar yarinyar yace.""Maza sako hijabin ki muje asibiti.""" Ta miqe da sauri domin dauko hijab Abba tsirawa yarinyar ido yay yaga fuskarta tayi jawur gashi sai "sauke ajiyar zuciya take tana harbe harbe da kafafunta, hankalinsa ya sake tashi sai ya miqe tsaye da yarinyar a kafadarsa ya shiga zagaye dakin da ita yana mata addua a kunnanta." "Zainab murmushi farin ciki take tayi kwafa tare da cizar lips dinta a ranta tace"" Wallahi ba zan bari kayi" "kwana ukun nan lafiya ba."" hijabin ta zura tace""Abban mufida muje kada ta sake suma dan wannan ajiyar zuciyar da take daga haka shikkenan sai numfashinta ya dauke.""" Da sauri ya kama hanyar fita daga dakin ta rufa masa baya zuciyarta wasai koda zaiyi asarar kudinsa gurin siyan magani ita babu ruwanta in dai bukatarta zata biya. K'wararran likitan yara Dr Mahir ya tsananta binkicensa kan baby Ummi yana so ya tabbatar da abunda "ke damunta, duk iya binkicen da yayi a kan yarinyar sai ya nuna masa abu guda. Yayi dan rubutu a jikin" "wata takarda kafin ya dago kansa tare da zare gilashin idonsa, ya kalli Abbah a nutse yace.''Yallabai babyn nan yunwa ce ta kama cikinta a gaskiya yarinyar bata samun ishashshen nono idan mamanta nada matsalar ruwan nono mai zai hana a dinga had'a mata da madara domin inganta lafiyarta. Dr ya 'karasa maganarsa daso ya tabbar masa da cewar lallai su dauki al'amarin da muhimanci Abbah Zainab ya" tsirawa ido kimanin minti uku yana mata kallon tuhuma kafin ya girgiza kansa ya mayar dashi gurin "likitan yace.""To Dr yanzu wace madara mai inganci kake ganin zata dace da yarinyar nan hankalina ya tashi da jin wannan magana wallahi bana so wani abu ya sake faruwa da ita." "Dr yace""Akwai madara mai kyau da zan sa yanzu a kawo bayan nan kuma akwai magani guda biyu da" za'a siya mata insha Allahu jikinta zai ginu koda bata samun nono a kai akai madarar zata gamsar da ita. "Abbah yace.""Okey to ina sauraranka ka sai ka had'a mata komai wanda ya dace nagode."" Dr waya ya" dauka domin kira................. Zainab sai da ta kusa fashewa da kuka a sakamakon irin fad'an da yake zazzaga mata a mota murya na "rawa take bashi hakuri da kawo masa misalai Yace.""Kiyi min shuru kawai ba zan dauki kowane misalin" "da zaki kawo min ba, kishi ya rufe miki ido kina nema ki cutar da kanki kuma ki kashe min yarinya babu yunwa balle ishirwa a gidana ki 'ki cin abinci sabida mugunta yarinya ta nemi abincinta ki hanata to bazan lamunci wannan ba, Mutukar kina so mu zauna lafiya dake to ki dinga ci kina koshi Ummina na samun ruwan nono idan kika sake ciwon yunwa ya kamata to sai nayi sharia dake tunda ban gaza yin" "komai a gidana ba.""" "Zainab hawaye take cikin kissa take bashi hakuri da fadin ""Insha Allahu ta daina zama da yunwa zata" "dinga ci tana koshi."" Shareta yay ya cigaba da dravig ransa a bace ." Suna isa gidan kira ya shigo wayarsa koda ya duba sai yaga Abdulhamid ne ya daga wayar da sauri "Abdulhamid ya gaisheshi ya amsa tare da fad'in ""Ina fatan lafiya ko.''? Abdulhamid yace."" Lafiya lau Yallabai wasu mutane ne ke jiranka tun misalin takwas da rabi sun kira wayarka sau uku baka amsa ba.."" Yace.""Okey ban gani ba wallahi yau banajin zan zauna a kasuwa komeye kayi magana dasu idan na shigo gobe sai ka sanar dani."" Abdulhamid ya tausa murya yace.""Nima nace musu hakan yallabai sai suka nuna cewar su lallai kai suke bukatar gani Agogon hannunsa ya duba tara da rabi yace.""Okey ganinan" "shigowa yanzu."" Kashe wayar yayi ya kalli Zainab dake rungume da 'yarta yace.""Ki shiga ciki saura kuma" mugunta tasa ki hanata magani a lokacin na dai fad'a miki idan ciwon yunwa ya kama yarinyar nan sai na "baki mamaki wallahi tunda duk abinda kike kina sane."" Zainab a sanyaye ta bude kofar motar ta fita" hannunta rike da ledojin magani da madara...Juya kan motar yayi da sauri ya bar gurin Zainab ta'be bakinta tayi ta tura 'karamar kofar gidan ta shiga bukatar ta biya ta ruguza ranar amarcin Najaatu sai dai kuma idan ta tuno kalmar d'auri sai gabanta ya fad'i tsoro take kada tsautsayi yasa ciwon yunwa ya kama yarinyar ya d'aure ta dan ta lura babu abinda ba zai iya ba akan 'Ya'yansa....... *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake Vip.....#600 normal...#300 account... 0542382124...Binta umar gtbank...Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *****83 Najaatu kuwa bayan tayi wanka ta shirya jikinta sai tayi tunanin shiga kicin domun ta shirya "musu breakfast ta gama komai a nutse ta shirya daining din tayi dan gyare gyaren ta a daki da falo tasa turaran wuta mai kamshi sai ta fito falo ta zauna tana duba wayar ta, gabadaya a dame take dan abin yayi mutukar ba'kanta mata rai wanda harda shi din ma ta 'kullaceshi a zuciyarta sai daga baya data zauna tayi tunani ta gane baida laifi a yanda Zainab ta kirashi tana kuka da salati kowaye dole hankalinsa ya tashi yaji cewar 'yarsa babu lafiya harda suma to dole mutum ya shiga yanayi na tashin hankali" mussaman shi da yake da jarabar son 'ya'yan tsiya. Tana zaune ta falo tana tunane tunane da duba agogo a qallah da fitarsa yanzu zai kai awa hudu ko fiye "da haka, tana ganin idan ba wata gagarimar matsala bace yaci ace sun gama da asibiti ya dawo gida," "zuciyarta ta shiga sa'ke-sa'ke ""Watakila ma tuntuni sun dawo daga asibitin Zainab din ta hanashi dawowa, taji gabanta ya fadi jin irin abinda zuciyarta ke sa'ka mata." "Number shi ta nema ta fara kira Wayar ta gaji da ringing ta katse ba'a daga ba, a take idanunta suka" "ciko da ruwa, babu Shakka Zainab ta zame mata kadangaran bakin tulu zuciya ta ciyo ta ta dinga ji kamar ta dauki mayafi taje gidan Zainab din suyi wacce zasuyi wannan ai rashin adalaci ne." Hanci ta sha'ka cikin tsantsar bakin ciki da takaici ta goge hawayen da ya zubo a fuskarta ta sake kiran wayar a karo na biyu Abbah na tare da 'bakin sa dalili kenan da yasa bai samu damar daga wayar ta ba koda ya duba yaga itace sai kawai ya katse wayar ya mayar da ita aljihu ya cigaba da abinda yake. Hakan yayi masifar d'aga mata hankali miqewa tayi tsaye ta shiga zurga zurga a falon zuciyarta sai sak'a mata mugun abu take tana cewa kawai taje taci uwar Zainab din shi kuma idan ya dawo ta nuna masa rashin adalacinsa a fili Zama tayi kan kujera ta rufe fuskarta da tafukan hannayenta tana kiran "sunan Allah, hakika kishi bala'i ne masifa ne dan yanda take jin wani irin zafi a zuciyarta tana ganin zata" iya aikata komai ganin yanda zuciyarta keta tunzurata yasa ta mayar da hankali gurin kiran sunan Allah tare da adduar Allah ya sassauta mata abinda takeji a cikin zuciyarta.. Haka ta gaji da zaman jiransa ta zauna a dainig tayi break dinta cikin kunci da bacin rai ta shiga daki ta "kwanta kusa da d'anta tana hawaye, a haka bacci mai nauyi ya dauketa." "Najaatu sai kusan la'asar ta tashi dan sallar azuhur ma ba tayi ba, sai da tayi wanka tukkuna ta tsaya kan" "dadduma ta gabatar da sallolinta, tana miqewa idanunta ta d'ora kan agogon dake kafe a dakin, hud'u da Rabi har ta gota." Zama tayi gaban dressing mirror tayi kwalliya daidai misali turaruka tasa a jikinta masu kamshi da sanyi "ta dauko wata bodywork white tasa a jikinta sai tayi amfani da wando roba jins blue wandon ya matseta ya fito mata da sharf dinta, after dressing ta d'ora akai ta ta d'aura dankwalin after din a kanta, falo ta fita ta zauna zuru tana kallon kofa tare da duba wayarta allai Abbah babu kiran waya bare text hummm! Kallo ta kunna ta kama tashar Arewa 24 lokacin suna maimaicin dadin kowa, sai film din ya dauki hankalinta sosai ta dinga dariyar (Adama da Kamaye) film din ya d'ebe mata kewa sosai wanda har yasa ta d'an samu sassauci a cikin zuciyarta, wannan karon ba ta sake tunanin kiran wayarsa ba text" ta tura masa kamar haka..... "_""Assalam Annuri barka da yamma na kira wayarka domin na tambayi jikin Ummi baka dauka ba to ina" "fatan Allah yasa lafiya, ka dawo lafiya.""_" "Tana tura masa ta miqe ta nufi kicin domin shirya abincin dare, tuwon semo tayi ta shirya miyar agushi" da busheshshen kifi sannan tayi miyar nama daidai misali ta gyara kicin din tsaf ta shirya gurin cin abincin ta nufi bedroom domin duba d'anta dake bacci! Daukarsa tayi ta goya a bayanta ina dalili tayi "ado da kwalliya shi wanda tayi dominsa yaki ya dawo ya gani, yamma tayi ba zata bar d'anta a kwance ba, dalili kenan daya sa ta goya shi a bayanta ta fito falo ta zauna, sai dai tana zama yaron ya fara motsi yana" "kuka da alama baya son goyon sauko dashi tayi tana dubashi, hannu yake sawa a baki yana kama rigarta" nono yake so.....Haka ta cire after dressing din ta fito da nono tasa masa a baki Fuskarsa ta tsirawa ido "tana kallo yaron kammaninsa da ubansa sai sake fitowa yake, taji zuciyarta na karyewa, idanunta ya cicciko da kwalla kawai sai ta shiga kiran innalilihi wa'ina ilahi raji'iun! Hakika tana fargabar zuwan ranar" da Daddy zai san waye ubansa me yayi a kashe shi. 'Bangaran Zainab kuwa yini sukayi cikin farin ciki ita da 'yan uwanta su d'ora su sauke a rana sai suyi "girki kusan kala biyar 'barna sukeyi sosai a gidan nama komai yawansa aka kawo baya kwana uku sun cinye al'amarin nasu sai gyaran Allah haka kawai bayan sunci sun koshi sai su tsiri had'a tea da tsakiyar rana suyi ta 'barnar madara da sauran kayan tea babu abinda ya damesu. Zainab tace""Wallahi aunty" "Balaraba kin iya tsara makirci ki duba dai ki gani lokaci guda al'amura sun dagule babban abinda ya sake sani cikin farin ciki shine muna dawowa yana niyyar ya koma gidanta aka kirashi a kasuwa cewa yana da b'aki nasan kuwa ba zai koma gidan ba sai lokacin tashi daga kasuwar yayi ai naji dadi da hakan ta kasance nasan tana can tana jin bakin ciki a zuciyarta."" Aunty Balaraba wacce suke shan farfesun kaji tace."" Ai na fad'a miki dole hankalinsa ya tashi tunda mutum ne mai son 'ya'ya yau da daddare misalin sha biyu ko sha daya kafin dai ya kashe wayarsa ya kwanta sai ki sake kiransa kina kuka na tashin hankali ki sheda masa cewa jikin Zainab ya rikice a guje zai zo sai kawai ki yaudareshi ya kwana a gurinki na" "tabbata sai ta kusa mutuwa dan takaici.""" "Zainab mirmushi tayi tace""To aunty haka za'ayi Dariya suka fashe da ita tare da fad'in ""Shegiya" "mutsiyaciya da kafarta zata gudu."" A daidai lokacin Halisa ta shigo ta samesu sai shewa suke, itama maigidan ne ya kirata a waya yake fada mata rashin lafiyar yarinyar dalilin daya sanya kenan ta shigo ta dubata." "A nutse suka gaisa tace""Ashe Ummi ba taji dadi ba wallahi sai yanzu ya kira ni a waya ya fad'a min Allah" "sarki Allah y bata lafiya.""" "Aunty Balaraba tace""Ameen ya Allah wallahi jiya munsha fama da yarinyar kamar ba zatayi rai ba ta" dinga suma gashi taki kar'bar nono wai ashe rashin abinci ne ya janyo mata kasancewar nono zainab "baida kyau da inganci yasa dr ya bata magani da madara kinga tunda aka dama mata madarar aka bata maganin take bacci lafiya lau.""" "Halisa tace""Allah sarki ai ciwon yaro da akwai abun tausayi Allah dai ya sawwake."" Suka amsa da" "ameeen."" Halisa na kokarin miqewa Zainab tace""Aunty Halisa ina amaryarki.""? Aunty Halisa ta kalleta tana mamakin maganarta...Tace""Najaatu wai.""? Zainab ta d'aga kanta tana ta'be bakinta. Aunty Halisa" murmushi tayi tana mamakin yanda Zainab ta damu da Najaatu babu shakka idan tace zata damu akanta akan Najaatu to zata jefa kanta a masifa dan Najaatu itace ruhin mijinsu shiyasa itama tunda ta fahimci haka ta watsar da makamanta tana ganin duk wani abu da ya dace tayi tayi akan Najaatun amma bata "samu nasara ba karshe ma nadama da dana sani ne ya biyo bayan abinda tayi, kuma gashi Najaatun na" "nan nata rayuwarta sannan mijinta bai fasa so da kaunarta ba, tana ganin da zata bawa Zainab shawara ta dauka to da tace ta watsar da makamanta ta zauna lafiya da Najaatu domun ta samu soyayyar mijinta........murmushi tayi tace.''Ki shiyar ki dai aini tuntuni anyi min kishiya Najaatu ba kishiya ta bace" "taki ce.""" "Aunt Balaraba tace""Kwarai kuwa aike kam yar kallo ce sai ki sakar musu su fafata.'' Halisa tace""Shine" "abinda nagani nima to ni daina zan shiga gurina Allah ya kara lafiya.'' Tana gama maganarta ta fita daga dakin, tana futa suka dasa gulmarta sai zaginta suke Zainab na cewa ai dama tuntuni ta fahimci so take ta had'a kai da Najaatun to duk zata iya dasu wallahi." Abbah Abbas bai samu kansa ba sai yamma likis ganinsa a kasuwar yasa Jamaa suka riqeshi sai da yay da "gaske sannan ya samu nasarar fitowa daga kasuwar, a hanya magariba tayi masa sai ya shiga tunanin ina zai fara nufa gidan Alhaji ko kuma zuwa duba jikin Ummi ko kawai ya wuce gidan Najaatu dan gabadaya hankalinsa na kanta yaga kiranta da text dinta amma rashin nutsuwa ya hana shi ya bata amsa, yanke shawarar zuwa gidan alhaji yay ya gaisa dasu bayan ya fito sai ya duba Ummi d'in A gurguje" "suka gaisa da mahaifiyar tasa nan yake sheda mata rashin lafiyar Ummin tace insha Allahu gobe zasuje su dubata, da zai tafi ta bashi wata leda viva da kayan mata a ciki wai ya kaiwa Najaatu kar'ba yay tare" dayi musu sallama ya tafi. Yaji dadi daya shiga gurin Zainab ya ganta a zaune tana cin abinci ga Ummi din a cinyarta tana bata nono "ya zauna yana tambayarta yanayin jikin yarinyar, tace""Alhamdullhi jiki yay sauki yini tayi bacci yanzu data tashi shine nake bata noni Yace.""To Alhamdullhi sai ki mayar da hankali gurin bata abincinta" "da kuma maganinta."" Tace""Insha Allahu."" Sallama yay mata ya miqe da niyyar tafiya taji tamkar taje ta janyo shi, kwafa tayi tare da jan tsaki kasa kasa......Abbah gurin Halisa ya shiga suka gaisa sosai ya tsaya ya duba yaransa yaji matsalarsu kafin yayi musu sallama ya tafi Najaatu ta sake sabon wanka tayi" gayu sosai tai kyau jikinta da gidanta sai kamshin turare yake. "Ganinta a nutse da yaronta yasa yaji wata nutsuwa ta saukar masa, yasan Najaatunsa ta wani gefan tana" "da hankali da nutsuwa zata kar'bi uzirinsa kuma ba zatayi masa hauka ba, hakika yaji dadin yanda ta tar'beshi ta bashi abincinta mai dad'i ya cika cikinsa." "Sai da ya nutsu tukunna tazo ta zauna kusa dashi tare da ri'ke hannunsa cikin alhini tace"" Wallahi tunda" "ka fita na kasa samu nutsuwa sai sa'ke-sake nake a zuciyata na abubuwa marasa kyau amma naji dad'i da naji kace jikin yarinyar da sauqi ina rokon Allah ya bata lafiya.""" "Abbah yana kallonta da kyakkyawan murmushi a fuskarsa yace."" Ameeen ya Allah nagode sosai da kika" "fahimce ni, ni kaina banyi tunanin yau zan zama busy ba wallahi naci burin na zauna a tare dake na gwangwaje amarcina sai wannan matsalar ta shigo ciwo ya wuce komai mussaman na k'aramin yaro bayan mun dawo daga asibiti ina kokarin dawowa gareki aka sanar dani ina da 'baki a kasuwa wannan" "dalilin ne yasa kikaga ban shigo da wuri ba ina fata dai ranki bai 'baci ba.""" "Murmushi tayi tace""Haba dai raina bai 'baci ba wallahi nasan ai duk inda kake ina cikin zuciyarka kuma" "dole aiyi maka uziri duba da yanayin yanda kake hurd'a da jamaa.'' Yay mirmushi mai kyatarwa, yace.""Jeki dauki min abokina mu gaisa." "A hankali ta miqe ta isa inda Daddy ke kwance ta daukoshi, Abbah ya kar'bi yaron yana dariya tare da" "daga shi sama yana masa wasa, yaron ya dinga dariya yana cilla kafafunsa, Ya kalleta da da mirmushi a fuskarsa yace.""Yaron nan wai zaiyi wata nawa yanzu."" ?" """Watanshi takwas da 'yan kwanaki."" Ya shiga girgiza kansa da fad'in abin babu wuya to Allah ya raya" "mana shi.'' Ta amsa da ameen tare da kar'ba yaron daga hannunsa....Abbah loptop d'insa ya janyo ya shiga dubawa kamar yanda ya saba, Tana kusa dashi suna hira sama- sama har ya d'an duba abunda zai duba ya rufe loptp din idanu a lumshe ta kalleta, tana kokarin miqewa dady za taje ta gyarawa shimfida, sai kawai ya bita da kallo har ta shiga bedroom din.....Minti biyar ya miqe yabi bayanta, lokaci har tasawa yaron pampars tasa shi a net tana kokarin miqewa ya shigo, hannunta ya rike suka zauna gefan gado, ta kalleshi taga yanayin da yake ciki sai ta sunkuyar da kanta tana murmushi...Yace.""Ina tunanin cikin satin nan zamuje miyi umara mu dan huta dan idan banyi da gaske ba jamaa na iya hanani na more" "amarcina so ki zauna cikin shiri insha Allah acikin satin nan zan shirya mana tafiya zuwa kasa mai tsarki.""" "Da murmushi a fuskarta tace""To shikkenan amma sai nake ganin anan din ma za'aka iya amarcinka.""" "Girgiza kansa yay yana wasa da hannayesa a jikinta yace.""Nafi so nayi nesa da gari sai nafi samun nutsuwa. shuru tayi tana jin yanda tsigar jikinta ke tashi, ya riga ya zuge mata zif din rigarta yana ta" "cakuda mata nonowa! gabadaya jikinta ya saki gashi wanka take so tayi A hankali tace""Abbah ka bari" "nayi wanka."" Fuskarsa yake goga mata a wuyanta gemunsa sai tsikararta yake yace.""Ba sai kinyi wanka a haka ma kina kamshi ."" shuru tayi tana sauke ajiyar zuciya. Abbah rikita mata lissafi ya shiga yi da" kalolin soyayyarsa wanda yasa ta hautsine ta dinga mayar masa da martani tana kesses din fuskarsa tare da shasshafa jikinsa. Maqale junansu sukayi bayan sun raba jikinsu da kaya suka dinga wasanni da jikinsu. Najaatu ta dinga bashi mamaki ganin yanda take sarrafa shi sai kace wata babbar mace ko Halisa da taga "jiya da yau ba zata nunawa Najaatu komai ba, a daidai lokacin da suke daf da biyawa junansu bukata, kiran waya ya katse musu hanzari Abbah gabansa ya fad'i! sai ya shiga tunanin wayar jiya zuciyarsa" "tace masa watakila jikin Ummi ne ya tashi, sai kawai ya fara kokarin sauka! Najaatu ta kamoshi ta qamqame shi tsam! ta hanashi sauka tana masa magana qasa-qasa! sam bai ma ji abinda take cewa ba yace.""Ki bari na duba wayar nan na gani ina tunanin Zainab ce."" Ranta ya sake 'baci! a sarqe tace""Umum!" "kawai ka cigaba idan komai yayi kammala sai ka kirata kaji komeye.""" "Kallonta yay duk da da akwai duhu a dakin sai da ya fahimci cewa tana cikin yanayi. Yace.""Bana jin zan" "iya samun wani kuzari a yanzu hankalina ba'a jikina yake ba dan ina tunanin jikin ummi ne ta tashi.""" Sai kawai ya zare jikinsa ta zura kafafunsa kasa wayar ya laluba kan bedside ya d'auka daidai lokacin wani kiran ya sake shigowa ganin sunan Zainab kan screen din wayar yasa da sauri ya daga wayar. Yau "ma da innalilhi ta fara kuma kukan da take har yaci uwar na jiya tace ""Abban Mufada Ummi tun misalin sha daya da rabi numfashinta ya dauke gashi yanzu sha biyu da rabi bata farfado ba.""! Cikin damuwa gami da tashin hankali yace."" Me yasa tun lokacin baki kirani ba sai yanzu..""? Haba Abban Mufida tun yaushe nake kiran wayar taka kaqi dauka ni dai har na fitar da rai da yarinyar nan wallahi."" Cikin gursheken kuka ta karashe maganar. ""Kashe wayar yay ya mike ciki tashin hankali ya lalubi jallabiyarsa" "da gajeran wanda yasa gabadaya ma baiyi tunanin wanke najasar dake jikinsa ba ya kama hanyar fita. Najaatu miqewa zaune tayi rai a bace ta kira sunansa""Abbah.""! Juyowa yay yana kallonta da" "fad'in ""Najaatu kiyi hakuri kinji ko bari naje na duba yarinyar nan naga halin da take ciki "" Karya ne fa" wallahi Ummi lafiyarta lau kawai tana so ta hanaka nutsuwa ne bayan haka kuma tana so ta kuntatawa zuciyata shiyasa ta d'orawa 'yarta ciwo. "A fusace! Yace""Saboda rashin hankali haka kawai sai ta d'orawa 'yarta ciwo ashe kenan abinda Dr ya" "fad'a karya ne ko? kada ki sake wannan maganar kawai kiyi addua Allah ya bata lafiya."" Najaatu sakin baki kawai tayi tana kallonsa ya kama handile zai bude kofa tace""To kada ka fita da najasa yana da kyau ka wanke ta."" karamin tsaki yaja ya dawo da sauri ya shiga toilet din, yayi wanka ya fito ya sanja jallabiya da gajeran wando duk tana zaune tana kallonsa yasa kai ya fice daga dakin ba tare da ya tanka mata ba, lallai kawai saboda tace ciwon Ummi karya ne yake jin haushi, lallai babu shakka Zainab tana so ta sanyawa mijinsu rashin nutsuwa, a gida da waje al'amarin gabadaya sai ya tsaya mata a rai ta dinga jin" wani irin tausayinsa na ratsa mata zuciya... *Afuwa Mommy naga Comment d'inki......Tunda Halisa ta ha'kura ta sakarwa Najaatu to ina ganin "abinda Zainab take 'karamin alhaki ne, Najaatu ta riga tayi mata illah tunda har ta fahimci cewa itace" tauraruwa a zuciyar mijinta to duk wani makircin ta gami da sharin ta ba za suyi tasiri ba dole za tayi ta gaji ta daina* *Littafin na kudi ne * Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abun yake Vip group #600 normal group #300 account.... 0542382124...Binta umar gtbabk idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan number. *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* "******84 Abbah cikin damuwa gami da mayar da al'amuransa ga Allah ya isa gidan, yanayin yanda" "yake horn da karfi yasa maigadi ya tashi a firgice!! ya fito da daga dakinsa da toch a hannunsa, k'aramar kofa ya bud'e tare da leka kansa, ganin motar maigidan yasa da sauri ya nufi bakin gate ya fara kokarin bud'ewa, ko 'karasa budewa baiyi ba yasa hancin motar a gidan, maigadin yay saurin ya matsa gefe, nan bakin gate din ya faka motar ya bude ya fito, maigadin ne ya karasa da sauri yana gaishe tare da fad'in ""Alhaji ina fata dai lafiya nagan ka cikin dare."" Yace.""Malam Halliru babu lafiya wallahi yarinya ce bata da lafiya."" Malam Halliru yace.""Ayya nima dama ganinka a cikin wannan daren yasa na zargi akwai wani to Ubangiji Allah ya bata lafiya."" Abbah na kokarin shiga gurin Zainab ya amsa da ameen Zainab" "dasu aunty Balaraba suna zaune suna magana kasa _kasa jin sallamarsa yasa Zainab ta shiga sheshshekar kuka had'e da fad'in ""Aunty Balaraba ki cigaba da shafa mata ruwa a fuskarta ko Allah zai sanya numfashinta ya dawo ni kam na fitar da raina da yarinyar nan."" Cikin kuka ta'karashe maganar, Aunty Balaraba dake rungume da baby ummi wacce take bacci sai kawai ta shiga shafa mata ruwa a fuskarta da jikinta tana fad'in ""Haba Zainab cuta ai ba mutuwa bace yarinyar nan dogon suma tayi zata farfad'o" "insha Allah.""" "Zainab na sha'kar hanci tace""Ai abun ne ya tsorata ni wallahi kina ganin fa ko motsi ba tayi."" Aunty" Balaraba na kokarin magana ya shigo dakin Zainab a guje taje ta rungumeshi tana kuka na fitar hankali take fadin shikkenan Abban mufida na rasa "'yata gatanan a hannun aunty Balaraba tun dazu ake shafa mata ruwa numfashinta yaki ya dawo.""" Cikin sanyi jiki gami da miqa al'amuransa ga Allah ya cireta daga jikinsa ya nufi inda aunt Balaraba ke "zaune. Hannu yasa ya kar'bi yarinyar aunty Balaraba na share hawaye tace""Gata nan dai mun rasa" "abinda ke damunta numfashinta ya dauke ya dawo haka yake gashinan dai yanzu ya dawo saboda ruwan da nake shafa mata a fuska da jikinta.""" "Ba tare da yace komai ba ya nemi gefan gado ya zauna da yarinyar a hannunsa, aunty Balaraba ita da yar" uwarta suka mi'ke simi simi suka fita daga dakin. Abbah yarinyar ya zubawa ido dake ta faman sauke ajiyar zuciya dalili ruwan da aunty balaraba ke sa "mata a jiki mai sanyi ne sai ma ta shiga makyarkyata tana cilla kafafunta da hannuwanta sama kafin ta fara wani irin kuka da atishawa.""" "Da sauri Zainab tazo ta zauna kusa dashi tare da fadin ""Alhamdullhi Allah nagode maka daka dawo min" "da numfashin yarinta Allah kaine abin godiya.""" "Kokarin kar'barta take daga hannunsa, ya hanata ido kawai ya tsirawa yarinyar kamar me neman wani" "abu, yana so ne ya gazgata naganar Najaatu nacewar rashin lafiyar na karya ne sai dai kuma yanda yarinyar ke janyo numfashi da kyar tana atishawa da makyarkyata yasa ya 'karyata maganarta tabbas ciwon Ummi ba karya bane gaskiya ne. Yace."" Jeki dauki mata kayan sanyi masu kauri ki shiryata" "muje likitanta ya dubata."" Zainab da sauri ta miqe daga kusa dashi ta nufi drowar kayan yarinyar. Shi" "kuwa cikin dubara ya cirewa yarinyar kayan jikinta saboda tsananin mugunta da rashin imani aunty Balaraba ta ji'ka mata jikinta jagab da ruwan sanyi......cikin tausayi ya shirya 'yarsa har pampars shi yasa mata, abinda bai ta'bayi ba amma yau yayi a kan Ummi wani irin tausayin yarinyar ne ke ratsa zuciyar" Karbar yarinyar tayi kamar gaske tasa towel ta goya ta mikewa yay yasa hannu cikin aljihun jallabiyar "jikinsa ya dauko wayarsa, number Dr Mahir ya nema yana addua Allah yasa ya sameshi Cikin ikon" "Allah kuwa tana fara ringing ya daga, gaisawa sukayi kafin ya sheda masa abinda keda akwai, Mahir yace kawai su sameshi a asibiti.......Dr Mahir ya jima yana duba yarinyar domin sanin abinda ke damunta, tabbas binkicensa bai nuna masa komai ba sai abinda ya nuna masa a baya sai kuma zazzabi da mura daya fahimci sun d'an kama yarinyar suma kuma ba suyi karfi ba amma maganar daukewar numfashi shi dai duk iya binkicen da yayi a kan yarinyar bai ga abinda zai janyo numfashinta ya dauke ba na farko yarinyar bata da sanyi a jiki mura mai zafi ko asma da sai sauran cututtukan dake sanya numfashin" mutum ya sar'ke! yarinyar nada lafiya matsalar rashin samun ingantaccen nono ne kawai yake damunta Wannan bayanin shi yayi Abbah Abbas yana sake jaddada masa cewar yarinyarsa lafiyayyace dan duk "binkicensa bai ga abinda ya sar'ke mata numfashi har ta suma ba sai dai yanzu daya fahimci shigar zazzabi da mura a jikinta yace."" Amma kuma hakan na iya faruwa da yarinyar mussaman idan ta nemi" nono a lokacin da take bukata bata samu akan lokaci ba hakan na iya janyowa tayi kuka mai tsanani "wanda zai sanya har numfashinta ya dauke """ "Abbah ajiyar zuciya ya sauk'e! bayan ya gama jin jawabin Dr mahir din yace."" Dr idan na fahimci" "maganarka kana so ka tabbatar min da cewar Yarinyar nan babu wani ciwo mai zafi a tare da ita wanda zai janyo mata shiga matsalar da muka zo maka da ita kenan."" Dr mahir yace.""Kwarai kuwa yarinya lafiyarta lau in bayan abubuwan dana fad'a maka a baya suma kuma ina ganin idan an kiyaye to ba za'a sake samun wata matsala ba."" Abbah yay shuru yana nazarin maganar ikon Allah dai ya wuce komai amma kuma ya soma hango k'amshin gaskiya a kan maganar Najaatu ta dazu Ajiyar zuciya ya sauke ya" "miqawa Dr din hannu tare da fadin Nagode kwarai dr insha Allah za'a kiyaye da dokokin daka fad'a."" Dr mahir "" Ya miqawa Zainab wata leda da magunguna a ciki yace."" Wad'annan magungunan zasu taimaka" "insha Allah yanzu ma idan kunje gida sai abata maganin mura da zazzabi ne.""" "Zainab tace""To mungode Dr."" Abbah hannu ya sake miqa masa hannu sukayi sallama kafin su fita daga" ofis din Tun mota yake nazari akan al'amarin tabbas yana ganin zai sanya ido sosai domin ya tabbatar da gaskiyar magana. maimakon daya sauketa ya wuce gidan Najaatu sai kawai yasa maigadi ya rufe "gate din, Zainab na gani haka taji tamkar ta zuba ruwa a kasa tasha dan farin ciki Tare suka nufi" "dakinta ya zauna gefan bed yana kallonta tana ta wani lallaba yarinyar yace ta zauna ta bata nono tukkuna sai ta bata maganinta, ta zauna kusa dashi ta fito da nono tasawa yarinyar a baki, Allah sarki baby Ummi ta kama nono ta dinga tsotsa kamar ba zata bari ba hakika Zainab na zalintar 'yarta. Sai da" "ta koshi tukkuna ta cire nonon daga bakinta, ya fito da maganin ya na nuna mata yanda zata bata" "Kar'ba tayi a nutse ta bata maganin ya kar'beta daga hannunta, addua yay mata ya tofa mata a jiki" "sannan ya sata a net dinta ya rufeta da bargo......Zainab kuwa kayan bacci tasa tazo ta kwanta kusa dashi tare da fad'in ""Abbahn Mufida ba zaka tafi ba dare yayi fa.""" "Yace""Zan kwana tare daku domin naga yanayin jikin Ummi.'' Farin ciki kamar ya kasheta tace""To ka" "kwanta ka huta mana."" Yace.""Kada ki damu zan kwanta. Shuru tayi tare da rufe jikinta da bargo," Wayarsa ya dauko ya duba lokaci d'aya da kwata na dare! Yanzu Najaatu watakila tayi bacci kuma bai "zama lallai ta bar wayarta a kunne ba, gwada kiran wayar yay sai ta shiga. Najaatu sai da taci" "kukanta ta koshi tukkuna taje ta tsarkake jikinta ta dawo ta kwanta da sha'awarta dan gabadaya ta kasa samun nutsuwar da take bukata, so take tayi bacci takaici da bakin ciki ya hanata, sai ta dauki wayarta ta kunna tana dube dube nan taga har d'aya tayi bai dawo ba jikinta yay sanyi zuciyarta tace watakila acan zai kwana kawai kiyi kwanciyarki ki kyaleshi kuma kada ki kira wayarsa. da wannan shawarar" "take kokarin kashe wayar sai kiransa ya shigo, da kamar kada ta dauka sai dai ta d'aga ciki ciki tayi" "sallama da fadin""Ya jikin Ummi.""" "Abbah ya sauke ajiyar zuciya a nutse yace.""Da sauki yanzu yanzu muka dawo daga asibiti dama na kira ki" "ne domin na fad'a miki cewar zan kwana tare dasu saboda gudun abinda ka iya zuwa ya dawo ba dai fata nake wani abun ya 'kara faruwa ba""." "Ta daure zuciyarta tace""Eh dama nima abunda nake tunanin kiran ka na fad'a maka kenan babu damuwa" "ka zauna kawai sai da safe."" Tayi gaggawar kashe wayarta dan ma kada yayi mata wata maganar da zata sanya ta fada masa mai zafi............shuru yay da waya a hannunsa yana mamakin katse masa hanzari da tayi, wannan maganar data fad'a ba har cikin zuciyarta ta fad'a ba saboda shi ba yaro bane ya fahimci kamar gatse tayi masa to idan ma hakane baya tunanin zai koma gidanta har sai ya tabbatar da zarginsa.....Wayarsa ya kashe ya dan juya bayansa gurin Zainab inda ita kuma tayi saurin rufe idonta kamar me bacci nan kuwa a kunnanta komai ya faru, murna da farin cikinta sai 'kara nunkuwa suke a" cikin zuciyarta. "Kwanciyar rigingine yayi a kusa da ita ya cigaba da nazari da tunanin al'amuran da suke faruwa, da" wannan tunanin bacci ya daukeshi Kiran sallar farko a kunnanshi ya miqe da sauri ya nufi toilet "wanka yayi ya fito daure da alwala, bashi da matsalar kayan sawa tunda ko'ina yana dasu, ya sanja jallabiya ya fita zuwa massalaci.......Zainab yana fita ta tashi da sauri ta bude kofa ta nufi dakin dasu aunty Balaraba suke kwana. Cikin murna da farin ciki take sheda musu abunda ya faru. Aunty balaraba murmushin samun nasara tayi tace""Ai na fad'a miki sharrina yafi kala dubu kinga dai lokaci kankani kin rikita musu lissafi jiya ya yini a kasuwa yau kuma ya kwana a gidanki haka zaki dinga kirkirar abubuwa iri iri duk ranar girkina dan ki raba masu hankali."" Zainab tace""Ai naji dadin shawarwarin ki wallahi dama ni babban burina na k'untatawa shegiya."" Aunty balaraba murmushi tayi ta miqe ta nufi toilet domin daura alwala Zainab zama tayi har suka idar da sallar suka cigaba da shirye shiryen makirci da sharrin da zasu shiryawa Najaatu. Abbah bai dawo gidan da wuri ba kasancewa ya tsaya gurin jana'izar wani" "bawan Allah daya rasu a bayan gidanshi a massalaci a kasanar da mutuwar sai ya tsaya akayi jana'iza dashi sannan ya dawo gidan koda ya shiga gidan kai tsaye gurin Halisa ya nufa, Baba Larai na ayyukanta yara kuma basu dade da tafiya makaranta, tsayawa yay suka gaisa da ita kafin ya nufi bedroom din Halisa......Tana zaune a kan kujerar mudubi tana gyara daurin dankwalinta ya shigo dakin sallamarsa ta amsa ya k'arasa bakin gado ya zauna.......Kallonsa tayi cikin nazari da tunani tace ""Abbahn Mufida lafiya" kuwa? na ganka a hargitse! "Ajiyar zuciya ya sauke tare da fad'in "" Jikin Ummi ne ya hargitsani Halisa na rasa abinda ke damun" yarinyar nan wallahi daga jiya zuwa yau duk na damu gashi likita yace lafiyarta lau amma kuma Zainab kullum sai ta kirani a waya da daddare tana kuka tana fad'amin cewar yarinyar babu yanda take jiya a rikice na shigo gidan nan sabida ta kira ni tana fad'a min yarinyar numfashinta ya dauke tun farkon dare har sha daya na dare be dawo ba haka nazo na tarar dasu suna shafa mata ruwa a jikinta a daran mukaje mukaga likita ya dubata yake tabbatar min da cewa yarinyar bata da ciwo mai zafi wanda zai sanya numfashinta daukewa na tsawon wannan lokacin. "Halisa mirmushi tayi ta girgiza kanta kafin tace""Yarinyar nan fa lafiyarta lau wallahi uwarta ce ke d'ora" mata lalurar 'karya duk dan ta hanaka zaman lafiya sannan kuma bukatarta ta biya ta kuntatawa Najaatu. "Ya dinga kallonta yana nazarin maganarta yace.""Yanzu Halisa Zainab sai ta 'kir'kiri ciwo ta d'orawa 'yarta" "dan biyan bukatarta."" Halisa dariya tayi kafin ta ta'be bakinta tace""Gashinan kuwa ka gani ni da kunnena naji suna maganar ita da 'yan uwanta a dazu dana shiga duba jikin yarinyar naji suna maganar to ban fahimta sosai ba sai da kayi min maganar wai ashe a gidan nan ma ka kwana.""" "Cikin wani irin yanayi Yace.""Kika ce kinji da kunnanki suna maganar kan al'amarin..""" """Idan nayiwa Zainab da 'yan uwanta sharri meye ribata wallahi kaji rantsuwar muslumi da kunnena naji" "suna maganar suna dariya sai da kayi min maganar a yanzu na sake fahimta amma ni ban fad'i maganar dan ka dauki zafi b. Hannu ya d'aga mata bai bari ta karasa ba ya miqe ya fita daga dakin, kai tsaye" "gurin Zainab ya nufa, Hayaniyarsu da shewarsu yaji a daya dakin can kunnuwansa suka jiyo masa kukan Ummi dake dakin Zainab da sauri ya nufi dakin yaga yarinyar saboda kuka da mutso mutso har ta fito daga cikin net dinta ga bargon dake jikinta ya toshe mata hanci! da mugun sauri ya ka'rasa inda take bargon yayi gaggawar daukewa yarinyar ta sauke wata zazzafar ajiyar zuciya! gumi hawaye majina duk sun 'bata mata fuska! Abbah hannusa yasa ya dauki yarinyar jikinsa sai kyarma yake ya shiga jijjigata inaa! kamar sake tunzurata yake ta dinga kuka tana yakushin fuskarsa, cikin tsantsar tashin hankali gami da" nadamar kar'bar auran Zainab ya fita da yarinyar a kafadarsa Cin karo yayi dasu sun fito daga dakin dik su ukun a sakamakon jin kukan yarinyar daya cika "falon......Zainab a tsorace! ta karasa kusa dashi ta miqa hannu zata kar'bi yarinyar ya wanke fuskarta da wani gigitaccan mari! Gefe guda ta matsa tare da dafe kumatun ta da hannunta jikinta in banda rawa babu abunda yake. Ya kalli su Aunty Balaraba yace.""Wallahi kunji kunya kun zama annoba a guri yanzu" "da girmanku da komai kuke aikata abu irin na marasa imani! me yarinyar nan tayi muku kuke azabtar da ita! Kuna manya masu shekaru wanda suke sama da nata ba zaku d'orata a hanya mai kyau ba sai ku d'orata hanya mara kyau! hanyar da zata cutar da kanta da abinda ta haifa, hakika zamanku a gidan nan be amfaneni da komai ba sai sharri! ya kalli Zainab dake wani irin kuka na tsoro yace.""Zainab ban ta'ba tunanin kishi zai rufe miki ido ki nemi hanyar halakar da abinda kika haifa ba, ashe dama karya kike Ummi lafiyarta lau amma kika dora mata lalura duk dan ki hanani samun nutsuwa shin yanzu meye ribarki nayin hakan? Jiya Dr sai da ya fad'a miki matsalar yarinyar nan ashe kamar 'kara tunzuraki yay kin barta ita kadai a daki tana ta kuka ke kina ta tare da wad'anda zasu kaiki su baro, wallahi in banda darajar mahaifinku da dukkaninku sai na baku mamaki ni ba shashashan namiji bane da zaku dinga wasa" "da hankalinsa, sabida haka ko wacce ta fita ta bar min gidana zaman ya isa haka, kuma ku sani sai na" "sanar da Ya sheik abunda ke faruwa."" Yana gama maganarsa ya shige ya barsu a gurin Zainab na wani" "irin kuka na nadama tabi bayansa. Zubewa tayi k'asan kafafunsa tana kuka hade da bashi hakuri, Abbah" "ya dinga jin tamkar yayi ta boll da ita gurin, hakuri ya bawa zuciyarsa ya buga mata tsawa tare da fadin""Kar'beta ki bata nono muguwa kawai."" Zainab jiki na rawa ta kar'bi yarinyar a hannunsa ta fito da nono tasa mata a baki.........Girgiza kafafaunsa yake yana tunanin irin hukuncin da zai dauka akanta, ba zai saketa ba amma sai ta gane kuranta harshi zata yiwa wasa da hankali lallai sai ya wulakantata dan baya iya had'a kowa da 'ya'yansa.....Zainab kuka take tana masa magajiya gami da kokarin wanke kanta yaki sauraranta data isheshi ma cewa yay ta rufe masa baki ko ranta yay mummunan 'baci! Gum tayi da" bakinta ta cigaba da shayar da 'yarta nono............. *Littafin na kudi ne. !* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar biyan kudin littafin ga yanda abin yake. Vip group #600 normal group #300 account.... 0542382124...Binta umar gtbank. Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 85*******'Bangaransu aunty Balaraba kuwa hankali a mugun tashe suka had'a kayansu suka bar gidan cikin nadama gami da dana sanin abinda sukayi dan sunyi masifar tsorata da yanayin 'bacin ran da suka ga maigidan a ciki tabbas daba dan darajar mahaifinsu ba to da babu shakka sun san sai ya dauki mataki a kansu kamar yanda ya fad'a musu fargabarsu daya kada ya sami mahaifinsu ya fada masa abunda ke faruwa babu shakka idan mahaifinsu yaji wannan al'amarin to sai sun fuskacin bacin rai mai tsanani. Abbah da babbar murya ya gargadin Zainab gami da kafa mata dokoki akan 'Yarsa duk da yasan rai da rayuwa na Allah ne haka kuma cuta da lafiya shima na Allah amma dan ya tsoratar da ita yasa yace mutukar wani abu ya samu 'yarsa tofa ba zai kyaleta ba sai ya dauki mataki a kanta tunda ya gane inda ta dosa wato yarinyar bata itace a gabanta ba kishin jahilci ne yake damunta to kome za tayi taje tayi akan kishinta amma kada ta kuskura ta sake yi masa yawo da hankali ko kuma ta dauki ciwon karya ta d'orawa 'yarsa wannan itace damarta ta karshe idan ta sake ta kuskura ta sake maimaita masa abu makamancin haka to zasuje gaban mahaifinta ya sheda masa abubuwan da faruwa. Sosai take kuka ta kuma raina kanta da wayonta bata ta'ba tsammani al'amarin zaiyi zafi hakaba hakuri take bashi ya'ki sauraranta sai da ya 'kare mata tanadi tukkuna yayi ficewarsa daga dakin ya barta cikin nadama mara amfani. Rai a bace ya isa gidan Najaatu a maimakon ya samu sassauci sai ya tarar da wani 'bacin ran dan kicin - kicin ya sameta tunda ta gaishe shi ta tambayi jikin Ummi bata sake masa magana ba fitowa ma falo tayi ta kyaleshi a dakin shi kadai Takaicin sa ya sake nunnkuwa a gaskiya al'amarin mata yana da wuyar sha'ani tabbas lusarin namiji ba zai iya had'a mata biyu ko uku ba. Wanka yayi ya kintsa jikinsa ya fito falo ya sameta a zaune tana wasa da d'anta tana murmushi kamar "yayi mata magana sai ya rabu da ita, gurin cin abinci ya nufa, a tunaninsa zata zo ta had'a masa abin kari, sai yaga ta kara gyara zamanta, girgiza kansa yay da kansa ya hada tea ya zuba soyayyar doya da kwai a plate a nutse ya gama karyawa ya miqe daga gurun, inda take ya nufa ya tsaya a kanta tare da tsira mata" idonsa. "Kasa d'ago kanta tayi ta kalleshi tana dai ganin Inuwarsa tsaye a kanta, yatsun hannuwanta ta shiga" wasa dasu kwallah na kokarin zubowa daga idonta tana kokarin mayar da ita. "Gyaran murya yay ya kira sunanta""Najaatu."" A hankali ta kalleshi tare da amsawa ciki ciki ta mayar da" "kanta kasa, Yace.""Gaisawa kawai mukayi da juna babu wata mu'amular arziki koda akwai wani dake damunki ne.""?" "Girgiza kanta tayi tace""Babu abinda ke damuna."" Yace.""Karya kike ai ba haka fuskarki take ba tunda na" shigo gidan nan na lura da canzawarki ko dan na kwana gidan Zainab ne kike fushi! kada ki manta fa na nemi alfarmarki kuma lalura ta wuce komai. "Tace""Haba dai saboda ka kwana a gidanka gurin iyalinka sai naji haushi nifa na baka damar haka wallahi" babu komai yau ma kaje can kayi kwanciyarka sai yafi maka akan a kira ka da tsakar dare ace kazo.. Ya dinga kallonta yana nazarin maganarta dik maganganun da take fad'a tana fad'arsu ne iyakacin "bakinta amma ba har zuciyarta ba. ""Wannan maganar da kike fada kina fadarta ne iyakacin baki ba" har zuciyarki ba na kuma fahimci cewar al'amarin beyi miki dadi ba kiyi hakuri kinji ko Ummi ta samu lafiya insha Allah yau tare dake zan kwana. "Shuru tayi tana dauke kanta, Ya kalli agogo hannunsa ya mayar da hankalinsa kanta da fadin""Zanje" "kasuwa tunda na fahimci kamar bakya bukatata a gidan Ba tare da damuwa ba tace""To Allah ya kiyaye" "hanya."" Ya amsa tare da kama hanyar fita, bayansa tabi da kallo tana jin tausayinsa da haushinsa duk wani abun da Zainab takeyi a ganinta duk shine yake bata dama ita kuwa duk tausayinsa da take ba zata yarda ya dinga daukar kwananta yana kaiwa wata ba, da dai da gaske ne yarinyar bata da lafiya sai" ta iya hakura amma ko shakka ba tayi Zainab ta shirya mata ma'karkashiya ne...... Abbah cikin rashin walwala ya isa kasuwa gabad'aya rashin walwalar Najaatu ta sanyayyar masa da jiki "ya dinga jin shigar zazzabi zazzabi a jikinsa, sai da ya kira wayarta sau biyar kafin a tashi daga kasuwar. Abbah Abbas gudun tsegumi da surutai irin na Yaya Ramlatu yasa bai shedawa" "mahaifiyarsa abinda zainab da yan uwanta sukayi ba, lokacin dai da ya isa gidan Hajian ke sheda masa cewar basu dade da dawowa daga gidan nasa ba sunje sun duba yarinyar sun sameta taji sauki sosai..............Godiya yayi dan jin cewa sunje duba yarinyar sannan yayi mata sallama ya nufi can" babban gidan nasa. "Gurin Zainab ya fara shiga domin ya tabbar da cewa ta dauki maganarsa da muhimanci ko kuwa, a" "zaune ya sameta a falo da yarinyar a hannunta, yaci kunu sosai kamar bai ta'ba dariya ba, koda ta gaisheshi kin amsawa yayi ya kar'bi yarinyar ya dubata sosai kafin yace.""Ina fata dai kin bata magani."" Da sauri tace""Eh na bata. anjima zan kara bata na dare."" Shuru yay na minti biyu kafin ya miqa mata" yarinyar ya kama hanyar fita ba tare da ya sake yi mata magana ba. "A sanayaye ta kira sunansa ya juyo tare da fadin""Menene kuma.""? Dan darajar Allah kayi hakuri ka yafe" "min wallahi bazan 'kara ba nima na gane nayi wauta da ganganci kishi ya rufe min ido ina nema na kashe 'yata."" Tsaki yaja mai kar'fin gaske yasa kai ya fice daga falon ta rushe da kuka tare da rungume 'yarta" hakika wannan fuskar gizagon da yake mata na masifar bata tsoro gashi kullum sonsa da kaunarsa kara karuwa yake a zuciyarta.. Ya jima a gurin Halisa suna hira da ita da yaransa sosai ya samu nutsuwa ganin yaransa na cikin walwala "da farin ciki yasa shima yaji duk k'uncin da yake ciki ya dauke ya zauna yana ta saurarar shirmen su yana tambayarsu yanayin karatunsu, gefe guda kuma yana fargabar tunkarar Najaatu dan tsoron shiga gidanta yake saboda ya fahimci acikin fushi take Halisa ta fito daga daki ta sameshi beda niyyar tafiya" "tace""Abbahn mufida baka duba lokaci ne tara saura fa."" Yay saurin kallon agogon hannusa yace""Kinga wa'inda suka tsayar dani nan kin san fa ni sune sanyin idanuna na gane a gurinsu kawai zan iya samun" nutsuwa da farin ciki. Wannan maganar yasa ta gane cewar akwai abinda ke faruwa tsakaninsa da Najaatu lallai babu shakka "Zainab ta samu galaba a kansu, shuru tayi masa domin itakam bata da abin cewa a cikin al'amarin, guri ta samu ta zauna tana kallonsa, sai da ya gaji da kansa ya miqe tare da daukan wayoyinsa dake kan center teble ya kalleta da fadin"" Zan tafi."" Tace""A gaishe da Najaatu."" Mussadiq ya rike hannunsa da fadin""Abbah muje tare."" Yace."" Akwai skull ka bari sai ranar da babu makaranta zan daukeka na kaika."" Su saddiqa suka ce Abbah harda mu ko."" Murmushi yay yace""To Allah ya kaimu asabar din."" Sai suka shiga Murna dan jin cewar zasu je suga Najaatun su, ya kama hanya da niyyar tafiya suka dinga bashi" sakon gaisuwarsu zuwa gareta............ Najaatu tsaf ta gyara gidanta tayi abinci har kala uku sannan ta shirya jikinta cikin atampa 'yar ingila mai "ruwan ganye atampar tayi mata kyau kuma d'inkin ya dace da jikinta fetted gwon ne da zif a gaba taji dadin zif din domin dama tana tunanin yanda zata shayar da danta nono, tattare jelolin kitson kanta tayi ta daure da ribbon ta daura dan kwalin atamfar akanta (ture kaga tsiya) tayi d'aurin dankwalin yay mata masifar kyau sosai ta fito falo ta zauna, zuciyarta sai sa'ke-sa'ke! takeyi ganin tara har ta gota yasa ta zauna taci abincinta ta k'oshi sannan koma falon ta kunna tashar tv Sky movies ta kama suna wani film mai suna Aganipath tsohon film ne na amita ta zauna tana kallonta tana lura da yaronta dake" gefanta a kwance yana wasa. Lokacin daya shigo gidan kallon da take ya dauke mata hankali motsin sa taji amma ba taji sanda ya "shigo ba, a nutse ta dago kanta ta kalli bakin kofar falon, lokacin ya juya domin rufe kofar koda ya juyo hada ido sukayi yaji gabadaya kuzarinsa ya k'are bata ta'ba kwalliyar data burgeshi irin ta yau ba daurin dankwalinta da yanayin fuskarta daya gani shi ya fahimta dashi cewar akwai tsiya kenan dan fuskarta har yanzu babu sasauci. Barka da zuwa tayi masa ya amsa yana kallonta tare da kallon tv dan ganin" wane film take kallo daya dauke mata hankali. Kusan minti biyu yana tsaye a gurun kafin ya nufi bedroom jikinsa duk a mace ya tsani ya ganta cikin "rashin walwala, ya zauna yay tunani da nazari ya gane akan duk abinda takewa fushi! wannan dalilin yasa ya d'aura d'amarar faranta mata rai , tabbas a tsakanin jiya da shekaran jiya Zainab ta shiga hakkinsu dan sai suna daf da biyan bukatarsu take katse musu hanzari yau kuwa duk zai fanshe bashin da ya tara........Har ya kimtsa jikinsa ya fito falon tana zaune a inda take dan ko tunanin binsa dakin ba" "tayi ba, itama yau akwai abinda ta k'udurta a zuciyarta." "Zama yay kusa da ita yana nani'karta! ta dan gyara zamanta gabanta na fad'uwa, hannunsa yasa ya" "zagaye 'kugunta ya d'ora kansa a kafadarta a hankali yace.""Amarya me zan samu ne.""? Cikin basarwa ta zame kafadarta tace""Akwai abinci nayi maka har kala uku sai wanda kake so Ya juyo da fuskarta suna" "fuskantar juna, yanayin kallon da yake mata yasa tsigar jikinta mikewa, kauda kanta tayi tana dan gyara" "zamanta, hannunsa yasa ya tuge daurin dankwalinta ya ajiye gefe da fad'in ""Tunda na shigo naga" "wannan daurin dankwalin nasan akwai sauran rigima ashe baki huce ba nifa dana kwana da Zainab ba wani abune ya shiga tsakanina da ita ba.""" "Cike da mamaki take kallonsa tace"" Nima ai bance kayi wani abu da ita ba dama ai nasan zaka kula da" "baby Ummi ne yau ma kuma nace kaje ka kwana dasu wallahi ban damu ba.""" "yana hargitsa mata jiki yace."" Baby Ummi ta samu sauki yau babu inda zanje insha Allah muna tare har" "gari ya waye."" Humm! kawai tace ta dauki dankwalinta zata daura, kar'bewa yay yace kiyi zamanki a haka inason wannan kitson yayi kyau."" Murmushi tayi ta dauke kanta," "Gefan kumatunta ya sumbata yace.""Muje ki bani abincinki mai sadi da gamsarwa! Ba tayi musu ba ta" miqe shima ya miqe da sauri ya rike hannunta suka nufi gurin cin abincin Tsaf ta hada masa abincin "ta tura a gabansa yana lumshe mata ido yace tare zamu ci ko'' Girgiza kanta tayi tace""Ni Tuntuni naci abinci."" Girgiza kansa yayi ya gyara plate din abincin tare da bisimillah ya fara ci a nutse, tana kallonsa ta gefan ido sai kallonta yake kamar me? koda wasa taki kallonsa ballantana ta sakar masa fuska, sai da ya kammala tukkuna suka nufi falo, nan ma ya dinga janta da hira wai dole sai ta bashi labarin film din da take kallo, ba ta'ki ba tiryan tiryan ta shiga bashi labarin film din yana kallonta sha'awarta na kara tsananta a tare dashi Da kyar ya bari goma da rabi tayi musu a falo yace ta tashi suje su kwanta, ta" "dauki d'anta ta bi bayansa," "Sai da ta gyarawa Daddy shimfida tukkuna ta shiga toilet ta sake sabon wanka, ta fito ta shirya jikinta" "cikin kayan bacci duk akan idonsa, tun kafin ta k'araso bed din kamshin turaranta ya rud'ashi tana zama ya kashe bedlamp janyo ta yay ya wani qamqameta yana sansana sassan jikinta, hannayensa duk biyun yasa ya kama Brest dinta yana murzawa had'e da lasar wuyanta yana kokarin kwantar da ita ta dakatar dashi da fadin.....""Nifa ba zan yarda a tayar min da hankali da karshe a tafi a barni da wahala ba wannan dalilin yasa nace kayi zamanka gurin jinyyar baby Ummi tunda na fad'a maka gaskiyar magana" kace k'arya nake...... *Littafin na kudi ne. * Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar biyan kudin book din ga yanda abun yake...Vip group #600 normal #300...account... 0542382124...Binta umar gtbabk. Idan katin waya zaki tura sai kiyi min mgn da wannan number ta WhatsApp *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* *BA HARAM BANE!* ****86 Jin abinda take fad'a yasa ya miqe zaune yana kokarin ri'keta tana matsawa tare da sake jadadda "masa maganarta ta farko, itafa ba zata yarda ya tayar mata da sha'awa ba zainab ta kirasa ya tafi ya barta da wahala, jikinsa ne ya shiga 'bari sai ya shiga yi mata kalamai cikin rarrashi gami da tausasa murya yace.""Nagane duk abinda kike so ki fahimtar dani sannan Halisa ma ta dad'a wayar min da kai" "akan al'amarin tunda na baki hakuri ai sai ki hakura kada kice zaki kauracewa bukatata.""" Shuru tayi masa tana jinsa yana ta rarrashinta had'e da kokarin so ya dauke mata hankali dan sai "shashshafa jikinta yake yana sumbatar wuyanta, duk sakon sa yana ratsa ta hakan besa ta sakar masa jikinta ba ta dinga turje turje tana kukan shagwaba, al'amarin daya kara rikita shi! sai kawai ya shiga rawar murya kamar wanda zai fashe da kuka ya dinga rarrashinta da kalamai na mussaman wanda bai ta'ba amfani dasu ba gurun wata mace harda cewa idan babu ita rayuwarsa bata da amfani shima yasan yayi mata ba daidai ba dan haka tayi hakuri kada ta hanashi biyan bukatarsa, Najaatu ganin yanda duk ya tashi hankalinsa yasa ta sassauta masa ta bari ya cigaba da yamutsa ta amma ta gagara mayar masa da" "martani kamar jiya, sandare masa tayi a gadon shi yake kid'ansa da rawarsa." Da dai ya gaji ya kama hannunta yana kokarin sanyawa a cikin wandonsa ta dinga fizge hannunta tana "dun'kuleshi, Abbah kamar zautacce haka ya zama ya dinga rawar jiki zufa ba keto masa, Najaatu ta'ki yi masa wassanin soyayya shiyasa gabad'aya hankalinsa ya tashi Wani irin salo na tashin hankali ya" "shiga yi mata wanda ya gigita ta dinga fitar da wani irin numfashi tana cizar lips d'inta, abinda tayi ta gardamar ri'kewa shi ta kama ta dinga wasa dashi da hannunta, Abbah ya sa'ke matseta a jikinsa suka" cigaba da wassanin irin na ma'aurata. "To a wannan daran amarya da ango sun gwangwaje sun kula da junansu sosai suka biyawa kansu bukata," "da asubah ma basu hakura ba sai da suka sake wata mu'amular basu suka samu kansu ba sai bayan takwas na safe, a tare sukayi wanka sai wassanin soyayya suke. Abbah ya mayar da kanshi yaro sai biye" mata yake tana tsokanarsa dan ita tayi masa wanka ta shiryasa tsaf suka fito falo. "Kicin ta nufa domun samar musu da abunda zasu karya, ya bita kicin din wai zai taimaka mata tana sane" "ta bashi yankan al'basa aikuwa yana fara yankawa yajin albasar yasa ya ajiye wukar babu shiri ya fita daga kicin din yana mutsika idonsa, Najaatu ta dinga kyalkyala masa dariya." "Ya jima yana wasa da takwaransa (Daddy) kafin ya ajiyeshi ya dauki wayarsa ya kunna, number Halisa ya" "kira suka gaisa a mutunce ya tambayeta kwanan yara tace""Lafiya lau sun tafi makaranta."" Zainab ya kira" "a dakile ya amsa gaisuwarta yace""Ya jikin Ummi."" Da sauri tace da sauki gata tana bacci."" Okey sai na" "shigo."" Abinda yace kenan ya kashe wayarsa saboda ya lura kamar da magana a bakinta shi kuma ba zai saurareta ba." Abbah a yinin ranar sai da ya kusanci Najaatu sau uku ko gajiya ba yayi itakam daurewa kawai take amma har tafiyarta ta sanja duk gwiwowinta sunyi sanyi dan goho yake sawa tayi masa yay ta bugunta kamar ba zai bari gabadaya salon be mata ba kawai tana kyaleshi ne dan yafi bukatar hakan Da zai "tafi kuka tasa kan lallai ya kawo mata Saddiqa ta taya ta kwana, yace akwai makaranta kuma zaki bawa direban su wahala tunda hanya ta baud'e. Najaatu da 'kyar ta hakura ta barshi ya tafi amma taso" zuwan Saddiqa kodan ta d'ebe mata kewa. Abbah koda ya kwana a gurin Zainab bata sauya zani ba dan falo ya fito ya raba dare yana hira da "Najaatu a waya....Har ta dinga mamakin al'amarin ganin kamar hakan be dace ba yasa tace masa bacci takeji zata kwanta, To jin haka yasa yay mata sallama ya kashe wayarsa, ya gyara kwanciyarsa kan doguwar kujera bargo yaja ya rufe kafafunsa. Zainab sai da taci kuka mai isarta sannan ta fito falon ta" "sameshi, lokacin har bacci ya soma daukarsa, ta tsuguna gabansa tana kuka." Bude idonsa yay tare da tashi zaune. """Menene.""? Yafada yana harararta, hannunsa ta riqe murya na rawa tace"" Dan Allah kayi hakuri kazo" "muje daki ka kwanta nayi maka lefi na baka hakuri Allah ma ana masa laifi ya yafe dan Allah kaima ka yafe min.""" "Sassauta fuskarsa yayi yace.""Na yafe miki kije ki kwanta zan shigo yanzu."" Jiki a sanyaye ta miqe, ya bi" "bayanta da kallo a lokacin da take kokarin shiga dakin, tausayi ta bashi ya fahimci tayi nadama sosai akan abinda tayi." Komawa yay ya kwanta dan baya jin zai bita dakin amma kuma zuciyarsa bata k'ullacinta dan yana mata uziri da yarinta da kuma rashin samun nagartattun 'yan uwa. Abbah haka ya gama kwana biyunsa a gurin Zainab babu wata mu'amular arziki data shiga tsakaninsu sai gaisuwa amma kuma ya daina hantararta gami da daure mata fuska fuskarsa a sake yake amsa mata gaisuwarta... Koda ya koma gurin Halisa sosai yay mamakin irin tar'bar daya samu Halisa ta gyara jikinta tamkar wata amarya ta kar'beshi hannu bibbiyu ta biya mishi bukatarsa ta kowane fanni. Najaatu tunda ya bar gidanta take gyara jikinta da magunguna irin wanda Hajia ta bashi kawo mata "dana gurin Aunty Hafsa, ita da kanta kafin zuwan ranar girkinta sai da tayi data sani dan kullum da" bukata take kwana take tashi pant kuwa ta sanja sau biyar a rana ta rasa waye ya kawo hajia magaji mai kyau haka. "A ranar daya dawo gidanta kasa hakuri sukayi dare ya shiga sosai ana sallar isha'i suka kulle kofa, ikon" Allah kamar wasu mayen k'arfe haka suka manne junansu suna abu daya basu samu kansu ba sai bayan sha biyu sukayi wanka sannan suka zauna domin cin abinci. ***** "Alhamdullhi jikin Salim yayi sauki sosai dan har ana shirye shiryen sallamarsa, ranar asabar Salimat ita da" "Naburago sukaje asibitin domin dubashi da kuma fad'a masa irin mugun abinda sukayi masa...Yanzu idan kuga Naburago sai ya baku tausayi rigar sanyawa bashi da ita duk komai nasa ya kare a gurin cha-cah! sai da yaga bashi da komai sannan ya hakura a lokacin ne kuma nadama gami da dana sani suka shiga jikinsa tabbas daya dauki shawarar mahaifiyarsa da duk haka bata faru ba, yana ganin da ya bude gurin chajin waya da ya dinga samun kwabo da dari amma yanzu baya aikin komai sai buge buge da kyar ma suke samun abinda zasu sa a baki.......Salimat ma ta lalace duk ta rame tayi ba'kikirin dan dama mai take shafawa na kara haske to babu kudin siya sannan alhazawan dake bibbiyarta sun daina yanzu komai ya cakude musu mahaifiyarsu tace hakki ne yake bibbiyarsu saboda haka su shirya suje su nemi gafarar wanda suka zalinta, a bakin yaran unguwa sukaji rashin lafiyar Salim din Naburago ya tambayi asibitin da" yake aka basu kwatance kai tsaye adaidata sahu suka shiga domin zuwa duboshi "Salim cikin sanyin murya yace""Na yafe miku abunda kukayi min amma nima wannan kudi ba halak dina" bane na tsohon ubangidana ne dana zalinta saboda haka gurinsa zakuje ku nemi afuwa. "Nabarugo yace""Aikuwa insha Allah zaije har kasuwa ya sameshi domin ya nemi gafararsa" "D'aya daga cikin yaran sa ne ya shigo yana fada masa wani naso ya ganshi, yace ya shigo dashi, Naburugo" "zubewa yay gabansa yana zubar da hawaye. Abbah ya nuna masa gurin zama tare da fadin""Ya zauna ya" daina kuka ya fada masa abinda ke faruwa "Naburago ya share fuska da hankici ya shiga fada masa abubuwan da suka faru, Abbah ya dinga" "mamakin al'amarin kafin ya kalleshi a nutse yace.""Babu komai na yafe maka insha Allah magana ta wuce Allah ya kiyaye gaba." "Naburago godiya yayi masa sosai ya miqe da niyyar tafiya, Yace.""Yanzu wace Sanaa kake.""? Naburago" "yace.""Bani da sanaa Alhaji sai buge buge nake."" Yace."" Gobe kazo kasuwa zan sama maka gurbin zama sai ka cigaba da taimakawa kanka da mahaifiyarka .""" "Naburogo ya rasa wace irin godiya zaiyi masa, Abbah yace.""Daina gode min ka godewa Allah domin" "shine ya nufe ni dana taimaka maka Allah yasa ka zama alkairi a tare dani."" Naburago ya daga hannu sama yana godewa Allah tare da adduar Allah ya daga darajar wanda ya taimakeshi Tun daga wannan" rana Naburago ya zama dan kasuwa. Allah kenan babu yanda baya shirya al'amuransa (Babu laifi idan mutum yayi maka sharri kayi masa alkairi kafi shi a gurin Allah) *BAYAN SATI BIYU* Ya kasance yau saura kwanaki biyu su tafi kasa mai tsarki kamar yanda ya fad'a mata duk wani shirye "shirye ya gama ya kuma shedawa matayensa, Halisa dai bata nuna wata damuwa ba, Zainab ce dai ya rasa inda ta dosa, kuka takeyi mai wai itama tana so yaje da ita, yace ta bari da azimi sai suje gabad'ayansu, K'in yarda tayi ta dinga kawo masa hujjojinta na cewar ai itama daya aureta be je da itaba dan haka idan umara zashi to kawai yayi tafiyarsa shi kad'ai ba sai yaje da kowa ba. Gajiya yay ya" kyaleta dan baya so ya fad'a mata maganar da zata sake hargitsa ta dan ya lura yarinyar nada masifar kishin tsiya. Ana ya gobe zasu tafi Najaatu taje tayi sallama iyayenta suka saka mata albarka tare da fatan zuwa da dawowa lafiya Hajia da Alhaji ma adduar da sukayi kenan Yaya Ramlatu ta dauki Daddy ta goya shi a bayanta dama yaron ya saba da ita shiyasa baiyi wani kuka ba da zata tafi ma tayi tai ta d'aukeshi ya'ki! "Hajia tace"" Koda kin tafi ba zai damu ba tunda ya saba damu kuma yana cin abincinsa ai babu abunda zai" "sameshi har kuje ku dawo."". Wannan maganar ta hajia yasa hankalinta ya kwanta dan dama tana ta" tunanin yanda za'ayi ta tafi ta bar yaron sai kuma gashi yayi mata bazata. Kamar jira ake su tafi Halisa ta kama ciwo zazzabi da mura kwana biyu data gaza gane abinda ke "damunta sai kawai ta tafi asibiti Dr Sa'adatu ta dubata tsaf ta fito da kyakkyawan result ciki na sati uku. Halisa ta dinga mamaki da ikon Allah, Ashe dai tana da rabon wata haihuwar wallahi ita har ta fitar" da rai addua ta shiga yi kan Allah ya bar mata cikin kada ya zube Ta koma gida cike da murna da farin ciki amma bata tunanin zata fad'awa maigidan sai cikin yayi kwari tukkuna dan saboda bata so yasa rai yazo ya zube. Abinda bata sani ba kuwa shine tuni Dr Sa'adatu ta kirashi a waya ta sheda masa. "Abbah ya kasa 'boye farin cikinsa Ya shedawa Najaatu samuwar cikin Halisan, murna ta dingayi da fad'in" "Ya kirata ya waya ya fad'a mata cewar ya samu labari tunda boye masa takeyi, Yace.""Kyaleta ai zamu koma ne sai naji hujjarta na 'boye min kyautar da Allah yayi min""" "Najaatu na dariya tace""Watakila ko kunya takeji."" Yace ""Wace irin kunya kuma? Halisa ba yarinya ba" "zataji kunyar fad'a min tana da ciki akwai manufarta na 'boyewa.""" "Tace""To Ubangiji Allah ya sauketa lafiya."" Ya amsa da amin 'kasa-'kasa yace""Kema tashi muje na sa miki" "na 'yan tagwaye dan na lura kece zaki iya d'aukarsu saboda jarumtarki.""" Dariya take tana kallonsa ya 'kankance idonsa had'e da kai hannunsa kan le'bunanta yana shafawa "yace.""Da gaske nake wallahi duk cikin matana ba wai ina kushe kokarinsu ba har Halisan kin fita juriya da kokarin daukar lalurata."" Dan murmushi tayi tana masa wani sihirtaccan kallo tace""Bana so kana fasa min kai kana sawa kaina yana girma."" Yasa dariya da fad'in ""Shikkenan tunda bakya so na yaba bajintarki sai nayi shuru da bakina."" Kasa 'kasa tace""Ai baka iya shuru ka dinga sambatu kenan jiya ma har kuka" "sai da naji kana yi."" Cike da mamaki" "Ya bud'e baki yana kallonta.Ta fashe da dariya tana nuna shi da hannu, fuska ya 'bata yace.""Ke nifa duk" "yanayin da nake ciki bana shashancin nan sharri kawai kikayi min."" Dariya ta dinga kyalkyala masa tace""Habawa ai duk abinda kake yi ina jinka sai dai kawai na kalleka."" Murmushi yay yana girgiza kansa yace""To naji ina sambatu amma bana kuka saboda haka abar maganar."" Ta gyara fuskarta tare da fad'in" """To shikkenan an bar maganar amma tunda kace baka kuka yau sai nasa kayi.""" "Yace""Haka kika ce dai."" Hannunsa ta ri'ke tana masa kallon k'asan ido tace ""Tashi muje to."" Mi'kewa yay" kamar ra'kumi da akala yabi bayanta. *Lol Bazance komai ba ku 'kiyasta abinda zai faru * "*Nono Hallita ne akwai matan da suke dashi har yaso yayi musu yawa, akwai kuma wa'inda suke dashi" "daidai misali, sannan akwai wa'inda zaku ga nasu cibir cibir su kansu baya cika musu hannu! To dan Allah duk wacce take da irin wannan hallitar ta nutsu kada ta tayar da hankalinta akan haukan shaye shayen maganin da dole sai sun girma wallahi zaki bawa kanki wahala dan ko sun girma kika haihu yaro na tsotsa sai yamutse idan kinyi yaye ya dawo kamar silifas shaye shayen maganin karin nono beda amfani mutukar bana hausa bane kiyi hattara kada garin neman gira ki rasa ido, nononki ba zai tashi lalacewa" ba sai kin haihu kinyi yaye sannan zakisha mamaki!* *Masu tambaya ta meye maganin girman nono na hausa ga wannan a saukake. Ki samu 'ya'yan hulba kina had'iyar bakwai da safe bakwai da yamma. Sannan kina dama garin hulbar da madara kina sha sau "biyu a rana, insha Allahu ba nonowanki kawai ne zasu girma ba har sharf din'ki zai sake bud'ewa sannan zakiyi ki'ba ki murmure hulba tana magani sosai......." *MADADI* ******87 Rayuwar aure mai tsafta suke gudanarwa a k'asar saudia sannan kuma kusan kullum suna "harami suna kad'aita kansu ga Allah anan suke yinu sai daf da magariba suke komawa masaukinsu, cikin satikan da sukayi a 'kasar ita dashi sunyi wani freesh kana ganinsu kaga ma'aurantar dake mutukar kaunar junansu sosai suke kula da junansu tare da rokon Allah ya dawwamar musu da zaman lafiya a" zamantakewar auransu. Abbah yayi wa iyalinsa tsaraba sosai mussaman Zainab da kullum cikin yi masa 'korafi take a rana sai ta "kira wayarsa sau uku tana tambayarsa yaushe zai dawo kasuwa suka shiga domun siye siyen daba'a rasa ba, Najaatu ganin kamar yafi d'aukarwa Zainab abu yasa taji rashin dadi a zuciyarta tace""Ita" "aunty Halisan ba mutum bace kenan.""? yana duba wata abaya yace."" saboda me kika fadi haka.""? Tabe" "baki tayi tace""Naga Zainab kakewa siyayya ita kadai."" shuru yay na minti biyu yace."" A gabanki fa take damuna da kiran waya akan sautun da ta bani itama Halisan wanda take bukata na siya mata." Shuru tayi masa tayi gaba tana dube dube ta lura kamar tsoron Zainab din yake dan watarana idan ta kira wayarsa fakar idonta yake yaje ya la'be a wani gurun ya jima yana waya sai ya shigo ya dinga wani muzurai. Tana kallonsa sai da ya daukar mata dogwayen riguna manya guda biyar ga kayan kwalliya da takalma hade da fashion masu kyau da tsada. Sai bayan ya gama yace mata wai ta dubawa su Saddiqa kayan da "suka dace, sharesa tayi ta cigaba da duba abunda take bukata , gefan gold ta nufa ta tsaya tana dubasu gasu nan reras a cikin glass wannan yana wane wannan, wani abu ta latsa gurin ya bude! Wasu guda biyu tagani masu iri d'aya set ne a cikin akwatinsu wato sar'ka da d'ankunne sai zobe guda biyu acikin ko wane akwati, ita da Halisa ta daukarwa duk da ta duba kudin sar'kar ta gani hakan be dameta ba, sai ya siya musu tunda ita Zainab nada ita......sosai tayiwa su Saddiqa siyayyar data dace aka had'a kayan guri guda kafin ayi total Abbah ba tare da damuwar komai ba ya biya kudin da'aka cajeshi, yaran dake gurin" suka sa musu kayan a mota. "Sai bayan sunci abinci Najaatu ta firfito da kayan tana dubawa, so take ta fitarwa da kowa nashi kada azo" "ana bacin rai, nan yaga set din sar'kar gold guda biyu, yace.""Wannan keda waye.""?" "Kai tsaye tace""Nida aunty Halisa."" Yay jim yana kallonta kafin yace.""Ita Zainab d'in fa.""" "Kanta a kasa tace""Ni dai ba 'yar aikenta bace ballanatana ta bani sautu."" Rai a 'bace! Yace.""Wannan" "wace iriyar magana kike? okey kina so ki fad'a min magana kenan lefi ne dan Zainab ta kira ni a waya tace ga abinda take so na siya mata.""?" "Tace""A'a ba laifi bane ai bance komai ba ka tambaye ni sar'ka ne nace tawa ce data aunty Halisa" "maganar ka da Zainab bata dame ni.""" "A zafafe! Yace."" Toke a ganinki hakan shine daidai inace ku duka matana ne mai zai sanya ki dinga" "kokarin had'e kai da wata kina kokarin ware wata idan so kike ki kawo zaman lafiya da daidaito a tsakaninku me yasa baki daukar muku sar'kar ku uku ba.""?" "Tace"" Kayi hakuri dan Allah naga kamar kaji zafi yanzu ma zaka iya komawa ka siyo mata ai da akwai" "irinta, ni dai babu abinda ya dameni da ita tayi sabgarta nayi tawa.""" "Takaici yasa kawai ya zuba mata ido yana kallonta, tana ta had'awa kowa kayansa, yace.""Ina na daddy.""" "Ba tare da ta kalleshi ba tace""Ai bakayi maganarsa su Saddiqa kawai kace."" Yaji kamar ya kwada mata mari saboda bala'in haushin data bashi, yace.""Wai ke dan Allah meke damunki yanzu har sai nace ki" "dauk'arwar Daddy abu zaki dauka wato kina so ki bambamata shi da abinda na haifa ko.""" "Kuka tasa tace""Wai to kai me yasa bakayi wannan tunanin ba sai da muka dawo gida kada fa ka manta" "su Saddiqar ma daka haifa ni kasa na d'aukar musu abinda suke bukata, gabad'aya kana can b'angaran Zainab saboda kana jin tsoron b'acin ranta.""" "Wannan kukan da take da maganganunta yasa ya fahimci cewar kishi ne ke damunta, mamaki yake da" "lamarin mata wato dai shi yanzu shi dik abinda zaiyi a cikin zargi yake, bega abun kishi a cikin abinda yayi ba......shuru yayi mata be sake magana ba ya dauki wayarsa yana dubawa, Ita kuma Tana gama had'a kayan ta tashi ta bar gurin Wanka taje tayi tasa kayan bacci tayi kwanciyarta tana jin wani" mugun kishin Zainab a cikin ranta. "Cikin rashin kuzari ya shigo dakin, Wayarsa ya ajiye gefan drawar ya shiga ya watsa ruwa,. Zainab ta" "kira wayar dama ta saba kiransa duk dare suyi hira, Dauka tayi ta duba da taga itace sai ta kashe wayar, Zainab ta sake kiran waya, Najaatu ta dauka tare da sallama, Zainab taji haushin hakan amma ta daure tace""Ina Abban Mufida.""? ""Me zakiyi masa.""? maganar ce ta su'buce mata bata shirya ba. Zainab tace""" "Ikon Allah nida mijina kike tambayata me zanyi masa.""? Najaatu tsaki taja tace""Yau ban bashi izinin d'aga wayarki ba malama sai kiyi hakuri insha Allah gobe i yanzu mun dawo sai ki zuba ruwa a 'kasa kisha."" Kashe wayar tayi tana jin wani irin zafi a kirjinta. Zainab a fusace ta sake kiran wayar akace mata a" "kashe take, tsabar bakin ciki da 'bakin kishi yasa ta zube a gurin tana zubar da hawaye amma Najaatu ta" takaiceta. hannu tasa ta dafe kanta kawai ta dinga zirarar da hawayen takaici Najaatu kuwa bargo taja ta lullube jikinta tana lumshe ido yau dai ko banza ta huce fushinta akan irin abubuwan da Zainab keyi mata. Turare kawai ya shafa a jikinsa ko jallabiya besa ba ya kwanta kusa da ita daga shi sai gajeran wando....Takure jikinta tayi guri guda tana dan janye jikinta..... hannuwansa yasa "ya janyota jikinsa ya matseta sosai tare da sumbatar gefan fuskarta, ajiyar zuciya ta sauke 'kamshin turaransa na hargitsa ta." Jin yana yawo da hannayesa a jikinta yasa tayi gaggawar sanya hannuwanta duk biyun ta rufe breast "dinta bata so ya ta'ba mata yasa shaawarta ta tashi, yau Zainab ta janyo masa. Ganin abinda takeyi ne" "yasa ya dora hannunsa kan nata yana kokarin cirewa tana sake rufewa tare da kokarin yin ruf da ciki 'Karfi yasa ya fincike hannayenta dake rufe da breast d'inta, 'kasa-'kasa yace.""Meye amfanin" "abinda kikeyi yanzu? kuma meye amfaninsu idan baki barni nayi wasa dasu ba."" Kuka ta shiga yi tana" "tureshi, Kawai ya yasa mata karfi ya danneta ya cire rigar jikinta, breast din ya shiga luguda yana murza" nipples d'in! sai kawai ta shiga yin wata iriyar sheshsheka tana rintse idonta tare da cizan lips d'inta. Ya riga ya gama gane lagonta shiyasa duk turjiyar da take masa daga yayi mata wannan salon take saduda yanzu ma shakaf tayi ta daina abinda take na rashin yarda tura masa breast d'in ma take a bakinsa tana shashshafa ilahirin jikinsa. "Bangaran Zainab kuwa da kyar ta iya bacci tana idar da sallar asuba ta kunna wayarta, number shi ta" nema lokaci suna airport jirginsu zai tashi bema kunna wayar ba yana so su tashi sai ya cire sim card din yasa na 'kasarsa. Zainab sai da ta kusa kuka jin wayar a kashe shin kodai da gaske Najaatu take ita ta hanashi ya dauki wayarta! Tayi zaune a gurin tana sa'kawa da kwancewa ta rasa yanda zata 'bullowa al'amarin. "Tunkafin su sauka ya kira wayar Dan Azimi yace masa yazo da mota ya daukesu, kai tsaye kofar na'isa" yace masa ya wuce dasu Abbah Abbas sai da ya gaisa da iyayensa tukkuna ya nufi gurin iyalinsa "Najaatu kuwa cewa tayi ba zata koma gidanta ba sai ta huta, shuru yay mata a lokacin da take maganar yasan kawai tana neman rigima dashi ne, bangaranta kuwa tana ganin kota koma gidanta ita kad'ai zata kwana yasa ta fad'i haka in yaso ranar da girki zai dawo hannunta sai ta koma. wannan dalilin yasa" "ta saki jikinta a tare dasu Hajia, Daddy na ma'kale a hannun Yaya Ramlatu sosai tayi mamakin wayon da yayi yayi ki'ba tamkar wanda ke tare da uwarsa, koda ta kar'beshi tana kokarin sa masa nono a bakinsa" "'kin kar'ba yayi, Hajia tace""Ai ba zai kar'ba ya riga ya yaye kansa kema kin huta tunda yana cin abinci.""" "Cikin farin ciki tace""Wallahi Hajia sosai nayi mamakin girman da yaron nan yayi sati uku kacal amma ya" "manta da nono."" Yaya Ramlatu tace""Abinci yake ci sosai shiyasa ya yaye kansa bayan tafiyarku ya d'anyi rigima amma kwana biyu ya bari ya manta dake ya kama abinci..Najaatu dariya tasa tana girgiza kai" To kafin ta shiga gidan Baba Malam duk sai da ta fitarwa da kowa tsarabarsa hajia da Ramlatu sunji "dadin ganin yanda Najaatun ta karramasu sai kace wacce taje aikin hajji ta kawo musu hijabai da mayafai masu kyau sai wani takalmi mai kyau data siyawa Hajia, takalmin ya birge hajia sosai tayi ta shi mata" albarka. Iyayenta ma tayi musu nasu tsarabar daidai gwargwado Baba malam daya ga abin yayi yawa ya shiga yi mata fad'a akan me zata sa mijinta kashe kudi idan ta kawo musa carbi da dadduma ma ya isa.....Murmushi kwai tayi saboda tasan mahaifin nata da gudun abin magana Baba malam sam bashi da kwad'ayi da son abun duniya shiyasa kullum yake zaune lafiya....... Sanin da tayi cewar idan tace zata kwana a gidansu Hajia ba zata ji dadi ba yasa tana idar da sallar ishai "tayiwa mahaifiyarta sallama domin komawa gidan Alhajin, da zata tafi Baba Talatu taba sa'kon gaisuwa zuwa ga Hajia." 'Bangaran Abbah Abbas kuwa yana isa gidansa a maimakon ya nufi gurin uwargida kai tsaye gurin Zainab "ya nufa dan ta kirasa a waya ya kai sau bakwai gabad'aya hankalinsa ya karkata kanta jin abinda tace masa wai kada yaci abinci a ko'ina akwai tanadin da tayi masa, Namiji kenan kamar wanda ya shekara be ganta ba ya dinga gaggawar zuwa yaga tanadin me zai samu, mugun marmarinta yake dan dama" tunda tayi ar'ba'in bai kusanceta ba shiyasa yake jin d'okinta gami da son kasantuwa da ita........... *Zainab ga maza nan a gabanki!!!!!* *BAHARAM BANE!!!* *******88 Zainab na zaune a falo tayi gayu sosai tana sanye da jan legos les wanda yaji uban stons kafafunta da hannayenta sunyi shar shar da lalle (kunshi) ja da baki sannan anyi mata kitso k'ananu irin "na bare bari, fuskarta tasha make up har da gashin ido le'bunta jajur da janbaki gayu tayi sosai duk na tar'bar maigidan nata." Abbah ganin irin uban kyawun da Zainab din tayi yasa duk ya wani susuce ya dinga kallonta yana "murmushi, Zainab farin ciki duk ya isheta dan ganin kwaliyarta ta samu shiga ta jere masa gabansa da kayan abinci nau'i nau'i, iyayi kawai take masa tana wani fari da idonta, Abbah abinci yaci sosai suna hira kamar babu wata matsala data ta'ba shiga tsakaninsu a baya. Bayan ya kammala cin abincin ya" "dauki Ummi yana mata wasa Zainab tazo ta shige jikinsa tana shafa fuskarsa tace""Habibi jiya da daddare na kira wayarka kamar yanda na saba kawai Najaatu ta dauka ta farfad'a min maganar da ranta yake so harda cewa wai duk abinda kakeyi da izininta kakeyi saboda haka yau bata baka izinin daukar waya ta ba. Al'amarin sai ya bani mamaki saboda ni dai nasan mijina jajurtaccan namiji ne babu wata mace da" "zata iya juyashi a gida da waje, sannan kuma ni dai banga laifi ba dan na kira ka a waya a matsayinka na" "mijina ai ina da hakkin a kanka to ita kuma sai naga ta dauki abin da wata manufa.""" Abbah sanja fuska yayi ranshi ya 'baci jin abinda zainab ke fad'a masa ashe akwai wata mace da zata iya "bashi umarni mutukar ba uwar data haifeshi ba, lallai Najaatu ta rainashi, shin wai ina ruwanta da abinda yake tsakaninsa da matarsa ne ? ya lura duk wata fitina daga gurinta take tasowa tunda gashi a gaban idonsa ta dauki sar'ka guda biyu ta kuma fada masa ita da Halisa wannan na nuna masa cewar zata kawo" masa rashin zaman lafiya a gidansa. "Yace"" Kiyi hakuri ki bar maganar kinji ko amma inaso na sheda miki cewar ni wata mace bata isa tace ga" abinda zanyi ba nafi karfin gidana gabad'ayanku a karkashina kuke babu wacce tafi wata a cikinku sai wacce tafi kyautata min Najaatu bata isa ta hanani na kula dake ba. "Zainab tayi murmushin samun nasara tare dayin wani irin fari da ido tace""Nagode Habibina dama" nasan kawai ta fad'i hakane dan ta tunzura min zuciya muzo muyi abinda be dace ba ni kam yanxu zaman lafiya nake so muyi da junanmu kai ma sai kafi samun nutsuwa mutukar iyalanka kansu a had'e yake. "Da sauri yace.""Yawwa ashe kin gane shiyasa kullum nake cewa daku ku zauna lafiya da juna dan wannan" "kishi da rikicin da kuke ba zai barni na samu nutsuwar da nake bukata ba."" tace""Nidai insha Allahu ta bangarena ba zaka sake samun wata matsala ba."" Cike da jin dadi yace.""To nagode sosai kayan ki na mota sai kisa yara su dauko miki." "Rungumeshi tayi tana murna da farin ciki tace ""Habibi saura mota dan Allah ka siya min."" Yace.""Kada ki" "damu zan siya muku keda Najaatu insha Allah."" Jin ya ambaci sunan Najaatu yasa ta rage walwalar da take, tace""To mungode sosai Allah y kara budi Zainab ri'ke wuta tayi da kyar ta barshi ya tafi" gurin Halisa . Cikin rashin walwala ya samu Halisa a zaune a falo ita da yaran duk sunyi ado da kwalliya sunata zaman "jiransa yana can gurin Zainab ta ri'keshi sama da awa biyu, shi kansa sai da yaji nauyin hada ido da Halisa saboda ya lura ranta a bace yake beyi tsammanin sun san ya shigo gidan ba shiyasa ya shantake a gurin Zainab Yaransa suka rungumeshi suna murna gami da yi masa sannu da zuwa, Cike da farin ciki ya" "rike hannun Mussadiq ya zauna kusa da Halisan tare da fad'in ""Mussadiq ina fatan na sameku lafiya.""? Gabayansu suka amsa da lafiya lau Abbah."" Yace.""To Alhamdullhi. Idonsa ya d'ora kan Halisa da taci" kunu kamar bata ta'ba dariya ba. "Ya kalli yaran a nutse yace.""Kuje dakinku kafin nasa a kawo muku abinda nazo muku dashi."" Da sauri" "suka miqe suka bar falon A nutse Yace.""Ranki ya dad'e ina fata na sameku lafiya.""" "Halisa ta ta'be baki tace""Lafiya lau gashinan idonka ya nuna maka ai."" Yace.""To masha Allah haka nake" "so dama nima ai ban jima da shigowa ba wallahi sa. Katseshi tayi da sauri tace""Abban mufida kada" kace min komai dan Allah! Ka shigo gidan nan tun misalin uku baka shigo gurina ba sai yanzu dubi agogo biyar da rabi kana can gurin 'yar gwal wallahi kada ka zama daya daga cikin mazajen da basa adalci a cikin gidajensu. "'Bata rai yay yace."" Shikkenan kuma ba zan zauna naji matsalarta ba sai nayi laifi na gama da dakinta" nazo gurinki kina nema ki 'bata min rai shin wai ya kuke so nayi ne? kowa akayi abu sai yace ba'ayi masa daidai ba. "Itama a fusace! tace""Aa ni ban ce kada ka zauna da matarka ba, amma ai bai cancanta ka share gindi ka" "zauna sama da awa biyu ba, ka barmu nida yara muna ta zaman jiranka kome ka shigo dashi gidan ka" bari kazo kaga lafiyar yaranka in yaso daga baya bukatarka ta biyo baya ni dama nasan baka sani a lissafin mata tunda ka gama morata kuma ba wata cikakkiyar lafiya ce dani ba kafi kowa sanin hakan. "Jikinsa yay sanyi yace""To naji nayi laifi ayi hakuri dan Allah kada ki kara cewa bana saki a sahun mata" wannan maganar sam bata dace ki fad'eta ba kin dai san kafin na nunawa ko wace mace so ke na fara nunawa kuma har yanzu kina da matsayi a zuciya saboda haka ki daina fad'in wannan magana bana so. Shuru tayi tare da kauda kanta. "Yace""Na samu labarin cikin dake jikinki dik da kina 'boye min kada na sani shin ko zaki iya fad'a min" "dalilinki.""" "Halisa ta dinga kallonsa cike da mamaki! Girarasa ya daga mata yace""A ranar da kikaje asibiti aka" "tabbatar miki da cikin aranar nima na samu labarin samuwarsa. A sanyaye tace""Dr Sa'adatu ce ta fada" "maka kenan.""? Yace.""Kwarai kuwa ita ta fada min kuma nayi farin ciki sosai na kuma roki Allah ya bar mana shi ya kuma saukeki lafiya.""" "Halisa murya na rawa tace""Wallahi Abban Mufida ba'kin fada maka nayi ba inaso yayi kwari tukkuna sai" na fad'a maka nasanka da sa abu a rai kada sai bayan mun saka rai a samu matsala shiyasa nayi maka shuru.. "Tausayi ta bashi yace.""Ki kwantar da hankalinki insha Allahu zaki haife abunda ke cikin lafiya keda ki" "tsananta addua da rokon Allah."" Tace.""Inayi sosai wallahi."" Yace.""Nima zan sanya a yi miki saukar al'akurani mai girma."" rungumeshi tayi tana masa godiya tare da rokon Allah ya amshi addua" Duk da yaci cika cikinsa a gurin Zainab hakanan ya daurewa itama Halisan yaci nata duk dan a samu zaman lafiya sabida yasan babban abinda mace ta tsana shine tayi abinci a'ki ci dalili kenan da yasa ya daure yaci abincinta ya kuma zauna tare da ita har misalin goma na dare kafin yay mata sallama ya nufi gurin Zainab. "Zainab Ta shirya cikin kayan bacci ta jik'a jikinta da turaruka masu kamshi! duk inda ta gifta sai kamshi," maigidan nata kawai take jira ya shigo a fara harka dan itama a d'okance take da al'amarin tayi shaye shayen maganin matanta dik domin ta gamsar da bukatarsa. Abbah ya sake rikicewa jin uban kamshin da dakin Zainab keyi ya kalleta yana lasar baki kayan baccin sun fito mata da tsaraicinta yaji jijiyarsa ta harba! da sauri ya nufi toilet domin ya watsa ruwa. "Koda ya fito daga toilet din gajeran wando kawai yasa ya kashe fitila, Ya nufi bed din, Yana zama ya" kamota rungumeta yay a jikinsa yana matsa mazaunanta to anan labari ya sauya. Da asubah "da bacin rai ya tashi ya nufi toilet wanka yake cikin takaici yana kallon joystick d'insa, tun jiya ta'ki ta kwanta masa yanda yake so, duk da ya jima kan Zainab yana suburbudarta hakan besa ya samu cikakken satisfaction din da yake bukata ba, ya dai rage abin da ya rage, Zainab haihuwa daya kacal duk ta sakawarkwace gashi bata da wata cikakkiyar ni'imar da yake bukata shi ya dauka tayi masa tanadi mai kyau shiyasa yake ta zumudi ashe takaici zai kwasa. Koda ya dawo daga massalaci kasa hakuri yay ya" "sake haike mata nan ma ba ta canza zani ba, dan zainab da taji wuya kuka ta dinga yi masa yay hakuri ya kyaleta ita ta gaji, shi kuma a yanda mararsa ke k'ullewa baya tsammanin zai kyaleta, da kyar ya samu ya zubar da abinda ke mararsa, ya jima a kwance a kanta kafin ya sauka, toliet ya nufa yana addua Allah yasa jijiyar tasa ta risina, cikin ikon Allah kuwa tayi laushi! yay wanka a gurguje ya fito yana kimtsawa yana jan tsaki! a rayuwarsa ya tsani yaji mace a bushe ko a bud'e! Zainab ta bashi wahala jiya gashi duk wasu dabaru bata iya ba sai shirmen kwalliya da iyayi amma daga an hau kanta zata fara ihu ita ta gaji" shiyasa Najaatu take burgeshi ta kowane fanni "To Ita kanta Zainab din sai da ta fahimci wani abu daga gurinsa, jikinta yay sanyi data zauna tayi nazari" "da tunanin akan abinda yake b'acin rai! ita dai tasan daidai gwargwado tayi gyaran jiki kuma a jikinta tana jin ni'ima to me yanyo yake jin haushinta, jiki a mace ta miqe ta nufi bandaki ko kafin ta fito ma yay ficewarsa daga dakin, ta zauna gefan gado tare da zabga tagumi da tunanin neman mafita( Wasu lokotan maza sune suke sanyawa matansu na haukan shaye shayen maganin mata idan namiji ya kusanci matarsa yaji ba daidai ba na rana daya kacal sai ya hau fushi da muzurai! shi dai kullum idan ya hau yaji daidai! kuma wasu mazan fa babu ruwansu da kula da matayensu babu abinci mai kyau ballantana azo ga maganar kayan marmarin da zasu saukar da ni'ima, wasu matan na kokari sosai da kudinsu zasu siyi magani duk domin kaji dad'i ka gamsu amma saboda rashin adalci rana d'aya idan kaji sauyi sai ka sanja fuska, dan Allah a dinga adalci idan kana so kullum kaji matarka zam-zam to kana kawo mata kayan ciye ciye irin su *Nama 'kwai kayan marmarni kwakwa dabino mazarkwaila cikwi zuma da" dai sauransu Team din Najaatu nifa yau ina gurin Zainab dan wallahi ta bani tausayi * Gurin Halisa ya shiga suka gaisa ya jima tare da ita kafin ya nufi gidan Alhaji Lokacin da ya isa gidan "Hajia na sama dakin Alhaji Ya Ramlatu da Najaatu na zaune a falo suna hira, zama yay suka gaisa kafin ya haura sama gurin iyayen nasa. Lokacin daya sauko kasan Yaya Ramlatu kawai ya tambayeta ina" "Najaatu tace yanzu ta shiga d'aki...Kai tsaye dakin ya nufa, lokacin tana kokarin shiga wanka dan bata dauka zaizo gidan da wuri ba shiyasa ba tayi wanka ba, Ganinta daure da towel yasa hankalinsa ya tashi dama ba wata cikakkiyar gamsuwa ya samu a gurin Zainab, ido a lumshe yake kallonta, Tace"" Dama" "yanzu nake so na kiraka a waya akwai maganar da zamuyi.""" "Ya zauna gefan gado tare da fad'in ""To gani ai zonan ki fad'a min ko menene.""" "Tace""To bari nayi wanka na fito."" Shuru yay yana binta da ido har ta shiga toilet din Mikewa yay yaje" "yasa key a dakin, ya cire rigar shaddar jikinsa da wandon ya ajiye gefan. Da gajeran wando ta sameshi" "a kwance a gado.gabanta ya fadi da sauri tace""Abbah meye haka.""? Ya miqe zaune yana kallonta da jan ido yace.""Abinda idonki ya gane miki.""" "Girgiza kanta ta shigayi tare da fadin""Ta'bdijam! dan ita al'amarin ma mugun mamaki ya bata a gidansu" ya cire riga da wando tsaf ta gane abinda yake nufi Shan kunu tayi ta nufi gurin jakar kayanta tana "kokarin dauko riga da zani na atampa yazo gurin ya tsaya, ta dago a tsorace tana kallonsa, ""Dan Allah ka mayar da tufafinka jikinka beda ce ba, kai da ka baro gidanka be kamata ace kana da wata bukata ba." "Yace."" Ni dai ba surutu nace kiyi min ba kaya kuma ba zan mayar ba sai na samu gamsuwa. Tace.'' To wai" "ina aunty Halisa da Zainab din."" kai tsaye yace.""Suna nan kalau jiya nayi da Zainab yanzu kuma naki nake so.''" Taji kamar ta kwada masa mari saboda takaici wato baya bambamce mai girki da mara girki a duk "lokacin daya bukaci mace kawai ya afka mata, murya na rawa tace""To ai ba girki na bane sai ka bari girki ya zagayo kaina."" Towel din dake jikinta ya fizge yace""Bana bukatar wasting time ki bani abinda nake bukata domun tun jiya bana cikin hayyacina." A tsorace ta dinga kallonsa tana ja da baya yana kara kusantota tamkar wani zaki! sai huci yake! hawaye "ne suka soma zubo mata tasa hannuwanta tana kare kirjinta, daukarta yay ya kwantar da ita kan bed din ya danneta..........Ya saba idan ya hau kanta baya sauka sai ya kawo sau uku sannan , tayi ta kuka da magiya akan ya hakura idan ya kawo sau daya ya sauka saboda kada su hajia su fahimci wani abu amma ko a jikinsa bai sauka ba sai da yay release sau uku ya d'agata! Takaici yasa ta takure jikinta gu guda tana" kuka "Tsaf yay wanka ya fito yana jin annushuwa a cikin ransa, haba jamaa sai yanzu yaji daidai amma jiya" "Zainab haukane kawai bata sa yayi ba, yana daura agogonsa yace""Wace magana zamuyi."" Juya masa baya tayi ta kyaleshi yana ta magana, da ya gaji ya fita daga dakin ya kyaleta." Tun daga ranar take ci masa kunu ko zuwa yay bata sakar masa fuska shi kuwa ko ajikinsa al'amuransa yake yi kai tsaye kuma da bukata zata ciyoshi haka zai zo ya danneta babu abinda ya dameshi Ranar "da girki ya zagayo kanta ya sameta a daki yanda take shan kunu shima haka yasha, yace""To zaman ya isa haka tunda girki ya zagayo kanki anjima Dan Azimi ya kaiki gida." "Kai tsaye tace""Ai mun gama magana da Hajia zan tafi jos nayi sati biyu." Ya bude baki yana kallonta da fad'in.''Ashe baki da hankali Hajia ce ke auranki ko ni? da har zaku gama "magana ban sani ba."" Tace""Ranar naso na fada maka ka fita." "Yace.""To babu inda zakije gida kuma ki tafi kafin yamma dan wallahi nazo gidan nan da yamma na ganki" "sai na 'bata miki rai.""" Yana gama maganarsa yasa kai ya fita daga dakin Najaatu na kuka ta shedawa hajia yanda sukayi Hajia tace daina kuka ki koma gidanki kamar yanda ya bukata insha Allah zan zauna dashi akan zuwanki jos ai ya dace ka gaishe da mai gaisheka Wa'yannan mutanan sun cancani ayi musu komai Wannan maganar da hajia tayi yasa taji sassuaci a cikin zuciyarta tana cin abincin rana Dan Azimi ya dauketa a mota ya kaita gidanta bayan tayi sallama da iyayenta *BAYAN SATI BIYU* Tana zaune a falon gidanta taji sallama da sauri ta daga kai tana kallon kofar shigowa ido suka had'a da Munira wanda da badan tayi mata kyakkyawan sani ba ba zata ganeta ba saboda ramar da tayi Najaatu ta miqe da sauri tana kallonta hade da kiran sunanta! Munira tun kafin ta karaso falon "kuka ya subce mata, tana isowa ta dauki Daddy ta rungumeshi kam a kirjinta kan kujera ta zube ta dinga" rizgar kuka tana sake 'kam'kame Yaron a kirjinta......... *MADADI!* ******89 Najaatu zubawa Munira ido kawai tayi tana kallonta sai kuka takeyi ta kasa cewa komai gashi ta matse yaro a jikinta yana ta kuka gami da son zuwa gurin uwarsa ta ri'keshi tsam a jikinta taki sakinsa. Kawai sai taji itama zuciyarta ta karye hawaye suka shiga zubowa daga idonta. Sun jima cikin wannan "yanayi kafin Munira ta sassauta kukan da takeyi tasa hannu ta goge hawayen fuskarta ta d'ago fuskar Daddy ta tsira masa ido sai kawai wasu hawayen suka sake kwace mata. Najaatu a sanyaye tace""Haba" Munira wannan kukan da kikeyi ya isa haka dan Allah ki daina komai kikaga ya faru dama can rubutaccene daga Allah. "Munira murya na rawa tace""Najaatu dole nayi kuka domin shi kadai zanyi na samu sassaucin abinda" "zuciyata hakika nayi nadamar rayuwa nayi dana sanin abinda na aikata hakika na cutar dake gashi da yake baki da hakki Allah ya musanya miki da alkairi Najaatu rayuwata data iyayena ta zama abin tausayi da kyama kowa gudunmu yake dalili kenan da yasa muka tarkata kayanmu muka koma kauyen zaria da zama, yanzu haka acan muke rayuwarmu, Mommy itace ta bani umarnin zuwa na sameki domin neman afuwarki abisa abubuwan da suka faru a baya, kai tsaye gidan Alhaji na sauka Hajia tayi min kar'bar mutunci tasa aka kawo min abinci naci na koshi, Itace take sheda min haihuwar wannan yaron nayi mamaki sosai kuma alokacin naji sake jin tsoron Allah ya kama ni hakika Ubangiji babu yanda baya tsara lamarinsa tsorona Allah da Annabi yaron nan ya girma ya mallaki hankalin kansa ya samu labarin abunda ya faru a baya dole yayi mana kallon lalatattun iyaye marasa nagarta domin mun cutar da rayuwarsa tun kafin yazo duniya mun ruguza farin ciki gami jin dad'in rayuwarsa saboda son zuciyarmu wannan dalilin ne yasa ki kaga tunda na shigo nayi tozali dashi nake kuka saboda nasan mun riga" "munyiwa rayuwarsa illah.""" "Najaatu shuru tayi tana tunanin abubuwan da suka wuce, ta goge k'wallar dake kokarin zubowa daga" "idonta tace""Munira a lokotan baya na dauki abunda ya faru da rayuwata na d'ora a matsayin kece sanadi sai daga baya kuma nagane cewa bake kadai keda laifi ba har dani dan da nabi umarnin iyayena ban kuma bi son zuciyata ba to na tabbata haka ba zata faruwa ba, to dukkaninmu muna aikata abune a duhu domin bamu san abinda Allah ya lullu'be ba, hakika aurana da 'Dan uwanki kaddara ce da kuma tsananin rabo gashi nan a hannuki rabon Wannan yaron ne yasa duk abubuwan da suka faru a baya suka kasance saboda haka ki daina kuka da damuwa wallahi tuntuni na yafe miki kuma na tausayawa rayuwar da kuke ciki keda iyayenki ina rokon Ubangiji Allah ya sassauta muku. Munira a sanyaye ta amsa da" "ameen ameen Najaatu nagode sosai da karamcin ki kema inayi miki fatan alkairi a rayuwarki Allah kuma ya tabbatar da zaman lafiya a tsakaninki da mijinta.'' Najaatu ta amsa da ameen ameen nagode kwarai da adduarki."" Falon yay shuru na minti uku kafin tace""Ina Muktar ina fata kunyi aure.""? Munira tayi wani irin murmushi kai kana ganinsa kasan na takaici ne tace""Najaatu Muktar ya yaudare ni ko kuma nace na cuci kaina na amince masa yana mu'amulanta ta kamar matar auransa sai da yayi min ciki tukkuna yayi min korar kare tare dayi min gargadi da cewar naje na nemi uban d'ana sannan kuma idan na sake na sake zuwa nace cikina nasa ne sai ya d'aure ni, a takaice dai yanzu haka yaron dana haifa yana nan yay" wayo shekaransa daya da wata hud'u. "Najaatu ta dinga girgiza kanta cikin alhini da damuwa tace"" Munira kinga irin abinda nake fad'a miki ko?" Yanzu meye ribar abinda kuka aikata keda muktar ashe kenan ba Daddy ne abin tausayi ba tunda shi kowa yasan sai da aka shafa fatiha aka haifeshi wannan yaron da kika haifa shine abin tausayi idan ya tashi yasan hanyar da akabi aka samar dashi dole ya shiga halin damuwa da tashin hankali. "Munira na kuka tace"" Hakane maganarki Najaatu wallahi naso tun yaron na ciki ya mutu ko kuma na" "haifeshi babu rai, ke har fatan mutuwa nake wa kaina a lokacin dana nake da cikin amma duk hakan bata samu ba.""" """Ki daina wannan maganar Munira dan shi Ubangiji babu ruwansa saboda kune kuka sa'bawa dokokinsa" "ba yaro ba Allah na iya raya shi kodan ya nuna muku ishara daku da masu irin halin ku."" Amma yana da kyau ki sake neman Muktar din idan da hali ki kaishi koton musulunci.""" "Munira girgiza kai tayi tace""A'ina zanga Muktar? yau watansa uku da aure yana can legos tare matarsa" amma kowa yaga Ahmad yasan d'ansa ne saboda suna kama sosai. "Najaatu tace""Kin sanya masa suna mai ma'ana kuwa to Ubangiji Allah ya raya shi tafarkin addinin" "musulunci Allah kuma ya karkato da hankalin mahaifinsa kansa yazo ya dube shi da idon rahama."" A sanyaye munira ta amsa da ameen ya Allah Haka suka kasance har yamma suna hirar yaushe gamo" "gami da jajantawa junansu, Najaatu ganin biyar ta wuce yasa ta shiga kicin domin d'ora girki duk da ba itake da girki ba a ranar watarana idan yazo yakan ci abinci a gurinta kafin ya tafi Munira ta dinga" sha'awar gidan Najaatu tana ta 'kiyasta abubuwa da yawa a zuciyarta hakika Allah ya musanyawa k'awarta da nagartaccan miji irin wanda yake da wahalar samu a duniya tana rokon Allah ya bata kwatankacinsa. Najaatu wanka tayi ta kintsa jikinta tsaf ta fito falon ta zauna suna hira kafin lokacin sallar magariba "yayi.........Bayan sunyi sallar ishai sai suka ci abinci tare, bayan sun gama Najaatu tace yana da kyau tayi wanka ko taji dadin jikinta, wani bedroom ta bude mata tace ta shiga akwai komai na bukata a ciki, a cikin kayan sawarta ta daukar mata riga da zani na atamfa ta kai mata dakin ta ajiye mata kan gado, ta fito ta zauna kan kujera tana sa'ke sa'ke gaskiya bata kaunar zaman Munira a gidanta saboda hausawa nacewa ruwan da ya dake ka shine ruwa Tsoron wani abu takeyi gashi tana jin nauyin tace mata ta koma" gidan hajia ta kwana a can. "Tana can cikin tunanin mafita Munira ta fito cikin atamfar data ajiye mata, Najaatu saurin gyara" "fuskarta tayi tana kallonta har ta karaso kusa da ita ta zauna, a sanyaye tace""Najaatu da zan samu aikin aikatau dana zauna nayi na tara kudi kafin na tafi.""" "Gabanta ne ya fad'i jin abinda Munirar ke fad'a! Tace"" A gaskiya da kamar wuya ki sami aikatau anan" "area ki bari zan baki jari idan zaki tafi sai kije can ki kama sanaa har Allah ya fito miki da mijin aure. Munira tace""Nagode sosai Najaatu hakika ina alfaharin kasancewar ki a matsayin aminiyata Allah" "ya 'kara miki rufin asiri da wadata.""" A hankali ta amsa da amin gefe guda tana nazarin maganarta shin wai har kwana nawa za tayi mata a gida itafa Munira tsoro take bata bata bukatar zamanta a gidanta to amma yanda za tayi ta fad'a mata ne bata sani ba Hira sukeyi sama sama Munira na sake bata labarin irin wuyar da tasha a hannun "kanwar mamanta, ita dai jinta kawai take tana tunanin mafita." "Cikin wannan yanayi ya shigo gidan, Najaatu ta miqe da sauri tana masa barka da zuwa. Amsawa" "yayi ya tsaya yana kallon Munira da fad'in ""Bakuwa kikayi ne.""?" "Munira ta zube har kasa tana gaisheshi, Yace."" Wannan fuskar kamar na santa.""? Munira sunkuyar da" "kanta tayi tana murmushi, Ita kuwa Najaatu a cunkushe tace""Kawata ce Munira 'kanwar Marigayi."" Yayi" "jim yana kallonta kafin yace ""Tazo ganin Daddy kenan.""? "" Umm."" Tace ba tare data kalleshi ba babban burinta ya bar gurin dan ita ba taga amfanin tsayuwarsa a gurin ba." "Shi kuwa gyara tsayuwa yay ba tare da wata Manufa ba yace.""Munira ina mutanan gida ina fatan duk" "kuna nan lafiya."" Tace.""Kowa lafiya Abbah suna gaisheku da kyau."" Yace.""Muna amsawa ."" yana gama maganar ya wuce ciki, Najaatu ajiyar zuciya ta sauke minti biyu tabi bayansa, Yana zaune a gefan gado ta shiga dakin, zama tayi a nutse ta gaisheshi tare da tambayarsa yanayin kasuwa, yace komai alhamdullih....Shuru dakin yay kafin yace.""Naji dadin zuwan Munira ko babu komai sun nuna damuwarsu akan yaron dan dama abin yana damuna ganin daga b'angaransu babu wanda ya ta'ba zuwa" "da sunanan yazo ganin yaron amma zuwanta ya nuna mana cewar sun san da zaman yaro a hannuki.""" "Babu cikakkiyar walwala a tare da ita tace""Munira ba ganin yaro tazo ba hasalima bata san dashi ba sai" da hajia ta sheda mata ita dai kawai tazo neman gafara akan abubuwan da suka faru. "Yace.""Allah sarki ai sai ki yafe musu tunda sun gane kuskuransu ko babu komai kun had'u tunda ga" "Daddy nan a tsakaninku sai suci albarkacinsa. Shuru tayi tana kokarin mayar da kwallar idonta, Ya kalli" "agogon hannunsa tare da fadin""Yau me kika girka.""" """Abinci ne mai sauki dan zuwan Munira yasa ban shiga kicin da wuri ba...jollop din macaroni nayi.""" "Girgiza kansa yay yace.""Bana jin zan iya ci."" Ta kalleshi tare da son tayi masa tambayar da ta jima a cikin zuciyarta "" Wai don Allah me yasa baka son cin abincin su Halisa da girkina da banawa ba sai kazo kaci" abinci. "Yace."" Babu wani dalili kawai dai inajin dadin duk abinda zai fito daga gurinki sannan kuma suma ba" "abincinsu ne bana ci ba, ina ci daidai gwargwado amma dai duk kin fisu iya girki shine dalilin daya sa nake so naci naki."" girgiza kanta tayi tace""To yanzu da a guri guda muke haka zaka dinga yi kenan kasan" rigima za'ayi. "Yace.""Saboda me.'? kai tsaye tace""Saboda wannan dalilin ba kowace macace zata yarda ba dan Allah ka" "dinga kamanta adalci Abbah bana so ranar Lahira ka tashi da shanyayyan jiki.""" "Shuru yayi yana tunanin maganarta kafin yace."" Dan nazo gidanki kin bani abinci naci hakan ba zai sanya" "ranar lahira Allah ya tuhume ni ba, nasan akan abinda kike cewa nayi adalci sabida ina neman ki a lokotan da ba girkin ki ba shiyasa kike fadin cewa na dinga adalci to abincin ma na daina zuwa naci kamar yanda kika hanani kanki a lokacin da nake bukata.'' Mi'kewa yayi ya kama hanyar fita da fad'in sai da safe ina fatan babu matsala.'' Ta mike tana kallonsa sai wani Muzurai yake tace''Daga magana sai ka hasala bani na hanaka abinda kake magana akai ba wanda ya hallice kane yace kayi adalci a tsakanin" "matanka to me zai saka ka dinga d'aukar kwanan wannan kana kaiwa waccan.""!" "Hannu ya d'aga mata a murtuke yace.""Kinga maganar ta isa haka ko kinga nazo miki da wata bukata ne.""?" "Da sauri ta girgixa kai Yace.""To kada ki sake kawo min hadisai akan wannan maganar.Tace."" Dama ai bani na fara maganar ba kaine."" Tsaki yaja ya kama hanyar fita, ta bishi da kallon mamaki! itakam bata san me yasa zuciyarsa ke saurin hasala ba kwana biyu tunda ta hanashi biyan bukatarsa a ranar da ba girkinta ba yake mata magana sama sama. A nasa 'bangaran kuwa haushi da takaici ne yake damunsa" "dan saboda yasan Zainab ba iyawa za tayi dashi ba, ita kuma Halisa ba cikakkiyar lafiya ba sam be ma fiye matsa mata ba dama Najaatun ce gwanarsa ita kuma ta kasa ta tsare tace bata yarda da wannan tsarin ba, idan ya gama kwana biyunsa a gurinta to haka yake shiga mugun yanayi a tsakanin kwanaki hud'un da zaiyi dasu Halisa ya galabaita mutuka abinka da wanda ya saba da sex duk sai ya fice daga hayaccinsa aikuwa ranar daya dawo gurinta tana raina kanta da farkon dare yayi asubah yayi da safe" "kafin ya fita kasuwa ma sai yayi, sai kace wani ayu!" Koda ta fito falon gani tayi yana sallama da Munira cikin sakin fuska kamar bashi ba yasa kai ya fita daga "falon ba tare daya kalleta, danne damuwarta tayi ta zauna suka cigaba da hira da Munirar kafin dare ya shiga sukayi sallama kowa ya shiga daki domin kwanciya. Wanka tayi kamar koda yaushe ta shirya" "cikin shirin kwanciya, wayarta ta dauka tana dube dube gabadaya bata cikin nutsuwarta na farko zaman Munira a gidanta ya tsaya mata a rai na biyu kuma wannan matsalar da take fuskanta a gurin maigidan nata, tasan yasan gaskiya amma yake takewa yanzu meye laifinta dan ta tunasar dashi abinda ya dace," ashe shi 'kullatarta yayi a cikin zuciyarsa gaskiya al'amarin ya bata mamaki sosai Washe gari da safe da yazo take fad'a masa bukatarta naso ya bata kudi zata taimakawa da Munira idan zata tafi Kai "tsaye yace bashi dasu."" Ta saki bakinta tana kallonsa har ya gama abinda yake a dakin ya tafi Da" wannan takaicin ta yini dan har sai da Munirar taso ta fahimci wani abun na faruwa. Da daddare da "yazo bai bukaci cin abincinta ba ita tayi masa tayi tare da fad'a masa abinda yake so ta dafa Yace.""A" "'koshe yake da zai tafi ta dakatar dashi tare da fadin tana so tayi magana dashi, yace sai dai ta bari sai da safe dan yanzu sauri yake Koda ta fito falo samunsa tayi yana magana da Munira tana fad'a masa" "cewar gobe zata tafi da safe. Yace.""To kada ki tafi sai nazo."" Najaatu gabanta ya dinga bugawa ta tsirawa bayansa ido har ya fita daga falon, kasa zama a falon tayi ta shiga daki ta kwanta, to itama Munirar ganin matar gidan na cikin damuwa yasa ta kashe tv taje ta kwanta. Najaatu kasa hakuri tayi ta dauki" "wayarta ta kirasa, ya dauka sama sama take jin muryarsa.""" "Hawaye ta share tana kokarin aro dauriya tace""Da kace kada ta tafi sai ta jira ka me za kayi mata idan" "sonta kake sai ka fad'a min ni zan baka goyon baya.""" "Murmushi yayi dan ya bata haushi yace.""Ai ba raham bane dan nace ina sonta nace kada ta tafi sabida" "akwai sirri a tsakanina da ita."" Sai kawai ya kashe wayarsa yana murmushin jin dadi shi dai yana so yaga ana kishi a kansa, Halisa ta gama yanzu Zainab da Najaatu ne keyi aure sai ya cikashe hud'u idan ma zasu hakura su hakura Najaatu ta dinga jin kamar taje dakin Munirar ta tuhumeta abinda ke tsakaninta da" "mijinta sai dai ta daure ta dinga nanata kalmar innalilihi wa'ina ilaihi raji""un. Da kyar bacci ya dauketa. Da safe Munira kasa gane kanta tayi sai tasha jinin jikinta tayi sanyi ta dinga Allah Allah" maigidan ya shigo ya sallameta ta tafi dan ta lura zamanta a gidan na nema ya haifar da matsala. Cikin galleliyar shaddarsa (wagambari) ya shigo gidan yay kyau har ya gaji kana kallonsa zaka gane bai da "damuwa dan har wani 'kiba da haske ya 'kara matsalarsa kawai rashin samun abunda yake so ranakun kwanan Halisa da Zainab, kamshin turaransa ya cika falon Munira ta gaishe shi tana sunkuyar da kanta" "wani abu take rayawa a ranta, inama inama! sake dago fuskarta tayi ta kalleshi tay saurin sunkuyar da kanta kasa tabbas ruwa ba sa'an kwando bane. Yace.""Ina matar gidan take ta barki ke daya a" "falo.""tace""Tana ciki bata fito ba."" Kai tsaye dakinta ya nufa. Najaatu na sane tasa k'ananun kayan da" "suka matseta wando iya gwiwa da rigar da bata rufe mata cibiya ba, kayan sun mata kyau sosai kuma dole su rikita wanda akayi dominsa. Ganin irin shigar dake jikinta yasa ya tsaya daga bakin kofa" "sabida tsaro, kallonsa tayi tace""Ina kwana.""? Cikin basarwa ya amsa, yana wani kauda kansa, Yace ina" fata baku da wata matsala ko.''? "''Uhm."" tace tare da mi'kewa yay saurin dauke kansa xuwa tayi ta gifta shi, kofa ta bude ta fita ta barshi" a tsaye a dakin Gabadaya ji yay gwiwarsa tayi sanyi anya kuwa zai iya wannan ya'kin? daurewa yayi ya "fita falon nan ya same su suna magana, Ya kalleta da fad'in Abunda yasa Nace 'kawarki ta tsaya kada ta tafi sabida bukatarki da kika fad'a a kanta inaso naji abinda take bukata kafin na fita. Kamar tace masa" "kaida kake da sirri da ita kuma! sai ta share maganar tana dauke kai tace""Sana'a zata fara bata da jari shine nace ko zaka taimaka mata."" Da sauri yace.""Me zai hana muka taimakawa na waje ma ballantana na gida, insha Allah zan tura miki sai kuje tare idan kin cire ki bata, ya kalleta da fadin "" Munira Allah ya" "kiyaye hanya a gaishe da mutanan gida."" Munira tace""Zasuji insha Allah nagode sosai Abbah Allah ya" "raya zuria."" Ya amsa da amin hankalinsa a kan Najaatu dake ta faman dauke kanta har yanzu taki sakar" masa fuska. Shi kam jikinsa ne yayi sanyi sanin da yayi yau a gidanta yake fargabarsa kada dare yayi "labari yasha bambam dan ya lura a fusace take, sasauta murya yayi yace.""Ni na tafi kasuwa."" Tace""Allah ya bada sa'a."" .Yana kokarin bude kofar falon ya amsa da amin ya rabbi" Abbah dubu dari cif ya bawa Munira Najaatu ta cire mata kudinta ta bata tare da kara mata dubu goma "akai bayan sutturu da kayan kwalliyar data had'a mata, Hajia da baba talatu suka harhad'a mata kayayyaki masu yawa, Munira kasa daurewa tayi ta dinga kuka tana gode musu ashe dama Najaatu alkairi ce a garesu! Allah kenan, Dan Azimi ne ya dauketa a mota ita da kayan ta domun kaita can" kyauyen nasu. *BAYAN WATA UKU* Salim yaji sauki sosai sai dai kullum yana gida babu abunyi sai yamma tayi yake fita ya zauna a cikin "abokansa marasa sana'a! Mahaifinsa ya yanke shawarar siya masa adaidaita sahu ya fara ja domin zaman hakan bashi da amfani, koda Sakina ta sheda masa maganar farin ciki yayi domin shima zaman ya isheshi, yanzu yana jiran dawowar mahaifin nasa daga tafiya tunda yace idan ya dawo zasuje gurin siyar" da napep din tare. "Abbah Abbas a nutse ya kalli 'yar uwarsa yace.""Bana jin dadin ganin Salim a zaune a bakin titi babu babu" "abinyi kullum idan zan shigo unguwar nan sai na ganshi a zaune wannan dalilin yasa na yanke bud'e masa gurin gurin siyar da takalma anan bakin titin unguwar taku nasan ba za'a rasa shaguna ba, dan haka zan nemeshi akan maganar idan yaso sai ya fara bunkicen gurin zama." "Yaya Ramlatu fashewa tayi da kuka tace"" Hakika dan uwana Bani da abinda zance maka sai dai na roki" "Allah yasa ka gama da duniya lafiya nagode sosai da wannan karamcin naka, dama shekaran jiya yazo yana fada min cewar mahaifinsa yay masa alkawarin zai siya masa adaidata sahu to kuma sai gashi kazo da wannan maganar .""" "Yace.""Ai ba wani abu bane idan ya siya masa adaidata sahun zai iya hada kasuwanci biyu."" Hajia" "tace""Hakane kam kaima kayi zumunci Allah ya saka da alkairi."" Amsawa yay da amin amin kana yayi musu sallama ya tafi gurin iyalinshi Ya Ramlatu a waya ta kira Salim ta sheda masa maganar a ranar" Salim da kyar ya iya bacci sabida murna da farin ciki hakika bai ta'ba ganin mutum mai kyakkyawar zuciya irin Kawun sa ba....... *BA HARAM BANE!!* *****90 Cikin sati biyu kacal komai ya kammala Abbah yasa an zubawa Salim kaya a k'aton shagonsa "takalma na manya da yara maza da mata, Salim tsabar farin ciki har hawaye sai da ya zubar Mahaifinsa kuwa har kasuwa yaje gurun Abbah Abbas din ya nuna masa farin cikinsa dangane da alkairin da yayi masa ya dinga godiya kamar wanda aka bashi kyautar kujerar makka. Abbah Abbas dakatar dashi yayi" "yace masa dan yayiwa Salim abu bai kamata yazo yana masa godiya ba saboda a har yanzu a matsayin uba yake a gurinsa dan haka ya daina masa godiya akan abinda yayi."" Ayuba ya dinga jinjina nagartarsa tabbas a yanzu samun mutune masu yin abu domin Allah irinsa sai an tona babu shakka Alhaji Abbas" yana kokarin aikata aikin alkairi da tarin dukiyar da Allah ya bashi. *BAYAN WATA BIYU* "Al'amura na tafiya cikin tsari da kwanciyar hankali, a zamantakewar gidan Abbah an samu daidaito ta" "kowane bangare yana kokarin ganin ya sauke hakkin dake kansa, shiyasa suma matan suka samu nutsuwa tunda ko wacce yana yi mata abinda take bukata, sai suyi wata da watanni basu had'u da junansu ba mutukar ba wani taro akeyi a 'bangaran maigidan nasu ba, to nan ma idan sun had'u su ukun suna gaisawar mutunci suna kokarin danne kishi a tsakaninsu, wannan nutsuwar daya samu ne yasa hankalinsa ya kwanta harkokin kasuwancinsa suka cigaba da bun'kasa, arziki da wadata sai nunnkuwa suke sai dai godiyar Allah Cikin Halisa nada wata shida Najaatu ta harbu, to da yake cikin nata ba" "me laulayi bane yasa babu wanda ya san tana da ciki harshi maigidan shuru tayi masa bata fad'a masa ba, ta godewa Allah da yasa cikin ba mai wahala bane irin na Daddy, ashe jira yake ya k'ara kwari ya bayyana akanshi, kariris ta kwanta ciwo dan sabida rashin kwarin jikinta sai kiran Dr Saadatu yay a waya yace tazo" "gidan ta dubata," Dr Saadatu kallo daya tayi mata ta gane abinda ke faruwa amma sabida ta tabbatar yasa tayi mata gwaje "gwaje result ya fito tana murmushi ta fad'a masa cewar ciki ne da ita na wata uku, Abbah Abbas kasa" 'boye farin cikinsa yayi godiya yake mata kamar itace ta bashi kyautar cikin kyauta yayi mata ta mussaman kamar koda yaushe. "Najaatu ta dinga mamakin irin murnar da yake kamar wanda ba'a ta'ba yi masa haihuwa ba, a ranar yini" "yayi tare da ita ya'ki zuwa kasuwa, sai yamma ya fita. koda yaje gidan Alhaji kasa shuru yay sai da ya" fad'awa hajia itama ta dinga farin ciki tana addua Allah ya raba lafiya. kasancewar ranar ba girkinta "bane yasa ya roki alfarma gurun 'yar uwarsa akan taje ta zauna da ita, Yaya Ramlatu ta shirya kayanta" "tsaf ta tafi gidan, Najaatu taji dad'in zuwanta dama tana ta tunanin yanda za'ayi ta kwana ita kadai a" gidan. 'Bangaran Salim da Salimat kuwa sun sake daidaita kansu a karo na biyu yanzu tsarkakken aure suke so "suyi Salim yini yake a shagonsa na siyar da takalma da daddare kuma ya dauki a daidata sahun sa ya tafi aiki, cikin kankani lokaci ya had'a kudin aure! Mahaifinsa da d'an uwansa sune suka je har gidan su Salimat din domin nema masa a auranta a karo na biyu, Naburago da Kanin babansa su suka kar'bi kudin" auran da sadakin kana suka tsayar da ranar daurin aure wata biyu masu zuwa....... To duk abunda ke faruwa Zainab bata da labari Halisa ce kawai tasan Najaatu nada ciki itama bashi ne ya "fad'a mata ba a bakin Yaya Ramlatu taji a lokacin da tazo dubata, taji takaicin abunda yayi mata meye a ciki dan ya fada mata najaatu nada a ciki ita a yanzu daga Najaatun har Zainab din bata daukesu a matsayin kishiyoyinta ba a matsayin 'kannenta ta daukesu, koda ta nuna masa b'acin ranta hakuri ya bata yace mantawa yayi, be fada mata ba, A nasa bangaran kuwa yana ganin rashin fad'ar shi yafi alkairi a gurinsa dan zai iya zuwa ya fad'a musu su mayar da abin kishi mussaman Zainab da ko maganar Najaatu bata so yayi idan yana gurinta shiyasa yake takatsantsan da al'amarin ko wacce dan baya so su dinga daukarsa a matsayin mutum mara adalci, Halisa Addua tayi akan Allah duk ya rabasu lafiya da" abinda suke dauke dashi. *RANAR BIKIN SALIM* Zainab da Halisa tare suka tafi gidan bikin ko wacce tayi ado daidai misali mussaman Zainab sarkin "kwalliya komai na jikinta mai tsada ne ta shirya 'yarta cikin 'yan kanti masu kyau, Halisa cikin atamfa super ta shirya tayi amfani da gold d'inta irin na Najaatu to da yake hijabi tasa shine dalilin daya sa Zainab bata gani ba, gabad'ayasu harsu Saddiqa direba ya daukesu a mota gidan Alhaji ake taron bikin" kafin yamma suje suga dakin amarya. Lokacin da suka shiga Zainab sai da ta kusa fad'uwa ganin Najaatu a hakimce akan kujera tayi wani 'bul "'bul kana ganinta kaga mai yaron ciki fuskarta sai sheki take annuri yana sauka, tayi kyau har ta gaji tana sanye da Material pink color mai wani irin kyalli da duwatsu, tunda suka shiga falon Zainab ta kasa dauke idonta daga kanta, Uban gold din da taga ni a wuyanta shine yayi masifar tayar mata da hankali, tsabar hassada yasa taji hawaye na kokarin kufce mata, 'kasa tayi da kanta tana kokarin daidata nutsuwarta" kada jamaar dake gurin su gane halin da take ciki. Sai da ta daidata nutsuwarta tukkuna ta d'ago kanta tana ya'ke ta shiga gaishe da Hajia da jamaar dake gurin Najaatu janyo hannun Ummi tayi tana mata wasa yarinyar ta bata sha'awa sosai ganin yanda mamanta tayi mata gayu tana kaunar 'ya mace a rayuwarta. Zainab dik irin kulawar da Najaatu takeyi "akan 'yarta hakan be burgeta ba harararta ma takeyi a fakaice k'yashi da bakin ciki duk ya cika mata zuciyarta..............Halisa kuwa da yake tayi sabo da dangin mijin nasu tana cikinsu suna ta hira Hajiya Rakiya tace"" Yanzu kuma idan an gama wannan taron sai na haihuwarki dan banyi tunanin ma zaki zo" "taron bikin nan ba ganin yanda cikin ki ya tsufa.""" "Halisa tace"" Lallai kuwa ni kam ko na haihu babu taro sai dai ku bari idan k'anwata ta haihu sai kuyi ni na" girma da taron suna. "Hajia Rakiya tace""To ashe bake kadai ce mai cikin ba. Najaatu tayi saurin sunkuyar da kanta tana jin" "kunya, Hajia Rakiya dariya tasa ganin yanda Najaatu ke sunkuyar da kanta tace""Allah to ya rabaku lafiya.....Zainab gumi ne ya shiga tsatstsafo mata lallai ma! Najaatu nada ciki ita tana zaune tabdijam! hankalinta ne ya tashi taji gabadaya zaman gidan ya isheta, daurewa kawai tayi la'asar tayi ta kalli Halisa tace""Ni ina ganin tafiya zanyi tunda kinga ni zanyi girki.'' Halisa tace ba zaki tsaya muje muga dakin" amarya ba. "Girzgiza kai tayi tana gyarawa 'yarta takalmi tace""Watarana naje."" Najaatu ta ri'ke hannun Ummi da" "fad'in ""Zainab ki bani ita ta kwana biyu mana.""" "Girgiza kanta tayi babu kunya tace""Ba zan iya ba.""" "Gabadaya mutanan dake falon suka zuba mata ido da mamaki a tare dasu Ya Ramlatu tace""Kafin ki" "haifa ita ta haifa gashin nan ma wani cikin ne da ita kije ki rike 'yarki haba jamaa ni ban ta'ba ganin mara kawaici irin wannan yarinyar ba wallahi."" Zainab tayi kwal kwal da ido tana so tayi kuka, Ya Ramlatu ta dinga farfada mata magana, hajia Rakiya ganin abun na nema ya zama rigima yasa ta dakatar da Yaya" Ramlatu daga hayaniyar da take. Zainab sama ta hau tayiwa Hajia sallama ta sakko babu wanda ta kula a cikinsu taja hannun 'yarta suka fita. Abinka da taron mata tana fita kowa ya shiga fad'in albarkacin bakinsa a kanta. "Zainab sai da taci kukanta ta koshi tukkuna ta dauki waya ta kirasa, Abbah jin yanda take sheshshekar" "kuka yasa hankalinsa ya tashi yace.''Tayi shuru tayi masa bayanin abinda ke faruwa, 'ki tayi tace""Ita dai yazo gida bata da lafiya....Jin maganar rashin lafiyasa yasa ya bar abinda yake ya tafi gidan nasa" A falo ya sameta ta had'a kai da gwiwa abun duniya ya isheta Najaatu nada ciki Halisa nada ciki sannan "sun had'e mata kai sunsa gold iri daya ita bata dashi bayan nan kuma Yaya Ramlatu ta tsaneta taci mata mutunci tare da zagin iyayenta, wannan abubuwan sune suka dameta suka tsaya mata a wuya." Da kyar ya rarrasheta ta shiga shirya masa karya da gaskiya tana kuka take fada masa Yaya Ramlatu ta "tara Jama'a taci mata mutunci tare da zagin iyayenta akan wani dalili wanda bai taka kara ya karya ba, Abbah yaji ransa ya 'baci amma baiyi saurin yanke hukunci ba sai da yace ta fada masa dalili Tace""" "Saboda kawai na 'kar'bi Ummi a hannun Najaatu shikkenan sai cin mutunci ya biyo baya wai nayiwa Najaatu gorin haihuwa kafin na haifa ita ta haifa gashinan zata sake haihuwar wani gabad""ayansu haka suka dinga cin mutuncina akan rashin gaskiya. Yace""Kiyi hakuri zanji dalilin daya sa suka tozarki a" "gaban jamaa taro idan na Ramlatu ne ki daina zuwa tunda bakwa jituwa da juna ita kuma Najaatu data bada goyon bayan aciki mutuncinki zanji dalili! ni kike aure ba wani ba saboda haka taro kin daina zuwa tunda ba alkairi suke shukawa ba! Tace"" sannan kuma Naga gold aunty Halisa da Najaatu sun sa iri d'aya" "ni ina nawa.""" Gabansa ne ya fad'i! kai Zainab rigimammiya ce tabbas gold din nan ne da Najaatu ta siyo musu lokacin "da sukaje umara ta gani, domin ya wanke kansa daga zarginta yace""Najaatu ce ta daukar musu su biyu kema zan baki kudi kwatankwacin na gold din ki siya."" Tana kuka tace""Ni wallahi irin nasu nake so me yasa bakya ce ta d'aukar min ba kaga irin rashin adalcin naka ko wannan uban gold din" "ai bai zama lallai a samu irinsa anan ba."" Yace.""To shikkenan ki bari idan munje tare sai ki siya dama" "farkon azimi nake so na sake tafiya zamuje tare insha Allah."" Shuru tayi tana goge fuska yace""Ina fata dai babu wanda kikayi wa rashin kunya acikin mutanan dake gurin.""" """Babu wanda nayi wa magana ai ganin sun had'e min kai suna cin mutuncina yasa nacewa aunt Halisa" "zan dawo gida."" Yace.""Ita Halisan tana zaune ake zagin ki ba tayi magana ba.""?" """Eh ba tace komai ba har na fito daga gidan."" Abbah ya jima kansa a kasa yana nazarin al'amarin tabbas" idan yay binkice ya tabbatar da gaskiya lamari to babu shakka Halisa da Najaatu sai sun raina kansu wato har dasu za'a hadu a ciwa matarsa mutunci ya rasa me yasa tsakanin Yaya Ramlatu da Zainab basa shiri A ranar beje gidan ba saboda yasan cike yake da jamaa zamansa yay tare da Zainab din tana ta kalallameshi da kalamai sai 'kara rura wutar al'amarin take. Bayan ya dawo daga sallar ishai gurin "Halisa ya wuce yaga bata dawo ba, rai a bace ya kirata a waya lokacin suna gidan Salim suna kar'bar amarya tunda sune iyaye.'' Hayaniya yasa ta fita daga cikin Jamaa ko kafin tace komai taji yana magana a fusace! Tace""Yi hakuri Abban Mufida na rana d'aya dai ai ka d'aga mana k'afa yanzu haka ma muna gidan amarya nida Najaatu."" Yace.""Dole sai daku za'a kar'bi amaryar kinfi kowa sanin bana son kuyi dare a waje sabida haka dake da ita Najaatu ina son ganinku a gida dan tun la'asar na dawo naji kuma" "dukkanin irin rashin arzikin da kukayi.""" "Halisa na kokarin tayi magana ya katseta da fadin""Ina jiranku yanzu yanzu."" Kashe wayarsa yayi ya ajiye" "gefe ya cigaba da girgiza kafafunsa, Zainab duk wasu matakan kare kanta ta tanade su tana jiran suzo ayi wacce za'ayi." "Halisa Najaatu taja gefe ta fad'a mata abinda ke faruwa, dukkaninsu jikinsu yayi sanyi da kiran gaggawar" "da mijin nasu yake musu. Halisa na draving tace""Najaatu anya ba Zainab ce taje masa da wani sharrin" "ba."" ? Cikin rashin damuwa tace""Idan taje masa da sharri kanta zai koma insha Allahu mu dai babu abinda mukayi mata.""" "Halisa ta shiga girgiza kanta tare da fad'in ""Al'amarin Zainab sai gyaran Allah ni tun zamanta a gurin na" "fuskancin sanjawarta tunda lafiya lau muka zo to amma ganin gold din dake wuyanki da wuyana yasa ta sanja fuska nasan abinda ya tayar mata da hankali kenan.""Murmushi Najaatu tayi tace"" To ai sai taje tayi ta damuwa ita ciwo zai kama ba wani ba gold kuwa ni dake nake so muyi anko ita tayi nata ita kadai tunda bata da mutunci da kawaici wallahi ba kiji yanda raina ya 'baci ba data fito fili ta nuna ba zata bani" 'yarta ba.'' "Halisa tace""Ai sai kiyi hakuri ki kyale mata 'yarta kema Allah zai baki." "A harabar gidan suka sameshi zaune akan wata farar kujera, Halisa ta gyara parking Najaatu ta bude" mata kofar motar ta fito tana yatsine fuskarta dan zaman draving din nan da tayi ya janyo mata ciwon mara dama dai tanayi sama sama tun a gidan bikin daurewa kawai take mikewa yay ya nufi gurun "Zainab duk suka rufa masa baya,zama yay kan kujera Zainab tayi wanka ta sanja kwalliya ta zauna kusa dashi tare da d'ora kafa d'aya kan daya a haka suka shiga suka same su. dukkaninsu sai da wani abu ya" "ta'ba zuciyarsu amma suka dake suka zazzauna, falon ne ya dauki shuru na minti biyu kafin yayi gyaran mirya ya kallesu d'aya bayan d'aya yace""Halisa kece babba a cikinku inaso ki fad'a min abunda ya faru a gidan bikin Salim."" Halisa tace""Bangane na fada maka abinda ya faru ba okey tazo ta fad'a maka wata magana ne.""? Tsawa ya buga mata yace.""Kada ki mayar dani sakarai mana kin san komai kina nuna baki sani ba kome akayiwa Zainab ai kune kuka bada goyon baya saboda kunga kuna da fada a gidan jamaa sunfi sanin ku shine zaku ware ta ku had'u kuci mutuncinta akan wane dalili.""? Yakare maganar cikin" tsawa. "Najaatu a dake! tace""Wallahi Zainab kiji tsoron Allah yanzu me akayi miki da har zaki zo ki fad'a masa" "duk dan ki had'ashi da 'yar uwarsa.""! A fusace! Tace""Ke dallah malama kiyi mana shuru duk bake ce kika janyo komai ba da har zakice naji tsoron Allah kune dai zakuji tsoron Allah bani ba."" Halisa tace""Kawai" "saboda ta nuna kaunarta akan 'yarki sai ki mayar da abin sharri a gaskiya Zainab ki sanja hali wallahi.""" """Ba zan canza Hali ba sai dai ku su sanja hali ni ba munafuka bace shiyasa ai kuka ware ni saboda ban iya" "gulma da munafurci ba yanzu meye na ware ni kuka saka gold irin d'aya bayan ni kunsan bani dashi Ai wallahi Najaatu kece babbar munufaka."" Najaatu ta bud'e baki tana kallonta cike da mamaki tace""Ni kike" "kira munafuka.""" """To idan ba munafuka ba mecece da har zaki siyo muku gold iri daya banda ni.""" "Dariya tayi tace""Okey sai yanzu na gane abinda ke damunki ba'kin ciki da hassada kikeyi mana gold kuma" na siyo bakya cikin tsarina shiyasa bana so nayi irin d'aya dake banza mara hankali kaw. kafin ta karasa ya buga mata tsawa wai tayi shuru! Ta kalleshi cike da mamaki me yasa lokacin da zainab take magana "bece komai sai ita zai katsewa hanzari aikuwa sai ta fusata! ta cigaba da watsawa Zainab ba'ka'ken maganganu wanda yasa itama ta fusata! ta miqe tsaye ta fara mayar da martani! kafin kice kwabo gurin ya hargitse Najaatu da Zainab sai hayaniya suke Halisa dashi uban gayyar na hanasu amma kamar sake tunzura su suke....Halisa ta kalleshi rai a b'ace tace""Yanzu meye amfanin abunda kayi ashe dama taramu kayi domin muyi hayaniya kawai saboda Zainab tazo ta fad'a maka magana sai ka hau kai ka zauna babu binkice wallahi ka gyara zamantak. Katseta yayi cikin d'aukar chaji yace.""Fita ki bani guri ki koma" "gurin ki."" Halisa tsaki taja ta dauki jakarta tinkis tinkis ta kama hanyar fita ba zata iya da jarabar nan ba......Shi kuwa tsakaninsu ya shiga yana musu magana su bari dan gabadaya hankalinsa ya tashi da" yasan hayaniya zasuyi da bai tarasu a guri d'aya ba. Najaatu jakarta ta dauko ido jawur ta kama hanyar fita sai dai kafin ta karasa bakin kofar ta yanke jiki ta "fad'i! A take ta shiga yin wani irin hakki! tana rike kirjinta, bashi kadai ba har Zainab din sai da hankalinta ya tashi, a gigice ya rirriketa yana kokarin mikar da ita tsaye tana kokarin kwanciya, Zainab tazo ta tsaya gabanta na faduwa! Abbah fita yay da sauri ya fito da mota ya umarci maigadi ya bude gate, Najaatun ya hango ta fito daga gurin Zainab tana kokarin fita. Bayanta yabi da sauri yana kiran sunanta ta bude" "karamar kofa da sauri ta fita daga gidan, hanya ta fara bi hawaye na zubo mata wannan masifa ina zata iya da ita ace mutum ya kasa fin karfin gidansa. Halisa ce ta fito daga gurinta tana kiransa, ya" "tsaya yana kallonta dik ya zama kamar zautacce mata suna so su haukatar dashi, tana cizar lips dinta tace""Haihuwa zanyi fa ka fito da mota muje asibiti."" Sai ya rasa ina zai nufa gurin Najaatu ko gurin Halisa (Allah sarki ya bani tausayi ) Gurin Halisan ya nufa ya taimaka mata suka fito tare mota ya sata ya kira" Zainab a gurguje ta fito ta shiga motar suka nufi asibiti. Najaatu kuwa na fita ta samu adaidaita sahu gidan Alhaji ta nufa ranta a mutukar 'bace! amma koda taje bata shedawa kowa abinda ya faru ba kawai ta bar abun a cikin ranta. Karfe tara da rabi na dare Halisa ta haihu an samu 'ya mace katuwa tubarkallah babyn na kama da babanta sosai dama duk yawanci 'ya'yansa kama suke dashI Ummi ce kawai ke kama da mamanta. Dr "Sa'adatu itace ta tsaya tsai a kan Halisa har sai da tabbatar komai yay daidai tukkuna hankalinta ya kwanta baby da mamanta sunyi tsaf gwanin sha'awa, karamcin Dr Sa'adatu ya tsaya masa a rai matar na mutukar kaunarsa da iyalinsa yasan duk abinda takeyi yafi karfin irin kudin da yake bata, lokacin guda yaji yana tausayinta a cikin ransa yana son mace mai hankali wacce tasan abinda take tabbas Dr Sa'adatu" ta cancanta a sota. "Sha d'aya shaura na dare ya shiga gidan Alhaji shuru gidan lokacin duk sun kwanta, gurin hajia Rabi ya" "shiga Allah yasa ba tayi bacci ba jin sallama yasa ta fito da sauri, ganinsa a tsaye yasa gabanta ya fad'i Tace.""Allah yasa dai lafiya."" Yace.""Lafiya lau Halisa ce ta sauka ta hafi 'ya mace yanzu haka tana gida" lafiya lau ita da yarinyar. "Hajia Rabi ta fad'ad'a fuskarta da faraa tace""Ikon Allah d'azu fa muna tare da ita babu wata alamar" "haihuwa a tare da ita koda yake ai ikon Allah ya wuce wasa.' Yace.""Wallahi kuwa Allah ya kawo mata da sauki."" Tace""Haka ake so ai Allah ya raya."" Ameen ya Allah bari na shiga gurin hajia."" bayansa tabi tana fad'in ""Allah yasa ba tayi bacci ba dan tun dazu naji tana kukan kafafunta na ciwo. jin muryoyinsu" "yasa Yaya Ramlatu da Najaatu suka fito daga daki da sauri, Hajia Rabi ta kalli Ramlatu da fad'in "" Kunji halisa ta haihu yanzu yanzu an samu 'ya mace."" Dukkaninsu farin ciki ya nuna a fuskarsu Yaya Ramlatu ta kalli Dan uwan nata cike da farin ciki tace""Yanzu tana asibiti ko tana gida.""? Hankalinsa nakan Najaatu yace tana gida yanzu haka."" Ramlatu tace""To ai sai mu tafi tare da kai na zauna a gurinta."" Tausayi ta bashi jin abinda tace Ramlatu na tsaye a kansa da iyalinsa mussaman Najaatu da Halisa amma ya rasa me yasa take nuna kiyayyarta akan Zainab, Hajia Rabi na kokarin fita tace""Hajia dai yanzu tayi bacci kada a tasheta da safe sai na sanar dasu haihuwar ita da Alhaji."" Yace.""To Allah ya kaimu."" Najaatu bayan Yaya Ramlatu tabi ba tare data kulashi ba, dan har yanzu haushinsa takeji Yaya Ramlatu tace""Kema ai sai" kizo mu tafi tare ko.'' Shuru tayi tana nazari! da tayi rantsuwar ba zata 'kara shiga gidan ba saboda abunda ya faru amma dole ta karya rantsuwarta Halisa ta wuce komai a gurinta.......Mayafi ta yafa suka fito tare. Abbah ganinta "tare da Yaya Ramlatun yasa shi sauke ajiyar zuciya, ya kama hanyar fita suka bi bayansa." Sai bayan sun hau titi ya kalleta tana zaune kusa dashi fuskarta babu yabo babu fallasa dan farin cikin "haihuwar Halisa yasa ta danji sasaauci a cikin zuciyarta. Sassauta murya yay yace.""Yaran sunyi bacci" "ko.""? Umm sunyi bacci sai dai da safe Dan Azimi ya kawo su."" Yace.""To shikkenan."" babu wanda ya sake magana a cikinsu har suka isa gidan." "Yaya Ramlatu da Najaatu kai tsaye gurin Halisa suka nufa, ikon Allah suna shiga dakin suka tarar da" "Zainab zaune a gefan gado da baby a hannunta ita kuma Halisa lokacin tana toilet Zainab saurin sunkuyar da kanta tayi tana jin kunyar had'a ido da Ramlatu addua take Allah yasa Najaatu bata fad'a mata abinda ya faru ba. Ya Ramlatu zama tayi kan sofa tare da cewa bani 'yar."" Zainab da sauri ta" "miqa mata babyn tana gaisheta. amsawa tayi hankalinta nakan babyn tana murmushi! Zainab simi simi ta kama hanyar fita! Najaatu ta bita da kallo cike da takaici Karo suka ci dashi yazo zai shigo yace.""" "Kina ciki dama."" Tace""Eh Aunty Halisan ta shiga toilet. "" Nazarinta yay na minti biyu kafin yace.""okey kije" "gurinki ganin nan zuwa."" Zainab ta wuce shi shi kuma ya shiga dakin Halisan.........." *MADADI!* *91*******Najaatu kasa tayi da kanta lokacin daya shigo d'akin kallon fuskarsa bata kaunar tayi saboda "abinda yayi musu dazu ita da Halisa a ganinta duk wani rashin son zaman lafiya daga gurin Zainab yake fitowa kuma yasan gaskiya amma yake takewa yake goyan bayan Zainab din a duk lokacin da zata kawo masa magana baya tsayawa yayi binkice a kai zai hau ya zauna ya yanke hukuncin da bai dace ba, tabbas Zainab zata iya raba zumuncin dake tsakaninsa da 'yar uwarsa tunda bata da hakuri! ta tabbata" Yaya Ramlatu ba itace bata kauna ba halinta ne bata so yanzu ina laifin wanda ya nuna yana kaunar d'anka a gaban mutane ta kunyata ta nuna ba zata bata 'yarta ba a gaskiya al'amarin yayi mata ciwo sosai tana rokon Allah ya bata nata itama. "Muryar Ramlatu taji tana fad'in ""Au! ashe wuta tazo ta kunna maka a gida anya kuwa Abbas wannan" "yarinyar baso take ta had'aka da kowa ba, ina tunanin ma zumuncin dake tsakanina da kai zata raba tunda har ta iya zuwa ta kawo maka 'karata kai kuma kazo ka tsaya a kaina kana tuhumata.""" "Sassauta murya yay yace.""Nifa ba hayaniya nace kiyi ba magana muke ta fahimtar juna Zainab tazo tana" "kuka tana fad'in ""Kin tara jamaa kun taru kun ci mutuncinta shine nake so naji dalili amma ni Zainab bata isa ta had'ani da kowa ba.""" "Yaya Ramlatu za tayi magana Najaatu ta katseta da fad'in ""Yaya kiyi shuru dan Allah ba girmanki bane" tunda ita ta raina ki bata ganin kimarki mu muna gani bana so kina sa kanki a cikin sabgar da zata sa girmanki ya zube. "Ramlatu tace""A'a Najaatu ba zanyi shuru ba tilas nayi masa bayani dan saboda ya daina ganin kamar" takurawa matarsa akayi ni da ita daku duk d'aya kuke a gurina abinda yasa na tsaneta mugun halinta kuma har yanzu idan na kalleta sai raina ya baci idan na tuna da marin da tayi min bayan haka tasa dan "uwana ya dauko min 'yan sanda."" Fashewa tayi da kuka tana fyatar majina!" Hankalinsa ne ya tashi shifa baya tayar da maganar bane dan rai ya 'baci yana so su fahimci juna da 'yar "uwarsa dan baya son irin bambamcin da take nunawa a tsakanin matansa amma ba dan ya 'bata mata rai ya tayar da maganar ba, Najaatu ganin Yaya Ramlatu na kuka sai itama ta fara, Halisa ta fito daga toilet ta tarar dasu suna kuka shi kuma sai magana yake musu. Tace""Yanzu ashe Abbah Mufida" "maganar nan bata mutu ba nifa tashin hankalin nan ya tayar min da nakuda wallahi."" Yace.""Halisa" "magana ta mutu tuntuni tambayarta nake akan abinda ya faru shine take kuka sabida rashin fahinta.""" "Halisa ta samu guri ta zauna tare da fad'in ""Yaya dan Allah ki daina kuka Zainab fa karya take ta shiga" "tsakaninki da Dan uwanki kome za tayi kuwa ki daina damuwa.""" "Yaya Ramlatu ta goge hawaye tare da kallonsa tace""Kace kana so kaji abinda yasa matarka kasa zama a" "gidan biki ta dawo gida ko."" Yace.""Eh."" Tace""To Najaatu tayi sha'awar 'yarta sai ta nuna ta bata aro tayi mata kwana biyu kai tsaye tace ba zata bayar ba, haushin haka yasa nayi mata fad'a saboda raina ya 'baci sosai da yanda ta nuna rashin kwaicinta a kan 'yar uwarta amma babu wanda ya zage ta ko yaci" "mutuncin iyayenta duk wata magana da tazo ta fad'a maka karya take.""" Shuru yay yana nazarin maganar. Abinda yasa yay saurin yarda da maganar Zainab din sabida yasan "akwai rashin jituwa a tsakaninsu sannan Halisa da Najaatu sun nuna masa kansu a had'e yake ma'ana sun cire Zainab daga cikin su shiyasa ya yarda da cewar za'a iya had'a baki dasu aci mutuncinta tunda kishiyarsu, sai kuma yanzu da yaji farkon al'amarin ya fahimci furucin Zainab din ya janyo duk hatsaniyar shima yaji rashin dad'in abinda tayi ina laifin wanda ya nuna yana son naka, a zamansa da Zainab ya fahimci halinta na rashin iya magana da rashin kawaici da hakuri mutukar akan hakkinta ne bata iya yin shuru shiyasa yake tsoron wani abu na sa'bani ya shiga tsakaninsa da ita sabida hanashi bacci take da daddare, ya lura su kuma su Halisan suna ganin kamar tsoro ne yasa yake biyewa Zainab din da duk abinda tazo masa dashi wanda kwata kwata ba haka bane a gurinsa kawai yana jin tsoron rashin hakurin ta da mitar ta dan kwata kwata abu naya wucewa a gurinta ta dinga nanata magana kenan Ya jima a tsaye a dakin yana nazarin al'amarin kafin ya sauke ajiyar zuciya ya kalli Halisa" "dake kokarin sawa babynta nono yace.""Ina fata babu wata matsala ko.""? Tace""Babu matsala."" Yace.""To sai kiyi kokari kici abinci kamar yanda Dr Saadatu ta fad'a miki kisha magani kafin ki kwanta."" Tace.""Insha Allahu."" Sallama yayi musu ya juya da niyyar fita daga dakin 'Yar uwarsa ce kawai tayi masa magana" Halisa da Najaatu shuru sukayi suka bishi da kallo har ya fice daga dakin. Bayan ya dawo daga sallar asubahi ya sameta ta idar da sallah zama yay gefan gado had'e da kiran "sunanta"" Zainab'' amsawa tayi tare da juyowa tana kallonsa, yace."" zo nan."" Jiki a sanyaye ta miqe taje ta zauna kusa dashi."" kallonta yayi a nutse yace.""Jiya Yaya Ramlatu dik ta sheda min abinda ya faru a tsakaninku wanda har yanjo ta kasa hakuri tayi miki fad'a kan abinda kikayi wanda ke kika daukeshi da wata manufa, banji dadin abinda kikayiwa Najaatu ba ina laifin wanda ya nuna yana son naka."" Shuru" "tayi tana zumbura bakinta ita yama za'ayi ta dauki 'yarta ta bawa ma'kiyarta ai ba zai yiwu ba.""" "Yace.""Koda ba zaki bata ba ai bai kamata ki fito ki fad'a mata gaban jamaa ba kin nuna mata iyakarta" akan abinda take da iko dashi koda bana auranta zan iya bata d'ana ta ri'ke sabida cancantarta to ballanata a matsayin uwa take a gurin Ummi tabbas nasan kamar yanda zata kula da d'an cikinta haka "zata kula da Ummi amma meye na nuna mata iyakarta.""" """Abbah Mufida nifa koda ba ita taba ba zan iya bada d'ana yaje wani guri ya kwana bs kuma ni ban fad'i" "maganar da wata manufa ba dan da nasan zasu dauki zafi to da nayi shuru da bakina yarinya dai 'yata ce sai nayi niyya zan bayar.""" "Cikin 'bacin rai yace.""Kiyi min shuru nace! wato har wani fuffuka kike kina maganar yarinya yarki ce" "bayan kin gama azabtar da ita ashe akwai ranar da zata zo kiyi wannan maganar to ki daina cika baki idan nayi niyya wallahi zan dauke yarinyar daga hannuki na kaita duk inda raina yake so sai naga k'aryar so."" Shuru tayi gabanta na bugawa jin abinda yake fada." "Yace""Anjima ki shiga gurin Halisa Yaya Ramlatun nan ki bata hakuri kan abinda ya faru kinji ko."" Murya" "na rawa tace ""To.""" "Kwanciya yay kan bed din tare da tsirawa rufin dakin ido, Zainab hijabin jikinta ta cire taje ta kwanta" "kusa dashi, itafa tunda taga Najaatu da ciki to itama sai ta samu hankalinta zai kwanta, jikinsa ta shiga tana shashshafa kirjinsa tare da sumbatar fuskarsa, duk da yasan wuya zata bashi hakan be hanashi kar'bar tayin ta ba rungumeta yay a jikinsa yana mayar mata da martanin abinda take masa." "Najaatu da Yaya Ramlatu na zaune suna karyawa suka shigo tare, Tinda tayi musu kallo daya ta dauke" "kanta, Zainab ta nemi guri ta zauna shi kuma ya tsaya suna gaisawa da 'yar uwarsa, Najaatu ba tare ta kallesa ba ta gaisheshi cikin kulawa ya amsa yana tambayarta Halisa tace""Tana bandaki Bakin bed din" "ya zauna yace ""Bani yarinyar."" Babyn dake hannuta ta bashi kamar yanda ya bukata ta juya ta cigaba" dayin break dinta. "Zainab a sanyaye tace""Yaya Ramlatu dan Allah kiyi hakuri akan abinda ya faru jiya."" Yaya Ramlatu" "tace''Haba ai ni bani da ri'ko 'yar nan magana ta wuce a gurina."" Zainab tace""Nagode insha Allah hakan ba zata sake faruwa ba kema Najaatu ki gafarce ni ban san maganata zata 'bata miki rai ba.""" "Najaatu murmushin takaici tayi tace""Babu komai magana ta wuce.""" Abbah yaji dadi sosai ganin yanda Zainab ta dauki nasihar sa dan baiyi tsammanin zata nemi afuwar "Najaatu ba sai gashi tayi masa bazata, sosai yaji dadin abinda tayi Sai da halisa ta fito daga toilet suka" gaisa sannan yay musu sallama ya tafi kasuwa. "Zainab kuwa zama tayi tana ta kokarin wanke kanta ita lallai sai sun manta abinda ya faru, Halisa dai da" Ramlatu suna sata a maganarsu amma Najaatu idan tana magana tasa mata baki shuru takeyi dan bata son abinda zai sake had'asu suyi ta hayaniya sai kace wasu karnuka a ganinta yanzu duk an daina irin wannan kishin jahilcin. Bayan sallar la'asar ya kirata a waya tare da sheda mata cewar yanzu yay magana da Dan Azimi zai zo ya "dauketa ya mayar da ita gida."" Tace.""Da kabari idan kazo sai mu tafi tare."" Yace.""Aa ki dai zauna a shirye Dan Azimi zai zo ya dauke ki shawarar dana yanke kenan."" shuru tayi bacin rai ya hanata cewa komai dan ma kada ta kashe masa waya yaji haushi da tuni ta kashe, tana jinsa yana magana ta dinga umm eh" da ya gaji da abinda take masa sai kawai ya kashe wayarsa ransa a 'bace Najaatu dauke masa wuta tayi lokacin daya shigo gidan ma tuni ta bar falo ta shige daki tayi kwanciyarta "tasan abinda yasa yace ta dawo gida sabida yana so yazo ya haye kanta yay abinda yake so, ita da take biya masa bukatarsa ta kowane fanni itace abar wulakantawa a gurinsa aikuwa zata nuna masa tasan" abinda take sai tayi sati bata amincewa bukatarsa ba in yaso yaje can gurun Zainab din ya 'karata Abbah babu yanda beyi da ita ba akan ta tashi taci abincin daya shigo dashi tace ta koshi alhalin data dawo ba tayi girki ba tunda ta cika cikinta da abincin mejego take jinta a koshe! A kammala cin abincinsa yaje yayi wanka kamar koda yaushe turare ya shafa a jikinsa sannan ya kwanta "kusa da ita. Matsawa tayi can karshen gado tana takure jikinta, ganin abinda tayi yasa ransa ya" 'baci sha'awarsa ya danne ya juya mata baya tare da jan bargo ya rufe kafafunsa. A haka sukayi bacci ita tana gabas shi yana yamma! Ta dauka da safe zai sanja mata fuska sai taga bai nuna mata komai ba yace tayi maza ta shirya da wuri "zai fita, a gurguje tayi wanka ta shirya ko beak fast ba suyi ba suka fita. Can babban gidan nasa suka" nufa tare. A tsaitsaye ya duba maijegon da 'yarta ya nufi gurin Zainab itama suka gaisa kana ya wuce kasuwa. Haka suka dinga yi har akayi suna duk ranar girkinta tare suke fitowa da daddare su tafi tsayin "sati guda babu wata mu'amula da ta shiga tsakaninsu, ya daure ne yana so ya nuna mata cewar bafa lallai sai da jima'i ne zai rayu ba idan dan saboda yana jin dad'i da ita take masa iskanci to taje ta huta. Bangaranta ta dinga mamakin dauriyarsa a yanda tasan shi da rashin hakuri bata ta'ba" "tsammanin zai iya yin sati daya ba ba tare daya kusance ta ba.......Ranar nan tana bacci kawai ta farka taga baya kusa da ita sai ta dauka ko toilet ya shiga kofar toilet din ta tsirawa ido tana jiran fitowarsa, shuru be fito ba, mikewa zaune tayi da sauri sabida jin maganarsa k'asa-'kasa a falo.'' Ta sauko daga bed din ta bude kofa ta fita. Samun sa tayi cikin duhu maqale da waya a kannensa, jin yana kiran sunan" "Saadatu yasa taji gabanta ya fad'i!. ""Inaso in aureki mutukar kina sona kuma zaki iya zama da iyalina" "lafiya."" Abinda kunnuwanta suka jiye mata kenan, ta sake kasa kunne tana sauraransa. ""To nagode" "sosai dama nasan ke nutststsiya ce kina da ilimi daidai gwargwado dalilin daya sanya ma kenan naji ina sha'awar auranki saboda haka insha Allahu cikin satin nan zan turo da sadaki bana so aja dogon lokaci tunda ni dake duka ba yara bane."" Najaatu jin tana neman faduwa a gurin yasa tayi saurin tura kofar dakinta ta shiga, wanda motsinta yasa yay saurin kallon bakin kofar. A nutse ya cigaba da maganar da" yake yi da Dr Saadatu a waya ba tare da ya nuna wata damuwa ba "Sai da ya gama wayarsa tsaf sannan ya koma dakin, samunta yay a zaune yayi saurin d'auke kansa daga" "kanta yaje ya kwanta inda yake kwanciya baya ya juya mata kamar koda yaushe yaja bargo ya rufe jikinsa, Najaatu taji kamar tayi masa magana sai dai ta daure zuciyarta ta kwanta hawaye na zubo mata" lallai dama ashe duk wannan abun soyayya ce a tsakaninsu Amma matar ta bata mamaki wallahi sai da ta gama sanin sirrinsu sannan zata zo ta aure musu miji hummm aikuwa ba ita kadai zata shaqi takaici ba dole ta sanarwa dasu Halisa halin da ake ciki dan ta lura kamar 'boyewa yake sai ranar daurin aure suji labari to yau dai Allah ya tona masa asiri "Washe gari da safe kadaran kadahan suka gaisa da juna har ya zauna yayi break fast a gidan, amma babu" wata mu'amular arziki a tsakaninsu ita dashi dai duk daurewa suke amma suna galabaita kansu "Koda Halisa taji maganar mamaki tayi sosai tace""Amma Dr Sa'adatu ta bani mamaki wallahi wato shiyasa" "ta'ki aure ashe shi take so ta aura to Allah ya sanya alkairi."" Najaat cikin takaici tace""Abinda zaki ce kenan aunty Halisa.""? Tace""To me zance in ba haka ba ni dake da zainab babu wacce ta isa ta hanashi abinda yayi niyya saboda haka sai mu taru muyi hakuri Allah yasa abokiyar arziki ce, itama zainab zan" "sameta nayi mata magana dan na santa da rashin hankali zata iya tada husuma abin yazo ya shafe mu.""" Najaatu dai shuru tayi tana jajanta al'amarin. "To koda Halisa tayi masa maganar kai tsaye yace.""Gaskiya ne maganar da taji zai auri Dr Sa'adatu a" "matsayin matarsa ta hud'u kamar yanda Allah ya hallata masa."" Saboda gudun 'bacin rai yasa tace'' To Allah ya sanya alkairi yasa abokiyar arziki ce."" Cikin jin dadi ya amsa da ameen Zainab kuwa ai" "haukane kawai ba tayi ba dan shi da kansa ya fad'a mata halin da ake ciki ta rasa inda zata tsoma ranta taji dad'i! hankali a tashe ta samu Halisa wai su tattauna maganar, Halisa tace""Kije ki kwantar da hankalinki kawai aure babu fashi! dan haka tayar da hankalinki na banza ne watakila ma ki janyowa kanki bacin rai! idan ta shigo zata zama daidai dake ai ba budurwa bace bazawara ce mu kuwa kinga da budurcinmu duk ya aure mu ai magana ta kare."" Zainab tayi zukud'um fargaba da damuwa duk sun" dameta. "Cikin sati hudu kacal akayi komai aka gama, Halisa da Zainab gida D'aya Najaatu da Dr Sa'adatu a gida" "d'aya, dan kafin zuwan ranar daurin auran ya siyi wani 'katon fili dake jikin gidansa wato gidan Najaatu ya shigar dashi gidan ya sanya ma'aikatansa suka tashi aiki abunka da masu abu a hannu kafin zuwan" "lokacin komai ya kammala, yanda ya zubawa Najaatu kayan daki ita amarya haka ya shirya mata dakinta" ita kadai a ka kawo masa gidan............. Abban ango sai zumudi yake yi matayen nasa suna kallonsa gami da kallon ikon Allah sai kace wanda zai auri budurwa duk ya tayar da hankalinsa. Amarya nayin kwana ukunta na musulnci ya dawo "zagaye kamar yanda ya saba! Zainab taga al'amarin bana zama bane yasa ta dage da gyara jikinta dan shiryawa tayi tsaf taje gurin wata mata me maganin gargajiya ta fada mata dukkanin abinda ke damunta, matar ta had'a mata maganin sanyi masu kyau tayi mata bayanin yanda zatayi amfanin dashi wai ashe rashin ni'ima da kuma bud'ewar da gabanta yay duk sharrin sanyi ne shiyasa bata gamsar da mijinta, sosai zainab taji dadin maganin dan dama itama al'amarin na damunta tasan kuma maigidan nata yana hakuri da lalurata wannan dalilin ya sanya data koma gida ta mayar da hankalinta sosai gurin amfanin da" maganin. Tsakanin Najaatu da Dr Sa'adatu akwai fahimtar juna dan duk masu hankali da nutsuwa ne Dr Sa'adatu duk sanda zata tafi gurin aiki sai ta shiga gurin Najaatu tayi mata sallama itama Najaatun sa'i da lokaci "tana shiga gurinta a cikin ranar ku da bata da aiki su jima suna hira kafin ta koma gurinta, hakika wannan jituwar da suka samu a tsakaninsu ta janyo suka 'kara martaba a idanun maigidan nasu." To alhmdullhi Zainab tana ganin amfanin maganin data kar'bo dan tun kafin ya 'kare kwalliya ta biya kudin sabulu dan duk sanda maigidan nata zai kusance yana samun biyan bukata sosai har ya nemi 'kari kuma itama a nata 'bangaran ta daina jin zafin da take ji tana bashi hadin kai dari bisa dari Abbah na samun kulawa sosai ta bangaran matayensa guda uku ta bangaran Najaatu ne har yanzu yake da matsala dan kusan sati uku kenan rabon daya had'a shimfida da ita gashi kullum cikin jin sha'awarta yake duk da yana samun biyan bukata a gurin matansa amma yana marmarin ni'imanta mai wahalar samu Yau dai girkinta ne yana ganin dole ya hakura ya nemi shiri dan yini yay yana tunaninta da yanayin salon soyayyar da take masa idan suna tare. Tunda ya shiga gurin nata yake ta janta da magana sai wani lalla'bata yake duk inda ta gifta idonsa a kanta tun bata gane komai ba har ta fahimci cewar ya sakko yana neman shiri wato ya gama zagaye zagayen nasa ya dawo dama ai tayi rantsuwar akan ba zata nemeshi ba tunda tasan tana da amfani a gurinsa dole ya kawo kansa Mikewa yay ya nufi bedroom tare da cewa tazo ta matsa masa jikinsa ya "gaji, tasan fad'a yay amma ba abinda yake nufi ba kenan Tana sane gurin matsar ta dinga tatta'ba" masa inda tasan hankalinsa zai tashi! aikuwa ba'aje ko'ina ba ya janyota rungumeta yay 'kam! ya shiga marmatsa mata jikinta jikinsa in banda rawa babu abinda yake. kirjinsa ta tura ya fad'i a bed din ta "haye kansa tare da kokarin cire kayan baccin dake jikinta, gabadaya ficewa yay daga hayyancinsa ya dinga sakar mata zafafan kesses tare da murza breast d'inta da mazaunanta, a daran soyayya sukayi irin" wacce suka dade basu irinta ba *BAYAN WATA BIYAR* "Lokacin cikin Najaatu yayi wata tara haihuwa ko yau ko gobe, girman cikin ya sanya babu abinda take" "iyawa sai dai komai Dr Sa'adatu tayi mata tun cikin na da wata bakwai Dr Sa'adatu ta dauki dawainiyar yi mata girki tsaf ta shirya mata daining kuma miji ya kwana da ita, Dr Sa'adatu nada mutunci da kyawun hali ta dauki ragamar kula da Najaatu hannu bibbiyu abunda take yi akan Najaatun yasa ta kara martaba da daraja a idon mijinta ya dinga alfaharin auranta dan ganin yanda take bada gudumawa a rayuwarsa data iyalinsa kwata kwata bata d nuna kishi ko ganin kyashi a kan abinda take Wannan karon ma Najaatu a gida ta haihu tare da taimakon Dr Sa'adatu Allah ya sauketa" "lafiya inda ta haifi 'yan tagwaye duk maza lafiyayyu dasu, sai dai bayan haihuwarsu mahaifa tayi gaddamar fitowa kamar dai lokacin haihuwar Daddy Dr Sa'adatu ta dinga fama tana dabaru irin nasu al'amarin yaci tura dan Najaatun tuni ta durkushe a gurin kanta yana juyawa! Da sauri tacewa mijin nasu ya fito da mota suje asibiti itama al'amarin yafi karfinta Abbah bai ta'ba sanin haka mata suke shan wuya gurin haihuwa ba sai akan Najaatu tsabar tausayi sai da ya zubar mata da hawaye, ga dai 'ya'yansa tsaf yana ganinsu da rai da lafiya amma Najaatunsa na halin rai da rayuwa. Tare da ita dashi suka sata" a mota Dr Sa'adatu ta goya d'aya ta rungume daya a kirjinta ta shiga motar yaja suka tafi asibitin nasarawa inda take aik. Ko kafin su isa ya kira Halisa a waya ya sheda mata tare da bata umarnin ta "biyo bayansu asibitin domin ta taimakawa Dr din da wani abu, Halisa bata tafi ba sai da ta sanar da zainab Halin da ake ciki Zainab jikinta yay sanyi ta nemi guri ta zauna gabanta na fad'uwa hankalinta ya kwanta ta samu ciki zuwan wannan ranar itace garari gadai Najaatu ta haihu amma rayuwarta na cikin" k'ila wa'kala! Jiki a sanyaye ta shirya ta nufi asibitin itama. Najaatu ta galabaita mutuka kafin mahaifar twins d'in ta fito ko bayan ta fito ma jini ne ya tsinke mata "hankalin narses din yay masifar tashi, itakam Dr Saadatu duk kwarewar ta akan aikinta kasa katabus tayi tsabar fargaba da tashin hankali! (Ubangiji Allah kasa muga da ita lafiya had'arin haihuwa nada yawa)" "Da kyar aka samu nasarar tsayar da jinin dake fita, aikuwa ba'aja da nisa ba aka sa mata wani gudun" "abunda ka iya zuwa ya dawo...........Sai bayan hankali ya kwanta ne ya samu damar kiran wayar 'Yar uwarsa Ramlatu ya fad'a mata haihuwar yace ta fad'awa su Hajia suna asibiti, Yaya ramlatu ta tambayeshi lafiyar maijego da yaran yace suna nan lafiya lau be fada mata abinda ya faru da Najaatun ba....." Naja'atu sai data kwana uku a kwance a asibiti sannan ta dawo daidai ta fahimci abinda ta haifa da kuma "jamaar dake zuwa dubata! Alhaji da Baba Malam zuwansu biyu asibitin dubata, Baba Talatu kuwa tunda tazo sau daya bata sake zuwa ba tana ganin kamar zuwan nata bashi da amfani tunda ba itake bada lafiya ba bayan haka kuma Mutanan na iya bakin kokarin su akan Yarinyar shiyasa ta zauna a gida ta cigaba dayin addua akan 'yar tata. Aunty Maryam kuwa kullum da ita ake yini a asibitin sai yamma tayi take tafiya. Koda suka koma gida ma haka 'yan uwa da abokanan arziki suka dinga zuwa dubata tare" da ganin yaran har bayan kwana bakwai 'kafa bata dauke a gidan ba. Abbah kudi ya fitar masu yawa yayi hidimar haihuwa dasu maijego da 'ya'yanta yay musu hidima sosai "hakanan suma sauran matansa da 'ya'yansa yayi musu daidai gwargwado ranar da suka ware domin suna kowa ya fito gwanin ban sha'awa, haihuwar Hassan da Husaini tayi albarka sosai dan gidan ma'kil yayi da jamaa ta kowanne fanni kowa yazo nuna farin cikinsa, Zainab ta sauko ta mayar da komai ba komai ba har 'yan uwanta sai da suka zo bikin sunan, Itama Halisa nata 'yan uwan sunzo kamar yanda itama Dr ta gayyato nata dangin dukkaninsu har yaran suka had'u a falon Dr Sa'adatu suka sashi a tsakiya suna ta daukar hotunan tarihi! Abbah Abbas sai murmushi yake duk ya rasa inda zai saka kansa sabida farin ciki duk inda ya waiga sai yaga iyalinsa cikin walwala da farin ciki sai kawai ya shige godewa Allah a bisa ni'imar da yayi masa burinsa ya cika ya had'a mata hud'u gashi sun fara tara masa zuria abinda yake mutukar so a rayuwarsa yanzu 'ya'yansa bakwai bayan d'an da Halisa ta haifa babu rai yana" rokon Allah ya cigaba da azurta shi da 'ya'ya masu albarka. Najaatu watanta uku da haihuwa yaranta sunyi kwari ta nemi alfarmar akan ya barta taje jos su gurin su "Mmm Sajida, hanata yayi yace ba zata je yanzu ba sai yaran sun sake 'kwari hakura tayi ta kyaleshi ta cigaba da kula da 'ya'yanta dama tuntuni Daddy ya zama d'an gidan hajia ya jima a can dan har ya" manta da cewa itace uwarsa Yaya Ramlatu ya ri'ke a matsayin uwa tunda da ita ya saba. Lokacin da sukayi wata shida ta sake masa maganar zuwa jos nan ma ya dinga yi mata wasa da hankali "ya'ki yayi mata magana d'aya, takaici yasa tasa shi a gaba tana kuka tana fad'a masa cewar bai dace ace ta watsar da mutanan ba koda be barta ta kwana ba to ya bari taje ta dawo a rana daya, da kyar ya barta tare da kafa mata dokoki tace to ta amince, Tare da Yaya Ramlatu suka tafi saboda ta taimaka mata da raino, a waya ta kira Mmn Sajida ta fada mata cewar gata nan akan hanya amma ba kwana za tayi ba, Mmn Sajida da sauri ta shiga gidan Mmn Ladi ta sheda mata a take suke shiga hidimar abinda zasu sauketa dashi...............Najaatu tayi mamakin yanda Mmn Sajida da Mmn Ladi suka karramata sun jere gabanta da kayan abinci nau'i nau'i sai farin cikin ganinta suke suna ta nuna farin cikinsu akan kyautar da Allah yay mata Mmn Sajida ta dauki Hassan ta rike tana ta sa masa albarka itama Mmn Ladi ta dauki Hussain sai addua take masa Najaatu hawaye ta shiga sharewa tana mamakin irin kaunar da mutanan ke" mata. Wannan karon ma manya manyan atampopi ta kawo musu da mayafai masu kyau da tsada "kana ta basu kudi masu yawa tace su cigaba da juyawa akan wanda suke, rasa bakin godiya sukayi" dukkinsu sai da suka zubar da hawayen farin ciki Sai da zata tafi Mmn Sajida ke fad'a mata cewar itama ta kusa aure dan har ta kar'bi sadakin wanda zata aura. Najaatu ta dinga farin ciki tana mata "fatan alkairi da zaman lafiya da mijinta, Cikin alhini na rashin son rabuwa sukayi sallama da junansu kowanne zuciyarsa babu dadi." Yaya Ramlatu ta jima tana mamakin mutunci da karamcin su Mmn Sajidan inda ita kuma Najaatun ke "fa'da mata irin taimakon da sukayi mata a lokotan baya lokacin da take bukatar taimako. Yaya Ramlatu tace ""Eh lallai kuwa mutanan nan ba mutanan da za'a yar bane yana da kyau ki cigaba da zumunci dasu duk nisan inda suke.""" "Ayuba Abbah Abbas ya samu a kasuwa da maganar son mayar da matarsa dakinta, Abbah yayi farin ciki" "da jin wannan maganar dama zaman 'yar uwar tasu a haka yana damunsu dan haka ba tare da wata shawara ba yace kawai ya tsayar da ranar daurin aure kada ya damu zai samu mahaifinsa da maganar itama kuma Yar uwar tasa zai fada mata.....Ayuba ya tsayar da ranar daurin aure sati daya mai zuwa, Abbah yace to Allah ya nuna mana ya sanya alkairi To koda ya samu iyayensa da maganar sai suka" nuna farin cikinsu akan al'amarin sannan sukayi fatan alkairi gami da adduar zaman lafiya. Bangaran "Yaya Ramlatu kuwa ai babu wanda ya kaita jin dadi da farin ciki hakika ta d'and'ana zaman gida taji yanda zawarawa keji duk da babu abinda ta nema ta rasa a gidan ubanta amma ta tabbata dakin mjinta yafi mata daraja da mutunci ba tare da bata lokaci ba ta amince aka daura aure ta tare a dakinta wanda Abbah Abbas ya sauya mata komai na ciki tamkar d'akin 'yar gatan budurwa Yaya Ramlatu d'an uwanta ya fito da ita sosai yasa mata komai na kyale kyale a dakinta, satin ta biyu da tarewa tazo da kanta ta had'a kayan Daddy tsaf ta daukeshi ta tafi dashi can gidanta, tace ai mai rabata dashi sai mutuwa shima" yaron sati biyu da yay babu ita har ciwo sai da ya kwanta. **** Wannan karon ma Zainab mace ta haifa yarinyar taci sunan Yaya Halimatu marigayiya Najaatu tayi "murna da farin ciki ganin yasa sunan yayarta sai ta dauki son duniya ta dorawa yarinyar kome ta gani na yara ta siya mata Zainab tayi ta jin dadi, shima Abbahn sunan da yarinyar taci yasa yake kaunarta kullum" adduarsa Allah yasa ta gaji me sunanta Halimatussadiya. Alhaji Aminu Dan jarida da Matarsa suka shirya tsaf domun zuwa suga abinda d'ansu ya tafi ya bari a "duniya, Munira ce ta jagoranci tafiyar......" Tar'ba ta mussaman akayi musu Alhaji yasa aka shirya musu abinci mai kyau aka saukesu dashi sannan yasa Dan Azimi yaje gidan Ramlatu ya dauko musu yaron Abbah Abbas na kasuwa ya samu labarin "zuwansu abinda yake ya bari yazo ya same su, Alhaji Aminu ya rungume yaron sai zubar da hawaye yake Baba Malam da Alhaji na bashi baki gami da nuna masa yanda yanayin rayuwa yake Ubangiji na iya zartar da hukuncisa akan ko wane bawan sa ba dan baya kaunarsa ba sabida haka ya daina kuka da damuwa insha Allah yaron ba zaiyi maraici ba tunda yana da uba wato mijin mahaifiyarsa wanda ya daukeshi tamkar shi ya haifeshi Abbah jin akan maganar da suke yasa shima ya shiga jajjada masa" cewar shine a matsayin mahaifin yaron a yanzu dan haka baya so koda ya girma su tayar masa da wata magana wacce zata d'aga hankalinsa abinda ya wuce ya riga ya wuce har abada. Jin wannan magana yasa Alhaji Aminu yaji ya sassauci a cikin zuciyarsa Kwanansu biyu a gidan Alhaji suka shirya tafiya Munira har gida ta samu Najaatu ta sheda mata cewar Muktar ya dawo gurinta sun sasanta junansu har sun tsayar da maganar aure a tsakaninsu. Najaatu ta nuna farin cikinta a fili tayi kuma adduar fatan alkairi Wannan karon ma sai da tayi wa Munira kyautar "sutturu da kudi dubu ashirin tace kuma idan auran yazo ta fada mata koda a waya ne."" Munira sai da ta zubar da hawayen farin ciki." *BAYAN SHEKARA GOMA* A cikin wannan shekarun da suka gabata abubuwa daya sun faru masu dadi da marasa dadi dama haka rayuwa take a cikin shekaru goma da suka wuce Allah ya dauki rayuwar mutumin kwarai nagartaccan mutum wato Alhaji Sama'ila wanda yayi mutuwar shahada watan azimi kuma ranar jumaa ga shedar arziki daya samu daga gurin Jamaar gari A dai cikin shekarun ne Allah ya daukaka darajar Alhaji Abbas inda ya shiga sahun matane masu kudi a jahar kano idan aka kira *Dangwate* a farko aka kira *BUA* a na biyu to za'a kira sunansa a na uku Alhaji Abbas Allah ya bashi duniya sosai "kuma yana neman lahirar sa a cikinta dan dukiyarsa ta talakawa ce gami da marayu da nakasassu da duk wani mabukaci, gidansa kullum baya rabo da jamaa kullum cikin raba kudi da abinci akeyi, massalatai da makarantu kam shi kansa bai san iya adadin wanda ya gina ba kullum cikin hidimtawa addinin Allah yake. 'Bangaran iyali sai godiyar Allah Uwar gida Halisa nada biyu duk mata Zainab nada shida mata" "hudu maza biyu Najaatu nada Bakwai duk maza har yanzu bata haifi mace ba, Dr Sa'adu ce har yanzu" bata haihuwa Allah sarki ashe rashin haihuwa ne yasa tsohon mijinta ya rabu da ita shi kuwa Abbah ya ri'keta tsakani da Allah rashin haihuwata besa yaji ya gaji da zama da ita ba saboda yasan Allah ne ke bada haihuwa ba wani mahalu'ki ba......... A yanzu zuriar sa su goma sha bakwai ne kuma yana rokon Allah ya 'kara masa wasu kafin ya dauki rayuwarsa ....... *To nima ina rokon Allah ya k'ara masa ya kuma had'a masa kansu tare da fatan ya cigaba da zaman lafiya da iyalinsa* *ALHAMDULILLAHI* _To Jamaa nan na kawo 'karshen wannan littafi mai suna MADADI BA HARAM BANE ina rokon Allah ya yafe min kusakuraina Ladan da yake ciki kuma Allah ya sadamu dashi bakid'aya. Ina mik'a godiya gare "ku dubbanin masoyana na nesa dana kusa wanda na sani da wanda ban sani ba, Nagode sosai da kaunar da kuke nuna min Especially masu fitar da kudinsu su siya book d'ina wallahi ina alfahari daku mutuka ina fatan Allah ya cigaba da bani ikon nishad'antar daku gami da faranta muku Nagode sosai 'yan uwana" 'kawayena iyayena 'kannena Yayyayena dukkaninku ina muku fatan alkairi Assalamu alaikum_